Katsina Post

Katsina Post A branch of a registered media outlet - POST MULTIMEDIA ENTERPRISES - with interest in Katsina State
(3)

Ma'aikatar lafiya ta jiha, ta shirya bada horon na kwana 2 kan kula da lafiyar Idanu a matakin farko (PRIMARY EYE CARE) ...
30/07/2025

Ma'aikatar lafiya ta jiha, ta shirya bada horon na kwana 2 kan kula da lafiyar Idanu a matakin farko (PRIMARY EYE CARE) a Katsina ta tsakiya

Gwamnatin jihar Katsina, a ɓangaren Ma'aikatar lafiya ta jiha, ta shirya bada horon na kwana 2 kan kula da lafiyar Idanu a matakin farko (PRIMARY EYE CARE) a Katsina ta tsakiya, bayan sun kammala kwana 2 kan bada horo a Shiyya Funtua.

Tunda farko, horon wanda aka fara bi Shiyyar Funtua don bada horo, tare da kammalawa da Shiyyar Funtua, inda ya zuwa yanzu ake ci gaba da gudanarwa a Katsina ta tsakiya, da kuma Shiyyar Daura nan ba da jimawa ba.

Kafin fara horaswsr, jami'an sun tsara cewa, daga kowacce mazaɓa sun ɗauki mutum ɗaya, daga cikin Mazaɓu 361 dake jihar Katsina, domin ba su horo kan inganta lafiyar idanu.

Kamar yadda Katsina Post ta samu, tunda farko, Kwamishinan Lafiya na jihar Katsina, Hon. Musa Adamu Funtua, shi ne ya umarci jami'an da su ɗauki Mutum ɗaya kowacce mazaɓa don ganin shirin ya inganta a sassan jihar.

Ya shaida ma su da su kasance masu bin kanun abubuwan da aka koyar da su, tare da bada ilimin da aka ba su ga al'ummar jihar Katsina don ganin kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

Shirin horaswar wanda gwamnatin jihar Katsina ta ɗauki nauyi, ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umaru Raɗɗa, za a kammala nan ba da daɗewa ba a jihar Katsina.

Kungiyar Gwagware Boys Jibiya Tayi Kira Ga Hon. Muhammadu Halliru (Sadaukin Jibiya) Da Ya Shigo Siyasar Karamar Hukumar ...
30/07/2025

Kungiyar Gwagware Boys Jibiya Tayi Kira Ga Hon. Muhammadu Halliru (Sadaukin Jibiya) Da Ya Shigo Siyasar Karamar Hukumar Jibiya

Kungiyar ta yi kiranyen gare shi da ya shiga cikin harkokin siyasar karamar hukumar ta Jibiya domin ci gaban al’umma a wani taro da ta shira.

An gudanar da taron a ranar Laraba, 30 ga Yuli, 2025, kungiyar matasa ta Gwagware Boys Jibiya ta gudanar da taro na musamman inda ta karrama Hon. Muhammadu Halliru, wanda aka fi sani da Sadaukin Jibiya, tare da nada shi a matsayin Uban Kungiya.

Shugaban kungiyar, a cikin jawabin da ya gabatar, ya bayyana cewa karamci da gaskiyar Hon. Muhammadu Halliru ne ya janyo wa kungiyar da sauran matasan yankin sha’awar kiranye gare shi. Ya ce matasa sun fahimci cewa halayen kirki da kishin al’umma da ke tattare da shi na iya taka rawar gani wajen kawo sauyi mai amfani a siyasar Jibiya.

Jami’in hulda da jama’a na kungiyar, Kwamarade Umar Labo, ya jaddada cewa kiranyen da kungiyar ta yi wa Hon. Halliru ya dace, ganin irin jajircewar da yake nunawa wajen tallafa wa jama’a. Ya ce shigowar matashi kamar shi siyasar karamar hukumar Jibiya zai kawo ci gaba, musamman a fannin rayuwar matasa da talakawa.

A nasa jawabin, Hon. Muhammadu Halliru ya gode wa kungiyar bisa wannan karramawa da kiranye da aka yi masa. Ya ce:

“Ni tun da fari ina cikin harkokin siyasar karamar hukumar Jibiya, kuma ina daga cikin kungiyar Gwagware Boys. Har ila yau, ina cikin wadanda ke hidima ga al’ummar Jibiya kai tsaye.”

Ya kara da cewa duk wanda ke tare da Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, wajen yada ayyuka da manufofin alheri, to shi ma yana tare da shi domin ciyar da Jibiya da Katsina gaba daya. Hon. Halliru ya bayyana cewa zai ci gaba da bayar da gudunmuwar da ake bukata domin ci gaban al’ummar yankin.

Taron wanda ya gudana a Munaj Event Centre da ke cikin birnin Katsina, ya samu halartar manyan baki, ciki har da Shugaban Dakin Karatu na Jihar Katsina, Hon. Shafi’i Abdu Bugaje, da shugabanni da mambobin kungiyar, tare da dimbin al’umma daga sassa daban-daban.

30/07/2025

Shugaban karamar hukumar Ingawa, Hon. Abubakar O2 yana kokari sosai kuma inshaAllahu zai cigaba da yin siyasa har karshen rayuwar sa - Inji Hon. Bishir Yandoma, dan jam'iyyar APC a Katsina

APPRECIATION TO HIS EXCELLENCY, THE EXECUTIVE GOVERNOR OF KATSINA STATE.On behalf of the good people of Sabuwa Local Gov...
30/07/2025

APPRECIATION TO HIS EXCELLENCY, THE EXECUTIVE GOVERNOR OF KATSINA STATE.

On behalf of the good people of Sabuwa Local Government Area and as a proud indigene, I wish to extend my appreciation to His Excellency, Governor Dikko Umar Radda, PhD, for the gracious approval of the Sabuwa to Tashar Bawa road construction project, valued at approximately ₦18.5 billion.

This timely and strategic intervention, which will directly link no fewer than 13 communities, is a monumental step toward transforming our local economy, enhancing access to essential services and addressing longstanding security challenges in the area.

Your Excellency, we are truly grateful for your commitment to the infrastructural development and welfare of rural communities across Katsina State.

May Almighty Allah continue to guide, protect and strengthen you in your leadership journey as you work tirelessly to uplift the lives of our people.

Signed: Engr. Tasiu S Abubakar Sabuwa. FNSE

Maiba gwamna shawara akan harkokin siyasa ya bayyana godiya ga Gwamna Radda daya amince da maida asibitin Mai’adua zuwa ...
30/07/2025

Maiba gwamna shawara akan harkokin siyasa ya bayyana godiya ga Gwamna Radda daya amince da maida asibitin Mai’adua zuwa babban asibiti.

Mai ba Gwamnan Jihar Katsina shawara kan harkokin siyasa, Hon. Yau Umar Gwajo-Gwajo, ya bayyana godiya ga Gwamna Dikko Umar Radda bisa amincewar da ya yi na maida asibitin Mai’adua daga karamin asibiti zuwa babbar asibiti wato General Hospital.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Hon. Gwajo-Gwajo ya ce matakin da Gwamnan ya dauka ya nuna irin damuwarsa da lafiyar al’ummar jihar, musamman ma mazauna yankunan karkara.

Ya bayyana cewa maida asibitin zuwa babban babban asibitin zai taimaka gaya wajen inganta lafiyar al'ummar karamar hukumar.

Hon. Gwajo-Gwajo ya kuma nuna godiya ga Majalisar Zartarwa ta Jihar Katsina bisa yadda ta amince da wannan kudiri da nufin inganta harkar lafiya a karamar hukumar.

Ya ce, Wannan mataki na Gwamna Radda da majalisar zartarwa ya nuna cewa gwamnatin Katsina na daukar lafiyar jama’a da muhimmanci, kuma suna godiya da wannan kulawa.

Ya kara da cewa al’ummar Mai’adua za su amfana da wannan gyara, inda ya bukaci su ci gaba da yin addu’o’i na fatan alheri da nasara ga Gwamna Dikko Umar Radda, domin Allah ya kara masa lafiya da ikon gudanar da ayyukansa cikin nasara.

Dan Majalisar Tarayya Arc. Usman Murtala Banye Ya Kaddamar da Rabon Takin Noma Tirela Tara Ga Al’ummar Rimi, Charanchi d...
30/07/2025

Dan Majalisar Tarayya Arc. Usman Murtala Banye Ya Kaddamar da Rabon Takin Noma Tirela Tara Ga Al’ummar Rimi, Charanchi da Batagarawa

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Rimi, Charanchi da Batagarawa, Arc. Usman Murtala Banye, ya kaddamar da rabon takin zamani Tirela tara (9) ga manoma a mazabarsa domin inganta harkar noma da rage radadin rayuwa ga al’umma.

A cewar Arc. Banye, a bara sun raba Tirela uku (3) na taki, amma a bana, cikin ikon Allah, sun samu damar raba Tirela tara (9), wanda ya ƙunshi nau’in takin zamani irin su UREA da NPK. Ya bayyana cewa wannan shiri na daga cikin kokarinsa na tallafa wa manoma don bunkasa aikin gona a yankunan Rimi, Charanchi da Batagarawa.

Ya kara da cewa zai ci gaba da samar da hanyoyi daban-daban da za su inganta rayuwar al’umma, tare da tabbatar da cewa an zuba jari a bangarorin da s**a fi tasiri ga cigaban al’umma.

A jawabin karshe, Arc. Banye ya yi kira ga shugabanni da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomin uku da su ji tsoron Allah, su tabbatar da cewa an bai wa wadanda s**a cancanta damar amfana da wannan tallafi.

Taron ya samu halartar manyan shugabanni daga kowace karamar hukuma da s**a hada da Hon. Yahaya Lawal Kawo daga Batagarawa, Muhammad Ali daga Rimi, da kuma Aminu Hassan wanda ya wakilci shugaban karamar hukumar Charanchi.

Za'a Raba Gidan Sauro Sama Da Miliyan 4 Ga Magidanta A Jihar KatsinaGwamnatin Jihar Katsina hadin guiwa da wasu Hukumomi...
30/07/2025

Za'a Raba Gidan Sauro Sama Da Miliyan 4 Ga Magidanta A Jihar Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina hadin guiwa da wasu Hukumomin Bada Agaji sun shirya tsaf domin fara raba ragar gidan sauro mai dauke da magani kusan miliyan 5 ga al'ummar Jihar.

Babban Jami'i daga Kungiyar Inganta Lafiyar Iyali(SFH)Gbue Denem Daniel ne ya sanar da hakan a lokacin taron yin jawabi ga Manema Labarai ciki har da Accuracy News Hausa akan tsare-tsaren da aka yi na samun nasarar raba gidan sauron.

Gbue Denem Daniel ya ce an kira taron ne domin nan goyon bayan Kafafen Yada Labarai domin ganin an cimma nasarar da ake bukata wurin aiwatar da shirin.

A cewar shi, Kafafen Yada Labarai na da gagarumar rawar da zasu taka domin ganin an cimma nasara,ta fuskar ganin rabon gidan sauron ya karade Kananan Hukumomi 34 na Jihar Katsina.

Ya roke su akan kada su gajiya wurin bullo da shirye-shiryen wayar da kan al'umma akan muhimmancin kwana cikin gidan sauro,domin kare kai daga zazzabin cizon sauro.

Gbue Denem Daniel ya ce Najeriya ita ce Kasa mai mafi yawan mutane da ke kamuwa da zazzabin cizon sauro a fadin Duniya,wanda ya kai kashi 25 na yawan adadin lalurar da ake samu.

Babban jami'in ya kuma magantu akan matsalolin da suke fuskanta a yaki da zazzabin cizon sauro,wanda s**a hada da rashin isassun kudade,sai ya roki gwamnatoci a dukkan matakai akan su duba yiyuwar kara kudade ta wannan fuska.

30/07/2025

Yadda Gwaman jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya kawo cigaba a harkar noma - Tare da Hajiya Hadiza Kadarko

30/07/2025

Jigo a jam’iyyar PDP, Hon. Zaharaddeen Babba Mazoji, ya bayyana damuwarsa kan halin ko-in-kula da ‘yan siyasa ke nuna wa game da matsalar tsaro a yankinsu.

Haka zalika, ya koka kan yadda malamai da masu addini ke kasa maida hankali wajen yin addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya a yankin.

Sai dai kuma, ya yaba da jajircewa da ƙoƙarin da Hakimin Matazu (Fagacin Katsina) ke yi wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.

The National Youth Council of Nigeria, NYCN, Katsina State Chapter will join other youth-led organizations in the world ...
30/07/2025

The National Youth Council of Nigeria, NYCN, Katsina State Chapter will join other youth-led organizations in the world in celebrating the International Youth Day 2025 with the theme 'Local Youth Actions For The SDGs & Beyond.

🗓️ Tuesday, August 12th
📍 Katsina State
🕘 9AM – 3PM

Address

Block 3 Behind Ɗadin Kowa Supermarket Sabon Titin Ƙwado Katsina
Katsina
234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Post:

Share