Katsina Post

Katsina Post This is where you will learn about all the latest developments in Katsina State and beyond.
(7)

MASU RUWA DA TSAKI NA ƘARAMAR HUKUMAR DUTSI A JAM'IYYAR ADC SUNYI ƘORAFI AKAN ƊAN TAKARAR DA AKA TSAIDA A MAJALISAR JIHA...
10/06/2026

MASU RUWA DA TSAKI NA ƘARAMAR HUKUMAR DUTSI A JAM'IYYAR ADC SUNYI ƘORAFI AKAN ƊAN TAKARAR DA AKA TSAIDA A MAJALISAR JIHA

Wasu masu ruwa da tsaki, shugabannin jam'iyya da mambobin jam'iyyar ADC a Karamar Hukumar Dutsi sun gabatar da takardar korafi (Pet**ion) ga Kwamitin Zabe na Jihar Katsina, da duk Shuwagabanni da masu ruwa da tsaki a ADC ta jihar Katsina, suna neman a sake duba da kuma yin nazari kan hukuncin zaben dan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar mazabar Dutsi.

Masu korafin sun bayyana damuwa kan batun karbuwa da kuma yiwuwar samun nasarar dan takarar da aka zaba, inda s**a bukaci jam'iyyar ta sake yin nazari domin ci gaban ADC a mazabar Dutsi da jihar baki daya.

Kwamishinar Harkokin Mata Ta Kai Ziyarar Gani da Ido ga Kungiyoyin Mata na Shirin Nigeria for Women a KatsinaKwamishinar...
10/06/2026

Kwamishinar Harkokin Mata Ta Kai Ziyarar Gani da Ido ga Kungiyoyin Mata na Shirin Nigeria for Women a Katsina

Kwamishinar Ma’aikatar Harkokin Mata ta Jihar Katsina, Hajiya Aisha Aminu Malumfashi, ta kai ziyarar gani da ido ga wasu kungiyoyin mata da aka kafa karkashin shirin Nigeria for Women Program Scale-Up Project (NFWP-SU) a garin Katsina.

Ziyarar, wadda ta samu rakiyar manyan sakatarori daga ma’aikatun da ke da ruwa da tsaki a shirin, ta mayar da hankali ne kan duba yadda kungiyoyin ke gudanar da ayyukansu tare da tantance nasarorin da s**a samu tun bayan fara shirin.

Da take jawabi yayin ziyarar, Shugabar Shirin NFWP-SU a Jihar Katsina, Hajiya Aisha Mohammed Yusuf, ta bayyana cewa Gwamnatin Jihar Katsina tare da hadin gwiwar Bankin Duniya sun ware makudan kudade domin tallafawa kungiyoyin mata da nufin bunkasa tattalin arzikinsu da karfafa musu dogaro da kai.

A nata bangaren, Kwamishinar Harkokin Mata, Hajiya Aisha Aminu Malumfashi, ta yaba wa mambobin kungiyoyin bisa yadda suke hada kai da gudanar da tsarin ajiya da taimakon juna cikin tsari.

Ta ce shirin wata muhimmiyar hanya ce ta inganta rayuwar mata ta hanyar hada su cikin kungiyoyi domin tara kudade, samun jari da gudanar da kananan sana’o’i.

Mambobin kungiyoyin da aka ziyarta sun nuna godiyarsu ga gwamnatin jihar da masu gudanar da shirin, suna masu bayyana cewa shirin ya taimaka wajen bunkasa sana’o’insu da inganta rayuwar iyalansu.

Kwamishinar ta bukaci matan da su ci gaba da gudanar da ayyukansu cikin gaskiya, rikon amana da hadin kai domin tabbatar da dorewar nasarorin da aka samu.

An gudanar da ziyarar ne a ranar Laraba a wasu kungiyoyin mata da ke cikin garin Katsina.

Jam'iyyar ADC ta nemi 'Yantakara da su hada kansu domin magance rikicin cikin gida tun bayan yin zaben fidda gwani ta ha...
10/06/2026

Jam'iyyar ADC ta nemi 'Yantakara da su hada kansu domin magance rikicin cikin gida tun bayan yin zaben fidda gwani ta hanyar sasanci a Jihar Katsina

‎Dantakarar shugaban ƙasar Najeriya a jam'iyyar ADC Atiku Abubakar ya turo da wakilai domin ziyara ga jagoran Adawa na jihar Katsina Dr. Mustapha Muhammad Inuwa da kuma Sanata Sadiq Yar'adua, da sauran wasu wadanda ba a yi ma daide ba.

‎K**ar yadda Katsina Post ta samu cewa an gudanar da ziyarar karkashin jagorancin Hon. Kashim Ibrahim ranar Laraba 10 ga watan Yuni 2026 a Jihar Katsina .

‎Da yake jawabi Hon. Kashim Ibrahim ya roki alfarma ga yan takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jam'iyyar ADC dasu zauna su sasanta kansu da sauran ya takara na kujerun Sanata, Majalissar Tarraya da ta Dokoki domin su samu nasara a zaben 2027

Mataimakin Shugaban Ƙasa Ya Wakilci Tinubu a Kaddamar da Titin Arterial Road N5 a AbujaDaga Ashir Mai Jama'a BadoMataima...
10/06/2026

Mataimakin Shugaban Ƙasa Ya Wakilci Tinubu a Kaddamar da Titin Arterial Road N5 a Abuja

Daga Ashir Mai Jama'a Bado

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wajen ƙaddamar da cikakken aikin gina Titin Arterial Road N5 (Obafemi Awolowo Way), wanda ya haɗa mahadar Life Camp da Ring Road III a yankin Dape da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

A yayin taron ƙaddamarwar da aka gudanar a Abuja, Sanata Shettima ya isar da saƙon Shugaba Tinubu, inda ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ta himmatu wajen bunƙasa Abuja domin ta zama babban birni da zai dace da yawan al’ummar Najeriya, burin tattalin arziƙinta da kuma martabar ƙasa.

Ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta ci gaba da bai wa ayyukan more rayuwa muhimmanci, domin inganta hanyoyin sufuri da zirga-zirga a babban birnin tarayya.

Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ƙara da cewa kammala wannan muhimmin aikin t**i zai taimaka wajen rage tsadar jigilar kayayyaki, ƙarfafa zuba jari, da kuma samar da guraben ayyukan yi ga al’umma.

Ya ce gwamnatin tarayya na ci gaba da aiwatar da manyan ayyukan ci gaba a sassa daban-daban na ƙasar nan, domin inganta rayuwar jama'a da bunƙasa tattalin arziƙin Najeriya.

AL’UMMAR BIRNIN KATSINA DA KEWAYE NA CIGABA DA NUNA JIN DAƊI DA GAMSUWA DA AYYUKAN HUKUMAR GYARAN HANYOYI TA JIHAR KATSI...
10/06/2026

AL’UMMAR BIRNIN KATSINA DA KEWAYE NA CIGABA DA NUNA JIN DAƊI DA GAMSUWA DA AYYUKAN HUKUMAR GYARAN HANYOYI TA JIHAR KATSINA (KASROMA)

Al’ummar Birnin Katsina da kewaye na ci gaba da bayyana jin daɗinsu da gamsuwarsu kan ayyukan da Hukumar Gyaran Hanyoyi ta Jihar Katsina (KASROMA) ke gudanarwa ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Injiniya Abba Junaidu.

Mazauna unguwannin da ayyukan hukumar s**a shafa ne s**a bayyana wannan farin ciki a lokacin da shugaban hukumar, Injiniya Abba Junaidu, ya kai ziyarar duba ayyukan gyaran hanyoyi da ake gudanarwa a sassa daban-daban na Birnin Katsina. Sun yaba da ƙoƙarin hukumar tare da yi mata fatan alheri da samun nasara a ayyukanta.

Mutane da dama da s**a tofa albarkacin bakinsu yayin ziyarar sun bayyana cewa gyaran hanyoyin ya taimaka matuƙa wajen rage afkuwar haɗurra, sauƙaƙa zirga-zirgar ababen hawa, da kuma rage lalacewar motoci sakamakon ramukan da ke kan tituna.

A nasa jawabin, shugaban hukumar, Injiniya Abba Junaidu, ya gode wa al’umma bisa irin yabawa da goyon bayan da suke bai wa hukumar KASROMA. Ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan ne a ƙarƙashin wani shiri na musamman na gyaran ramukan hanyoyi a Birnin Katsina mai taken “Operation Zero Tolerance to Potholes in Katsina Metropolis.”

Har ila yau, Injiniya Abba Junaidu ya nuna godiyarsa ga Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, bisa irin goyon baya da yake bai wa hukumar domin tabbatar da nasarar ayyukanta. Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa gwamnan haɗin kai da goyon baya domin ya samu damar ci gaba da aiwatar da ayyukan ci gaba da alheri a faɗin Jihar Katsina.

Farmers Laud Governor Radda as Katsina ACReSAL Distributes free Agricultural Support to FarmersIn continuation of its ef...
10/06/2026

Farmers Laud Governor Radda as Katsina ACReSAL Distributes free Agricultural Support to Farmers

In continuation of its efforts to strengthen agricultural productivity and improve the livelihoods of rural communities, the Katsina ACReSAL Project has distributed various farm inputs to selected farmers across communities of Katsina, Jibia and Kaita local government areas of the State.

Speaking during the distribution exercise held at Kabukawa in Katsina, the Katsina ACReSAL Project Coordinator Alhaji Nafiu Muhammed Musa represented by the M&E Officer, Aminu Ahmed said the intervention was part of the projects commitment to support farmers and enhance agricultural production across the state.

He explained that the distribution is among the objectives of the ACReSAL Project, which focuses on promoting livelihoods, improving climate resilience and supporting vulnerable communities.

According to him, the beneficiaries were carefully selected through a transparent process.

The project coordinator disclosed that the project constituted a committee that visited several communities across Katsina, Jibia and Kaita local government areas to identify genuine farmers who would benefit from the intervention.

He said the committee went round various communities to ensure that the support reaches deserving farmers who are actively engaged in agricultural activities.

He stated that this was done to guarantee fairness, transparency and impact of the intervention.

Alhaji Nafiu Muhammed Musa further revealed that about 600 beneficiaries from the three Local Government Areas would benefit from the gesture free.

He urged the beneficiaries to make effective and judicious use of the items provided in order to increase agricultural output, food security and development of their communities.

The items distributed included solar-powered water pumps, pesticides, improved crop seeds, wheelbarrows, fertilizers, planters, sprayers and among others.

In their reactions, the beneficiaries expressed gratitude to the Katsina State Governor, Malam Dikko Umar Radda, World Bank and the Katsina ACReSAL Project for the timely intervention.

Speaking on behalf of the beneficiaries, Malam Jamilu Lawal Jibia, a farmer from Gadirge in Jibia described the support as timely and impactful, noting that it came at a time when many farmers were facing difficulties due to the rising cost of agricultural inputs.

He said the intervention would reduce hardship among farmers and increase crop production in the benefiting communities and beyond.

Malam Jamilu Lawal commended Governor Radda and the Katsina ACReSAL Project for their commitment to supporting rural farmers across the state.

He therefore pledged to make use of the items which according to him would increase farming activities across Katsina State.

Communication Officer
Katsina ACReSAL

Kungiyar ’Yan Kwangila Ta Jihar Katsina Ta Jaddada Muhimmancin Gaskiya da Bin Ka’idoji a Ayyukan KwangilaKungiyar Associ...
10/06/2026

Kungiyar ’Yan Kwangila Ta Jihar Katsina Ta Jaddada Muhimmancin Gaskiya da Bin Ka’idoji a Ayyukan Kwangila

Kungiyar Association of Katsina State Contractors (AKSC) ta gudanar da taronta na shekara-shekara domin ƙarfafa haɗin kai tsakanin mambobinta tare da tattauna hanyoyin inganta harkokin kwangila a Jihar Katsina.

Taron wanda ya gudana a ranar Laraba, 10 ga Yuni, 2026, a dakin taro na Fams Hotel da ke Katsina, ya samu halartar ɗaruruwan mambobin kungiyar daga sassa daban-daban na jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, shugaban kungiyar, Alhaji Abdullahi Esha, ya bayyana cewa manufar taron ita ce wayar da kan mambobi kan muhimmancin sabunta rajista, bin doka da oda, da kuma riƙo da gaskiya da amana yayin gudanar da ayyukan kwangila.

Ya ce ƙungiyar na ci gaba da ɗaukar matakai domin tabbatar da cewa mambobinta suna gudanar da ayyukansu bisa ƙa’idojin da s**a dace tare da kiyaye martabar sana’ar kwangila.

Babban baƙo mai gabatar da kasida, QS Faisal Ahmed, ya yi bayani kan ma’anar aikin kwangila da irin ƙalubalen da masu sana’ar ke fuskanta. Ya kuma yi karin haske kan yadda ɗan kwangila zai gudanar da kyakkyawar mu’amala da masu ba da kwangila da kuma ma’aikatan da ke aiki ƙarƙashinsa domin samun nasarar ayyuka.

A nasa jawabin, sakataren ƙungiyar, Alhaji Yakubu Ali Mai-Chanji, ya bayyana cewa daga wannan shekara ƙungiyar za ta ƙara tsaurara matakan sabunta rajistar mambobi tare da tabbatar da cewa kowane ɗan kwangila yana da takardun da s**a dace da sana’arsa.

Ya ce hakan zai taimaka wajen inganta aikin kwangila da kuma kare mutuncin ƙungiyar a idon jama’a da hukumomi.

Taron ya kuma ba mahalarta damar gabatar da shawarwari da ra’ayoyi kan hanyoyin da za su taimaka wajen bunƙasa ƙungiyar da magance matsalolin da ke fuskantar mambobinta.

Mahalarta taron sun yaba da shirin, suna masu bayyana cewa irin waɗannan tarurruka na taimakawa wajen ƙarfafa haɗin kai, musayar ilimi da samar da sabbin dabarun gudanar da harkokin kwangila a jihar.

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci k...
10/06/2026

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci kusan dazukan anan da dama wuraren kiyon dabbobi ne. To, bayan da aka kirkiri Abuja, an tanadi wurare da aka tsara jama'a za su zauna, tare da wuraren ofisoshi da wuraren gina kasuwanni da sauran wuraren more rayuwa, amma aka manta a keɓe tare da inganta inda dabbobi za su yi kiwo.

Akwai gandun daji guda huɗu da faɗin su ya kai hekta 33 a Abuja da aka ware tun da, sannan tun da aka ware waɗannan gandun dajin a wancan lokacin da aka kirkiri Abuja, ba a taɓa yin wani abu na inganta wurin ta yadda za a maida makiyaya wurin ba.

Tun bayan kafa ma’aikatar kula da bunƙasa kiyon dabbobi kusan shekara biyu da s**a wuce, ma’aikatar ta kulla alaƙa tare da Hukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya ta yadda za a inganta waɗannan wurare da ke yankunan ƙauyen Kau, Karshi da sauran wurare da ke Abuja.

Muna aiki tare da masu ruwa da tsaki wajen inganta waɗannan gandun dajin, sannan a duba yiwuwar maida makiyaya wurin sannu a hankali."

— Idi Muktar Maiha, Ministan Bunƙasa Kiyon Dabbobi, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai na Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026 da aka gudanar a ranar Talata, 9 ga Yuni, 2026.

10/06/2026

Kalli yanda ruwan sama yayi ambaliya bisa t**in IBB Way gab da roundabout na Ɗanɗagoro.

Shin ko kuma ambaliya ta shafi unguwannin ku?
Ku tura mamu a comment!

Address

Block 3 Adjacent Ɗadin Kowa Supermarket Sabon Titin Ƙwado Katsina
Katsina
234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Post:

Share