Apc Media Leads

Apc Media Leads page din da yake Tallata Aiyyukan Alheri na masu madafun iko a Jam,iyyar Apc tun daga Shugaban kasa har zuwa kansila

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Ranar Litinin 14 ga watan Yuli 2025, A Matsayin Ranar Hutu Domin Nuna Jimami Da Kuma A...
14/07/2025

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ayyana Ranar Litinin 14 ga watan Yuli 2025, A Matsayin Ranar Hutu Domin Nuna Jimami Da Kuma Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata takarda da daraktan yaɗa labarai na Ofishin sakataren gwamnatin jihar Katsina Abdullahi Aliyu Yar'adua, ya sanya ma hannu.

Takardar ta kuma ce Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, yana ƙara taya al'ummar jihar Katsina jimami da kuma alhinin rashin tsohon shugaban ƙasar, tare da yin addu'ar Allah SWT ya jikan shi da rahama.

Shugaba Karama Hukumar Katsina Hon Isah Miqdad AD Saude  ya kula yarjejeniyar haɗin gwiwa da Gidauniyar UNICEF domin tal...
08/07/2025

Shugaba Karama Hukumar Katsina Hon Isah Miqdad AD Saude ya kula yarjejeniyar haɗin gwiwa da Gidauniyar UNICEF domin tallafa wa ilimin yara, musamman mata, tare da taimaka musu wajen samun ci gaba a fannoni daban-daban na koyon Sanao,i

Hon Aliyu Albaba yayi Kira ga Gwamnatin jihar Katsina da ta fidda Hanyoyin Ruwa a Unguwannin Janbango da Rahamawa domin ...
08/07/2025

Hon Aliyu Albaba yayi Kira ga Gwamnatin jihar Katsina da ta fidda Hanyoyin Ruwa a Unguwannin Janbango da Rahamawa domin gudun Ambaliya,

Dan majalisar Dokoki mai wakiltar karamar hukumar Katsina a zauren majalissar jiha Hon Aliyu Abubakar Albaba ya Gabatar da kuduri wato (motion) A Gaban zaure. majalisa na kira ga Gowamnatin jihar katsina ta fidda Hanyoyin Ruwa a Unguwar Jan Bango da Rahamawa duba da zaizayar kasa da suke fama da ita,

Hon Albaba ya Kara da Chewa idan ba'a Dauki matakin Gaggawa ba Al-Ummar yankin zasu iya Rasa Gidajen su ta dalilin Ambaliyar Ruwa ganin yanda damana tazo Kuma damanar tazo da Ruwa masu karfi Kuma yache kasantuwar An Rushe Jan bangon Wanda Asali shine yake tare Ruwan Baya shigowa Unguwar Amma yanzu mahadar Ruwa biyu zuwa Uku take barazana kawo Ruwa Wanda shine yake zaizaye Hanyoyin Unguwar Wanda yanzu haka ko Hanyar mota Babu,

Don haka yake kira ga Sauran membobin majalissar da su goya mashi baya a Kai wannan kuduri ga majalisar zartaswa don yin Abinda ya Dace ba tare da an dauki wani dogon lokachi ba

Lokachin da ya gabatara kudirin akwai membobin majalissar da s**a Yaba Mashi Kan wannan kudiri da ya kawo domin taimaka ma Al,ummar da yake wakilta kamar Dan majalissar karamar hukumar kankiya Dana karamar hukumar Malumfashi,

Majalissar ta tura wannan kuduri Ga majalisar zartaswa ta jiha don yin Abinda ya Dace.

Apc Media Leads
✍️✍️✍️✍️ 08//07/2025

NOTICE OF NATIONAL EXECUTIVE COMMITTEE (NEC) MEETING Date: Thursday, 24th July, 2025 Time: 11AM prompt Venue: APC Nation...
05/07/2025

NOTICE OF NATIONAL EXECUTIVE COMMITTEE (NEC) MEETING

Date: Thursday, 24th July, 2025
Time: 11AM prompt
Venue: APC National Secretariat, 40 Blantyre Street, Wuse II, Abuja.

Matasa Maza da Mata 634 Gwamnatin jihar Katsina ta koya ma Sanao,I Kala,Kala Kuma ta Basu kalar Kayan Aikin da s**a koyi...
02/07/2025

Matasa Maza da Mata 634 Gwamnatin jihar Katsina ta koya ma Sanao,I Kala,Kala Kuma ta Basu kalar Kayan Aikin da s**a koyi Sana,ar,

Gwamnan jihar Katsina Mal Dr Dr. Dikko Umaru Radda PhD Con ya Jagoranchi yaye matasan da s**a kammala makarantar koyon Sanao,I Katsina youth craft village (KYCV)
Gwamnan ya Jagoranchi yaye Dalibai NE a Yau Laraba 02/07//2005 a Babban filin Wasa na Garin Katsina Muhammad Dikko stadium

A Lokachin yayewar Gwamnan ya gargadi daliban da s**a kammala Amsar horon inda yache Kada Wanda ya sayar da Kayan Sana,ar da aka bashi domin su dogara da kansu harda Sauran dagi da iyayen
Daga karshe ya Jagoranchi bada Kayayyakin ga wasu daga chikin daliban tare da Basu takardun kammala wannan makaranta KYCV)(certificate)

Ma, aikatar Aiyyuka Gidaje da sufuri ta jihar Katsina (MOW) tayi Zaman hadin gwiwa da Hukumar Tsara birane ta jiha (KURP...
27/06/2025

Ma, aikatar Aiyyuka Gidaje da sufuri ta jihar Katsina (MOW) tayi Zaman hadin gwiwa da Hukumar Tsara birane ta jiha (KURPB)

Hukumar Kula da Tsara birane ta jihar Katsina KURPB karkashin Jagoranchin G,M, TPL Abbas Sambo tare da wasu daga chikin injiniyoyin hukumar sun kawo ziyarar Aiki a ma,aikatar Aiyyuka Gidaje da sufuri Ranar Alhamis 26/06/2025
Sun kawo ziyarar ne domin tattauna yanda za,ayi hadin gwiwa a kauda gine,ginen da Al'umma sukeyi ba tare da izinin hukumar ba Wanda hakan Yana kawo Ambaliyar Ruwa,chunkushewar hanyoyin Ruwa dana mutane Akan t**ina,

Babban sakatare ma,aikatar Aiyyuka Q'S Samaila Umar Rugoji shine ya wakilci Kwamishinan Aiyyuka Engr Dr Sani Magaji Ingawa tare da dukkanin Darectochin ma,aikatar,
A chikin jawabin barka da zuwa da yayi masu Babban sakataren ya nuna Jindadin Shi Akan wannan ziyarar da s**a kawo Kuma ya sanar dasu ma,aikatar Aiyyuka shirye take dukkanin Abubuwan da za,a tattauna Indai zasu kawo ma Al,ummar jihar Katsina chigaba,

A Lokachin da yake jawabi makasudin zuwan nasu Shugaban hukumar KURPB TPL Abbas Sambo ya bayyana matsaloli da yawa zasu iya faruwa idan har mutane suna yin gine gine ba bisa Ka,Ida ba Kuma suna tare hanyoyin Ruwa da hanyoyin da Gwamnati ta tanada domin wuchewar mutane,

Ya Kara da Chewa kamar Yanda Gwamnatin Mal Dr Dr. Dikko Umaru Radda take da kudirin sabunta birane ta hanyar Gina tagwayen tituna irin Yanda ta fara kammala su daga Kofar Soro zuwa kofar Guga da Wadda ta tashi daga Round about na masallachin Juma zuwa Round About na WTC,

Yache idan kabi hanyoyin zakaga mutane sunata maida gine,ginen su ba tare da Neman izinin hukumar Tsara birane ba inda yache yin gine ginen ba tare.da Neman izinin hukumar ba laifin ne babba Kuma hukumar tan da ikon tsaida ginin ko Kuma ta ruguza inda aka wuche iyakar da Gwamnati ta Aminche ginin ya tsaya,

A Lokachin da yake jawabi Shugaban bangaren Kula da Aikin tituna da magudanan Ruwa na ma,aikatar Aiyyuka Engr Falalu Hussaini yayi jawabi Mai tsawo tare da bada shawara domin tabbatar da dukkanin gine ginen da Al'umma suke yi basu Saba dokar hukumar ba

Daga karshe Babban sakataren ma,aikatar Aiyyuka Q'S Samaila Umar ya Kara tabbatar ma tawagar KURPB zasu Samu dukkanin hadin Kai da suke bukata domin ganin jihar Katsina ta Samu chigaban da zaya zarta na Sauran jihohi
Kuma yayi Jan hankalin ga Al,ummomin da zasu Gyara wuraren su Akan sabbin titunan da Ake gyarawa su rika tuntubar hukumar Tsara birane ta jiha KURPB a ofishin ta domin gudun Sai Ka fara Aiki a dakatar da Aikin ko Kuma a Rosa Shi a Gwamnatanche,

Mustapha Ibrahim Kofar Marusa
Media Assistant to Katsina state
Governor Ministry of Works
Housing and Transport
27/06/2024.

Majalissar zartaswa ta jihar Katsina karkashin Jagoranchin Gwamna Dr. Dikko Umaru Radda   ta Aminche da Bude Rumbun sauk...
26/06/2025

Majalissar zartaswa ta jihar Katsina karkashin Jagoranchin Gwamna Dr. Dikko Umaru Radda ta Aminche da Bude Rumbun sauki a dukkanin Kananan hukomomi 34 na jihar Katsina,

A wani ci gaban da aka Samu Akan Tsarin sayar da Kayana abinchi mai suna Rumbun sauki maiba Gwamnan jihar Katsina shawara na musamman kan bunkasa tattalin arzikin karkara Hon. Muktar Nuhu Danja, ya sanar da manema labarai cewa majalisar ta samu rahoton ci gaba kan shirin sayar da Abinchin Mai sauki na Rumbun-Sauki da gwamnatin Radda ta bullo da shi domin samun saukin kayan abinci ga al’umma masu rauni. Wanda aka Zuba zunzurutun kudi har biliyan 4 a cikin shirin,

majalisar ta yi nazari a kan halin da ake ciki a kasuwanni tare da amincewa da rage farashin kayan abincin da ake sayarwa ga masu cin gajiyar shirin," in ji Hon Danja. Kuma Ya bayyana cewa kawo yanzu Rumbun-Sauki ya yi rijistar sama da mutane 15,000 da s**a ci gajiyar tallafin wanda mutanen s**a hada da ma’aikatan gwamnati na jiha da na kananan hukumomi da ma’aikatan UBEC Da farko dai an fara gwajin a kananan hukumomin Katsina, Daura, da Funtua,

majalisar ta amince da fadada shirin zuwa dukkanin kananan hukumomin jihar 34, hakan na nufin za a bude shaguna da dama, kuma Allah,umma da dama za su ci gajiyar shirin wannan Rumbun sauki na Kayan abinci inji Hon Danja Kuma ya Kara jaddada kudirin gwamnatin Mal Dikko Radda na samar da saukin rayuwa ga ‘yan jihar Katsina ta hanyar Saida masu Kayan masarufi chikin farashin Mai sauki

A wani bangaren Kuma ma,aikata ana Basu bashi kafin ayi Albashi ana chirewa ba tare da Karin ko Sisi ba Kuma basuda bambanchi tsakanin su da Mai kudi hannu .

Mustapha Ibrahim Kofar Marusa
Media Assistant to Katsina state
Governor Ministry of Works
Housing and Transport.

Hukumar NBTE ta amince da makarantar koyon Sana,oi ta  Katsina Youth Craft Village (KYCV) ta zama cibiyar horas da matas...
25/06/2025

Hukumar NBTE ta amince da makarantar koyon Sana,oi ta Katsina Youth Craft Village (KYCV) ta zama cibiyar horas da matasa tare da bada satifiket

Hukumar kula da ilimin fasaha ta ƙasa (NBTE) ta amince da Katsina Youth Craft Village a hukumance a matsayin cibiyar bayar da horo karkashin tsarin National Skills Qualifications (NSQ).

Wannan amincewa na kunshe ne a cikin wata takarda da Sakatare Janar na NBTE, Farfesa Idris M. Bugaje, ya sanya wa hannu, bayan nasarar binciken kayan aiki da ingancin horo da hukumar ta gudanar.

Da wannan ci gaba, Katsina Youth Craft Village dake da rassansa a Katsina da Malumfashi, yanzu zata rika horar da matasa a fannoni daban-daban kamar ink
Gyaran motoci, aikin kafinta, gyaran kwamfuta, gyaran jiki (cosmetology), girki da hidimar abinci, dinkin kaya, kera takalma da jikkuna da Sauran kayayyaki na fata, gini, gyaran wayoyin hannu, daukar hoto da fina-finai, aikin famfo, walda, da gyaran na’urorin tauraron dan adam (satellite).

NBTE ta bayyana cewa wannan amincewa ta fara aiki daga 24 ga Yuni, 2025, tare da buƙatar cibiyar ta yi rajista da hukumomin bayar da takardar shaidar NSQ bisa kowane fanni.

Gwamnan Jihar Katsina,Mal Dr Dikko umaru Radda ya taya cibiyar murna bisa wannan nasara.
Acewar Gwamnan Wannan wata babbar nasara ce ga jihar Katsina, kuma ta tabbatar da kudirinmu na samar da sana’o’in dogaro da kai ga matasa, tare da buɗe masu ƙofofin arziki a matakin ƙasa.

Shi ma Injiniya Kabir Abdullahi , shugaban cibiyar, ya bayyana wannan ci gaba a matsayin wani tarihi ne da ya dace da hangen nesa na Gwamna Radda na karfafa matasa da basu sana’o’in da zasu dogara da kansu da kuma samar da ayyukan yi.
Kuma Ya tabbar da cewa wannan mataki yana daga cikin muhimman manufofin gwamnatin jihar Katsina karkashin shuganchin Dikko Radda na gina rayuwar matasa da rage rashin aikin yi a jihar Katsina.

Sakon APC MEDIA LEADS Katsina

Gwamna Raɗɗa Ya Halarci Taro Akan Saka Hannun Jari A Ƙasar China Domin Samar Da Ayyukan Raya Ƙasa Gwamnan jihar Katsina ...
25/06/2025

Gwamna Raɗɗa Ya Halarci Taro Akan Saka Hannun Jari A Ƙasar China Domin Samar Da Ayyukan Raya Ƙasa

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya ƙarfafa ƙudirin gwamnatin shi na gina goben mu "Building Your Future" bayan ƙulla alaƙa da kamfanin gine-gine na ƙasar China "China Civil Engineering Corporation CCECC".

Tattaunawar ta wakana ne a wani babban taro tsakanin gwamna Raɗɗa da Darakta Manaja na Kamfanin CCECC Mista Cheng Sichang a birnin Macao na ƙasar Sin (China) a lokacin da gwamnan ya halarci babban taron ƙasa na zuba hannun jari karo na 16 akan ayyukan raya ƙasa na kamfanin na CCECC.

Gwamnan Raɗɗa ya bayyana irin nasara da kamfanin ya samu wajen kammala aikin t**in da ya zagaye birnin Katsina ta gabashi (Eastern Bypass) mai nisan kilo mita 24 da kuma aikin da aka kusa kammalawa wanda ya taso daga Babban masallacin gidan Sarki zuwa shataletalen makarantar ƴan mata WTC.

Gwamnan ya kuma sanar da shirin shi na sake ƙaddamar da wasu manyan ayyuka guda biyu, wanda tuni an kammala biyan mutane diyyar wuraren su, ya kuma bayyana muhimmancin kammala ayyukan musamman a yadda ake fuskantar kakar zaɓe.

Haka kuma gwamnan ya ce gwamnatin shi tana gina makarantun gwamnati na musamman (Special Schools) a shiyoyi uku na jihar, inda ya nemi gudummuwar kayan fasaha daga kamfanin domin inganta gine-ginen.

Daga ƙarshe Gwamnan ya gode ma kamfanin bisa alaƙar shi da jihar Katsina da kuma tarbar tawagar jihar a birnin Macao.

Tun da fari Darakta Manaja na Kamfanin CCECC Mista Cheng Sichang, ya yi bayanin irin nasarorin da kamfanin ya samu a jihar Katsina da ma Najeriya tun kafuwar shi a shekarar 1979, bayan fara ayyukan kamfanin a ƙasashen ƙetare a cikin shekarun 1980.

Cikin nasarorin da kamfanin ya samu a Najeriya akwai gina hanyar Abuja zuwa Kaduna, gina filin wasan ƙwallon ƙafa a Katsina, sai hanyar zuwa masarautar Daura, ɗaukar nauyin karatun ɗalibai 1,000 ciki har da masu karatun digiri na biyu.

Bayan zama da wakillan kamfanin CCECC, gwamna Raɗɗa ya kuma halarci taron zuba jari mai taken "Enhanced Connectivity for Win-win Corporation" Wanda ya ƙunshi manyan jami'an gwamnati da masu kamfanoni daga sassa daban daban na duniya.

Tawagar gwamnatin jihar Katsina da ta mara wa gwamnan baya akwai Mai ɗakin shi Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa, jami'in bibiya Haroun Abba Gana, Sakataren Gwamnan Hon. Abdullahi Aliyu Turaji.

A chikin kudirorin Shugaban karamar hukumar Katsina Hon Isah Miqdad AD Saude  Wanda yasa Al,ummar Shi suke alfahari dash...
24/06/2025

A chikin kudirorin Shugaban karamar hukumar Katsina Hon Isah Miqdad AD Saude Wanda yasa Al,ummar Shi suke alfahari dashi kullum Yana Dubar abunda zaya Amfani Al,ummar da yake Shugabanta,

Bangaren tallafin ilimi Hon isah miqdad Yana kokarin bada tallafi Kala daban daban tun kafin ya Zama shugaban karamar hukuma daga matakin primary har zuwa Jami,a ta dalilin haka a yanzu ma yayi tunanin Kara FADADA wannan akidar tashi ta tallafa ma ilimin a karamar hukumar Katsina inda ya dauki kudirin daukar nauyin Yan Asalin karamar hukumar Katsina karatu a makarantar KSITM dake nan chikin Garin Katsina,
Katsina Institute of Technology and Management (KSITM), cibiyar da ke ba da ingantaccen horo na zamani a fannonin:

✅ Accountancy
✅ Computer Science & Engineering
✅ Electrical/Electronic Engineering
✅ Library & Information Science
✅ Business Informatics
✅ Islamic Banking & Finance
✅ Cybersecurity, Networking & da sauran Su.

Wannan shiri-na-ilimi na da nufin cike gibi tsakanin baiwa-ta-kokari da kuma samun-dama, tare da bai wa matasanmu ilimin da zai taimaka musu, su yi fice a duniyar tattalin arzikin zamani.

Shiga nan domin cikawa da samun dama:
https://bit.ly/43T9JiU?r=qr
An bude wannan damar ne ga ’yan asalin Karamar Hukumar Katsina kadai.

Kuma za a rufe rijista ranar 25 ga watan June 2025. Allah ya bada sa’a.

Gaskiyar magana Akan wannan Aikin gadar da Naga wani ya dauki hoton ta Yana yi Mata lakabi da Aika,Aika ina tunanin duk ...
20/06/2025

Gaskiyar magana Akan wannan Aikin gadar da Naga wani ya dauki hoton ta Yana yi Mata lakabi da Aika,Aika ina tunanin duk mai hankali yasan yanda Aikin Gwamnati yake lokachin da kamfanin CCECC tazo Aikin t**in Sarki Mukhtar Road duk a lokachin anba MOTHER CAT Aikin fidda hanyoyin ruwan chikin garin Katsina Wanda Ake Kira ACRESAT Kuma kamfanin daban daban ne wanda dole kowane kamfani Sai yayi Aikin Shi yanda aka bashii kamar Yanda mother cat s**a kammala Gyaran gadar Gawuna ta Kan hanyar kofar marusa har s**a sanya Mata wannan karfen shine shedar sun kammala nasu aikin
Abunda ya rage yanzu CCECC zasu chigaba da FADADA wannan Gadar ta Gawuna

Ma,aikatar Aiyyuka Gidaje da sufuri ta jihar Katsina karkashin Jagoranchin Kwamishina Engr Dr Sani Magaji tana tabbatar ma Al,ummar jihar Katsina da Chewa wannan gadar ta Gawuna ba haka za,a barta ba saboda tun asali kamfanin CCECC zaya FADADA ta kamar Yanda aka fadada t**in an Samu tsaiko ne domin kamfanin mother cat su kammala nasu aikin sakamakon yanda Aikin Gwamnati yake tafiya,

Yanzu haka manyan motochi da kanana masu zuwa Lagos da Sauran garirwa a kudaanchin Najeria sunchi gaba da bin hanyar dat...
16/06/2025

Yanzu haka manyan motochi da kanana masu zuwa Lagos da Sauran garirwa a kudaanchin Najeria sunchi gaba da bin hanyar data tashi daga Shargalle zuwa Ingawa chewar Al,ummar chewar Al,ummomin Dutsi da Ingawa dake nan jihar Katsina,

Kwamishinan Aiyyuka Gidaje da sufuri na jihar Katsina Engr Dr Sani Magaji Ingawa yakai ziyarar gani da ido a Aikin t**in da ya tashi daga Shargalle yabi ta Dutsi, Yandoma, ya fita Ingawa
Ziyarar Duba Aikin Gyaran t**in da yayi yau Litinin 16/06/2025 ya Jagoranchi tawagar directochi tare da injiniyoyin ma,aikatar Aiyyuka tare dana kamfanin mother cat domin tabbatar da anayin Aiki mai inganchi kamar Yanda yake rubuche a takardar yarjejeniyar da s**a sanya ma hannu,

A Lokachin da yake jawabi Shugaban bangaren Aikin t**i da magudanan Ruwa na ma,aikar Aiyyuka Engr Falalu Hussaini ya bayyana yanda yarjejeniyar Aikin take Kuma ya aminta da dukkanin ka,idojin da kamfanin suke bi na yin Aikin,

Suma mutanen garuruwan da muka zanta dasu sunche sun kai kokensu ga Yan siyasa babu adadi a lokutta da dama Amma ba,a Samu Nasarar samun yin wannan Gyaran t**i ba sai lokachin Gwamnatin Mal Dr. Dikko Umaru Radda,

A Lokachin da yake jawabin abubuwan da yagani da idonshi kwamishinan Aiyyuka ya nuna Jindadin Shi ganin yanda wannan kamfanin na mother cat suke yin Aiki ingantache Kuma da nagarta Kuma ya Kara yaba ma Gwamnan jihar Katsina Mal Dikko umaru Radda Akan wannan jajirchewa da namijin kokari da yayi ma Al,umma domin habbakar tattalin Arzukin yankunan su.

Mustapha Ibrahim Kofar Marusa
Media Assistant to Katsina state
Governor Ministry of Works
Housing and Transport .

Address

Katsina

Telephone

+2347032043337

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Apc Media Leads posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Apc Media Leads:

Share