28/09/2025
Sabon Sarkin Zuru, Mai Martaba Sanusi Mikailu Sami, Ya Kai Ziyarar Godiya Ga Gwamnan Jahar Kebbi Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu.
Sabon Sarkin Zuru da aka zaɓa kuma aka rantsar, Mai Martaba Alhaji Sanusi Mikailu Sami, a ranar Lahadi, 28 ga Satumba, 2025, ya kai ziyarar godiya ta musamman ga Mai Girma, Dr. Nasir Idris, Kauran Gwandu, Gwamnan Jihar Kebbi, a Masaukin Fadar Shugaban Ƙasa, dake Birnin Kebbi.
Ziyarar ta biyo bayan nasarar da ya samu a matsayin Sarkin Zuru, bayan rasuwar magabacinsa, marigayi Mai Martaba Alhaji Sani Sami Gomo.
A jawabin da ya gabatar, Sarkin ya nuna matuƙar godiya ga Gwamna da kuma al’ummar Jihar Kebbi bisa goyon bayan da s**a nuna masa. Ya jaddada cewa al’ummar Zuru suna cike da farin ciki da alfahari da hawansa kan karagar mulki, tare da tabbatar da aniyarsa ta tafiyar da mulki bisa adalci, gaskiya da kuma hidima ga jama’a.
Mai Girma Gwamna Nasir Idris Kauran Gwandu ya tarbi Sarkin cikin farin ciki tare da taya shi murna bisa sabon mukamin da Allah Ya ɗora masa, inda ya yi addu’a domin samun zaman lafiya da jagoranci mai albarka, wanda zai ƙara haɗin kai, ci gaba da bunƙasar Zuru Emirate da kuma Jihar Kebbi baki ɗaya.
Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Kebbi, Rt. Hon. Usman Muhammad Ankwe, shi ne ya yi maraba da Sarkin tare da tawagarsa. Haka kuma, Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, dattijon ƙasa tsohon Janar mai ritaya Muhammad Magoro, Sakataren Gwamnati, Shugaban Ma’aikata, Kwamishinoni, Mashawarta na Musamman, Shugabannin Kananan Hukumomi, da sauran manyan baki daga ciki da wajen jihar sun halarta.
Allah ya kara taimakon Mai girma gwamnan jahar kebbi DR NASIR IDRIS KAURAN GWANDU Amin, Allah ya kara bashi nasara cikin sauki Amin.
Daga:
Ƙungiyar Ƙafafen Yaɗa Labarai ta Ciroman Koko
28/09/2025