SalihuAbdullahi

SalihuAbdullahi Labari Da Dumin-Dumin Sa

MASHA ALLAHU! BABBAR GUDUMMUWAR MASHUNA GUDA BAKWAI (7) GA JAMA'A DA KWAMITIN HIZBA.A yau Lahadi, 22/02/2026, Mai Girma ...
22/02/2026

MASHA ALLAHU! BABBAR GUDUMMUWAR MASHUNA GUDA BAKWAI (7) GA JAMA'A DA KWAMITIN HIZBA.

A yau Lahadi, 22/02/2026, Mai Girma Alhaji Mohammed Bello Koko II, Sarkin Koko, ya sake nuna kulawa da karamci ga al’ummarsa ta hanyar bayar da mashuna kirar Daylong guda bakwai (7) ga wasu manyan jama’a da ma’aikatan Masarautar Koko tare da Kwamitin Hizba na yankin Koko.

Wannan babbar kyauta an yi ta ne domin saukaka musu harkokinsu na yau da kullum da kuma kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyukansu cikin sauki da inganci.

Wadanda s**a amfana da wannan babbar gudummawa sun hada da:

1. Babban Limamin Garin Koko
2. Sabon Hakimin Baraya
3. Kwamitin Hizba Koko
4. Alhaji Bala Yaro
5. Abo Sarkin Dogarai
6. Sani Gwabji Sarkin Gida
7. Isah Siga

Hakika, baiwa Sabon Hakimin Baraya wannan mashin na musamman wata babbar alama ce ta karfafa masa guiwa da goyon baya, domin ya samu damar gudanar da ayyukan masarauta cikin kwanciyar hankali da sauki.

Wannan kyauta mai dimbin daraja tana kara tabbatar da irin kulawa, tausayi da jajircewar da Mai Girma Sarkin Koko ke nunawa ga al’ummarsa. Lallai samun shugaba mai hangen nesa, karamci da kishin jama’a k**ar Mai Girma Sarkin Koko babbar ni’ima ce ga Masarautar Koko.

Muna kara jinjinawa Mai Girma bisa wannan gagarumar kokari da ya yi, wanda ya kara kusantar da shugabanci da al’umma tare da bunkasa ayyukan tsaro da masarauta a yankin.

Allah ya saka wa Mai Girma Sarkin Koko da alkhairi, ya kara masa lafiya, hikima da jagoranci nagari.
Allah ya kara daukaka Masarautar Koko.

Haka kuma muna addu’ar Allah ya kara wa Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris (Kauran Gwandu), taimako da jagora wajen sauke nauyin da aka dora masa.

Masarautar Sarkin Koko
22/02/2026

GUDUMMUWAR MOTA ZUWA GA WAKILIN MAI GIRMA SARKIN KOKOA yau Lahadi, 22/02/2026, Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Be...
22/02/2026

GUDUMMUWAR MOTA ZUWA GA WAKILIN MAI GIRMA SARKIN KOKO

A yau Lahadi, 22/02/2026, Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, ya kara nuna karamci, girmamawa da kulawa ta musamman ga Wakilin Sa, Alhaji Musa Salihu Koko (Dan Galadiman Koko), ta hanyar ba shi sabuwar mota domin kara saukaka masa gudanar da ayyukan Masarautar Koko cikin nagarta, kwazo da kwarewa.

Wannan kyauta ba kawai tallafi ba ce, illa wata shaida ce ta amana, yarda da kuma girmamawar da Mai Girma Sarkin Koko ke yi wa Wakilin Sa, bisa irin jajircewa da yake nunawa wajen hidimtawa Masarauta da al’umma baki daya.

Hakika, wannan gudummawa za ta kara masa kuzari da himma wajen ci gaba da wakiltar Masarautar Koko da mutunci, tare da tabbatar da cewa ayyukan alheri da cigaban al’umma suna tafiya yadda ya k**ata.

Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya saka wa Mai Girma Sarkin Koko da alkhairi mai yawa, Ya kara masa lafiya, nisan kwana da basira wajen jagorantar al’umma. Haka kuma Allah Ya taimaki Wakilin Sa, ya kara Mai Lafiya Da nisan kwana Amin.

Masarautar Sarkin Koko
22/02/2026

BABBAR GUDUMMUWAR SABABBIN MASHUNA KIRAR DAYLONG ZUWA GA JAMI’AN TSARO NA MASARAUTAR KOKODomin ƙara inganta tsaro da tab...
22/02/2026

BABBAR GUDUMMUWAR SABABBIN MASHUNA KIRAR DAYLONG ZUWA GA JAMI’AN TSARO NA MASARAUTAR KOKO

Domin ƙara inganta tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin Masarautar Koko, a yau Lahadi, Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, ya bai wa jami’an tsaro na yankin sabbin mashuna kirar Daylong domin sauƙaƙa musu wajen gudanar da ayyukansu.

Wannan gagarumar gudummawa na da nufin ƙarfafa jami’an tsaro tare da ƙara musu kuzari wajen tabbatar da tsaro, kare rayuka da dukiyoyin al’umma, da kuma bunƙasa zaman lafiya a Masarautar Koko.

Jami’an Tsaron da s**a amfana sun haɗa da:
1. DSS
2. NDLEA
3. S.I.B

An miƙa mashinan ga shugabannin kowanne sashe na jami’an tsaron da s**a amfana da wannan kyauta.

Hakika, samun shugaba nagari k**ar Mai Girma Sarkin Koko a cikin al’umma babbar ni’ima ce da baiwa ta musamman daga Allah. Wannan aiki nasa ya sake nuna kishin al’umma, jajircewa da sadaukarwa wajen cigaban Masarautar Koko.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara masa lafiya, basira da jagoranci nagari.
Allah Ya ƙara taimakon Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), Ya saka masa da alkhairi, Amin.

Masarautar Sarkin Koko
22/02/2026

KYAWON ALKAWALI CIKAWAAL’UMMAR GARIN DAN DASHE SUN KAWO ZIYARAR GODIYA A FADAR MAI GIRMA SARKIN KOKOA yau Asabar, al’umm...
21/02/2026

KYAWON ALKAWALI CIKAWA

AL’UMMAR GARIN DAN DASHE SUN KAWO ZIYARAR GODIYA A FADAR MAI GIRMA SARKIN KOKO

A yau Asabar, al’ummar Garin Dan Dashe sun kai ziyarar bangirma da godiya zuwa fadar Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, domin nuna farin ciki da jin dadinsu bisa alkawalin da ya dauka a gare su kuma ya cika.

Tun a baya Mai Girma Sarkin Koko ya dauki alkawalin kammala ginin Babban Masallacin garin Dan Dashe. Cikin ikon Allah Madaukakin Sarki, an kammala aikin k**ar yadda aka tsara, lamarin da ya sanya al’ummar garin s**a fito domin nuna godiya da jinjina ga jagorancin sa na gaskiya da rikon amana.

A yayin ziyarar, al’ummar sun bayyana cewa cikawar wannan alkawali ya kara musu kwarin gwiwa da yakini a kan nagartar shugabanci da kulawar Mai Girma Sarkin Koko ga al’ummarsa. Sun kuma yi masa addu’ar samun nasara, karin lafiya da kuma dorewar zaman lafiya a Masarautar Koko.

Muna rokon Allah (SWT) ya kara taimakon Mai Girma Sarkin Koko, ya ba shi lafiya, basira da jagoranci nagari. Amin.

Masarautar Sarkin Koko
21/02/2026

KWAMITIN ZAKKA DA SADAKA NA MASARAUTAR KOKO, SUN YI ZAMA NA MUSAMMAN DA MAI GIRMA SARKIN KOKO, YA BADA GUDUMMUWAR NAIRA ...
18/02/2026

KWAMITIN ZAKKA DA SADAKA NA MASARAUTAR KOKO, SUN YI ZAMA NA MUSAMMAN DA MAI GIRMA SARKIN KOKO, YA BADA GUDUMMUWAR NAIRA MILIYAN BIYAR (5,000,000) DON TAIMAKA WA MARAYU DA GAJIYAYYU.

A yau Laraba, 18/02/2026, Kwamitin Zakka da Sadaka na Masarautar Koko sun gudanar da zama na musamman da Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, a fadarsa, domin tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi tattara da rabon Zakka da Sadaka a wannan wata mai alfarma na Azumin Ramadan.

A watannin da s**a gabata, Mai Girma Sarkin Koko ya umarci kwamitin da su zagaya wajen masu hannu da shuni domin karɓar Zakka da Sadaka, k**ar yadda aka yi a shekarar bara, da nufin tallafawa marayu da gajiyayyu wajen samun abinci da sauran bukatun yau da kullum a cikin watan Ramadan.

A yayin zaman, kwamitin ya gabatar da cikakken bayani ga Mai Girma Sarkin Koko kan nasarorin da s**a samu, tare da bayyana irin gudummawar kuɗi da kayan abinci da aka tara daga masu hannu da shuni. A shekarar da ta gabata, kwamitin ya kasance na farko wajen ƙoƙari da jajircewa, wanda hakan ya sa Kwamitin Zakka da Sadaka na Jihar Kebbi ya yaba musu a taron gabatar da kayan tallafi ga marayu da gajiyayyu a Masarautar Koko.

A nasa jawabin, Mai Girma Sarkin Koko ya jinjina wa kwamitin bisa irin ƙwazo da gaskiya da s**a nuna wajen sauke nauyin da aka dora musu. Haka kuma, ya bada babbar gudummawar Naira Miliyan Biyar (₦5,000,000) domin ƙara ƙarfafa ayyukan tallafawa al’umma a wannan wata mai daraja.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki ya saka wa Mai Girma Sarkin Koko da alheri, ya ƙara masa lafiya da nisan kwana, ya ƙara ɗaukaka da jagoranci nagari. Amin.

Masarautar Sarkin Koko
18/02/2026

TAFSIRIN AL-QUR’ANI MAI GIRMA NA FARKON WATAN AZUMIN RAMADANLaraba, 18/02/2026Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bel...
18/02/2026

TAFSIRIN AL-QUR’ANI MAI GIRMA NA FARKON WATAN AZUMIN RAMADAN
Laraba, 18/02/2026

Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, a yau Laraba, daya ga watan Azumin Ramadan, ya kai ziyara zuwa Babban Masallacin Juma’a na Garin Koko da ke harabar fadarsa, domin sauraren Tafsirin Al-Qur’ani Mai Girma.

Ziyarar ta kasance cikin yanayi na ibada da natsuwa, inda Mai Girma Sarkin Koko ya hada kai da al’ummar Musulmi wajen sauraron bayanai da nasihohi daga Al-Qur’ani Mai Tsarki, domin karfafa imani da inganta rayuwar al’umma.

Muna rokon Allah Maɗaukakin Sarki Ya kara wa Mai Girma Sarkin Koko lafiya da nisan kwana.
Allah Ya kara masa taimako da jagoranci nagari. Allah Ya tabbatar da zaman lafiya da ci gaban Masarautar Koko baki daya. Amin.

Daga
Masarautar Sarkin Koko
18/02/2026

GIDAUNIYAR SARKIN KOKO MALAM MUSA FOUNDATION, TA KADDAMAR DA FARA RABON ABINCIN AZUMIN RAMADAN, WANDA TASABA DA YI DUK S...
17/02/2026

GIDAUNIYAR SARKIN KOKO MALAM MUSA FOUNDATION, TA KADDAMAR DA FARA RABON ABINCIN AZUMIN RAMADAN, WANDA TASABA DA YI DUK SHEKARA, A CIKIN WANNAN WATAN MAI DARAJA, DON SAUKAKAMA AL'UMMA WAJEN NEMAN ABINCI.

Shahararriyar Gidauniyar nan mai suna
Sarkin Koko Malam Musa Foundation, karkashin jagorancin Mai Girma Sarkin Koko, ALH. MOHAMMED BELLO KOKO II, da Mai girma Ciroman Koko, ALH. SHEHU MOHAMMED BELLO KOKO, ta kaddamar da rabon abincin azumin watan Ramadan, Wanda tasaba da yi duk shekara acikin wannan watan mai daraja, inda a yau talata 17/02/2026, anfara rabawa al'umma wannan abinci, domin saukaka musu wajen neman abinci acikin wannan watan mai daraja, duba da yanayin tsadar rayuwa, inda ankafara rabawa Malamai, Limamai, Hakimai da ke yankin Masarautar Koko.

Bisaga yadda wannan Gidauniyar ke rabon abincin duk shekara irin wannan watan, wagga shekarar, Shuwagabannin ta sun kara, fadada rabon abincin, ta yadda zai kara kai ga al'umma, inda sunka umurci duk wani hakimi dake karkashin Masarautar Koko, irin su Hakimin Tudu, Hakimin Firchin, Hakimin Bayara, Hakimin Dada, da Magajin Gari, da su je, su kara zakulo mabukata domin ganin abincin yakara kai garesu don a saukaka musu neman abinci a wannan watan mai daraja, a halin yanzu, za'a sake raba abincin a garkar Wadannan hakimai Kamar yadda ankayi shekarar da tagaba, bisaga sunayen mabukata da anka umurcesu s**ara zakulowa.

Za'a raba abincin ne zuwa ga:-
1. Marayu da Zaurunoni, Wadan da aka umurci hakimai su zakulo.
2. Limammai da Malamai
3. Al'ummar Garin Koko da kewaye
4. Al'ummar yankin Besse
5. Al'ummar yankin Maiyama
6. Al'ummar da ke cikin gundumomi goma sha biyu na yankin Koko-Besse (12 Wards).
7. Kungiyoyi
8. Musakai, Kamar Guragu, Makahi, da Kutare
9. Uwayen Kasar yankin Koko-Besse da Hakiman Masarautar Koko.

Bayan kuma wannan gidauniyar mai fafutuka kan al'umma, ta buda wajen bayar da abincin buda baki guda goma Sha hudu (14), ga al'ummar da ke tsakanin yankin Koko, Besse da kuma Maiyama, domin saukakamusu wajen neman abincin buda baki wanda takeyi duk shekara. A kowane wuri guda, za a ciyar da mutanen a kalla mutun dari (100) a kullum, mutane dubu daya da dari Hudu (1,400) kenan a kowace rana, har kwana 30 na Ramadan, inda jimlar mutanen da zasu ciyar ta k**a mutane dubu arba'in da biyu (42,000) a cikin wannan watan mai alfarma na Ramadan, inda gobe larba 18/02/2026, Daya ga watan na Ramadan.

Daga cikin abincin da suke ciyarwa a kowane mazauni, akwai:- Shinkafa/Kwai da Ruwan Sanyi da Kuma Kunu/Kosai da Ruwan Sanyi a kowace Rana.

Haka zalika wannan gidauniyar ta bude wasu wurare guda uku (3) a cikin Garin Birnin kebbi, Kamar yadda sunka sabayi duk Shekara don ciyar da Al'umma abincin buda baki, inda za'a ciyar da mutun 100 a kowane waje, mutun 300 kenan a rana, mutane 9000 kenan a watan azumin Ramadana. Daga cikin abincin da suke ciyarwa a kowane mazauni, akwai:- Shinkafa/Kwai da Ruwan Sanyi da Kuma Kunu/Kosai da Ruwan Sanyi a kowace Rana.

Al'umma sun nuna farincikin su, bisa ga wannan babbar gudummuwar da akabasu domin saukakamusu wajen neman abinci acikin wannan watan mai daraja. Samun irin wadannan Shuwagabanni na wannan Gidauniyar Mai fafutuka don nemo hanyoyin da zasu kawo sauki ga Al'umma, bakaramin baiwa bace ga al'ummar yankin, duba da irin gudummuwar da sukeba al'ummar su.

Muna rokon Allah ya sak**a wadannan Shuwagabanni da alkhairi Amin, Allah ya kara taimakon su, a duk inda suke, Allah kabiya musu bukatun su na alkhairi Amin.

Sarkin koko Malam Musa Foundation.
17_02_2026

SHAHARARRIYAR GIDAUNIYAR SARKIN KOKO MALLAM MUSA FOUNDATION TA BUƊE WURAREN SHAN RUWAN WATAN RAMADAN GOMA SHA HUDU (14) ...
16/02/2026

SHAHARARRIYAR GIDAUNIYAR SARKIN KOKO MALLAM MUSA FOUNDATION TA BUƊE WURAREN SHAN RUWAN WATAN RAMADAN GOMA SHA HUDU (14) KAMAR YADDA AKA SABA DUK SHEKARA, DA KUMA GUDA UKU A CIKIN GARIN BIRNIN KEBBI, DOMIN SAUKAƘAMA AL’UMMA

Shahararriyar gidauniya mai suna Sarkin Koko Malam Musa Foundation, ƙarƙashin jagorancin Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II da Mai Girma Ciroman Koko, Alhaji Shehu Mohammed Bello Koko, ta buɗe wurare goma sha huɗu (14) da Kuma wasu guda uku (3) a cikin Garin Birnin kebbi, Kamar yadda s**a Saba duk Shekara, domin bayar da abincin shan ruwa kyauta ga al’umma a wannan wata mai albarka na Ramadan. wannan tallahi anyi shekaru bakwai anayi.

Wannan shiri na sadaka fisabilillah ya zama al’ada a duk shekara, inda gidauniyar ke ƙoƙarin sauƙaƙama al’umma wajen samun abincin buɗa-baki cikin sauƙi ba tare da wata wahala ba.

Wuraren da aka tanada domin buɗa-baki sun haɗa da:

1. Masallacin Sarki Muhammadu Bello Koko a koko
2. Masarautar Sarkin Koko
3. Masallacin Juma’ar Besse
4. Masallacin Juma’ar Garin Damba
5. Masallacin Juma’ar Dutsin Mari
6. Babbar Asibitin Koko (GH Koko)
7. Masallacin Juma’ar Maiyama
8. Kofar Gidan Magajin Garin Koko
9. Kofar Gidan Baraya Koko
10. Kofar Gidan Firchin Koko
11. Shagon Goro Giwatazo
12. Bayan NEPA Office, Koko
13. Kofar Gidan Sarkin Gobir, Dada
14. Mallamawa Koko

A kowanne wuri, za a ciyar da mutum 100 a kullum, mutane 1,400 a kowace rana. wanda ya k**a mutane 42,000 cikin kwanaki 30 na wannan wata mai albarka.

za a bada Shinkafa, ƙwai tare da ruwan sanyi. Da kuma Kunu, kosai tare da ruwan sanyi.

Haka zalika akwai wurare guda uku a cikin Garin Birnin kebbi da za'a bayar da abinci ga mutane 100 a kowane waje, mutun 300 kenan a rana, yawan 9,000 kenan cikin kwana 30 a watan Ramadana. suma za a bayarda Shinkafa, ƙwai tare da ruwan sanyi, Kunu, kosai da ruwan sanyi.

Hakika, samun shugabanni masu tausayi da kishin al’umma irin su Mai Girma Sarkin Koko da Mai Girma Ciroman Koko babbar baiwa ce daga Allah. Wannan aiki na alheri shaida ce ta jajircewarsu wajen talladawa.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara ɗaukaka wannan gidauniya mai albarka, Ya saka wa shugabanninta da mafificin alkhairi, Ya ninka musu lada, Ya kuma sanya wannan aiki a ma’aunin hasanarsu. Amin.

Ciroman Koko Media Team
16/02/2026

14/02/2026

Sarkin Ruwan Argungu, Makwashen Argungu Acikin Ruwan Matan Fada kafin asoma gasar Kamun kifi. Sarkin Ruwa Makwashe Dan Makwashe.

14/02/2026

Video wajen bikin kamun kifi na Argungu dake jihar Kebbi, Allah yasa agama Lafiya Amin.

14/02/2026

Argungu Fishing Festival an kandama ruwa

14/02/2026

Tamburan Yaki na Masarautar Sarkin Kabi ila

Address

Koko

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SalihuAbdullahi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share