01/06/2026
Wata babbar tawaga mai ƙarfi ta Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta kai ziyara a ranar Lahadi zuwa al’ummomin Esiele da Yawota da ke Ƙaramar Hukumar Oriire a Jihar Oyo, domin jajanta wa al’ummar yankin tare da duba halin da ake ciki bayan sace ɗalibai da malamai da aka yi daga makarantu daban-daban a ranar 15 ga Mayu, 2026.
Makarantun da lamarin ya shafa sun haɗa da:
• Community Grammar School (Makarantar Sakandaren Al’umma),
• Baptist Nursery and Primary School (Makarantar Firamare da Gandun Yara ta Baptist),
• L.A. Primary School (Makarantar Firamare ta L.A.).
Ziyarar tawagar gwamnatin tarayyar ta zo ne a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnati na bibiyar lamarin, jajanta wa iyalai da al’ummomin da abin ya shafa, tare da tabbatar da cewa jami’an tsaro suna ci gaba da ɗaukar matakan da s**a dace domin ceto waɗanda aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.
Har ila yau, tawagar ta gana da shugabannin al’umma, iyayen yara da malamai, inda s**a tattauna kan yadda za a ƙara ƙarfafa tsaro a makarantu da kuma hana sake aukuwar irin wannan mummunan lamari a nan gaba. Ziyarar ta nuna damuwar Gwamnatin Tarayya da kuma aniyarta na tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin ƙasar nan.