21/01/2026
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da wasu muhimman matakai guda biyar da gwamnatinsa za ta ɗauka domin tallafa wa Malam Haruna, mahaifin matar da ƴaƴansa shida da aka kashe a unguwar Chiranci Dorayi a Kano.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar bayan ziyarar ta’aziyya da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kai wa iyalan marigayan.
Ga abubuwa biyar da Gwamnan ya yi wa Malam Haruna:
1. Kujerar Umrah shi da ɗan’uwansa
Gwamnan ya amince da ɗaukar nauyin tafiyar Umrah ga Malam Haruna tare da ɗan’uwansa, a matsayin tallafin jin kai da kuma ƙarfafa masa zuciya bayan mummunan abin da ya same shi.
2. Kujerun Hajji shi da ɗan’uwansa
Baya ga Umrah, Gwamnan ya kuma amince da ba Malam Haruna da ɗan’uwansa kujerun Hajji, wanda gwamnati za ta ɗauki nauyin tafiyar gaba ɗaya.
3. Gina masa sabon gida a wata unguwa
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da umarnin a gina wa Malam Haruna sabon gida a wata unguwa daban, domin taimaka masa ya fara sabuwar rayuwa nesa da wurin da lamarin ya faru.
4. Ɗaukar nauyin sake yin aurensa
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar Kano za ta ɗauki nauyin sake aurar da Malam Haruna idan ya samu mace ta gari, tare da kula da dukkan buƙatun da s**a dace.
5. Tabbatar da ɗaukar nauyin shari’a
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin cewa gwamnatin jihar za ta tabbatar da ganin an gaggauta shari’ar lamarin, domin a hukunta duk wanda aka samu da laifi.
Gwamnan ya kuma tsine wa waɗanda s**a aikata wannan mummunar ta’asa, inda ya jaddada cewa ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen sanya hannu kan duk hukuncin da kotu za ta yanke a kansu, matuƙar aka same su da laifi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa adalci dole ne ya yi aiki, domin kare rayuka da kuma hana sake faruwar irin wannan ta’adi a Jihar Kano