
31/01/2025
*DARAJAR ƊAN ADAM (PART 2)*
*DAGA HAUWAU ABUBAKAR IMAM (Maman Afnan*
Cikin salo da ƙwarewar tuƙi Musa dereba ke tuƙi, shi kuwa ranka shi daɗe in ban da latse-latsen waya babu abin da yake yi.
Cinkin ƙanƙanin lokaci s**a isa gurin gagarumin taron da aka gayyace shi, cikin isa da tinƙaho na 'ya'yan manyan da s**a taso cikin daula yake tafiya daga ganin sa ka san akwai masu gida rana.
Shigarsa ɗakin taro, idanu s**a yi ca a kansa kasancewar sa gwani wajen iya saka kaya da iya tafiya ta isa. Ya samu kyakkyawar tarba da karramawa ta musamman a wurin.
Can gefen Musa dereba kuwa ya yi tagumi. Tunani fal cikin zuciyarsa da tausayin yarinyar da ya buge da kuma yadda ƙaramin yaro ɗan cikinsa ke gana masa azaba don kawai ya kasance talaka. Sam bai biyo halin mahaifinsa ba.
*FMC*
Bayan kwana biyu sannan ta farka da salati tana faɗin ina ne nan cikin razana da gigicewa take faɗin hakan.
Da sauri malaman jinyar da ke kusa s**a ƙaraso kanta suna faɗin sannu baiwar Allah, sannu kin ji. Ita kuwa sai faɗi take ina nake? Me ya same ni? Ku bar ni in tafi, ku bar ni in tafi. Ta yunƙura za ta tashi ta ji ƙafarta ta riƙe gam. Da ƙyar s**a iya jinginar da ita. Nan take wasu zafafan hawaye ke gangarowa bisa kuncinta.
Ɗaya daga cikin nas ɗin ta ce, baiwar ki yi haƙuri mota ce ta buge ki, kuma tun da aka kawo ki nan babu wanda ya zo wurin ki. Mutum ɗaya ne daga cikin waɗanda s**a kawo ki ya zo jiya shi ma ya ce ba danginki ba ne.
Nan take ta yi murmushin baƙin ciki gami da ƙara tsanar kanta da kanta.
"Baiwar Allah mene ne sunanki?" Tambayar da wata nas ta yi mata ke nan. Cikin sarƙewar murya gami da gyaɗa kai gefe guda ta ce, sunana Lubna. Faɗar hakan ke da wuya numfashinta ya sarƙe idanuwa s**a fara yin sama-sama. A gigice s**a fara kiran dakta, dakta......
*GIDAN MUSA DEREBA*
A hankali cikin natsuwa ta shigo gidan nasu wanda ko ƙyaure babu kanta ɗauke da bokitin ruwa fal, duk ta galabaita. Amma a hakan a zuciyarta tausayin mahaifiyarta ce cike da zuciyarta wanda take ayyano cewa idan ta yi kuɗi za su ji daɗi a rayuwa.
Muryar mahaifiyarta inna Mairo ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da take yi. Ta ce Hamida kin san yau itacen nan har yanzu ya ƙi kamawa wallahi, na rasa yadda zan yi. Ga shi Babanki ba ya son ya dawo gida ban idar da girki ba.
Cikin sanyin murya ta ce, Inna kawo in taya ki, yanzu zai tashi. Inna Mairo ta ce, ka ji mini ja'ira ni ban iya ba sai ke, je ki ɗauki gari ki tankaɗe kawai. Hamida ta ce to, Inna.
Sallamar Malam Musa s**a ji. Da karsahi Hamida ta miƙe don karɓar ledar da ke hannunsa gami da rusunawa ta ce, sannu da zuwa Baba. Ya ce, yauwa sannu Hamida.
Cikin natsuwa Inna Mairo ta ce, yau an ɓata wa maigida rai, a yi mini aikin gafara, ba laifina ba ne.
Malam Musa ya gyaɗa kai gami da zama a tabarmar da aka shimfiɗa masa, sannan ya ce hmmm! Ni wallahi ba na ma jin yunwar sam hankalina ba a kwance yake ba wallahi. Baki buɗe, Inna Mairo ta ce, lafiya dai ko, me ya faru?
Cikin minti 20 ya ba ta labarin abin da ya faru.
Inna Mairo ta fara tafa hannu tana faɗin, innalillahi wa innah ilaihir-rajiun. Dole jikinka ya yi sanyi, kuma dole ne a kanmu mu bincika mu gano asibitin da aka kai yarinyar ko don ka nemi gafarar ta ko. Ya ce, ai yin hakan ya zama dole.....
*WASA FARIN GIRKI*
Mai karatu mu haɗu a kashi na 3.
*TAKU HAUWAU ABUBAKAR IMAM (Maman Afnan)*
*09037234426*