14/07/2026
DA ƊUMI-ƊUMI: Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un! Allah Ya Yi Wa Hafiza Bahijjah Adam Rasuwa
Rahotanni sun nuna cewa Hafiza Bahijjah Adam, 'yar asalin jihar Kaduna, ta rasu, lamarin da ya jefa iyalanta, abokanta da al'ummar Musulmi cikin alhini.
An ce marigayiyar ta kasance daga cikin masu hidima ga Alƙur'ani Mai Girma, inda ta yi fice wajen karatu da koyar da Alƙur'ani, tare da barin kyakkyawan tarihi na ilimi da tarbiyya.
Lamarin ya jawo alhini a tsakanin al'ummar Musulmi, yayin da ake ci gaba da yi mata addu'ar Allah Ya jikanta da rahama.
Allah Ya jikanta da rahama. Wace addu'a za ku yi wa marigayiyar?
Ku shiga shafin jaridar ATV Hausa domin samun Sahihan Labarai.