NBS HAUSA 92.5FM KEFFI

NBS HAUSA 92.5FM KEFFI Tashar rediyo mai alfahari da kyawun al'umma ɗaya

Yayin da gobara ta tashi a gidan Alhaji Modibbo da ke daura da Masallacin Yarbawa, Keffi, Jihar Nasarawa.Iftila'in ya au...
30/10/2025

Yayin da gobara ta tashi a gidan Alhaji Modibbo da ke daura da Masallacin Yarbawa, Keffi, Jihar Nasarawa.

Iftila'in ya auku ne a ranar Laraba.

Gwamna Jihar Nasarawa, Abdullahi A. Sule, ya buɗe bikin al’adun gargajiya na Jihar Nasarawa karo na 22 wanda zai gudana ...
22/10/2025

Gwamna Jihar Nasarawa, Abdullahi A. Sule, ya buɗe bikin al’adun gargajiya na Jihar Nasarawa karo na 22 wanda zai gudana na tsawon makonni biyu.

Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da bikin a birnin Lafia, Gwamna Sule ya jaddada kudurin gwamnatinsa na ci gaba da bunƙasa wannan biki, yana mai cewa al’adun gargajiya na taka muhimmin rawa wajen haɗa kan al’umma da bunƙasa tattalin arziki.

TALLAFIN MINISTAR HARKOKIN MATA A KEFFI - Ko waɗanda aka shirya shirin domin su sun amfana? A ranar Juma'a, Ministar Har...
11/10/2025

TALLAFIN MINISTAR HARKOKIN MATA A KEFFI - Ko waɗanda aka shirya shirin domin su sun amfana?

A ranar Juma'a, Ministar Harkokin Mata, Iman Suleiman, ta shirya rabon raba tallafi ga al'ummar shiyyar Keffi wanda ya gudana a Keffi Square.

Kayayyakin da aka baje domin raba wa jama'a sun haɗa da: Shinkafa, kekunan ɗinki, zannuwa, tukwanen gas ɗin girki, injunan markaɗe da sauraran su.

Sai dai, da alama rabon tallafin bai samu kyakkyawan tsari ba, lamaeon da ya sa a ƙarshe jama'a s**a daka wawa a kan kayayyakin ta yadda mai rabo ka ɗauka.

Lamarin da ya sa galibin waɗanda aka gayyato daga sassa daban-daban domin cin gajiyar tallafin, haka s**a koma gida hannu-rabbana.

MENE NE RA'AYINKU KAN WANNAN BATU?

Ƙa’idojin Ma’aikatar Hajji ta Saudiyya Kan Tanadin Masauki Da Kamfanonin Hidimta Wa MahajjataDaga Ibrahim MuhammadMa’aik...
10/10/2025

Ƙa’idojin Ma’aikatar Hajji ta Saudiyya Kan Tanadin Masauki Da Kamfanonin Hidimta Wa Mahajjata

Daga Ibrahim Muhammad

Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta fitar da sabbin ƙa’idoji da ke tsara yadda ƙasashe za su ɗauki kamfanoni masu yi wa alhazai hidima da kuma yadda za su samar da masauki da abinci ga mahajjatansu a biranen Makkah da Madina yayin aikin Hajjin shekarar 2026.

Takardar da aka raba wa dukkan ofisoshin Hajji yayin kammala zagayen ƙarshe na jigilar alhazai a 2025, yanzu ita ce madogara wajen ɗaukar masu yi wa mahajjata hidima da kuma kula da walwalarsu a biranen Makka da Madina.

Muhimmin abin da aka fi jaddadawa a cikin wannan sabuwar doka shi ne taƙaita yawan kamfanonin da kowace ƙasa za ta iya ɗauka. Kamar yadda shafi na 2, sashi na 5 na ƙa’idar ya nuna: “Ofishin Hajji na ƙasa yana da ikon ƙulla yarjejeniya da kamfanoni biyu kacal; ba a yarda a wuce wannan adadi ba.”

Wannan umarni yana nufin kowace ƙasa za ta iya ɗaukar kamfanoni biyu ne kawai, ɗaya don hidima a Masha’ir da Makkah, ɗaya kuma don shirye-shiryen ƙarin hidima don tabbatar da daidaito da tsari mai inganci wajen kula da mahajjata.

Har ila yau, shafi na 2, sashi na 7 ya bayyana cewa: “Kamfanin da aka ɗauka don yi wa mahajjata hidima shi kaɗai ne ke da izinin ƙulla dukkan yarjejeniyoyi da s**a shafi masauki da abinci ga mahajjata a Makkah da Madina ta hanyar amfani dandalin Nusuk.”

A aikace, wannan yana nufin Najeriya za ta iya ɗaukar kamfanoni biyu ne kawai don aikin Hajjin 2026, ɗaya don mahajjatan jihohi, gudan kuma domin kamfanoni masu zaman kansu - duk za su gudanar da shirye-shiryen masauki da abinci ta yin amfanin manhajar Nusuk.

Masu lura da al’amura na ganin wannan sabon tsari yana nuna yadda Ma’aikatar ke ƙoƙarin haɗa dukkan ayyukan Hajji a cikin Saudiyya. Wannan tsari ya riga ya rage ayyukan wasu hukumomin Hajji na ƙasa, kamar Hukumar Hajji da Umrah ta Afirka ta Kudu (SAHUC), zuwa matsayin masu sa ido kawai yayin Hajjin 2026.

Wata majiya daga Ma’aikatar ta bayyana cewa, wannan shawara ta biyo bayan matsalolin da aka fuskanta a lokacin Hajjin 2025, inda ta buga misali da Indonesia wadda ta ɗauki kamfanoni fiye da 11 a Hajjin bara.

“Bisa wannan dalilin ne Ma’aikatar ta rage yawan kamfanonin yawon buɗe ido masu zaman kansu da ake ɗauka daga kowace ƙasa. Misali, Pakistan tana da kamfanoni kusan 965, yayin da Bangladesh ke da kusan 658. Mu’amala da irin wannan yawan kamfanoni na haifar da ƙalubale mai sosai ga Ma’aikatar,” in ji majiyar.

A cewar Ma’aikatar, sabuwar dokar na da manufar sauƙaƙa lura da aikin Hajji, inganta sa ido kan kula da alhazai da kuma hana watsewar mahajjata daga ƙasa ɗaya a wurare daban-daban a Makkah.

Inna Lillahi Wa Inna Illaihir Raji'un: Ahmad Sani Maigoro, Keffi, ya riga mu gidan gaskiya. Ya rasu ne a cikin daren da ...
10/10/2025

Inna Lillahi Wa Inna Illaihir Raji'un: Ahmad Sani Maigoro, Keffi, ya riga mu gidan gaskiya.

Ya rasu ne a cikin daren da ya gabata bayan fama da rashin lafiya na taƙaitaccen lokaci.

Da safiyar nan ake sa ran yi masa jana'iza a family house na Marigayi Alh Sani Maigoro da ke tsohuwar Mayanka, Keffi, Jihar Nasarawa.

ALLA YA JIƘAN AHMAD DA RAHMA🙏

06/10/2025

Yayin da Prince Attajiri ya karɓi baƙuncin ƙungiyar "Himma Ba Ta Ga Rago

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule ya zira ƙwallo a raga a wasa na musamman da aka shirya na bikin cikar Na...
02/10/2025

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule ya zira ƙwallo a raga a wasa na musamman da aka shirya na bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun 'yancin kai da kuma cikar Jihar Nasarawa shekaru 29 da ƙirƙiro ta.

Shekaru 12 ke nan farashin burodi bai sauya ba daga Riyal 1 a Saudiyya. Shin yaya lamarin yake a Najriya?
02/10/2025

Shekaru 12 ke nan farashin burodi bai sauya ba daga Riyal 1 a Saudiyya.

Shin yaya lamarin yake a Najriya?

HAJJI 2026: Ga tsarin farashin kujerun Hajji na bana kamar yadda  Hukumar Hajji ta Ƙasa, NAHCON ta sanar. Yayin da jihoh...
27/09/2025

HAJJI 2026: Ga tsarin farashin kujerun Hajji na bana kamar yadda Hukumar Hajji ta Ƙasa, NAHCON ta sanar.

Yayin da jihohin Arewa za su biya miliyan N8,244,813.67, su kuwa jihohin Kudu miliyan N8,561,013.67 za su biya.

Sannan jihohin Yobe, Borno, Adamawa da Taraba, su biya miliyan N8,118,333.67.

25/07/2025

A Sada Zumunta Ga Mutum 10

MENE NE RA'AYINKU?Ta tabbata cewa, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya fice daga Jam'iyar PDP.Shin ko fice...
16/07/2025

MENE NE RA'AYINKU?

Ta tabbata cewa, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya fice daga Jam'iyar PDP.

Shin ko ficewar tasa za ta yi wa PDP illa?

16/07/2025

Address

Keffi-Akwanga Road
Keffi

Telephone

+2348087615698

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NBS HAUSA 92.5FM KEFFI posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category