12/05/2026
WAI YA ABIN YAKE?
Shaidanu sunfi yawa a cikin hidimar siyasa fiye da masu son gyaranta. Tun daga Ex-officio na Party har izuwa mafi kololuwar girman mukamin siyasar Karamar Hukumar Kusada Rt. Hon. Abubakar Yahaya Kusada ya taka rawa fiye da kowa wajen kafuwar sa. Idan kuwa hakane banga dalilin da zaisa wani ya dibge cikin daki yana tunanin wai Garkuwa zai bar Jam’iyar APC saboda an hana shi tikitin takara. Ko dan saboda mutanan da Garkuwa ya kwashe shekaru yana hidimar siyasa dasu a cikin Jam’iyar APC kuma sun girma sun zama wasu cikinta bai kamata ace ya bar APC ba. Kai kodan Hon Malam Sani Aminu Dangamau kadai da yayi ruwa yayi tsaki wajen ganin Garkuwa ya samu nasara bai kamata wani yayi tunanin cewa Garkuwa zai iya barin APC ba. Irin gudunmuwar da Malam Sani Aminu ya bayar a wannan karon ko haihuwar shi Garkuwa yayi iyakar abinda zaiyi kenan, saboda haka Malam Sani Aminu yana da alfarma wajen Garkuwa kowace iri ce amma dai abinda ya kamata mutane su sani shine; dole ne Garkuwa ya mayar da raddi ko ba na kaitsaye ba ga duk wanda yake da hannu wajen hana shi takara saboda irin kiyayyar da aka nuna mashi ta kaitsaye. A siyasance idan akace ka lissafo makiyan Garkuwa dole sai ka hada da sunayen wadanda s**a hana shi takara.
Malam Sani Aminu zai iya cin alfarmar Garkuwa ta kowane fanni amma bangren masu ruwa da tsakin da s**a hanashi takara, sai ya yima Garkuwa da duk wani dan a mutun shi uzuri. Ka bugi mutum kuma kace kar yayi kuka? Ina da yakinin Garkuwa zaiyi APC ne a yanzu saboda yayi acknowledging gudunmuwar da Malam Sani Aminu ya bashi. Wannan shi ake cema hallaci.
A DAYAN BANGAREN
A dayan bangaren, a matsayin Malam Sani Aminu na shugaban Karamar Hukumar Kusada wanda ke amsar umarni daga Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, wajibin shine ya kare martabar gwamnatin matukar yana son ya zauna lafiya da ita amma kuma wannan bai kamata yasa mu mabiya bangarorin biyu mu kasa fahimtar juna ba. Bai kamata mu jirkitar da fahimtar ba zuwa son zuciyoyin mu. Shaidanun da s**a dawo daga wasu Jam’iyyun zuwa APC da kuma shaidanun dake cikin APC suna neman irin wannan damar domin su cigaba da taka rawar da s**a iya takawa. Idan shugabannin mu sun basu kofa to gidan zai rushe, a rasa matsugunni. Allah shi kyauta.
DAGA BANGARE NA
Bari mu dauki misali da karon kaina, zan iya kin Dr. Dikko Umar Radda saboda Abubakar Yahaya Kusada zan kuma iya son Dr. Dikko Umaru Radda saboda Malam Sani Aminu Dangamau. Dalili na farko al’umma ta shaida ni yaron Garkuwa ne kuma Garkuwa ya taimake ni, zan iya kin abinda yake ki zan kuma iya son abinda yake so. Dalili na na biyu kuma al’umma ta shaida Malam Sani Aminu amini na ne kuma yana mutunta ni yana taimakona yana kuma mutunta tare na dashi, zan iya yi mashi kara akan abinda yake so hakazalika zan iya yi mashi kara akan abinda yake ki.
ME NE NE MASALAHA A WANNAN BATUN
Masalaha a nan itace indai taba gwamnatin Dr. Dikko zai bama Malam Sani Aminu matsala a wajen aiwatar da mulkin shi, zabi biyu gare ni, zabi na farko, ko dai inyi shiru da bakina ko kuma in cigaba da yima Dr. Dikko Radda. fatan alkhairy. Dalilina akan hakan shine idan Malam Sani Aminu ya rasa kujerar shi ba mu san wa za’a turo ya mulki Karamar Hukumar ba kuma bamu kyauta mashi ba indai muka bari hakan ta faru dashi. Na tabbata shima Garkuwa wannan itace matsayar shi har a zuciyar shi duk dai banyi magana dashi akan wannan dambarwar ba.
Don Allah don girman Allah mu mutunta juna mu cigaba da zama al’umma daya masu kyautatama juna zato, masu son cigaban Karamar Hukumar mu ba masu son neman gindin zama ta hanyar shaidanci ba.
Amb Abubakar Kabir Kusada