Katsina Post

Katsina Post This is where you will learn about all the latest developments in Katsina State and beyond.
(3)

Yan Wasan Uku Yan Asalin Jihar Katsina Sun Kulla Yarjejeniya Da Wata Kungiyar Kwallon Kafa a Kasar Belarus‘Yan wasa uku ...
14/09/2026

Yan Wasan Uku Yan Asalin Jihar Katsina Sun Kulla Yarjejeniya Da Wata Kungiyar Kwallon Kafa a Kasar Belarus

‘Yan wasa uku daga Katsina Football Academy sun ɗauki wani sabon mataki a rayuwarsu ta ƙwallon ƙafa, bayan samun nasarar sanya hannu kan kwangilar ƙwallon ƙafa ta ƙwararru da ƙungiyar Prolex FC ta ƙasar Belarus.

‘Yan wasan su ne Isma’il Nuhu (Sare), Alhassan Muhammad Sheriff da Aliyu Abdullahi, waɗanda s**a samu wannan dama ne sakamakon ƙwazon da s**a nuna da kuma ci gaban da s**a samu a lokacin da suke gudanar da gwaji da horaswa a Belarus.

An Ƙaddamar da Shirin Ba da Tallafin Kuɗi na Conditional Cash Transfer Karo na 6 ga Mutane 3,000 a Ƙaramar Hukumar Kaita...
14/09/2026

An Ƙaddamar da Shirin Ba da Tallafin Kuɗi na Conditional Cash Transfer Karo na 6 ga Mutane 3,000 a Ƙaramar Hukumar Kaita

An ƙaddamar da shirin ba da tallafin kuɗi na Conditional Cash Transfer karo na shida ga mutane 3,000 a Ƙaramar Hukumar Kaita ta Jihar Katsina.

Da yake jawabi yayin ƙaddamar da shirin, Shugaban Shirin na Ƙaramar Hukumar Kaita, Alhaji Bishir Sa’idu, ya fara da gode wa Allah, sannan ya bayyana cewa al’ummar ƙaramar hukumar Kaita suna amfana da shirin.

Ya ce shirin ba shi da alaƙa da wata jam’iyya ta siyasa, yana mai cewa mutane 3,000 da aka fara ba wa tallafin ba su ne kaɗai za su amfana ba, domin akwai wasu waɗanda za su amfana nan gaba.

Shi kuwa Shugaban Biyan Kuɗi, Usman Sha’aibu, ya yi bayani kan yadda waɗanda s**a cancanta za su karɓi katinsu da kuɗinsu. Ya shawarci masu cin gajiyar shirin da su bi layi tare da tabbatar da cewa sun zo da lambar BVN. Haka kuma, ya yi kira ga waɗanda za su amfana da shirin da su ba da cikakken haɗin kai domin gudanar da aikin cikin sauƙi.

A nasa jawabin, Shugaban Shirin na Jihar Katsina, Alhaji Aminu Alhassan Faskari, ya ce sun zo ne domin ƙaddamar da ba da wannan tallafi da ake bayarwa lokaci-lokaci, bisa haɗin gwiwar Gwamnatin Jiha da Gwamnatin Tarayya.

Ya bayyana cewa ana gudanar da shirin ne domin taimaka wa mutane masu rauni da mabukata, tare da rage musu wahalhalun rayuwa.

Alhaji Aminu Alhassan Faskari ya ƙara jaddada cewa ba dole sai mutum ɗan jam’iyyar APC ba ne zai amfana da shirin, domin tallafin na kowa ne.

Ya ce, “Haƙƙin kowane ɗan ƙasa ne,” sannan ya ƙara da cewa nan ba da daɗewa ba mutane da dama za su amfana da shirin.

Ya kuma bayyana cewa tsarin ana yin sa ne domin samar da sauƙi da rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta. Ya ce sama da mutane 60,000 ne za su amfana da wannan tallafi a faɗin Jihar Katsina baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa tallafin zai kai kusan kashi uku, inda wasu daga cikin waɗanda s**a cancanta za su karɓi tallafin kashi biyu, yayin da wasu kuma za su karɓi kashi uku, bisa tsarin da aka tanada.

Haka kuma, ya bayyana cewa an samar da tsarin da zai bai wa waɗanda s**a cancanta damar karɓar kuɗaɗensu cikin aminci da sauƙi.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kaita, Hon. Bello Yanɗaki, wanda Mataimakinsa, Alhaji Jamilu Sani Dankama, ya wakilta, ya fara da gode wa Allah SWT, sannan ya miƙa godiyarsa ga Shugaban Ƙasa bisa samar da wannan shiri na tallafa wa al’umma.

Ya kuma bayyana cewa, in Allah ya so, al’ummar Ƙaramar Hukumar Kaita za su ba da cikakken haɗin kai domin ganin an samu nasarar shirin.

Wasu daga cikin wakilan waɗanda s**a amfana da shirin yayin ƙaddamarwar sun haɗa da Hauwa Isiyaka, Amina Nura, da Hafizu Sulaiman.

Tasi’u Abubakar ne ya gabatar da jawabin godiya a madadin waɗanda s**a amfana da shirin.

’Yan Sanda Sun Kwato Dabbobi 50 Daga Masu Satar Shanu A JibiaKarin bayani a comment👇
14/09/2026

’Yan Sanda Sun Kwato Dabbobi 50 Daga Masu Satar Shanu A Jibia

Karin bayani a comment👇

DAGA FARKAWAR MATASA, CANJIN ƘASA ZAI FARADaga lokacin da matasanmu s**a gane su waye, s**a fahimci ƙarfinsu, haƙƙoƙinsu...
14/09/2026

DAGA FARKAWAR MATASA, CANJIN ƘASA ZAI FARA

Daga lokacin da matasanmu s**a gane su waye, s**a fahimci ƙarfinsu, haƙƙoƙinsu da kuma irin rawar da ya kamata su taka wajen gina ƙasa, daga wannan lokacin ne za a fara samun sauyi mai ma’ana a ƙasar nan.

Ya kamata mu fahimci cewa idan Allah Ya nufi taimakon wata al’umma, sau da yawa sauyin yana farawa ne daga canjin tunanin matasanta. Duk al’ummar da ta rasa nagartattun matasa masu hangen nesa, kishin ƙasa da kyawawan ɗabi’u, zai yi mata wahala ta samu ci gaba mai ɗorewa.

Mu matasa ne kashin bayan kowace al’umma. Saboda haka, duk wanda yake son rusa wata al’umma, zai fara ne da lalata matasanta, domin su ne ginshikin da al’umma ta dogara da shi wajen gina makomarta.

Saboda haka, ya kamata mu matasa mu fahimci cewa ba shugabanci kaɗai ne nauyin da ke kanmu ba. Muna da babban nauyi wajen gina al’umma, inganta rayuwar jama’a da kuma kare makomar ƙasarmu.

Mu sani cewa mu ne goben al’umma, kuma mu ne goben Najeriya. Saboda haka, makomar ƙasar nan tana hannunmu.

Daga: Khames Bn Sabit Kakumi

Cikin Hotuna:Na Yadda Kungiyar Lado Connect Ta Rarrraba Ruwa Da Kayayyaki Ga Zagayen Maulidi a Katsina.Shugaban Kungiyar...
14/09/2026

Cikin Hotuna:

Na Yadda Kungiyar Lado Connect Ta Rarrraba Ruwa Da Kayayyaki Ga Zagayen Maulidi a Katsina.

Shugaban Kungiyar Hon. Hassan Umar Saulawa na mika sakon godiyarsa ga mambobinsa sama da 300 da s**a taimaka wajen tabbatar da shirin tare da yin bangajiya ga daukacin al’ummar da s**a halarci taron Maulidin.

Haka kuma sakataren Kungiyar Hon. Khalifah Aliyu Sani ya bayyana aniyar Sanata Yakubu Lado wajen ganin ya inganta rayuwar al’ummar jihar Katsina baki daya.

Engr. Abubakar Matazu Ya Ƙudiri Niyyar Kai Ayyukan Ci Gaban Gwamnati Zuwa Kowane lungu da sako a KatsinaGM Engr. Matawal...
14/09/2026

Engr. Abubakar Matazu Ya Ƙudiri Niyyar Kai Ayyukan Ci Gaban Gwamnati Zuwa Kowane lungu da sako a Katsina

GM Engr. Matawale Matazu Abubakar Matazu ya bayyana aniyar ƙara mayar da hankali kan wayar da kan al’ummar karkara da kuma haɗa su da bayanai kan ayyukan ci gaba da ake gudanarwa a Jihar Katsina.

A matsayinsa na jagoran Independent Campaign Council (ICC) a Katsina, Engr. Matazu na ƙoƙarin inganta hulɗa tsakanin al’ummomi da hukumomin gwamnati ta hanyar kai bayanai kan manufofi, shirye-shirye da ayyukan ci gaba zuwa ƙananan hukumomi, mazaɓu, ƙauyuka da wuraren da ke da wahalar isa.

Ƙoƙarin ya fi karkata kan ayyukan da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar al’umma, musamman samar da wutar lantarki a karkara, hasken rana, samar da transformers da sauran abubuwan more rayuwa. ICC ta ce irin waɗannan ayyuka na da muhimmiyar rawa wajen inganta tsaro, harkokin kasuwanci, karatu da walwalar al’umma.

Har ila yau, ICC ƙarƙashin jagorancin Engr. Matazu na da burin wayar da kan jama’a kan tallafin hasken rana ga makarantun Tsangaya, wanda ƙungiyar ta ce zai taimaka wajen samar da ingantaccen yanayin karatu ga ɗalibai a wuraren da ke fuskantar ƙarancin wutar lantarki.

Engr. Matazu ya kuma bayyana muhimmancin yin aiki tare da shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, malaman addini, matasa, mata, masu buƙata ta musamman da sauran masu ruwa da tsaki wajen inganta fahimtar jama’a da ƙarfafa shiga cikin harkokin ci gaban jihar.

ICC ta ce tana mutunta jagoranci da hangen nesan Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, tare da ƙudirin bayyana wa jama’a manufofi da ayyukan ci gaba na gwamnati cikin hanyar da za ta taimaka musu fahimtar tasirin waɗannan ayyuka a rayuwarsu.

A cewar ƙungiyar, burin Engr. Matazu shi ne ganin cewa bayanan ci gaba ba su tsaya a birane da ofisoshin gwamnati ba, sai sun isa ga al’ummomin da ake nufi da ayyukan, domin su fahimce su, su tattauna kansu kuma su bayar da ra’ayinsu.

Matawalle Ya Ƙara Haɗa Kan Jiga-jigan Siyasar Zamfara Domin Tallafa wa Tinubu a 2027Ministan Ƙarƙashin Ma’aikatar Tsaro,...
14/09/2026

Matawalle Ya Ƙara Haɗa Kan Jiga-jigan Siyasar Zamfara Domin Tallafa wa Tinubu a 2027

Ministan Ƙarƙashin Ma’aikatar Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya buƙaci tsofaffin ’yan majalisar dokokin Jihar Zamfara, tsofaffin kwamishinoni da sauran jiga-jigan siyasar da s**a yi aiki a ƙarƙashin gwamnatinsa, da su ƙara himma wajen ganin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu nasarar komawa kan mulki a zaɓen 2027.

Matawalle ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki na siyasa da s**a yi aiki tare da shi a lokacin da yake gwamnan Zamfara tsakanin 2019 zuwa 2023. Taron ya mayar da hankali kan batutuwan da s**a shafi tsaro, haɗin kan ’yan siyasa da hanyoyin bunƙasa jihar.

A yayin taron, Matawalle ya jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne babban nauyin gwamnati, tare da bayyana cewa gwamnatin Shugaba Tinubu na ƙara ƙoƙari wajen tunkarar matsalar ’yan bindiga da sauran ƙalubalen tsaro.

Ministan ya kuma yi kira ga shugabannin siyasar da su ƙara wayar da kan jama’a tare da tallata Tinubu Again Movement domin samun ƙarin goyon baya ga Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

Ya buƙaci mahalarta taron da su kai saƙon goyon bayan Tinubu zuwa garuruwa da ƙauyuka daban-daban na Jihar Zamfara da sauran wuraren da suke da alaƙa da jihar, domin ƙarfafa haɗin kai da goyon bayan siyasa.

A nasu ɓangaren, shugabannin ƙungiyoyi da sauran masu ruwa da tsaki da s**a halarci taron sun yaba da yadda Matawalle ya ci gaba da riƙe da tasirinsa na siyasa tun bayan kammala wa’adinsa na gwamna, tare da bayyana aniyarsu ta ci gaba da tallafa wa Shugaba Tinubu.

Sun kuma bayyana cewa za su ci gaba da yaɗa manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu, tare da yin kira ga magoya bayansu da sauran al’umma da su ba gwamnatin goyon baya domin samun ci gaba da inganta rayuwar jama’a.

Shugaban Kamfanin Jaridar Katsina Reporters Nura Siniya Zai Angwance da Amaryarsa Aisha AbubakarShugaban Kamfanin Jarida...
14/09/2026

Shugaban Kamfanin Jaridar Katsina Reporters Nura Siniya Zai Angwance da Amaryarsa Aisha Abubakar

Shugaban Kamfanin Jaridar “Katsina Reporters” Malam Nura Siniya Katsina, zai angwance da amaryarsa Aisha Abubakar a ranar 25 ga watan September, 2026.

Katsina Reporters ta bayyana farin cikinta game da wannan al’amari, tana taya shugaban ta da amaryarsa murna tare da fatan Allah ya basu zaman lafiya da zuriya ɗayyiba.

Za a ɗaura auren da karfe 1:30 a masallacin Bani Commassie GRA a cikin garin Katsina.

AL-AMANAH GROUP OF SCHOOLS — WHERE EXCELLENCE MEETS FAITH!At Al-Amanah Group of Schools, we provide a balanced integrate...
14/09/2026

AL-AMANAH GROUP OF SCHOOLS — WHERE EXCELLENCE MEETS FAITH!

At Al-Amanah Group of Schools, we provide a balanced integrated curriculum combining Western Education, Islamiyyah and Tahfiz—all in one nurturing environment.
📚 Quality Western Education
🕌 Sound Islamic Education
📖 Qur’an Memorisation (Tahfiz)
🗓️ Classes: Monday–Sunday
📖 Intensive Tahfiz: Weekends
💳 Flexible Payment Plans
✅ No Hidden Fees

Give your child the advantage of quality education, strong Islamic values and excellent character.

Al-Amanah Group of Schools is your trusted choice for sound Western and Islamic education.

Al-Amanah Group of Schools — Building Minds, Nurturing Faith, Shaping the Future.

📍 Admissions are ongoing into PRE-NURSERY to Primary 4. Enrol your child today!
📞 Contact us for admission and further enquiries on 07087876469 0R 08149991578

Dole ku tashi tsaye ku yi aiki tuƙuru domin nasarar APC daga sama har ƙasa - Ɗan Arewa ga masu ruwa da tsakin Dutsanma d...
14/09/2026

Dole ku tashi tsaye ku yi aiki tuƙuru domin nasarar APC daga sama har ƙasa - Ɗan Arewa ga masu ruwa da tsakin Dutsanma da Kurfi

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kurfi da Ɗutsinma, Honarabul Aminu Balele Ɗan Arewa, ya buƙaci masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a yankunan biyu da su ƙara ƙaimi wajen ganin jam’iyyar ta samu gagarumar nasara a zaɓen 2027 dake tafe a ƙasar baki ɗaya.

Dan Arewa ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi, 13 ga Satumba, 2026, yayin wani taron ganawa da masu ruwa da tsakin jam’iyyar na ƙananan hukumomin Kurfi da Dutsanma, da aka gudanar domin tattauna shirye-shiryen zaɓen mai zuwa.

Taron ya samu halartar shugabannin ƙananan hukumomi, shugabannin APC na ƙananan hukumomin Kurfi da Ɗutsinma, masu riƙe da mukaman gwamnati a jihar, da sauran jiga-jigan jam’iyyar.

Aminu Balele Dan Arewa ya bayyana cewa, ya shirya taron ne domin gode wa Allah bisa damar da ya ba shi ta sake samun tikitin takarar kujerar majalisar tarayya a karo na biyu, inda tuni INEC ta fitar da sunan sa a shafin ta, da kuma tattauna batutuwa kan zaɓen da ke tafe.

Ya kuma nuna godiyarsa ga masu ruwa da tsaki da sauran waɗanda s**a taimaka wajen tabbatar da nasarar takararsa, tare da yabawa kwamitin rabon taki bisa rabon takin da aka yi wa al’ummar ƙananan hukumomin da ya samar da kansa a watannin baya.

Da yake magana kan zaɓen 2027, Dan Arewa ya buƙaci shugabannin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki da su mayar da hankali wajen ganin APC ta samu ƙuri’u masu yawa a zaɓen shugaban ƙasa, gwamna, sanata mai wakiltar shiyyar Katsina, ɗan majalisar tarayya da ɗan majalisar jiha.

Ya ce burinsa shi ne ganin ƙananan hukumomin Kurfi da Ɗutsinma sun kasance cikin waɗanda s**a fi kowace ƙaramar hukuma yawan ƙuri’un da s**a samar wa jam’iyyar a zaɓen mai zuwa.

A wani sabon tsari da ya gabatar, Dan Arewa ya buƙaci shugabannin kowace mazaba da su sake duba jerin sunayen masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, domin tabbatar da cewa an shigar da dukkan mutanen da s**a cancanci kasancewa cikin tsarin.

Ya ce, idan akwai wasu mambobin jam’iyyar da s**a cancanci shiga cikin masu ruwa da tsaki amma ba a saka su ba, ya kamata a shigar da su domin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyar da samar da nasara a zaɓe.

Ya kuma ba da shawarar cewa, kowace mazaba ta kasance tana da masu ruwa da tsaki da ba su gaza mutum 20 zuwa 30 ba, tare da tabbatar da cewa an haɗa shugaban jam’iyya, sakataren jam’iyya, kansilan da ke da ofis da kuma wanda ba shi da ofis.

A nasu ɓangaren, masu ruwa da tsakin da s**a halarci taron sun tabbatar wa Dan Arewa da za su yi aiki tuƙuru domin ganin APC ta samu nasara a zaɓen 2027.

Sun ce ayyukan da gwamnatin tarayya, gwamnatin Jihar Katsina da kuma ɗan majalisar nasu s**a gudanar a yankunan, sun isa su sa al’umma su sake zaɓar jam’iyyar a karo na biyu.

Address

Block 3 Adjacent Ɗadin Kowa Supermarket Sabon Titin Ƙwado Katsina
Katsina
234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Post:

Shortcuts

Share