Rana24

Rana24 Domin Samun Labaru Masu Sahihanci Kasance da Jaridar Rana24 akoda yaushe. Muna Maraba da kowa da kowa. VISION:
To be a best print and online world newspaper.
(1)

JARIDAR RANA24 MULTIMEDIA AND COMMUNICATION SERVICES:
_______________________________________
Rana24 is an independent online newspaper which is outlet of RANA24 MULTIMEDIA AND COMMUNICATION SERVICES. We conduct research and investigations before publish the news in order to develope,promote peace, and report fearlessly on insecurity and terrorism in Nigeria and Africa. MISSION:
Always to dissemi

nate credible information to the general public. PRODUCTS:
Rana24
Rana24. Katsina Facts. Supreme News. Arewa Plus

E-MAIL:
[email protected]
[email protected]
[email protected]
[email protected]. TEL:
07032340606

Gina Gidan Biredi Yafi Gina Masallaci Amfani Awurin Mutane...........Cikakken bayani na Comment Section👇
03/01/2026

Gina Gidan Biredi Yafi Gina Masallaci Amfani Awurin Mutane...........

Cikakken bayani na Comment Section👇

Amadadin Shugaban Kamfanin Jaridar Rana24 da sauran masu taimakawa wajen kawo masu sahihan labaru. Muna farin cikin isar...
03/01/2026

Amadadin Shugaban Kamfanin Jaridar Rana24 da sauran masu taimakawa wajen kawo masu sahihan labaru. Muna farin cikin isar da sakon murnar shigowar mu cikin sabuwar shekarar 2026 miladiyya ga Hon. Hassan Sufiyanu Yargoje Ksmsilan Mazabar Danmaidaki A Karamar Hukumar Kankara jigar katsina.

Muna fatan alheri gareku mabiya mu, kune abin alfaharin mu.

CEO RANA24
Mannir Idris

Da Dumi Dumi: Masu garkuwa da mutane sun nemi Naira miliyan 450 domin sakin Sarkin Kwara.Masu garkuwa da mutane sun nemi...
03/01/2026

Da Dumi Dumi: Masu garkuwa da mutane sun nemi Naira miliyan 450 domin sakin Sarkin Kwara.

Masu garkuwa da mutane sun nemi kuɗin fansa na Naira miliyan 450 domin sakin Sarkin Kwara, Oba Simeon Olaonipekun, ɗansa, da wasu mazauna yankin su takwas da aka sace.

Menene ra'ayin ku?

A Siyasar Kano Idan Kaji Ance " Aci Dadi Lafiya" Me Hakan Ke Nufi?
03/01/2026

A Siyasar Kano Idan Kaji Ance " Aci Dadi Lafiya" Me Hakan Ke Nufi?

03/01/2026

Akwai Yuyuwar Sen. Rabiu Kwankwaso Fice Daga Jam'iyyar NNPP ✋

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zai shiga jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance a ranar Litinin, kamar yadda DAILY NIGER...
03/01/2026

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, zai shiga jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance a ranar Litinin, kamar yadda DAILY NIGERIAN ta rawaito.

Abba Yusuf, wanda shi kaɗai ne gwamna a jam’iyyar NNPP, ya riga ya isa Abuja domin kammala shirye-shiryen sauya shekar tasa.

Majiyoyi da ke da masaniya kan shirin sauya shekar gwamnan sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Yitwalda Nentawe, ne za su karɓi gwamnan a Abuja.

Tuni dai an dawo da jagoran APC a Kano, Abdullahi Ganduje, daga wata tafiya da yake yi a Dubai. Haka kuma an umarci shugaban jam’iyyar APC na jihar, Abdullahi Abbas, da ya taƙaita tafiyarsa ta Umara domin ya miƙa katin zama ɗan APC ga gwamnan a mazabarsa ta Diso, da ke Karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano, a cikin makon nan.

Sabon Haraji Zai Jefa Ƴan Najeriya Cikin Baƙar Wahala, Cewar Peter ObiTsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, ...
02/01/2026

Sabon Haraji Zai Jefa Ƴan Najeriya Cikin Baƙar Wahala, Cewar Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya yi gargaɗin cewa sabon tsarin haraji da Najeriya ta fara amfani da shi zai ƙara tsananta wahalar rayuwa da ’yan ƙasa ke ciki.

Ya ce ba za a samu ci gaba a ƙasa ba ta hanyar ƙaƙaba wa talakawa haraji.

A wata sanarwa da ya wallafa a ranar Juma’a, Obi ya ce dole ne tsarin haraji ya kasance na adalci, gaskiya da kuma kula da jin daɗin jama’a.

Ya bayyana cewa shugabanni na gari s**an gina amana ta hanyar gaskiya da bayyana komai a fili ga al’umma.

“Ba za ka iya fita daga talauci ta hanyar ƙaƙaba haraji ba; sai dai ta hanyar samar da abin yi. Haraji a kan talakawa yana ƙara jefa su cikin wahala,” in ji Obi.

Obi ya kuma nuna damuwa kan rahotannin da ke nuna matsaloli a tattare da dokokin haraji.

Ya bayyana cewa bai dace a tilasta wa ’yan ƙasa biyan karin haraji ta hanyar da ba ta fayyace komai ba.

Ya ce dole ne a bi doka tare da sanar da jama’a a fili kan yadda komai ke ƙunshe cikin dokokin.

“Babu wani abun alfahari a samun ƙarin kuɗin shiga na gwamnati alhali jama’a na ƙara faɗa wa cikin talauci,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa a lokuta da dama ana buƙatar ’yan Najeriya su biya haraji ba tare da fahimtar yadda za a yi amfani da kuɗin ba ko ganin amfaninsa a rayuwarsu ba.

A cewarsa, rashin bayyana gaskiya kan haka na rage amincewa tsakanin gwamnati da jama’a.

Obi, ya ce ya kamata gwamnati ta mayar da hankali wajen ƙarfafa ƙananan da matsakaitan ’yan kasuwa domin samar da ayyukan yi, ƙara kuɗin shiga, da faɗaɗa tushen haraji.

Ya kammala da kira ga samar da tsarin haraji na gaskiya da zai kula da talakawa tare da ƙarfafa haɗin kai da ci gaban ƙasa.

Majiya: Aminiya

Yadda Jagora Kwankwasiyya Dr  Rabiu Musa Kwankwaso yake jagorantar taro na musamman tare da jagororin Kwankwasiyya na Ka...
02/01/2026

Yadda Jagora Kwankwasiyya Dr Rabiu Musa Kwankwaso yake jagorantar taro na musamman tare da jagororin Kwankwasiyya na Kananan Hukumomi 44 dake Jihar Kano.

Wani Jirgi Mara Matuki (Drone) Ya Sake Faduwa A Dajin Kontagora Dake Jihar Neja A Yammacin Yau Juma'a
02/01/2026

Wani Jirgi Mara Matuki (Drone) Ya Sake Faduwa A Dajin Kontagora Dake Jihar Neja A Yammacin Yau Juma'a

Iran ta gargadi shugaban Amurka Donald Trump game da yin katsalandan a zanga-zangar da ta barke kan faduwar darajar kudi...
02/01/2026

Iran ta gargadi shugaban Amurka Donald Trump game da yin katsalandan a zanga-zangar da ta barke kan faduwar darajar kudin kasar.

Wannan na zuwa ne bayan da Shugaba Trump ya bayyana yiwuwar tura sojojin Amurka zuwa Iran domin kare masu boren.

A cikin wani sako, mai ba wa shugaban addinin Iran shawara, ya ja kunnen Trump game da yunkurin shiga sharo ba shanu.

Jaridar Rana24 na isar da sakon barka da Juma'ar Farko a Sabuwar shekarar 2026 ga daya daga cikin mabiyan ta Hon. HADIZA...
02/01/2026

Jaridar Rana24 na isar da sakon barka da Juma'ar Farko a Sabuwar shekarar 2026 ga daya daga cikin mabiyan ta Hon. HADIZA HASSAN MAIKUDI

Muna godiya Da kulawa da kuke nuna mana.

DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta ƙone wani ɓangare na gidan cin abinci Cake Hot Restaurant da ke wurin shaƙatawa na River Plate P...
02/01/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta ƙone wani ɓangare na gidan cin abinci Cake Hot Restaurant da ke wurin shaƙatawa na River Plate Park, Wuse a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Majiyar Karaduwa Post, Jaridar Arewa Updates ta rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, DCF P.O. Abraham, ya fitar, inda ya bayyana cewa gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 12:23 na dare.

Sanarwar ta ce jami’an kashe gobara sun isa wurin cikin gaggawa, inda s**a dakile wutar kafin ta yaɗu zuwa sauran sassan wurin shakatawar.

Sanarwar ta ƙara da cewa an samu ceton dukiya da aka kiyasta kimarta ta kai Naira biliyan 1.5, yayin da asarar da gobarar ta haifar ta tsaya a kusan Naira miliyan 500, ba tare da asarar rai ko jikkata ba.

Binciken farko ya nuna cewa gobarar na da alaƙa da abubuwan da aka jefa yayin shagulgulan sabuwar shekara, lamarin da ya sa hukumar kashe gobara ta sake jan hankalin jama’a da su guji amfani da wasan wuta da kyandira, musamman a lokacin sanyi.

Arewa Updates ta rubuta muku wannan labari da taimakon fasahar AI.

Address

Katsina
KATSINA

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rana24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rana24:

Share