Fresh Media Garden

Fresh Media Garden Domin samun ingantattun labarai acikin harshen Hausa da Turanci da Larabci har da Faransanci. Babu shaci fadi acikin labaranta

03/04/2026

Zabi guda:- 1. Kuɗi 2
Mulki 3. Ilmi. Me yasa kayi wannan zabin?

PoliceDay2026: OUR AIM IS TO HAVE CLEAN AND HEALTHY ENVIRONMENT - Katsina CP By Kabir Ahmed S/Kuka, Katsina As Police 20...
30/03/2026

PoliceDay2026: OUR AIM IS TO HAVE CLEAN AND HEALTHY ENVIRONMENT - Katsina CP
By Kabir Ahmed S/Kuka, Katsina
As Police 2026 National Day is taking place throughout the country, Katsina State Police Command under the able leadership of Police Commissioner CP Ali Umar Fage, psc(+), mnips, stated that one of the Command aimed during sanitation exercise is to promote clean and good healthy environment.
The Commissioner said this today during sanitation and medical outreach exercise at Kofar Soro Quarters in Katsina Metropolis. He also said that, the exercise also try to strengthening police-community relations as the police team cleaned up Motor Park.
"The medical outreach provided free medical services to residents of Kofar Soro quarters and surrounding communities".
Medical personnel from the command, offered check-ups, treatments, health advice and distributed free mosquito nets to hundreds of beneficiaries. The activities were part of the week-long celebration of the 2026 National Police Day, themed "Community Partnership: Building Trust".
The CP Fage emphasized the importance of community engagement and collaboration in maintaining peace and security in Katsina State.
According to the press release signed by the Command Public Relations Officer, DSP Abubakar Sadiq Aliyu, anipr, the command appreciate the public for their support and participation, reaffirming its commitment to serving the community with professionalism and integrity.

Hajj2026: AN FARA YIWA MANIYATAN JAHAR BITAR AIKIN HAJJIN BANAKamar yadda aka saba a duk shekara, a bana ma hukumar jin ...
30/03/2026

Hajj2026: AN FARA YIWA MANIYATAN JAHAR BITAR AIKIN HAJJIN BANA
Kamar yadda aka saba a duk shekara, a bana ma hukumar jin dadin Alhazai ta jahar Katsina ƙarƙashin jagorancin Babban Daraktan hukumar Alhaji Yunusa Abdullahi Dank**a ta fara yiwa maniyatan jahar bitar aikin wannan Hajji na 2026 domin ilmantar da maniyatan don samun yin aikin ingantacce tare da fatan samun karɓuwarsa daga Ubangiji.
A lokacin zantawar shi da wakilin mu, shugaban hukumar ya ce, a fara yin wannan taron bita a wannan rana ta Litinin a dukkan shiyyoyin hukumar guda bakwai da s**a haɗa da Daura, Dutsinma, Mani, Malunfashi, Funtua, Kankiya da kuma Katsina.
"Shi amfanin yin wannan bita ga maniyata shine, domin ilmantarwa musamman akan shi aikin Hajjin da kuma wasu dokoki ko sharuɗɗan aikin da kuma na ita ƙasar Saudiyya. Sannan kasan shi aikin duk shekara akwai irin abubuwan da yake zowa da shi. Misali, ka ga a bana ita ƙasar ta Saudiyya sai ta sake shigo da wani tsari na batun kiwon lafiya wanda in babu wannan takardar gwajin ba zasu bari a shiga cikin ƙasar mu ba. Akwai batun shi kan shi yadda maniyaci ya k**ata ya zamo tun daga nan gida har zuwa can".
Da aka tambaya shi cewa, baya ganin k**ar an buɗe wannan taron bita k**ar ba lokacin da aka saba gani ba, wato, an bude shi acikin watan salla ƙarama? Alhaji Yunusa yace, ai shi wannan taron bita bashi da lokacin cewa an fara shi da wuri, babbar bukata dai shi ne, ilmantar da maniyata tare kuma da basu damar yin tambayoyi ta yadda zasu yi aikin karɓaɓɓe. Sannan ya ƙara jaddada niyar taimakawa maniyatan a kowane lokaci. Ssidai ya ja hankalinsu da su cigaba da zuwa wajen wannan taron bita har zuwa lokacin da aka gama.
Babban Daraktan har'ila yau, ya jinjinawa Gwamna Malam Dikko Umar Radda wanda yace, hukumar basu da abinda zasu cewa Gwamnan na godiya saidai addu'o'in fatan alheri da samun nasara akan mulkin shi. "A lokacin da aka ƙaiyade na rufe biyan kuɗin kujerun, Maigirma Gwamna ya biyawa mana dukkan kujerun da aka bamu a matsayin rance wanda zai bayar da dama ga sauran maniyatanmu don biya wanda ya haɗa har da sabbi bayan masu cikon kuɗin. Wannan damar muka yi amfani da ita har zuwa cikin watan Janairu, Allah kuma yasa muka ƙara samun waɗanda s**a biya. Muna yi mashi kyakkyawar addu'a akan wannan. Sannan nasan har zuwa yau, sauran alhazan wannan jaha wanda s**a je aikin 2024 da 2025 suna yi mashi addu'a musamman ta biya masu kuɗaɗen hadaya da yayi wanda ya zamo shi ne Gwamna na farko a duk Najeriya da yayi wannan aiki ga maniyatan jahar shi ba tare da nuna wani bambanci ba kuma shekaru biyu a jere",inji Alhaji Yunusa Dank**a

28/03/2026

Al'Ƙur'ani ne gwanin yin lissafi

24/03/2026

Wai ina wakillan mu - ƘILA BATA DA DAƊI MAGANAR TAWA. Shin wakillan mu a waɗannan sassa biyu sunyi mantuwa ne ko fin ƙarfin su aka yi? Shin sojojin wata ƙasa na iya shigowa cikin Najeriya ba tare da amincewar su ba sai shugaban ƙasa kawai zai bugi gaba ya bayar da dama? Batun samun kuɗi ko tara dukiya don kuna bisa wannan matsayin ba shi ne ba, don duk abinda ya biyo baya, akwai naku aciki da zai shafa.
Anan ina magana ne akan batun kasancewar sojojin Amerika dake cikin arewacin ƙasar mu, kuma ma har da ƙaro wasu tare da jirage marassa matuƙa wai da sunan tsaro? Waiyo Allah! Shin wa ake baiwa tsaron? Su masu aikin ta'addanci gari gare su nasu na kan su ko cikin jama'a suke shigewa? Tun daga cikin da waɗannan sojoji na Amerika s**a shigo ƙasar nan aka ajiye su a can yankin Maiduguri tun a wancan lokaci abubuwa s**a fara lalacewa. Tashin bama-bamai ya fara dawowa, shin daga ina abin yake? Ina matsaran?
Abin ban haushi da takaici, kuma a yanzu sai muke jin cewa, ita Faransa zata kawo nata sojojin da kayan aiki don ƙara tallafawa tsaron. AMERIKA DA FARANSA ACIKIN ƘASA GUDA, NIGERIA UWAR ƘASASHEN AFIRKA. Shin mantawa muka yi da illar Faransa tun daga yaƙin Basasar da aka yi? Shin mun manta da cewar duk matsalar tsaron da muke samu muna zargin da sa hannun ƙasar Faransa? A hukumance an k**a sojojin Faransa acikin dajin Sambisa suna koyar da 'yan Boko Harwm, amma kuma wai a hukumance sune ake so a kawo su bayar da tsaro akan rashin tsaron da s**a haddasa, kuma a yankunan arewancin ƙasar nan.
Can sama na ambaci wakillan mu wadanda nike gani hakkin su ne suyi dauki mataki akan wannan sayar da mu da ake shirin yi. Shin wai ma abin tambaya, ina jami'an tsaron da muke da su a ƙasar, ina mak**an da ake cewa ana ciyo bashi ana saye? Ina jiragen yaƙin da aka sayo daga ita Amerikar a lokacin mulkin Marigayi Shugaba Buhari?
Hakkin mu na kan ku. Dukkan ku da mu, babu wanda baisan bala'in da wadannan ƙasashe ke haddasawa ba. A tambayi ƙasar Nijer musamman a sha labari. WANNAN ƘORAFI NA NE A MATAYINA NA ƊAN ƘASA, KUMA A WANNAN KAFA WADDA ITA CE KAƊAI NIKE GANI ZANYI AMFANI DA ITA DON IN ISAR DA WANNAN ƘORAFI.

GWAMNA RADDA YA CANCANCI YABO - NURTW Taxi long journey Sabuwar Tashar KatsinaA lokacin da suke mika sakon barka da sall...
21/03/2026

GWAMNA RADDA YA CANCANCI YABO - NURTW Taxi long journey Sabuwar Tashar Katsina
A lokacin da suke mika sakon barka da salla ga Gwamnan Jahar Katsina Malam Umar Dikko Radda membobin ƙungiyar direbobin ƙananan motoci masu cin dogon zango ƙarƙashin shugabanci Alhaji Abdullahi Ɗandume, membobin a hannu guda sun yabawa Gwamnan tare da nuna goyon bayan su ga manufofin gwamnatin jahar wadda ke ƙoƙarin ciyar da jahar gaba musamman akan batun daƙile matsalar tsaro, ɓullo da hanyoyin ci gaba tare da tallafawa domin samar da abin yi a tsakanin al'umma musamman matasa.
A lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishin ƙungiyar, Alhaji Ɗandume yace, "lallai Gwamna Radda ya cancanci yabo musamman idan muka dubi ta sashen mu na direbobi wanda hanya na daga cikin abubuwan da muke alfahari da su, to a yanzu sai muce, jahar Katsina na daga cikin jihohin da suke da hanyoyi masu wadanda rabon da aji an samu wani haɗari saboda rashin kyawon hanya har an mance. Ko anan kawai muka tsaya ba sai mun ƙara komi ba, wani abin a zo a yaba ne
Shugaban ya ƙara da cewa, "sake farfaɗo da al'adun mu na gargajiya musamman lokuttan bikin salla na daga cikin ƙoƙarin da wannan gwamnati ke yi musamman sake gaiyato jakadun ƙasashen wajen musamman domin zuba hannun jari da kuma faɗaɗa harkokin yawon buɗe ido a wasu sassan jahar wanda hakan wani fanni ne na samun kudaden shiga wadda hakan na iya shafar mu direbobi kartsaye ta hanyar daukar mu domin zagaye.
Ɗandume ya ƙara da cewa, hatta da ziyarar kwana biyu da Gwamnan yayi tare da shugaba Tinubu zuwa ƙasar Birtaniya ba ƙaramin cigaba bane ga jahar, duba da cewaGwamnan mutun ne mai son kawowa jahar abubuwan ƙaruwa da ci gaba. "Sai dai har yanzu, muna ƙara yin matashiya ga shi Maigirma Gwamna da ya waiwayi wannan ƙungiya ta mu da idon rahama domin ganin cewa sana'ar tamu ta tuƙi da ita kanta ƙungiyar mun cigaba maimakon hasashen da wasu ke yi na ganin cewa tamkar ana mayar da mu baya. Amma muna da yakinin cewa, Gwamna bai manta da mu ba, domin muna tare da shi da manufofin shi k**ar yadda muka ambata a baya. Sannan kuma ba da jimawa ba, muna sashen aiyukan alheri daga gwamnatin zasu riske mu".

RABON TALLAFIN AZUMI DA HAƊIN GUIWAR MUTANE 13 S**A YI A KATSINA YAKAMATA A TUNA MAƘABARTA FARKO - Ra'ayin wasuA farko-f...
11/03/2026

RABON TALLAFIN AZUMI DA HAƊIN GUIWAR MUTANE 13 S**A YI A KATSINA YAKAMATA A TUNA MAƘABARTA FARKO - Ra'ayin wasu
A farko-farkon wannan wata na Azumin shekarar 1447/2026 wasu mutane 13 da s**a fito daga ƙungiyar NURTW dake babbar tashar mota ta Katsina s**a yi haɗin guiwa domin bayar da tallafin kayan azumi ga mabukata don neman yardar Allah da kuma neman lada, kuma sunyi wannan ne don ƙashin kan su bada sunan Ƙungiya ba. Shirin wanda aka gudanar da shi ƙarƙashin jagorancin tsohon jami'in dake kula da lafiyar motoci da kuma ƙa'idar tuƙi (VIO) Alhaji Mannir, shirin da har ya fita wajen tashar inda wakilin wannan kafa yayi kiciɓis da waɗanda s**a riƙa bayar da wannan tallafin har muka kawo labarin.
To kasantar ɗan-Adam tara yake bai cika goma ba, wasu al'umma musamman waɗanda ke hidimar neman abincin su acikin tashar sun gabatar da wani ƙorafi tare da bayar da shawara ga su masu wannan hidima don yin gyara anan gaba. Ɗaya daga cikin su yace, "gaskiya ban san an bayar da wannan tallafi acikin tasha ba sai daga baya, bayan kuma nima ina cikin mabukatan. Mai maganar ya tunasar da wata magana da Manzon tsira yayi akan hakkin maƙwabtaka."Ina ganin ta kanmu ya k**ata ace an fara duk da cewa naji ance an baiwa wasu. Amma ina basu shawara don gaba. Don Allah su fara bincikawa acikin gida don tantancewa. Ba wai nace kada a fita waje ba, amma a fara da maƙwabta. Kuma gaskiya na jinjina masu akan wannan tunani, wani abu ne da ba'a taɓa yi ba.
Mun yi ƙoƙarin ta bakin shi jagoran gabatar da wannan shirin bayar da tallafin, wato, Alhaji Mannir VIO don jin abinda zaice dangane da wancan ƙorafi da kuma shawara. A tattaunawar da aka yi da shi ta wayar salula ya ce, "mu dai wannan shiri munyi tunanin aiwatar da shi ne ba tare da la'akari da wani sashe ba. Kuma acikin tashar muka fara yi. Sannan kasan duk abin ka ba zaka iyawa kowa ba saidai kayi abinda kawai zaka iya yi. Sannan abu ne ba na mutun guda ba, sai da aka samu shawarwari a tsakanin mu 13 wanda muke fatan ƙara samun waɗanda zasu shigo don bayar da tasu gudunmuwar. Kuma mun fara jarabawa acikin wannan wata mai albarka. Ganin irin yadda muka nasarar abin, to mun fara tunanin yadda zamu riƙa tallafawa 'yan uwanmu direbobi. Kuma wannan aikin bada sunan ƙungiya muka yi ba, kuma ba zamu yi da sunanta nan gaba ba. Illa kawai duk wanda yaji zai iya shigowa muyi tare muna maraba. Sannan koda mutun shi kaɗai ne yaga akwai wani wurin da zai bayar da tashi gudunmuwar abu ne mai kyau.
Da aka tuntuɓe shi akan cewa, baya ganin wasu zasu yi fahimtar cewa akwai wata manufa ɓoyayya da wannan shirin nasu yake da shi? Alhaji Mannir yace, "kai ka taɓa ganin inda mutun zaiyi aikin alheri ba tare da sheɗan ya shigo ciki don tarwatsa abin ba? Inma har muna da wata manufa ai bata wuce ta neman lada daga wajen mai ba kowa. Da ma ce, sai wanda Allah yake so da rahamar shi ya bashi irinta. Mu kam saboda Allah muka yi abin mu kuma shi muke neman yardar shi. Amma duk wata fassarar da wani ko wasu zasu yi sai muce sai sun gama. Amma su sani, suna taya sheɗan aiki ne na kawo naƙasu ga aikin alheri, sai dai kuma sai su ma ɗin sheɗanu ne, to sai suyi. Sannan ga waɗanda suke ganin k**ar ba'a basu ba, sai ince suyi haƙuri akwai gaba. Yanzu ne aka fara", inji Alhaji Mannir VIO.

07/03/2026

Dan jaridar Israila, Alon Mizrahi yace:

“Abin da muke gani a yanzu tarihi ne ke faruwa. Iran ta ba kowa mamaki. Ta yi wa sansanonin Amurka duka—duka rauni mai tsanani, mai faɗi, kuma mai yanke hukunci, har duniya ba ta shirya ta karɓi abin da take gani ba.

Ya ƙara da cewa: “A cikin kwanaki huɗu kacal, Iran ta faɗaɗa ikon tasirinta na soja a yankin. Ta lalata wasu daga cikin mafi tsada kuma mafi muhimmancin sansanonin soja da kayan aiki a duniya.

Sansanonin Amurka da ke Bahrain, Kuwait, Qatar da Saudiyya na daga cikin manyan cibiyoyin soja mafi girma a doron ƙasa. Wadannan kadarori ne da aka gina da kuɗaɗe masu kai wa tiriliyan. cikin shekaru da dama A zahiri muna magana ne kan wani babban ɓangare na kuɗaɗen da Amurka ta kashe wajen sojinta fiye da shekaru talatin, yanzu suna ƙonewa suna zama toka.

Muna ganin na’urorin radar da kowacce ta kai daruruwan miliyoyin dala ana lalata su cikin daƙiƙa guda. Muna ganin cikakkun sansanonin soja ana barinsu, ana ƙone su, ana ragargaza su. Kuma bisa abin da na sani, Amurka ba ta taɓa fuskantar irin wannan ɓarna a tarihinta ba. Wataƙila sai dai harin Pearl Harbor lokacin yaƙin duniya na biyu. Wannan kuma hari guda ɗaya ne kawai.

Babu wani maƙiyi a yaƙin al'ada da ya taɓa yi wa rundunar sojin Amurka abin da Iran ke yi a yanzu. Abin ya wuce abin da hankali zai iya ɗauka. Halin da sojan Amurka ke ciki ya kai ga ana toshe kusan duk wani sabon bayani game da wannan yaƙi. Idan kuka lura, kullum ana rage abin da ake nuna mana ne.

Shekaru talatin da biyar da s**a wuce, lokacin Yaƙin Iraƙi na Farko, ana nuna mana bidiyo marasa ƙarewa daga Iraki. A lokacin, bom ɗin da ake kira smart bombs da kyamarori sabuwar fasaha ce. Amma kowane dare ana nuna hotunan dare daga filin yaƙi. Yanzu kuwa kusan babu wani bidiyo da ake gani.

Ku fahimci wannan. Ana cewa Amurka ita ce mafi girman ƙarfin soja a duniya, tare da mafi girman ikon sama. Amma tsawon kwanaki huɗu, duk da cewa ana cewa Amurka ce ke kai hari kuma ya k**ata ta ratsa kariyar Iran, babu wata alamar mamayar sararin samaniyar Iran. Ina hotunan jiragenmu suna shawagi a kan Tehran ko wani ɓangare na Iran? Kai ka gan su?

Sojojin Amurka ma ba za su iya mafarkin taka ƙasa a Iran ba. Kuma don ku fahimci yadda yaƙin ya kai matakin ruɗani, tun a rana ta huɗu ana jin shawarwari masu ban mamaki daga gwamnatin Donald Trump. Ana magana a kan tura jiragen rakiya ga tankokin mai da ke fitowa daga Tekun Fasha.

Me suke nufi da hakan? Suna so su tura jiragen Amurka cikin wurin da dubban mak**ai masu linzami na Iran za su iya kaiwa? A yanzu babu wanda zai iya ƙetare Zirin Hormuz.

Iran ta shafe shekaru da dama tana shirin wannan rana. Sannan ana magana a kan ba wa mayaƙan Ƙurdawa mak**ai su kai hari cikin Iran. Wane irin magana ce wannan? Kun taɓa duba taswirar Iran? Da alama gwamnatin Trump ba ta taɓa ganin taswirar Iran ba. Kun san girman ƙasar? Me ake nufi da ‘mamaye Iran’?

Kuna tunanin rundunar mayaƙa dubu goma za ta iya mamaye Iran? Ko dubu hamsin? Ko dubu ɗari? Iran za ta haɗiye su ne kawai. Amurka da Isra’ila sun riga sun sha kaye a wannan yaƙi. Za su iya kashe miliyoyin fararen hula a gidajensu. Suna da manyan bama-bamai da za su iya rusa gine-gine.

Amma ba za su ci wannan yaƙi ba. Kayan aikin sojan Iran da manyan cibiyoyinta suna ɓoye can ƙasa ko’ina a cikin Iran. Babu yadda Amurkawa, b***e Isra’ilawa, za su iya kai wa gare su. Sun faro wani yaƙi da ba su da damar kawo ƙarshensa. Idan wannan ya ƙare.

Amurka ba za ta sake dawowa Yammacin Asia ba. Ba za a sake samun fuska ko kayan Amurka a Gabas Ta Tsakiya ba. Ina faɗa muku wannan da cikakken tabbaci.

Domin samun ingantattun labarai acikin harshen Hausa da Turanci da Larabci har da Faransanci. Babu shaci fadi acikin labaranta

GWAMNA RADDA YA BAYAR DA ZAKKAR NAIRA MILYAN HAMSI GA KWAMITIN ZAKKA DA WAQAFI A KATSINA   Daga Ahmed Kabir S/Kuka, Kats...
03/03/2026

GWAMNA RADDA YA BAYAR DA ZAKKAR NAIRA MILYAN HAMSI GA KWAMITIN ZAKKA DA WAQAFI A KATSINA Daga Ahmed Kabir S/Kuka, Katsina
A ranar wannan Talata 3 ga watan Maris, 2026 kwamitin Zakka da Waqafi da gwamnatin jahar Katsina ta ƙirƙiro bayan hawan kujerar mulki da Gwamna Radda yayi ta gabatar da amsar zakka daga al'ummar da ta rataya akan su domin rabawa waɗanda shari'a ta baiyana a ba su. Kamar yadda Babban shugaban hukumar ta Zakka da Waqafi Dokta Ahmad Musa Abdullahi ya shaidawa mahalarta taron da s**a haɗa hakimai da masu ruwa da tsaki a harabar hedkwatar hukumar ya shaida, "ita Zakka ana bayar da ita ne daga lokacin da ya k**ata, amma mafi yawan masu bayar da zakkar sun fi ganin bayar da ita acikin wannan wata na Ramadan domin kwaɗayin falalar dake cikin watan. Shugaban a cikin jawabin shi ya baiyana cewar a bara an tara zakkar kayan amfanin gona sama da buhu 86 da kuma wasu buhun nan sama da 100 daga sashen hakimai, kuma duk an rabawa mabukata.
Shi kuwa Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa, jan hankali yayi musamman ga mawadata akan cewa su riƙa taimakawa na ƙasa da su wanda hakan zai sanya su riƙa girmama su tare da yin duk abin da ya dace don ganin sun kare marbatar su. "In har ba mu taimakawa na ƙasa da mu, wata rana wata wuta tana iya taso mana, maimakon su taimaka mana, wasu suna ina ƙullo fetur domin ganin sun ƙara rura wutar. Amma wannan taimako da muke yi masu, shi zai sa suyi duk iya ƙoƙarin su na ganin sun kashe mana wannan wuta".
Bayan jawabin na shi, Gwamna Radda ya bayar da Zakkar naira milyan hamsin daga cikin abin da yace yake samu. Kazalika, Mataimakin Gwamna Malam Faruk Lawal Jobe yace, a matsayin shi na mai kiwon dabbobi ya bayar da umarni a tafi a ƙidaya dabbobin a fitar da zakkar k**ar yadda addinin musulumci ya aiyana.
Shi ma matashin Ɗan kasuwan nan Alhaji Ɗahiru Usman Sarki mai kamfanin Ɗanmarna dake sayar da man fetur wanda Alhaji Isa Usman Sarki ya wakilta, ya bayar da zakkar naira milyan 25. Har'ila yau, wasu bayin Allah da s**a fito daga maƙwabciyar ƙasa, wato, jamhuriyar Nijer sun shirya yin buɗa baki da marayu sama da ɗari a wannan rana.

03/03/2026

SANSANIN SOJOJIN AMURKA DA ISRA’ILA BARAZANA CE GA MUSULUNCI - Dr. Goni M. Ja'afaru

03/03/2026

SAUDIYA TA NUNA ƁACIN RANTA GA AMERIKA: SAI YANZU AKA FARA GANE HAKAN
Saudiyya ta nuna ɓacin ranta game da alaƙarta da Amurka inda tace Amurka ta fi karkata ne wajen kare kasar Izra@ila ba tare da la’akari da kare sauran ƙasashen Larabawan ba, duk da cewa su ne ke dauke da mafi yawancin sansanonin sojojin Amurka a gabas ta tsakiya...

A zahiri yanzu mun fahimci cewa sansanonin da muke bawa masauki ba komai ba ne illa wata dabara da Amurka ke amfani da ita wajen karbar makudan kudade da kuma tattara bayanan sirri akan al'ummar musulmi dake yankin..

Tabbas dole abubuwa su canza, tunda dai Amurka da Izra@ila ta damu bamu Larabawa ba.

Address

Dutsin Safe Lowcost Jibia Road
Katsina
820261

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fresh Media Garden posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share