Notifying.ng Hausa

Notifying.ng Hausa Shafin jaridar dake wallafa ingantattun labarai a cikin harshen hausa

Alhamdulillah, yau na ɗaya daga cikin lokutan da s**a fi taɓa zuciyata a rayuwa, domin na kaddamar da aikin gina sabon o...
11/08/2025

Alhamdulillah, yau na ɗaya daga cikin lokutan da s**a fi taɓa zuciyata a rayuwa, domin na kaddamar da aikin gina sabon ofishin Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC) a Dutsin Amare, Gabas II.

Wannan aiki ba daga kuɗin gwamnati ba ne. Sadaukarwa ce ta kaina, wacce na bayar a matsayin Sadaqatul Jariyah don tunawa da mahaifina, 𝐇𝐨𝐧. 𝐌𝐢𝐪𝐝𝐚𝐝 𝐀𝐃-𝐒𝐚𝐮𝐝𝐞 (Allah ya jikansa da rahama), mutum ne wanda rayuwarsa ta kasance abin koyi wajen hidima ga al'umma, gaskiya, da tsantsar jajircewa akan hidimar al’umma.

Mahaifina ya koya min cewa nagartaccen shugabanci ba-a-auna-shi da abinda mutum ya samu, a'a sai dai-abin-da-ya-bayar. A cikin girmamawa gare shi, ina roƙon Allah ya sanya wannan aiki ya zama alheri mai ɗorewa ya kai ladar gareshi, kuma ya tsare jama’armu har bayanmu, In shaa Allah. Dutsin Amare a Gabas II da sauran mazabu a cikin Karamar Hukumar Katsina za su ci gaba da kasancewa cikin tsaro, zaman lafiya, da haɗin kai In shaa Allah.

Ina kira ga matasanmu da su rungumi zaman lafiya, su zam ma su ladabi, girmamawa, da haɗin kai ga jami’an tsaro, domin zaman lafiya shi ne tubalin ginuwar ci gaba.

Allah Ya albarkaci Katsina.
Allah Ya albarkaci jiharmu mai albarka.
Allah Ya albarkaci ƙasarmu, Najeriya

Gwamna Malam Dikko Radda ya kaddamar da bude ofishin din-dindin na Gidauniyar Gwagware (Gwagware Foundation) tare da Kad...
12/03/2024

Gwamna Malam Dikko Radda ya kaddamar da bude ofishin din-dindin na Gidauniyar Gwagware (Gwagware Foundation) tare da Kaddamar da bada tallafin abinci da dinkin sallah na marayu

A ranar Litinin, 11 ga watan Maris 2024, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda, ya Kaddamar da bada tallafin kamar yadda aka saba duk shekara tare da bude ofishin gidauniyar na din-dindin dake akan hanyar zuwa Daura kusa da rukunin gidaje na makera.

Kayyakin da aka bayar sun hada da tirela 1 ta shinkafa da tirela 1 ta Gero tare da Masara, sai Kayyakin Sallah na yara marayu guda 4,000 da kayyakin makarantar na yara marayu su 3,000.

Da yake gabatar da jawabin shi Malam Dikko Radda ya yi godiya ga Allah wanda da ikon sa ne yasa shi ganin wannan rana domin sake gudanar da irin wannan tallafi mai mahimmanci.

Gwamnan ya bu'kaci masu hannu da shuni dasu taimakama wanda basu da shi watau mabukata da abinda Allah ya h**e masu wanda haka zai taimaka wajen kara rage rad'ad'in hali da al'umma suke ciki.

Daga karshe Malam Dikko Radda ya bu'kaci al'umma dasu yawaita addu'a a lokacin bud'e Baki domin neman afuwar Allah tare da neman gafara.

Har Ila yau, An karrama muhimman mutane da su ka assasa Gidauniyar tare da bada gudunmuwa domin habbaka ita gidauniyar.

Wadanda s**a tofa albarkacin bakin su sun hada da Shugaban Gidauniyar, Alh. Yusuf Ali Musawa, Minista ta al’adu da tattalin arziki na fasaha, Haj Hannatu Musa Musawa, Alh. Bilya Sanda, Mal Abu Ammar, Shugaban Hisba ta Jihar Kano, Mal Daurawa da sauran su.

Notifying.ng Hausa
12/3/2024

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda tare da takwaransa na jihar Nasarawa, Gwamna Abdullahi Sule, da ministan ...
11/02/2024

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda tare da takwaransa na jihar Nasarawa, Gwamna Abdullahi Sule, da ministan raya wasanni, Sanata John Enoh, sun tashi daga Filin jirgin saman Nmandi Arzkwe na kasa da kasa dake Abuja zuwa Cote d'Ivoire don halartar wasan karshe na gasar cin kofin Afrika da ake sa ran za a yi.

Gwamna Radda mamba ne na tawagar shugaban kasa, wanda aka dora wa alhakin bayar goyon baya ga Super Eagles ta Najeriya yayin da suke kokarin ganin sun samu nasarar lashe gasar cin kofin Afrika karo na hudu.

Notifying.ng Hausa
11/02/2024

Gwamnatin Jihar Katsina ta Hana Sayar da Fili a Cikin Kadarorin Gwamnati da Bayar da Filaye a Gaban Kadarorin Gwamnati t...
05/02/2024

Gwamnatin Jihar Katsina ta Hana Sayar da Fili a Cikin Kadarorin Gwamnati da Bayar da Filaye a Gaban Kadarorin Gwamnati tare da Tsaida duk Wani Rabon ƙasa ba Tare da Bin Ka'ida ba

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, ya yi zama na musamman da masu ruwa da tsaki akan Kasa da Tsare-tsaren Birane a fadin Jihar Katsina a ranar Litinin, 5 ga watan Fabrairu 2024 a fadar Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

A lokacin taron, Malam Dikko Radda ya bayyana dalilin kiran taron masu ruwa da tsaki domin shawo kan matsalolin tsare-tsare da kuma jaddada dokoki da Gwamnatin Jihar ta tanada domin tsara birane da filaye wanda a cewar shi rashin bin doka ya kawo ma Jihar cinkoso da matsaloli masu tarin yawa.

Gwamna Radda yace “ an sanar da gwamnati cewa wasu jami’an Kananan Hukumomi da masu rike da sarautu na gargajiya, ko dai a gefe guda ko kuma tare da hadin gwiwar wasu jami’an gwamnatin Jiha, suna yin watsi da dokokin da ake da su da kuma tsarin tafiyar da filaye ciki har da raba filaye ba bisa ka’ida ba da sauran hada-hadar kasuwanci da makamantan su.

Ya cigaba da cewa “ Dokar amfani da kasa (Land use act 1979) ta baiwa gwamnan jihar damar kula da duk wani fili na birni wanda ya hada da filayen da ke cikin kowace hedikwatar karamar hukuma da duk wani gandun dajin da ke kan gaba.”

A saboda da Haka Gwamnatin Jihar Katsina ta tsaida duk wani rabon ƙasa ba tare da bin ka'ida ba, yanke gandun daji ta kowace manufa, saida wani ɓangaren fili a cikin kadarorin gwamnati (wanda aka fi sani da curve-out) ko a cikin gidajen gwamnati da kuma bayar da filaye a gaban kadarorin gwamnati, a mafi yawan lokuta a matsayin kasafi na wucin gadi don shaguna da sauran abubuwan amfani.

Daga karshe Gwamna Radda ya shaida cewa “Duk abubuwan da s**a shafi ƙasa dole ne su bi ta Ma'aikatar Filaye da Tsare-tsare (Ministry of Lands and Physical Planning) sannan kuma Hukumar tsare birane ta Urban and Regional Planning Board zata kula da harkokin habbaka birane”

Za a sami hukunci mai tsanani ga duk wanda yayi watsi da wadannan Dokoki da gwamnati ta gindaya.

Taron ya samu halartar Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Hon. Faruk Lawal Jobe; Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Abdullahi Garba Faskari; Kwamishinan filaye da tsare-tsare, Dr. Faisal Umar Kaita; Kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautun Gargajiya, Orof. Badamasi Lawal Charanchi; Kwamishinan Muhalli, Hon. Musa Adamu Funtua; Dukkannin Hakimai na masarautun Katsina da Daura, Dukkannin Shugabannin Kananan Hukumomin Jihar Katsina, Dukkanin Daraktocin filaye da gandun daji na Jihar Katsina, Kungiyar Dillalai da sauran su.

Gwamna Dikko Radda ya Halarci Gangamin Yakin Neman Zaben Jam’iyyar APC na Kankara,Faskari, Sabuwa a mazabar GarakiMai gi...
01/02/2024

Gwamna Dikko Radda ya Halarci Gangamin Yakin Neman Zaben Jam’iyyar APC na Kankara,Faskari, Sabuwa a mazabar Garaki

Mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci taron rufe gangamin yakin neman zabe na Dan Majalisar Tarayya a mazabun Kankara, Sabuwa da Faskari, Hon. Shehu Dalhatu Tafoki a mazabar Garaki (Tsamiyar Jino) dake Karamar Hukumar Kankara ranar Alhamis, 1 ga watan Fabrairu 2024.

A lokacin gangamin, Gwamna Radda ya sha alwashin daukar jami’an sa kai na Community Watch Corps a mazabar Garaki cikin gaggawa domin ci gaba da bada kariya ga al’ummar wannan yanki. Bugu da kari, ya kuduri aniyar gina masu makarantar Sakandare duba da yadda suke fama da rashin makaranta ta sakandare. Ya kuma shaida masu albishir cewa za a gina masu rijiyoyin birtsatse domin samun wadataccen ruwan sha mai tsafta.

Daga karshe yayi kira a gare su da su zabi Jam’iyyar APC a zaben da zai gudana a ranar Asabar 3 ga watan Fabrairu 2024, saboda duk alkawarin da ya dauka a lokacin yakin neman zabe ya fara cika su a cikin dan karamin lokaci.

Taron ya samu halartar Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Hon. Faruq Lawal Jobe; Kakakin Majalisar Dokoki na Jihar Katsina, Rt. Nasir Yahya Daura; Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Barrister Abdullahi Garba Faskari; Shugaban Jam’iyyar APC na Jiha, Sani Aliyu Daura; Sanata Muntari Dandutse, Sanata Abdulaziz Musa Yar’Adua, Yan Majalisar Zartaswa na Jihar Katsina,Yan Majalisun Dokoki na Jihar Katsina,Shugabannin Kananan Hukumomi da sauran su.

Kotu ta ɗaure matar tsohon Firaministan Pakistan shekaru 14Kotu ta ɗaure matar tsohon Firaministan Pakistan Bushra Bibi,...
31/01/2024

Kotu ta ɗaure matar tsohon Firaministan Pakistan shekaru 14

Kotu ta ɗaure matar tsohon Firaministan Pakistan Bushra Bibi, shekaru 14 a gidan yari kan laifin siyar da kayayyakin gwamanti ba bisa ƙaida ba.

Ɗaure Bushra Bibi na zuwa ne kwana guda bayan ɗaure mijinta, tsohon Firaministan Pakistan Imran Khan, shekaru 10.

Tun da fari an zargi Imran Khan da laifin fitar da sirrin ƙasa, kafin daga bisani kotu ta tabbatar da zargin. Yanzu hukuncin na zuwa mako guda kafin gudanar da zaɓen ƙasar a 8 ga Fabrairu.

Notifying.ng Hausa
31/01/24

Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya ya kaddamar da Gwamna Dikko Radda da wasu 36 a matsayin kwamitin samar da sabon mafi ...
31/01/2024

Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya ya kaddamar da Gwamna Dikko Radda da wasu 36 a matsayin kwamitin samar da sabon mafi kankantar albashi a Najeriya

Mataimakin shugaban kasar Najeriya Kashim Shettima ya kaddamar da kwamitin mutum 37 da zai bayar da shawara kan sabon mafi kankantar albashi a kasar.

An rantsar da kwamitin ne wanda yake karkashin jagorancin tsohon shugaban ma'aikata na kasar, Bukar Aji , a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Talata, 30 ga watan 2024.

A jawabin da ya gabatar a wurin mataimakin shugaban kasar ya ce, kaddamar da kwamitin abu ne da ya tabbatar da alkawarin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi na inganta jin dadin ma'aikata.

Kwamitin wanda ya kunshi bangaren gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi da 'yan kwasuwa da kuma kungiyoyin kwadago zai bayar da sahawara ne kan abin da ya kamata a tsayar a matsayin sabon albashi mafi kankanta a kasar, inda a yanzu naira 30,000 ne.

Idan kwamitin ya mika shawararsa bangaren zartarwa zai mika ta a matsayin kudurin doka ga majalisar dokokin kasar domin samun amincewa.

Notifying.ng Hausa
31/01/2024

A woman from Saudi Arabia bought a signed football jersey of Cristiano Ronaldo, who plays for Al-Nassr, during an auctio...
30/01/2024

A woman from Saudi Arabia bought a signed football jersey of Cristiano Ronaldo, who plays for Al-Nassr, during an auction for $125,000. The auction took place at a dinner party related to the Diriyah ePrix event.

The bidding for Ronaldo's shirt started at $77,500 and quickly increased. The auctioneer encouraged bidders until it reached $125,000, and a woman from the business community made the final bid. Cristiano Ronaldo joined the Saudi Pro League team Al-Nassr in January 2023.

Notifying.ng Hausa
30/01/24

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, ya kasance babban bako mai jawabi a taron kwana biyu kan matsalar t...
24/01/2024

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, ya kasance babban bako mai jawabi a taron kwana biyu kan matsalar tsaro a arewacin Najeriya mai taken “matakai da dama na magance matsalar tsaro a arewacin Najeriya” da ya faru a cibiyar samar da tsaro ta sojoji dake Birnin Tarayya Abuja.

A yayin taron, Gwamna Radda ya jaddada muhimmancin hadin kai a yankin Arewa maso Yamma wajen yaki da matsalar rashin tsaro da ta addabi yankin Arewacin Najeriya.

Gwamnatin Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umaru Radda PhD za ta dauki nauyin karatun dalibai 41 zuwa kasar Masa...
21/01/2024

Gwamnatin Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umaru Radda PhD za ta dauki nauyin karatun dalibai 41 zuwa kasar Masar don karatun likitanci

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD Zai Kaddamar Da Shirin daukar nauyin karatun dalibai 41 zuwa Kasar Masar da za su yi karatun digiri na farko a likitanci (Medicine) a jami’ar Kasar ta Nahda University, Cairo.

Bikin kaddamar da shirin da kuma ba da takardun shaidar shiga jami'a na 'admission letter' zai gudana ne a fadar Gidan Gwamnatin Jihar Katsina a ranar Litinin, 22 ga watan Janairu 2024 da misalin karfe 10:00am na safe.

Wannan yunkurin na daga cikin kudirin Gwamna Malam Dikko Umaru Radda wajen ganin 'ya'yan talakawa sun samu Ilimi ingantacce da kuma shawo kan karancin likitoci a Jihar Katsina.

Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci daurin auren yar gidan Gwamnan jihar Kebbi wanda ak...
20/01/2024

Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci daurin auren yar gidan Gwamnan jihar Kebbi wanda aka daura jiya a garin Birnin Kebbi.

Daurin auren ya samu halartar yan kwamitin gudanarwa na jam'iyar APC na kasa, da Gwamnonin jihohin Borno, Zamfara, Sokoto, Kaduna, Jigawa, Nasarawa, da kuma ministoci da sauran manyan jami'an Gwamnatin Tarayya .

Cikin Hotuna:Kanwan Katsina kenan hakimin Ƙetare Alhaji Usman Bello Ƙankara mni da yake zantawa da shugaban 'Yanjarida n...
20/01/2024

Cikin Hotuna:

Kanwan Katsina kenan hakimin Ƙetare Alhaji Usman Bello Ƙankara mni da yake zantawa da shugaban 'Yanjarida na jihar Katsina, Comrade Tukur Hassan Dan-Ali a wajen laccar da ƙungiyar ta shirya domin tunawa da marigayi Sir Ahmadu Bello a ranar Litinin ɗin da ta gabata 15 ga watan Janairu 2024.

Address

Garu Musawa
Katsina
833101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Notifying.ng Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Notifying.ng Hausa:

Share