Muryar Hausa

Muryar Hausa Domin kawo maku sahihan Labarai a cikin harshen hausa daga ko ina a fadi kasa Najeriya da ma duniya baki daya.


@[282807705155462:0] News online

Innalillahi Wainna Ilaihirrajuun.Wannan Shine Kosan Waka Wanda Yayi Wakar Abba Kacika Gwarzo,Yau Gashi Allah Ya Jarabces...
26/07/2026

Innalillahi Wainna Ilaihirrajuun.
Wannan Shine Kosan Waka Wanda Yayi Wakar Abba Kacika Gwarzo,Yau Gashi Allah Ya Jarabceshi Da Matsanan Cín Rashin Lafiya Ance ko Magana Baya Iyayi, Yanzu Haka Gwamnan Jihar Kano yaje duba jikin nasa ne Amma sai hawaye yakeyi Baya Iya Cewa gwamnan Komai.

Lallai Mutane mukula Da Duniyar Nan Allah Zai iya tsaida Komai naka Lokaci Guda.

Daga Abdullahi Dahiru.


Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Kuma Tsohon Jakadan Najeriya A Ƙasar Saudiyya Alhaji Abdullahi Garba Aminchi Aka...
13/07/2026

Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Kuma Tsohon Jakadan Najeriya A Ƙasar Saudiyya Alhaji Abdullahi Garba Aminchi Akan Hanyar Sa Ta Zuwa Ƙasar Masar Domin Neman Lafiya.

Barrister Auwal Adam Ingawa ya rubuta. Kowa yana kallon Abu ne dai dai wayewarsa da kuma ilmin da Allah ya h**e masa. A ...
23/06/2026

Barrister Auwal Adam Ingawa ya rubuta.

Kowa yana kallon Abu ne dai dai wayewarsa da kuma ilmin da Allah ya h**e masa.

A mahanga ta doka ya k**ata hankalin mai saran kaba ya koma ga rina.

Abubuwa da yawa suna faruwa amma sai hankali ya gushe wajen gano musabbabin abinda ke faruwa.

Case ɗin wannan baiwar Allah ya tayar min da hankali kwarai dagaske.

Abinda yafi bani tsoro shine yadda al'umma s**a nuna ƙarara da rashin yadda da hukuma wajen ɗaukar mataki game da matsalolin rayuwarsu.

Da ace al'umma sun gamsu cewa jami'an tsaro za suyi abinda ya k**ata, to da ina tabbatar maku da cewa da wannan abin bai faru ba.

Wannan abin shine era mafi haɗari da muke ciki, kuma ban cire ma kowa hula ba indai muka cigaba a haka to kowa zai iya zama victim.

Kwanan a karamar Hukumar Ingawa dake a Jihar Katsina muka ga Yadda al'umma s**a k**a ɓarayin machine aka kashe kuma aka qona.
In a normal society ana Mika mai laifi wajem hukuma domin yanke masa hukunci, amma saboda al'ummar basu yadda da adalcin hukuma ba s**a kwammace su ɗauki doka a hannunsu.
Yau gashi a jihar Kaduna al'umma sunje da kansu sun kwato wadda ake zargi daga hannun hukuma kuma sun hukunta ta da kansu kan abinda basu tabbatar ba.

A dazu nake karanta wani artabu da ya fari tsakanin jami'an tsaron farin kaya da mutanen sawore, inda s**ayi turjiya s**a hana DSS tafiya dashi saboda Court ba abinda ta bada umarni ba kenan.

Indai hukumar tsaro a ko wane mataki na ƙasar nan ba za su mike tsaye wajen tabbatar da adalci ba, to ina tabbatar maku babu wani shafaffe da mai.

Ya k**ata mufarka.

Allah ya jikan ta ya gafarta mata.

Innalillahi wainna ilaihi Rajiun!sun kashe Malamar Islamiyya, Magidanciya, agaban hukuma, agaban Malamanta agaban Mutane...
21/06/2026

Innalillahi wainna ilaihi Rajiun!
sun kashe Malamar Islamiyya, Magidanciya, agaban hukuma, agaban Malamanta agaban Mutane, sabidda zargin da babu tabbaci akai.

Malama Ummulkhairi ta fito gida daga sabon Garin Maraban Jos zuwa yankin tsohuwar Maraba domin sauraran muhadara da su Malam Umar waliy (Mahaifina) s**a shirya, a makarantan Malama mardiyya (Mad. Tashiyhul Iman)

Sabidda abokan tafiyanta sun wuceta, ita kuma bata gane makarantar ba, ta tambayi yara su nuna mata, sai wasu mata s**a zargeta da laifin satan yara, bayan matasa sun taru, aka samu aka kaita police station, wakilin mijinta da babammu sun iso domin bada shaida akan cewa malama ce mai karantarwa ansanta kuma babu shaida akan zargin da ake mata.

Matasan basuji ba, ƴan sanda kuma s**a ce an basu umarni da cewa afitar da ita daga station ɗin safidda tention da pressure na matasan.

Matasan s**a aikata abinda s**a aikata, agaban jama'a, agaban police station, Malam yana basu haquri yana magiya, ƴan uwa dake wajen ma haka, amma matasan basuji ba, s**a ma Malama kisan gilla, s**a ƙona, s**a ɗauki mashin ɗin Malam s**a ƙona tare da ita.

Yanzu Idan Mahaifiyarka ne ya zakaji?
Ka san tana da yara sama da biyar?

Lokacin da mijinta ya iso daga inda yake hayaƙi kawai ya hango? Ya barta lafiya agida, sunyi bankwana zata tafi wajen wa'azi? Yanzu idan kaine ya zakaji?

Me ya samu Al'ummarmu ne haka?
A haka ƙasarmu zata zauna lafiya matasa suna irin wannan ɗanyen aikin?

Allah ya gafarta ma Malama Ummulkhairi, ya karɓa shahadanta, yabamu haqurin rashinta.

Ni; Allah na gode maka da ka ke bayyana hakikanin fuskar mutanenmu na Arewa

Ukasha Umar.
21/06/2026.

DANGOTE yafi kowa kudi a Africa, Amma abinda ake zargin Mele kyari da sacewa ya linka dukiyar DANGOTE SAU 4Abinda Dangot...
11/06/2026

DANGOTE yafi kowa kudi a Africa, Amma abinda ake zargin Mele kyari da sacewa ya linka dukiyar DANGOTE SAU 4

Abinda Dangote ya mallaka $36.5B

Abinda mele kyari ya Sace $154B

Yanzu idan DANGOTE yanason tara wannan dukiyar seya linka nemansu sau 4, sai Dukiyarsa ta linka sau hudu 😭

Banajin Akwai kasar da Da*bbobi suke jagorantarta irin Nigeria.

Akwai Videon Mallam Sadiq pharmacy dana gani...

Yace Wallahi Nigeria tafi dubai kudi, yace tafi Saudiyya kudi...

Yace wallahi akwai mutum daya a Nigeria da yasace kudi, kudin dayafi trillion 100...

Lokacin danaga videon kawai dana tuna yawan kuɗin ban gamsu ba, Ashe malam ya takaita ne ma 🙆

Write Mallam Auwall

Maganar gaskiya Kwankwaso kowa ya shaida mutum ne mai son cigaban al'umma da kuma gina ta , musamman ma ga 'ya'yan talak...
15/05/2026

Maganar gaskiya Kwankwaso kowa ya shaida mutum ne mai son cigaban al'umma da kuma gina ta , musamman ma ga 'ya'yan talakawa a fannin ilimi.

Amma maganar gaskia a wannan lokacin ya zaɓi son ranshi fiye da abinda yafi dacewa ya dauki son ranshi ya ajiye cancanta,abinda ake fata na chanjin wannan azzalumar gwamnatin,

Haɗuwar Atiku, Peter Obi , El-Rufai ,da kuma shi kwankwason ta bamu ƙwarin gwiwa da kuma hasashen indai wannan haɗin ya tsaya toh kawar da APC kawai lokaci ne ya rage ,amma ya tashi ya fice tare da hadisin cewa wai sunga matsala siyasar nan fah a fili take yasan dai shi da Obi shiririta ce kawai zasu yi amma babu wani zaɓe da zasu iya ci.

Indai kwankwaso ba Tinubu ne ya aiko shi ba toh ya k**ata ya koma ADC ayi dashi in kuma ba haka bane toh ya k**ata ya jaddada kallon da ake masa na mai son kishi da cigaba na mutane musamman Arewa toh ya k**ata ya koma.

Inji Comrd Umar Musa Tukur II

Sponsored:Assalamu alaikum jama'ar ƙaramar hukumar Ingawa.Da godiya ga Allah da kuma neman goyon bayan al’umma, na tsaya...
12/05/2026

Sponsored:

Assalamu alaikum jama'ar ƙaramar hukumar Ingawa.

Da godiya ga Allah da kuma neman goyon bayan al’umma, na tsaya takarar kujerar Majalisar jiha ta Ingawa Katsina domin in wakilce ku da gaskiya, adalci, da ci gaban al’umma.

Burina shi ne in kasance muryar talaka, ga matasa, mata, da dukkan jama’ar ƙaramar hukumar mu. Ina son ganin an samar da ingantaccen ilimi, lafiya, aikin yi ga matasa, da kuma ci gaban noma da kasuwanci.

Wannan tafiya ba tawa kaɗai ba ce—ta mu ce baki ɗaya. Ina roƙon addu’o’inku, shawarwarinku, da goyon bayanku domin mu gina makoma mafi alheri tare.

Lokaci ya yi na sauyi na gaskiya. Lokaci ya yi na aiki, ba alkawari kawai ba.

Nagode sosai. Allah Ya albarkaci Ingawa, Allah Ya albarkaci Jihar Katsina, Allah Ya albarkaci Najeriya.

Hon saifullahi Umar


da Amana

Innalillahi wa inna ilaihir rajiun Allah ya yiwa Alh surajo Mai asharalle katsina rasuwa.Allah ya jikan sa.
30/04/2026

Innalillahi wa inna ilaihir rajiun Allah ya yiwa Alh surajo Mai asharalle katsina rasuwa.
Allah ya jikan sa.

AKWAI MATSALASashi na 376 na Kano State Shariah Penal Code Law 2000 ya haramta bude gidajen c**a a jihar Kano kuma ya ka...
15/04/2026

AKWAI MATSALA

Sashi na 376 na Kano State Shariah Penal Code Law 2000 ya haramta bude gidajen c**a a jihar Kano kuma ya kaiyade hukuncin shekara 5 a gidan yari, ko bulala 30 ko tarar N500,000 ga duk wanda aka k**a yana yi ko bude gidan c**a.

Amma yanzu haka a Kano gidajen c**an da s**ayi shuhra a kudancin Nigeria suna ta bude santoci a Kano e.g BetNaija, Betking da sauran su.
Kuma samarin mu da alama sun karbi wannan harka matuka saboda tururuwar da suke yi a wadannan wurare.

Saboda haka lallai ya k**ata yan Hisba, yan sanda da sauran al'umma su tashi tsaye. C**a musiba ce babba ga al'umma.

Allah ya tsare mu Baki daya.

Address

Katsina
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share