Muryar Hausa

Muryar Hausa Domin kawo maku sahihan Labarai a cikin harshen hausa daga ko ina a fadi kasa Najeriya da ma duniya baki daya.


@[282807705155462:0] News online

Allah ya jikan maza.An haifi Malam Umaru Musa Yar’Adua a ranar 16 ga watan August 1951,  ya kuma koma wajen mai mulkin d...
05/05/2025

Allah ya jikan maza.

An haifi Malam Umaru Musa Yar’Adua a ranar 16 ga watan August 1951, ya kuma koma wajen mai mulkin da ba ya da karshe a ranar 5 ga watan May 2010, yau shekara 7 daidai da rasuwarsa kenan .
Kamin shigar Malam Umar Musa jam’iyyar PDP ya fara da jam’iyyar PRP sannan daga bisani ya koma jam’iyyar SDP a shekarar 1989 zuwa 1998. Bayan nan ya shiga jam’iyyar PDP a shekarar 1998 zuwa 2010.
A ta bangaren iyali kuwa Malam Umar Musa ya auri matarsa ta farko Hajiya Turai Yar’Adua (1975–2010), sai kuma Hajiya Hauwa Umar Radda (1992–97), ya kuma rasu ya bar ‘ya’ya guda tara (9).
A ta fannin ilimi kuwa Malam Umaru Musa Yar’Adua ya halarci makarantar Barewa College, da kuma jami’ar Ahmadu Bello dake Zaria.

Malam Umar Musa ya yi gwamnan jihar Katsina har karo biyu tun daga 29 May 1999 har zuwa 28 May 2007.
Ya ci zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 21 ga watan Aprilun 2007 inda aka kuma rantsar da shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya a ranar 25 ga watan Mayun 2007, a karkashin tutar jam’iyyar PDP .
Bayan nan Allah Ya jarabce shi da rashin lafiya a lokacin yana shugabantar kasar nan, in da aka wuce da shi wani asibiti dake kasar Saudi Arabia, bayan ya dan samu sauki aka dawo da shi gida Nijeriya a ranar 24 ga watan Febrerun 2010, Allah kuma Ya yi masa rasuwa a ranar 5 ga watan May 2010.
1. Malam Umar mutum ne mai son gaskiya komin dacinta koda kuwa a kansa fadin gaskiyar ya k**a, k**ar yadda ya bayyana cewa zabubbukan da aka yi a baya akwai ‘yan kurakurai, kuma za a gyara, daga cikin gyaran da ya yi ne ya dakko Malamin Jami’a Farfesa Attahiru Jega ya nada shi shugabancin hukumar zabe mai zaman kanta, wanda sanin kowa ne an samu canji matuka a fannin zabe.
2. Malam Umar Musa mutum ne mai rikon amana, tattare da 3kishin al’amura

Arewa Dai Baza'a barmi mu zauna lafiya ba Amma Allahu shine Gatanmu.An sake samun tashin wani abin fasshewaa a kan hanya...
12/04/2025

Arewa Dai Baza'a barmi mu zauna lafiya ba Amma Allahu shine Gatanmu.

An sake samun tashin wani abin fasshewaa a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa ɗazu-ɗazun nan a jihar Borno, inda ya yi sanadiyar mutùwar mutane 8 tare da jikkata wasu da dama.

Wannan ya faru ne kanwani musayan kalamai tsakanin Ministan Yaɗa Labarai Muhammad Idris da gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum kan halin da jihar ke ciki na bar@zanar sake daw0war B0k0H@ram.

Allah kayi mana maganin Abun da bazamu iyaba.

Da ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta ki amincewa da takardar neman Belin Shahararren Mawakin Asharalle Alh. Surajo Mai Asharalle, in...
12/04/2025

Da ɗumi-ɗuminsa: Kotu ta ki amincewa da takardar neman Belin Shahararren Mawakin Asharalle Alh. Surajo Mai Asharalle, inda Alkalin Kotun ta 10 dake a Jihar Katsina, ya bukaci a cigaba da tsaron Mawakin, a Gidan gyaran hali har ya zuwa lokacin da Kotun za ta cigaba da sauraren Ƙarar.

A wata zantawa da Wakilin Gidan Radiyon Katsina ya yi da Lauyan wanda ake tuhuma Barista Muhammad Muktar Lawal ya bayyana cewa, sun bukaci Kotun da ta bada Belin wanda ake Tuhumar Alh. Surajo Mai Asharalle tare da wasi Yaran sa guda biyar, sai dai Kotun bata amince da takardar bukatar ta su ba, inda suke sauraren wata ranar da Kotun zata sake sanya wa, domin cigaba da Shari'ar.

12/04/2025

INNALILLAHI WAINNALAIHI RAJI'UN

Yanzu jami'an Hukumar Custom sun kashe Mutum 1 tare da jikitta Mutum 2 a ƙaramar Hukumar Mai'adua

Kashi 80 cikin 100 na Alumar Bauchi sun halarci jana'izar Sheikh Dr. Idris Dutsen Tanshi.Muma addu'ar Allah ya jaddada R...
04/04/2025

Kashi 80 cikin 100 na Alumar Bauchi sun halarci jana'izar Sheikh Dr. Idris Dutsen Tanshi.
Muma addu'ar Allah ya jaddada Rahama gare sa.

04/04/2025

Allah ya gafarta wa Dr. Idris

03/04/2025

Me kuka fahimta a nan ?

KWAMANDAN YAKISarkin Yakin Nigeria DCP Abba Kyari babban Kwamandan rundinar IRT ya sadaukar da rayuwarsa, ya shiga inda ...
03/04/2025

KWAMANDAN YAKI

Sarkin Yakin Nigeria DCP Abba Kyari babban Kwamandan rundinar IRT ya sadaukar da rayuwarsa, ya shiga inda ya gagari har Sojoji shiga, ya k**a 'yan ta'addan da s**a gagari hukumomin tsaro kamuwa

A lokacin da DCP Abba Kyari yake bakin daga, ya kan tashi da tsakar dare ya nufi hanyar Kaduna hanyar da a wancan lokaci ake mata lakabi da tarkon mutuwa, duk wani dan ta'addanci a Nigeria idan yaji an ambaci sunan Abba Kyari sai hantar cikinsa ta kada

DCP Abba Kyari ne ya kawo karshen rundinar 'yan B0K0 Ha'r@m masu tsara harin b0m a yankin Arewa, ya shafe a kalla watanni shida yana hada bayanan sirri akan motsinsu, ya k**asu a tsakanin kwanaki biyu

A Nigeria kowa yaji ya gani irin kokari da jajircewan da DCP Abba Kyari yayi domin tabbatar da tsaron Kasar nan

Amma saboda tsabagen cin amana ku kalli irin sak**akon da aka masa, an boyeshi a gidan yari

Munyi imani da Allah wannan sadaukarwa da DCP Abba Kyari yayi ba zai taba tafiya a banza ba

Ubangiji Allah Ka bashi mafita na alheri

Fiitaccen Ɗan Bindiga Kachalla Isuhu Yellow An Kashe Shi A Zamfara Tare Da Hare-haren Da Ya Kai.Sarautar Kachalla Isuhu ...
27/03/2025

Fiitaccen Ɗan Bindiga Kachalla Isuhu Yellow An Kashe Shi A Zamfara Tare Da Hare-haren Da Ya Kai.

Sarautar Kachalla Isuhu Yellow, fitaccen kwamandan ‘yan bindiga kuma kanin Ado Alero, ta ƙare a yau bayan wasu ƴan bindiga masu biyayya ga Dogo Gide sun kashe shi a kasuwar Dan Jibga da ke karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara. Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa kafin kashe shi, an yi fafatawa tsakanin ‘yan ta’adda da dakarun tsaro na Operation FANSAN, Hybrid Forces, da ‘yan banga a kauyen Keita da misalin karfe 7:00 na safe. A yakin, an kashe ‘yan bindiga tara (9), yayin da jami’an tsaro uku s**a mutu.

Kachalla Isuhu Yellow ya samu raunuka a harbin kuma ya tsere. Daga baya, bayan an gano cewa yana boye a wani shago a kasuwar Dan Jibga, wasu ƴan bindiga s**a kai hari s**a kashe shi. Kisan ya zo ne bayan rikici da ya barke tsakaninsa da wani shugaban ‘yan bindiga, Kachalla Bakin Sifindi. A ranar 25 ga Maris, 2025, Isuhu Yellow ya kashe Bakin Sifindi da daya daga cikin abokansa a wajen Sabon Birni. Dogo Gide, wanda ake ganin shi ne babban shugaban ‘yan bindiga a Zamfara da Neja, ya dauki kisan Bakin Sifindi a matsayin hari kai tsaye. Don haka, ya tura mayakansa domin farautar Isuhu Yellow, wanda ya kai ga kashe shi a yau.

Isuhu Yellow ya kasance daya daga cikin manyan ‘yan bindiga da s**a yi sanadiyar tashin hankali a Arewa maso Yammacin Najeriya, musamman a jihohin Zamfara da Katsina. Kisan nasa na iya zama farkon sabon yanayi a fagen ta’addanci a yankin.

Ango da amarya idan kunga dama ku zauna lapiya nidai nayi abinda yakawo ni wajen bikin -  Inji mawaki Abba Danjuma Coppe...
05/01/2025

Ango da amarya idan kunga dama ku zauna lapiya nidai nayi abinda yakawo ni wajen bikin - Inji mawaki Abba Danjuma Copper

Address

Katsina
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share