Katsina Post

Katsina Post A branch of a registered media outlet - POST MULTIMEDIA ENTERPRISES - with interest in Katsina State
(5)

22/09/2025

Ku ziyarci kasuwar zamani ta Al-Musik Complex & Al-Musik Annex domin yin cinikayya da kasuwanci na haƙiƙa.

Suna nan a Gefen Gadar Ƙofar Ƙaura dake cikin birnin Katsina.

Suna aiki ba dare ba rana tsawon awa 24.

Kwamitin Tuntuba Na Sarkin Adon Danja, Malam Abdul Danja Sun Mika Sabuwar Waya Ga Shugaban Soshiyal MediaKwamitin Mal Ab...
22/09/2025

Kwamitin Tuntuba Na Sarkin Adon Danja, Malam Abdul Danja Sun Mika Sabuwar Waya Ga Shugaban Soshiyal Media

Kwamitin Mal Abdul Danja (Sarkin Adon Danja) sun mika sabuwar tablet waya mai darajar Naira 200,000 ga shugaban kwamitin soshiyal media na gidan Mal Abdul Danja, Idris Masaka Danja.

An bayar da wayar a madadin Mal Abdul Danja domin tallafawa cigaban harkokin soshiyal media da kasuwanci. Idris Masaka Danja, wanda ke gudanar da sana’ar kai tumatir daga Danja zuwa Legas a lokutan tumatir, ne ya amfana da wannan kyauta.

A cewar Kwamitin, wannan tallafin na daga cikin jajircewar Mal Abdul Danja wajen karfafa matasa da kuma bayar da gudummawa ga cigaban kasuwanci da al’umma.

Sun kara da addu’ar Allah ya sanya wannan aiki cikin alheri tare da kawo karin nasara a fagen raya al’umma.

Sarkin Adon Danja Media Team

22/09/2025

Speech delivered by Dr. Dikko Umar Radda during the one-day stakeholders’ engagement on reforming the Almajiri and Islamiyya system of education.

22/09/2025

Kai tsaye: jawabin Sheikh. Prof. Isa Ali Pantami, daga babban dakin taro na (Local Government Service Commission)

During the one-day stakeholders’ engagement on reforming the Almajiri and Islamiyya system of education.

ADC Katsina Mata Sun Gudanar da Shirin "35% Na Mata Ce" a FuntuaFuntua, 15 Satumba 2025Jagorar Mata ta jam’iyyar African...
22/09/2025

ADC Katsina Mata Sun Gudanar da Shirin "35% Na Mata Ce" a Funtua

Funtua, 15 Satumba 2025
Jagorar Mata ta jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Jihar Katsina, Hajiya Lawal Yargata, tare da hadin gwiwar ADC Action Awareness Forum, sun gudanar da taro na musamman mai taken: 35% Na Mata Ce, a Labaran Kaura Event Centre, Funtua.

Taron ya samu halartar wakilai daga dukkan kananan hukumomin Funtua Zone, tare da manyan jiga-jigan jam’iyyar ADC da masu ruwa da tsaki a yankin. Wannan ya nuna irin karbuwa da muhimmancin shirin wajen hada kai da karfafa mata a fagen siyasa.

A cikin jawabin nata, Hajiya Lawal Yargata ta haskaka muhimmancin shigar mata cikin siyasa da shugabanci, tare da jaddada cewa jam’iyyar ADC ta banbanta da sauran jam’iyyu saboda ADC ce jam’iyyar da ta bayar da 35% na guraben shugabanci ga mata, kuma kowace mace tana da cikakkiyar damar tsayawa takara a kowanne matsayi.

Babu wani matsayi da aka haramta wa mata a ADC. Muryar mata dole ta karade siyasa da shugabanci idan ana son a samu ci gaba mai dorewa, in ji ta.

Shugabanni da mahalarta daga kananan hukumomi 11 na Funtua Zone sun yaba da wannan tsari, tare da kira ga sauran mata a Katsina su shiga jam’iyyar ADC domin amfani da damar da aka tanada musamman garesu.

Taron ya kare cikin nasara da addu’o’i, yayin da aka dauki hotuna don tarihi tsakanin mahalarta da shugabannin jam’iyyar.

SIGNED:
Comr. Bello Ashiru Bazanga
Sakataren Ƙungiyar ADC Action Awareness Forum
Katsina State

KUNGIYAR INGANTA KARATUN ISLAMIYYU (K.I.K.I) RESHEN ZONE C TA GUDANAR DA TARON KARAMA JUNA SANI NA WUNI ƊAYA TARE DA NAD...
22/09/2025

KUNGIYAR INGANTA KARATUN ISLAMIYYU (K.I.K.I) RESHEN ZONE C TA GUDANAR DA TARON KARAMA JUNA SANI NA WUNI ƊAYA TARE DA NADA DAYA DAGA CIKIN SHUGANINTA.

Kungiyar Inganta Karatun Islamiyyu na Ahlu Sunnah (K.I.K.I), reshen Zone C, ta shirya taron seminar na wuni ɗaya ga malaman makarantun Islamiyya da ke ƙarƙashin wannan zone mai albarka.

A yayin taron, an samu halartar malamai kusan 270 daga ɓangaren maza da mata, waɗanda s**a fito daga makarantun Islamiyya kusan hamsin.

Da yake gabatar da jawabin sa a wajen taron babban jojin jihar Katsina Mai Shari'a Musa Danladi Abubakar yace makarantu Islamiyya da makarantun boko gurbin su daya a tsarin mulki a dokokin kasa abun da kasar nan ta sa ma hannu a majalisar dinkin duniya ilimi karatu da rubutu ba'a ce na turanci ba ba'ace na Indiyanci ba ko Chanis ba ilimi koyon shi shine.

Ya kara da kira ga malamai da s**a jajircewa wajen koyar da yara abun da ya dace domin kuwa yanzu bazara kara wulakanta malamin islamiyya ba dan ya bugi dalibi a makaranta ba.

Shima da yake gabatar da jawabin sa shugaban kungiyar ta jihar Katsina Malam Sani Yunusa Mani yace malamin islamiyya yana da gata kuma an mashi gata nasan irin kokarin da malaman Islamiyya suke yi babu cikakken lokacin da za'a iya bayanin sa sai dai ince Allah ya saka masu da alkhairi kuma duk malamin islamiyya sai ya daukaka nan gaba ma ko Kansila Za'a zaba zakaga malamin islamiyya ne insha Allahu kuma mutane zasu ga abun alkhairi da za'ayi.

Kazalika an gabatar da kasidu akan yadda malaman zasu kara Inganta harkokin koyo da koyarwa a makarantun su daga cikin waɗanda s**a gabatar da kasidun akwai Malam Aminu Usman Abu Ammar, Imam Safiyyu Alkasim Saulawa

Mutane da dama ne s**a tofa albarkacin bakinsu a yayin taron daga cikin su akwai Malam Aminu Lawal Shugaban Kungiyar Na Zone C, maitaimakama gwamna akan harkokin Izala, wakilin sanata mai wakiltar shiyyar Katsina da dai sauran su.

Daga Bisani, kungiyar ta kuma sanar da naɗin ɗaya daga cikin shugabanninta, Malam Umar Sulaiman, a matsayin Mai Ba wa Commandan Ḥizba ta Katsina Local Government Shawara a Harkar Islamiyyu (S.A Islamiyyu). Wannan naɗi kuwa ya samu ne bisa amincewar DC Malam Kabir Shamsu.

Taron ya gudana a ranar Lahadi 21/09/2025 a dakin taro na Sansanin Horar da Alhazzai na jihar Katsina.

Matawalle ya tabbatar da ingancin tsaro bayan wata fashewa da aka faru a kamfanin DICON na KadunaMinistan kasa a ma'aika...
22/09/2025

Matawalle ya tabbatar da ingancin tsaro bayan wata fashewa da aka faru a kamfanin DICON na Kaduna

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, a ranar Lahadi ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa kamfanin kera makamai na kasa DICON yana nan cikin tsaro da aminci kuma yana aiki yadda ya kamata duk da fashewar da ta faru a masana’antar a Kaduna.

Matawalle, wanda ya kai ziyara wurin a ranar Asabar, ya ce lamarin yana “cikin cikakken iko da tsari tun bayan fashewar,” tare da rokon jama’a da su yi watsi da rahotannin da ke yawo da ba su da tushe bare makama kan abin da ya faru.

Wata sanarwa daga mai taimaka masa a harkokin yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ta bayyana cewa Ministan ya samu bayani daga Darakta Janar na kamfanin DICON, Manjo Janar B.I. Alaya, da kuma Daraktan da ke kula da kere-kere, Air Commodore E. Benson.

A yayin duba wurin, Matawalle ya tabbatar cewa fashewar ta takaita ne a cikin wani dan tsuki da ke dauke makaman da s**a rigaya s**a lalace ko kuma wa'adin aiki da su ya kare da tuni tawagar kwararru ta shawo kan lamarin cikin gaggawa.

“Babu wata ko da tagar window da ta samu matsala a yayin da lamarin ya faru,” in ji Ministan, ya ƙara da cewa gine-ginen masana’antar, ɗakunan ajiya, rijiyar adana dizal da al’ummomin da ke kewaye ba su sami wani lahani ba.

Ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare lafiya da tsaron ma’aikata, tare da shan alwashin cewa abin da ya faru zai haifar da ƙara tsaurara matakan tsaro bisa tsarin ƙa’idodin duniya.

A halin yanzu, an kafa kwamitin bincike don gano musabbabin fashewar.

Bisa Umarnin Gwamna Radda, Ƙungiyar G-Y 34 Local Government ta cika shekaru uku tana rarraba Lemu da ruwa da Litattafan ...
22/09/2025

Bisa Umarnin Gwamna Radda, Ƙungiyar G-Y 34 Local Government ta cika shekaru uku tana rarraba Lemu da ruwa da Litattafan Muslunci da cin cin ga masu Zagayen Maulidi a Katsina

Ƙungiyar G-Y 34 Local Government ta rarraba lemuna da ruwa da cin-cin da kuma Hadisai da ƙawa'idi da Ahalari ga masu zagayen maulidin Annabi Muhammad SAW a cikin birnin Katsina.

A yanzu dai ƙungiyar ta cika shekaru uku da fara wannan aiki na neman lada, inda a bisa Umarnin Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, Ƙungiyar ke rarraba wa ga duk wani zagayen maulidin Annabi Muhammad SAW da ake gudanarwa a cikin birnin Katsina.

Shugaban Ƙungiyar Hon. Naziru Sale Jino shine ya jagoranci rarraba kayayyakin ga masu maulidin da aka gudanar da shi a babban birnin jihar Katsina a yayinda Sakataren Ƙungiyar Hon. Nura Haske ya taimaka masa wajen rarraba kayayyakin.

22/09/2025

Hanyoyin bunƙasa tattalin arziki da Gwamnatin Shugaba Tinubu ke bi wajen samar da gidaje masu rangwamen kuɗi ga al'ummar Najeriya.

PIONEER AFRICA: Empowering Youth, Restoring Hope, and Building a GreenerFuture in Katsina and Beyond.Born out of the vis...
22/09/2025

PIONEER AFRICA:

Empowering Youth, Restoring Hope, and Building a Greener
Future in Katsina and Beyond.

Born out of the vision of Abubakar Sani Yahaya, a Ban Ki-moon Global Citizen Scholar, PIONEER AFRICA is not just another initiative; it’s a movement. A movement to create opportunities where none seem to exist, uplift the hopeless, and empower underserved youth in Africa, starting with Katsina as a model ground.

“Our conscience is simple and clear: to create opportunities for the underserved and empower youth through skills in crafts often overlooked - shoemaking, plastic recycling,and sustainable environmental practices,” says Abubakar.
Since its launch, PIONEER AFRICA has carried out impactful interventions in Katsina State, including; Tree Planting Campaigns to combat desertification and teaching communities the importance of environmental stewardship; Feeding Programs in IDP Camps to reach internally
displaced persons with essential food support to fight malnutrition and Skills Acquisition Training which equipped youth and IDPs with entrepreneurial skills in crafts like shoemaking, leatherworks, graphic designing and recycling.

Each of these initiatives reflects the project’s guiding philosophy: empowerment over dependency, sustainability over quick fixes, and people-centered change over profit.

Looking forward, PIONEER AFRICA is preparing to launch its boldest initiative yet - the De growth Programme - this December, with the aims to: train 5,000 youths in Katsina on sustainable vocational skills; roll out a Plastic Sanitation Drive to tackle waste and promote recycling as well as launch the “Plant a Tree in Your Home” Challenge, a community-wide effort to encourage every household to fight desertification through tree planting.

This ambitious program is designed not only to transform lives locally but also to create a
replicable model for community-led sustainability across Africa.

Unlike many initiatives, PIONEER AFRICA stands firm in its identity: a non-profit, non-
governmental project with no pursuit of financial gain. The project is not funded by government allocations but thrives on partnerships, collaborations, and in-kind support from individuals, institutions, and organisations that share its vision.

PIONEER AFRICA invites collaborators and partners from across the globe to join its mission. Whether through technical expertise, financial support, or solidarity, every contribution brings Africa closer to a future where young people are empowered, communities are resilient, and
the environment is protected.

Katsina today, Africa tomorrow. A single seed planted can grow into a forest of change; a single
youth empowered can transform a generation. PIONEER AFRICA is proof that sustainable development and youth empowerment are not distant dreams but realities already unfolding.

As Abubakar concludes: “We are not just planting trees; we are planting hope. We are not just training youth; we are building futures. The story of PIONEER AFRICA is the story of resilience, peace, and possibility which is still unfolding”

CHAIRMAN GWAGWARE FOUNDATION DONATES ₦500,000 TO YOUTH MOBILIZERS FOR PEACE AND PROGRESS FORUM The Gwagware Foundation h...
22/09/2025

CHAIRMAN GWAGWARE FOUNDATION DONATES ₦500,000 TO YOUTH MOBILIZERS FOR PEACE AND PROGRESS FORUM

The Gwagware Foundation has reaffirmed its commitment to peacebuilding, social reintegration, and youth empowerment as it received executives and members of the (Youth Mobilizers for Peace and Progress Forum) on Thursday 18th September 2025 at the foundation hqtrs in katsina state.

Speaking during the visit, the Public Relations Officer of the forum Shamsu Rabiu, explained that the association is a coalition of repentant youths with over 1,500 members in Katsina Local Government Area. He noted that while many of the members were previously engaged in anti-social activities such as theft, phone snatching, and thuggery, they have now embraced positive discipline, peace, and community progress. He further emphasized that the forum is now actively engaged in consistent advocacy to promote peace and social inclusion.

The forum also highlighted the urgent need for support to integrate its members into empowerment programs, vocational training, and state sponsored skills acquisition schemes. According to the leadership, the group has already profiled its members and compiled their data, making them ready for any sustainable livelihood or empowerment initiatives that would help them support themselves and their families.

In his response, the Chairman o Gwagware Foundation Alh Yusuf Ali musawa, commended the forum for their courageous decision to abandon negative practices and embrace peace. He assured them of the Foundation’s readiness to collaborate with stakeholders and relevant institutions to create lasting opportunities for them.

As a demonstration of immediate support, the Chairman donated five hundred thousand naira, N500,000 to the forum and pledged to include them in the Foundation’s forthcoming empowerment activities.

The interaction underscored the Foundation’s conviction that with the right support, repentant youths can become agents of positive change, contributing meaningfully to peace, stability, and progress in society.

Salim Ahmad Gaiwa
PRO, Gwagware Foundation

Address

Block 3 Behind Ɗadin Kowa Supermarket Sabon Titin Ƙwado Katsina
Katsina
234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Post:

Share