16/08/2026
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gudanar da mulkin Kano ba abu ne mai sauƙi ba, saboda yawan al’ummarta da kuma kasancewarta jiha mai cike da mutane daga sassa daban-daban na Nijeriya. Ya ce saboda haka Kano tana k**a da “ƙaramar Nijeriya.”
Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ambassador Ibrahim Waiya, wanda ya wakilce shi a taron shekara-shekara na farko na Institute of Security and Strategic Studies (ISSS), inda aka karrama Gwamna Abba da lambar yabo ta ƙwarewa wajen tafiyar da harkokin tsaro.
Amira Reporters ta ruwaito cewa Waiya ya ce gwamnatin Kano ta rungumi dabarun tsaro na amfani da ƙarfi da kuma hanyoyin da ba na ƙarfi ba wajen yaƙi da rashin tsaro. Ya bayyana cewa an horar da kusan matasa 2,000, maza da mata, ƙarƙashin tsarin Neighbourhood Watch, sannan aka tura su cikin ƙananan hukumomi 44 domin taimaka wa hukumomin tsaro.
Ya kuma ce gwamnatin ta kafa Anti-Phone Snatching Corps, tare da shirin Safe Corridor, wanda aka tsara domin ƙarfafa matasan da ke shiga daba ko tashin hankalin siyasa su ajiye mak**ai su rungumi zaman lafiya. A cewarsa, an yi wa matasa kusan 340 rajista tare da tantance su a ƙarƙashin shirin, yayin da gwamnatin ta ware sama da Naira miliyan 500 domin gudanar da shi.
Da yake magana kan ƙalubalen shugabanci, Gwamna Yusuf ya ce Kano tana da yawan jama’a sosai kuma mutane daga sassa daban-daban na Nijeriya suna rayuwa a cikinta. Ya ce wannan yanayin ya sa gudanar da jihar ke buƙatar ƙoƙari da jajircewa sosai.
A nasa jawabin, masanin tsaro Dr Muhammad Ali ya yi kira ga ƙasashen Arewa maso Yamma da su ƙara haɗin gwiwa wajen yaƙi da ’yan bindiga, satar shanu, garkuwa da mutane, haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ma sauran laifuka. Ya kuma buƙaci gwamnonin jihohin Arewa maso Yamma guda bakwai su haɗa kai wajen musayar bayanan sirri da sintiri a iyakoki.
Me za ku ce?