14/09/2026
An Ƙaddamar da Shirin Ba da Tallafin Kuɗi na Conditional Cash Transfer Karo na 6 ga Mutane 3,000 a Ƙaramar Hukumar Kaita
An ƙaddamar da shirin ba da tallafin kuɗi na Conditional Cash Transfer karo na shida ga mutane 3,000 a Ƙaramar Hukumar Kaita ta Jihar Katsina.
Da yake jawabi yayin ƙaddamar da shirin, Shugaban Shirin na Ƙaramar Hukumar Kaita, Alhaji Bishir Sa’idu, ya fara da gode wa Allah, sannan ya bayyana cewa al’ummar ƙaramar hukumar Kaita suna amfana da shirin.
Ya ce shirin ba shi da alaƙa da wata jam’iyya ta siyasa, yana mai cewa mutane 3,000 da aka fara ba wa tallafin ba su ne kaɗai za su amfana ba, domin akwai wasu waɗanda za su amfana nan gaba.
Shi kuwa Shugaban Biyan Kuɗi, Usman Sha’aibu, ya yi bayani kan yadda waɗanda s**a cancanta za su karɓi katinsu da kuɗinsu. Ya shawarci masu cin gajiyar shirin da su bi layi tare da tabbatar da cewa sun zo da lambar BVN. Haka kuma, ya yi kira ga waɗanda za su amfana da shirin da su ba da cikakken haɗin kai domin gudanar da aikin cikin sauƙi.
A nasa jawabin, Shugaban Shirin na Jihar Katsina, Alhaji Aminu Alhassan Faskari, ya ce sun zo ne domin ƙaddamar da ba da wannan tallafi da ake bayarwa lokaci-lokaci, bisa haɗin gwiwar Gwamnatin Jiha da Gwamnatin Tarayya.
Ya bayyana cewa ana gudanar da shirin ne domin taimaka wa mutane masu rauni da mabukata, tare da rage musu wahalhalun rayuwa.
Alhaji Aminu Alhassan Faskari ya ƙara jaddada cewa ba dole sai mutum ɗan jam’iyyar APC ba ne zai amfana da shirin, domin tallafin na kowa ne.
Ya ce, “Haƙƙin kowane ɗan ƙasa ne,” sannan ya ƙara da cewa nan ba da daɗewa ba mutane da dama za su amfana da shirin.
Ya kuma bayyana cewa tsarin ana yin sa ne domin samar da sauƙi da rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta. Ya ce sama da mutane 60,000 ne za su amfana da wannan tallafi a faɗin Jihar Katsina baki ɗaya.
Ya ƙara da cewa tallafin zai kai kusan kashi uku, inda wasu daga cikin waɗanda s**a cancanta za su karɓi tallafin kashi biyu, yayin da wasu kuma za su karɓi kashi uku, bisa tsarin da aka tanada.
Haka kuma, ya bayyana cewa an samar da tsarin da zai bai wa waɗanda s**a cancanta damar karɓar kuɗaɗensu cikin aminci da sauƙi.
A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kaita, Hon. Bello Yanɗaki, wanda Mataimakinsa, Alhaji Jamilu Sani Dankama, ya wakilta, ya fara da gode wa Allah SWT, sannan ya miƙa godiyarsa ga Shugaban Ƙasa bisa samar da wannan shiri na tallafa wa al’umma.
Ya kuma bayyana cewa, in Allah ya so, al’ummar Ƙaramar Hukumar Kaita za su ba da cikakken haɗin kai domin ganin an samu nasarar shirin.
Wasu daga cikin wakilan waɗanda s**a amfana da shirin yayin ƙaddamarwar sun haɗa da Hauwa Isiyaka, Amina Nura, da Hafizu Sulaiman.
Tasi’u Abubakar ne ya gabatar da jawabin godiya a madadin waɗanda s**a amfana da shirin.