Lajnatul Hisbah Association Of Nigeria, Dandagoro Detachment.

Lajnatul Hisbah Association Of Nigeria, Dandagoro Detachment. Domin karewa da tsayar da Shari'ar Musulunci a Najeriya

09/05/2024

*KYAKKYAWAR RAYUWA*

✍️ Abdallah Salihu Almujawwid (Abu Muhammad)

*1.0 Gabatarwa*
Abu ne sananne, lallai shi addinin Musulnci ya zo domin saita rayuwar al'umma da kuma samar da hadin kai. Kuma samun nasara da cigaban kowace al'umma yana samuwa ne ta hanyar zaman lafiyarsu da dinkewarsu wuri guda. Duk kau al'ummar da ta rasa hadin kai to lallai ta dauki hanyar dakushewar gobenta, kuma ta bude hanyoyin shigowar matsaloli a cikinta babu kaidi.

Wannan ne ya sa Musulunci ya zo da ladubba, halaye ko dabi'u wadanda siffantuwa da su zai samar da kwanciyar hankali hadi da soyayya a tsakanin mutane. Daga cikin mafi cikar Halittun Allah SWT kyawawan Halaye shi ne Annabi Muhammad S.A.W, wanda da kansa yake fada "Lallai an aiko shi ne domin ya cikasa mafi daukakar halaye. Shi yasa ma ya zamto ya fi kowa yawan masoya, saboda dabi'unsa kyawawa.

Haka ma, an ruwaito da yawa daga cikin wadanda s**a mika wuya a zamaninsa, babu abin da ya fi jan hankalinsu irin kyawawan halayensa. Tun kafin a aiko shi suke yaba halayensa, suna ba shi ajiyar ababensu saboda amanarsa, kai har ya kai ga sun yi masa lakabi da AL'AMIN.

Da wannan za mu gane cewa lallai ba za mu so juna ba, har sai ya kasance mun siffantu da kyawawan halaye irin na sa S.A.W, domin shi ne mafi girman wanda za mu yi koyi shi da shi, sannan Dalibansa (Sahabbai), sannan Dalibansu (Tabi'ai) kasancewarsu mafifita a wannan al'umma ta annabi S.A.W. Duk kau wanda ya bi wani tafarki sabanin na su to lallai zai halaka. Allah SWT ya tsare mu baki daya. Amin

KATSINA STATE HISBAH BOARDFITOWA TA UKKU (3)Nura A Yar'adua Assalafy 09031599997Assalamu Alaikum,GYARA KAYANKA BAI ZAMOW...
18/04/2024

KATSINA STATE HISBAH BOARD

FITOWA TA UKKU (3)

Nura A Yar'adua Assalafy
09031599997

Assalamu Alaikum,
GYARA KAYANKA BAI ZAMOWA SAUKE MU RABA

Dan sanda abokin kowa... HISBAH AIKIN ALLAH.
Ita Hukumar Hisbah tana so ne ta kawo dauki na hadin guiwa ga iyaye da alummar gari, domin gyara kayanka kuma d'a na kowane. Saboda haka yana k**ata ga iyayen 'ya'ya da mutanen gari su zamo masu had'in guiwa da goyon baya wajen gusar da 'barna. Bai k**ata Hibah ta zo hana badala a unguwa ba a ce wasu sun hana aikin hanawar, bai k**ata a zo k**a d'anmu ba a ce mu iyaye mun hana a k**a shi. Mu ya k**ata mu k**a ayi maganin matsalar, domin gyara kayanka ne.

Babban laifi ne hana doka ta yi aiki, babban laifi ne hana k**a mai laifi, babban laifi ne fada da jami'an Hisbah... Idan har amarya ba ta hau doki ba, to ba a aza ma ta kaya (wato indai ba mu k**a ma Hisbah ba waje hana barna da k**a masu laifi ba, to bai k**ata mu hana su aikinsu ba)

Hukumar Hisbah ba abokiyar gaba ba ce da kowa, saidai tana gaba da dukkan ayyukan badala, har shi mai yin barna Hisbah na so ya bari ne don tana son shi.

Matasan da ku ke shagulgulan badala da mata ku ji tsoron Allah, ku dauka idan 'ya'yanku ne ko kannenku ba za ku so ayi da su ba. Ku kuma 'yan mata ku ake lalata ma rayuwa, kuna cin amanar iyayenku da ta 'ya'yanku da mazajenku. Ku ji tsoron Allah... Domin akwai mutuwa da zaman kabari da hisabi, abin da kowa ya shuka shi zai girba.

Dan Uwanku A Muslunci kuma mai kaunar ku saboda Allah mai fatan alkhairi ga Jahar Katsina da al'ummarta:-
Nura A Yar'adua Assalafy
09031599997
E-mail:- [email protected]

KATSINA STATE HISBAH BOARDFITOWA TA BIYUNura A Yar'adua Assalafy 09031599997Assalamu Alaikum,YADDA AKE SAMUN IZININ GUDA...
17/04/2024

KATSINA STATE HISBAH BOARD

FITOWA TA BIYU

Nura A Yar'adua Assalafy
09031599997

Assalamu Alaikum,

YADDA AKE SAMUN IZININ GUDANAR DA TARURRUKA NA AL'ADA DAGA HUKUMAR HISBAH TA JAHAR KATSINA

Wannan hukuma mai albarka ba ta haramta dukkan tarurruka na al'ada ba, saidai wadanda s**a saba ma shari'ah ta Muslunci, musamman wadda cikinta akwai shaye-shaye, DJ, cakuduwar maza da mata, Gala, da sauransu. Kamar yadda hukumar ta fitar da sanarwar cewa ta haramta duk wadancan miyagun al'adu.

Amma idan mutane s**a shirya taron da babu wadancan abubuwan ko masu k**a da su, to Hisbah ba ta hanawa.

Saidai ana so kafin ku gudanar da tarurruka na al'ada ana so ku rubuto takardar neman izini tare da bayyana abubuwan da taron ya tattaro da yadda taron zai gudana, hade da takardar tsarin gudanar taron (programme of events).

Hukumar Hisbah za ta duba ta gani, idan taron bai ci karo da doka ba, za ta bada izini a rubuce, inda gyara za ta gyara. Sai ku je ku yi taronku lafiya. Idan ko ku ka yi cin amana bayan an ba ku izini, ta hanyar shigo da abubuwan da aka hana ku, to hukumar Hisbah za ta dauki matakin da ya dace.

Dan Uwanku A Muslunci kuma mai kaunar ku saboda Allah mai fatan alkhairi ga Jahar Katsina da al'ummarta:-
Nura A Yar'adua Assalafy
09031599997
E-mail:- [email protected]

17/04/2024

KATSINA STATE HISBAH BOARD

FITOWA TA DAYA

Assalamu Alaikum,
Al'ummar jahar Katsina masu albarka da mutunci da son alkhairi da tarbiyya da sanin ya k**ata, ina mai farin cikin sanar da ku cewa HUKUMAR HISBAH TA JIHAR KATSINA taku ce, kuma tana tare da ku, kuma ta zo ne don gyara kayanka (wanda ba sauke mu raba ba ne ba).

Wannan hukuma alkhairi ce a jahar Katsina, kuma ta zo ne ta k**a mana wajen tarbiyyar 'ya'yanmu da 'yan uwanmu da rage yaduwar barna da badala a cikin wannan gari mai tsarki da al'ummarsa masu albarka.

Mu ji tsoron Allah mu ba ta goyon baya da hadin kai kuma mu taya ta addu'a da fatan alkhairi, tare da bata shawara, domin cin nasararta tamu ce.

Wadanda kuma suke neman wannan hukuma da sharri Allah Ta'ala ya shirye su kuma ya kare wannan hukuma daga dukkan sharri.

Al'ummar wannan jaha ta Katsina masu albarka, ku sani cewa wajibi (dole) ne a kanmu mu tashi tsaye wajen bada kariya ga wannan hukuma, domin amana ce a kanmu, sai Allah Ta'ala ya tambaye mu! Ita wannan wannan hukuma ba ta siyasa ba ce ba, ta addini ce kuma ta al'ummar wannan jaha ce mai albarka.

Dan Uwanku A Muslunci kuma mai kaunar ku saboda Allah mai fatan alkhairi ga Jahar Katsina da al'ummarta:-
Nura A Yar'adua Assalafy
09031599997
E-mail:- [email protected]

FOR IMMEDIATE RELEASEKATSINA STATE HISBAH BOARD CRACKS DOWN ON IMMORAL ACTIVITIES, ENSURING COMPLIANCE STATEWIDE The Kat...
09/04/2024

FOR IMMEDIATE RELEASE

KATSINA STATE HISBAH BOARD CRACKS DOWN ON IMMORAL ACTIVITIES, ENSURING COMPLIANCE STATEWIDE

The Katsina State Hisbah Board, under the astute leadership of Commander General Mallam Aminu Usman (Abu Ammar), Ph.D., has effectively curbed various immoral activities prevalent among the youth of Katsina State.

The board's recent initiatives have successfully halted the following illicit behaviors:

1. DJ Music Performances

2. Sara S**a Movement (Ƙauraye)

3. Galla Night

4. Conducting weddings ceremony that contravene Sharia law

In a bid to uphold the sanctity of Sharia law, the Hisbah Board reaffirms its commitment to monitoring and enforcing compliance throughout the state.

Collaborating closely with Katsina State security forces, the Hisbah Board pledges decisive action to eradicate all forms of vandalism and immorality within Katsina State. The Board urges parents, Islamic religious educators, and community leaders to remain vigilant and actively support efforts to guide and supervise the youth.

Signed,

Mallam Nafi'u M. Aƙilu
Public Relations Officer
Katsina State Hisbah Board

- April 7, 2024 -

WANI MALAMI A AJIWA YA JAGORANCI MAYAR DA AURE AKAN N4,000A jiya Laraba 27 March, 2024, wanda ya yi daidai da 17 Ramadan...
28/03/2024

WANI MALAMI A AJIWA YA JAGORANCI MAYAR DA AURE AKAN N4,000

A jiya Laraba 27 March, 2024, wanda ya yi daidai da 17 Ramadan, 1445, Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina karkasin jagorancin Babban Kwamandanta na Jiha Dr. Aminu Usman (Abu Ammar), ta yi hukunci akan wasu ma'aurata guda biyu; Yakubu Husamatu Ajiwa da; Nafisa Adamu Ajiwa.

Hukumar Hisbah ta samu labari, kuma ta yi binciki ta tabbatar da saki uku da Yakubu Husamatu Ajiwa ya yi wa Nafisa Adamu Ajiwa, kuma aka sami wani Malami mai suna Abdurrahman Abdurra'uf Ajiwa ya jagoranci mayar da auren akan N4,000. Wannan ne yasa Hukumar Hisbah ta dauki matakai k**ar haka:
1. Tabbatar da lalata wannan auren da kuma raba tsakanin ma'auratan.
2. Yin hukuncin bulala ga dukkan bangarorin guda uku a matsayin "TA'AZIR" gare su, sak**akon keta alfarmar Shari'ar Allah da s**a yi.
3. Yin nasiha a gare su a cikin abin da ya yi masu saura na rayuwa, da kuma bin hukuncin abin da Allah ya tsara masu.

A karkashin wannan Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina ta nemi al'umma da su ji tsoron Allah, su kuma bi Ka'idoji da Dokokin da Allah SWT ya gindaya a cikin rayuwarmu. Kuma bayan haka Hukumar Hisbah na yi ma al'ummar Jihar Katsina fatan alheri.

KTSHB Media

SANARWAR LAKCAR  WATAN RAMADAN GA MATA Ana sanar da iyaye Mata   Lakca da aka shirya za'a gabatar k**ar haka:Rana: Asaba...
22/03/2024

SANARWAR LAKCAR WATAN RAMADAN GA MATA

Ana sanar da iyaye Mata Lakca da aka shirya za'a gabatar k**ar haka:

Rana: Asabar 13 Ramadan, 1445/ 23 March, 2024
Lokaci: karfe 09:00 na safe
Wuri: Dakin Taro na Multi-purpose Women Center, Filin Samji, Katsina

Malami Mai Gabatarwa:
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa

Allah ya bada ikon halarta. Amin

JIBWIS Katsina
12 Ramadan, 1445
22 March, 2024

Hotuna:- A Ranar Talata 19 ga watan Disamba, 2023, Tawagar National Commandant na Lajnatul Hisbah Association of Nigeria...
22/12/2023

Hotuna:- A Ranar Talata 19 ga watan Disamba, 2023, Tawagar National Commandant na Lajnatul Hisbah Association of Nigeria LAJHAN sun kai ziyarar taya murna ga Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina wato.

LAJHAN karkashin jagorancin Babban Kwamandan ta na Kasa Alkali Mal. Hamisu Abubakar Imam da Yan rakiyarsa sun kai ma Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina Dr. Aminu Usman Abu Ammar ziyara ta fatan alheri da taya murna.

Tafiyar ta samu rakiyar manya masu muk**ai a matakin Jiha da kuma Kasa , tare da dayawa daga cikin Shuwagabannin Kananan Hukumomi.

Daga cikin wadanda s**a raka Shugaban akwai P.R.O I na Jihar Katsina wato Mal. Halliru Umar, Mai bada shawara akan Harkokin siyasa kuma Discipline Officer II, Mal. Muhammad Sh*tu, Amirud Da'awa I I da sauransu.

Shugaban ya taya Dr. Aminu Usman Abu Ammar murna tare da bashi shawarwari da bashi tabbacin goyon baya dari bisa dari.

Dr. Yayi matukar murna da wannan ziyara da wannan shawarwari da bada tabbacin yin aiki tare kasancewar aikin Allah ne, ya kuma nuna irin kaunar da yake yi ma Mal. Hamisu Abubakar Imam tun lokutan baya, wadda yace bai taba jin ta sauka ba ko da da rana daya.

Yan Hisbah sun yi masa Fareti da kuma Kata domin girmamawa.

Divisional ICT Officer
Batagarawa Division
Abdallah Almujawwid
22-12-2022

SABON SHUGABAN HISBAH NA BATAGARAWA DIVISION YAYI MATAIMAKI NA BIYUA yau  5 ga watan Rabee' u Thani, 1445 wanda yayi dai...
20/10/2023

SABON SHUGABAN HISBAH NA BATAGARAWA DIVISION YAYI MATAIMAKI NA BIYU

A yau 5 ga watan Rabee' u Thani, 1445 wanda yayi daidai da 20 ga watan October, 2023 ne Sabon Shugaban Hisbah na Karamar Hukumar Batagarawa, Mal. Sadiq Ibrahim Gyaza ya nada Mataimaki na Biyu.

Shugaban ya nada Mal. Ibrahim Ali Yaro, a matsayin Mataimaki na Biyu. Wannan ya faru ne saboda irin gajurtar sa, da kuma irin gudummuwar da yake bada a wurin aikin Hisbah.

Mal. Ibrahim Ali Yaro ya rike mukamin Discipline I, inda daga baya aka mayar da shi Mataimakin Shugaba. Kuma shine yake jagorantar Kwamitin Discipline na Batagarawa Division.

Shugaba da sauran mukarrabansa sun yi masa fatan alheri da fatan nasara a cikin aikinsa.

Div. ICT Officer
Abdullahi Salihu Almujawwid
5th Rabee' At-Thani, 1445
20th October, 2023

Address

Katsina

Telephone

+2348102369270

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Lajnatul Hisbah Association Of Nigeria, Dandagoro Detachment. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Lajnatul Hisbah Association Of Nigeria, Dandagoro Detachment.:

Share