22/02/2026
MASHA ALLAHU! BABBAR GUDUMMUWAR MASHUNA GUDA BAKWAI (7) GA JAMA'A DA KWAMITIN HIZBA.
A yau Lahadi, 22/02/2026, Mai Girma Alhaji Mohammed Bello Koko II, Sarkin Koko, ya sake nuna kulawa da karamci ga al’ummarsa ta hanyar bayar da mashuna kirar Daylong guda bakwai (7) ga wasu manyan jama’a da ma’aikatan Masarautar Koko tare da Kwamitin Hizba na yankin Koko.
Wannan babbar kyauta an yi ta ne domin saukaka musu harkokinsu na yau da kullum da kuma kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyukansu cikin sauki da inganci.
Wadanda s**a amfana da wannan babbar gudummawa sun hada da:
1. Babban Limamin Garin Koko
2. Sabon Hakimin Baraya
3. Kwamitin Hizba Koko
4. Alhaji Bala Yaro
5. Abo Sarkin Dogarai
6. Sani Gwabji Sarkin Gida
7. Isah Siga
Hakika, baiwa Sabon Hakimin Baraya wannan mashin na musamman wata babbar alama ce ta karfafa masa guiwa da goyon baya, domin ya samu damar gudanar da ayyukan masarauta cikin kwanciyar hankali da sauki.
Wannan kyauta mai dimbin daraja tana kara tabbatar da irin kulawa, tausayi da jajircewar da Mai Girma Sarkin Koko ke nunawa ga al’ummarsa. Lallai samun shugaba mai hangen nesa, karamci da kishin jama’a k**ar Mai Girma Sarkin Koko babbar ni’ima ce ga Masarautar Koko.
Muna kara jinjinawa Mai Girma bisa wannan gagarumar kokari da ya yi, wanda ya kara kusantar da shugabanci da al’umma tare da bunkasa ayyukan tsaro da masarauta a yankin.
Allah ya saka wa Mai Girma Sarkin Koko da alkhairi, ya kara masa lafiya, hikima da jagoranci nagari.
Allah ya kara daukaka Masarautar Koko.
Haka kuma muna addu’ar Allah ya kara wa Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris (Kauran Gwandu), taimako da jagora wajen sauke nauyin da aka dora masa.
Masarautar Sarkin Koko
22/02/2026