Northern Media Crew

Northern Media Crew Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Northern Media Crew, No 140 Nagogo Road Kofar Durbi katsina, Katsina.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Allah ya yiwa mai martaba sarkin GUMEL Alh Dr Ahmed Muhammad Sani II rasuwa a kasar E...
03/09/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah ya yiwa mai martaba sarkin GUMEL Alh Dr Ahmed Muhammad Sani II rasuwa a kasar EGYPT

Muna addu'a Allah yajikansa da gafara Allah yasa yana Aljannar firdausi Amin

Hukumar Binciken Laifuka ta Amurka FBI ta taba tuhumar Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan zangin safarar miyagun kwayoyi a sh...
02/09/2026

Hukumar Binciken Laifuka ta Amurka FBI ta taba tuhumar Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan zangin safarar miyagun kwayoyi a shekarun baya.
DW Hausa

Gwamna Umaru Mohammed Bago na Jihar Neja ya bada gudunmawar Naira Miliyan Ashirin ga yan darika masu shirya zagayen Maul...
02/09/2026

Gwamna Umaru Mohammed Bago na Jihar Neja ya bada gudunmawar Naira Miliyan Ashirin ga yan darika masu shirya zagayen Mauludi a garin Minna Babban Birnin Jihar.

Ƙungiyar Majama'au Ihiya'uzzikira ne ke shirya zagayen wanda akayi ranar Talata data gabata

Nawa Gwamnan jihar ku ya bayar gudummuwa ga masu shirya zagayen maulidin manzon Allah a jihohin ku

Rubuta mana a comments section

Kana Ci Gaba da Zama Amintaccen Jagora Wajen Gina Ƙasa” — Gwamna Radda Ya Taya Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Murnar ...
02/09/2026

Kana Ci Gaba da Zama Amintaccen Jagora Wajen Gina Ƙasa” — Gwamna Radda Ya Taya Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Murnar Cika Shekara

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya taya Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, GCON, murnar zagayowar ranar haihuwarsa, inda ya bayyana shi a matsayin amintaccen jagora wajen gina ƙasa wanda ƙwarewarsa, jajircewarsa da sadaukarwarsa wajen hidimar jama’a ke chigaba da bayar da gagarumar gudummawa wajen ci gaban Najeriya.

Gwamna Radda ya bayyana cewa Mataimakin Shugaban Ƙasar ya kafa tarihi mai ɗorewa na hidimar jama’a, tun daga lokacin da yake jagorantar Jihar Borno har zuwa matsayinsa na yanzu, inda yake taimaka wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, wajen tafiyar da harkokin mulkin ƙasar nan.

A cewar Gwamna Radda nutsuwar Mataimakin Shugaban Ƙasar, fahimtarsa kan muhimman batutuwan ƙasa da kuma iya mu’amalarsa da mutane daga sassa daban-daban, yana daga cikin kyawawan halayen da s**a taimaka masa wajen sauke nauyin dake kansa.

Gwamna Radda ya kuma yaba wa Sanata Kashim Shettima bisa kulawarsa da al’amuran da s**a shafi Arewacin Najeriya, musamman ƙoƙarin ƙarfafa tsaro, bunƙasa noma, jawo jarin zuba jari da samar da damammaki ga matasa.

Ya ƙara da cewa shugabancin ƙasa na buƙatar haƙuri, kyakkyawan tunani da kuma shirye-shiryen yin hidima ga al’umma ba tare da fifita muradun kai ba, yana mai cewa Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ci gaba da amfani da ƙwarewarsa wajen yi wa Najeriya hidima.

Gwamna Radda, a madadin Gwamnati da al’ummar Jihar Katsina, yana taya Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, murnar zagayowar ranar haihuwarsa, tare da yi masa fatan ƙarin shekaru masu albarka, lafiya da kuma ci gaba da samun nasarar hidima ga ƙasa.

01/09/2026

Ana siyasa A Kano

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a yau zuwa Turai domin fara hutun makonni uku, a wani bangare na hutun...
30/08/2026

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a yau zuwa Turai domin fara hutun makonni uku, a wani bangare na hutunsa na shekara-shekara.

Tinubu zai fara hutun ne a birnin Landan na Burtaniya.

Ana sa ran shugaban zai komo Najeriya bayan kammala hutun, domin shiga cikin harkokin yakin neman zaben watan Janairun 2027,

Wache shawara yan Najeriya zasu baiwa mataimakin shi Akan wannnan matsin rayuwar da suke chiki a jaraba kafin dawowar shi,

28/08/2026

Muna bukatar Gwamna Dikko Radda ya chika mana Alkawalin da muka raka shi yankin Neman zabe Wanda yachi nasara saboda ga wani kamfen din ya dawo - Shu,aibu Scoorer Dan jamiyyar Apc a jihar katsina.

26/08/2026

Jawabin gwamna Dikko Radda a bikin sallar Gani a garin Daura ta jihar katsina
hawan sallar gani Ana yin shi ne duk shekara idan watan haihuwar manzon Allah ya K**a ranar 12 da 13 ga watan Rabi,ul Awwal ,

26/08/2026

Gwamna Radda tare da Babbar ƴar shugaban ƙasa Tinubu, Mujidat Folashade Iyaloja Tinubu, a shirye-shiryen tafiya Daura wajen naɗin da Mai Martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Faruk Umar zai yi mata.

25/08/2026


Labarai na siyasa
Labarai na Al,ajabi
Fira da yan siyasa na jamiyyu daban daban
Fira da Jami,an Gwamnati
Fira da masu Adawa
Labarai chikin natsuwa
Inganacchen Hoto
Tsabtataccen sauti
Sahihan labarai
Labarai da dumi dumin su
Labarai Akan Lokachi
Tare da tallata dukkanin Hajojin ku

Ku ziyarchi ofishin Northern Media Crew dake kan titin Nagogo Road Akan titin Kofar Durbi tsallaken masallachin Govt Printing a chikin garin katsina ko kuma ku tuntube mu Akan wadannan lambobin :

070 8453 0041
080 8671 6066
080 3954 8728.
Sai kunzo

Address

No 140 Nagogo Road Kofar Durbi Katsina
Katsina

Telephone

+2347032043337

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Northern Media Crew posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Northern Media Crew:

Shortcuts

Share