21/06/2026
Innalillahi wainna ilaihi Rajiun!
sun kashe Malamar Islamiyya, Magidanciya, agaban hukuma, agaban Malamanta agaban Mutane, sabidda zargin da babu tabbaci akai.
Malama Ummulkhairi ta fito gida daga sabon Garin Maraban Jos zuwa yankin tsohuwar Maraba domin sauraran muhadara da su Malam Umar waliy (Mahaifina) s**a shirya, a makarantan Malama mardiyya (Mad. Tashiyhul Iman)
Sabidda abokan tafiyanta sun wuceta, ita kuma bata gane makarantar ba, ta tambayi yara su nuna mata, sai wasu mata s**a zargeta da laifin satan yara, bayan matasa sun taru, aka samu aka kaita police station, wakilin mijinta da babammu sun iso domin bada shaida akan cewa malama ce mai karantarwa ansanta kuma babu shaida akan zargin da ake mata.
Matasan basuji ba, ƴan sanda kuma s**a ce an basu umarni da cewa afitar da ita daga station ɗin safidda tention da pressure na matasan.
Matasan s**a aikata abinda s**a aikata, agaban jama'a, agaban police station, Malam yana basu haquri yana magiya, ƴan uwa dake wajen ma haka, amma matasan basuji ba, s**a ma Malama kisan gilla, s**a ƙona, s**a ɗauki mashin ɗin Malam s**a ƙona tare da ita.
Yanzu Idan Mahaifiyarka ne ya zakaji?
Ka san tana da yara sama da biyar?
Lokacin da mijinta ya iso daga inda yake hayaƙi kawai ya hango? Ya barta lafiya agida, sunyi bankwana zata tafi wajen wa'azi? Yanzu idan kaine ya zakaji?
Me ya samu Al'ummarmu ne haka?
A haka ƙasarmu zata zauna lafiya matasa suna irin wannan ɗanyen aikin?
Allah ya gafarta ma Malama Ummulkhairi, ya karɓa shahadanta, yabamu haqurin rashinta.
Ni; Allah na gode maka da ka ke bayyana hakikanin fuskar mutanenmu na Arewa
Ukasha Umar.
21/06/2026.