SalihuAbdullahi

SalihuAbdullahi Labari Da Dumin-Dumin Sa

Kanada Ta Tabbatar Najeriya A Matsayin Muhimmin Abokiyar Hulɗa A Nahiyar Afirka – Bagudu Ya Ce Zuba Jari Ya Fi Tallafi A...
29/07/2026

Kanada Ta Tabbatar Najeriya A Matsayin Muhimmin Abokiyar Hulɗa A Nahiyar Afirka – Bagudu Ya Ce Zuba Jari Ya Fi Tallafi Amfani

Jakadan riƙo na Babban Ofishin Jakadancin Kanada a Najeriya, Dr. David Sproule, ya bayyana cewa Najeriya na daga cikin manyan ƙasashen da Kanada ke bai wa muhimmanci a Afirka. Ya ce ƙasarsa za ta ci gaba da haɗin gwiwa da Najeriya domin bunƙasa tattalin arziki, samar wa matasa aikin yi, ƙarfafa kamfanoni masu zaman kansu, yaƙi da sauyin yanayi, da kuma inganta hukumomin gwamnati.

Dr. Sproule ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, a hedikwatar ma’aikatar da ke Abuja.

Ya ce Kanada ta ware sama da dala miliyan 127 domin tallafawa Najeriya a shekarar 2024 zuwa 2025, ta hanyar shirye-shirye daban-daban da s**a haɗa da bunƙasa tattalin arziki, daidaiton jinsi, kiwon lafiya, yaƙi da sauyin yanayi, da ƙarfafa cibiyoyin gwamnati.

A cewarsa, sabuwar manufar Kanada game da Afirka ba ta taƙaita ga bayar da tallafi kawai ba, tana kuma ƙarfafa zuba jari, samar da ƙwarewa ga matasa, da bunƙasa harkokin kasuwanci.

Da yake mayar da martani, Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya yabawa Kanada bisa ci gaba da haɗin gwiwa da Najeriya, yana mai cewa dangantakar ƙasashen biyu ta ginu ne kan mutunta juna da kuma burin ci gaba.

Bagudu ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na ci gaba da aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki domin jawo masu zuba jari, ƙara damar kasuwanci, da rage talauci.

Ya jaddada cewa zuba jari ya fi amfani ga Najeriya fiye da karɓar tallafi, domin hakan yana samar da ci gaba mai ɗorewa da kuma ƙarin ayyukan yi ga al'umma.

Ministan ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da Shirin Ci gaban Ward na Renewed Hope, wanda zai tsara bukatun ci gaba a dukkan ƙananan yankuna 8,809 na Najeriya, domin gwamnati da abokan hulɗa su san inda ake buƙatar ayyukan ci gaba, su guji maimaita aiki, kuma su tabbatar da cewa ci gaba ya kai ga al'umma.

Bagudu ya gayyaci Kanada da kamfanoninta masu zaman kansu su zo su zuba jari a Najeriya, yana mai cewa ci gaban ƙasa ba zai samu ba sai da haɗin kan gwamnati, masu zuba jari, da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa.

Ya ƙara da cewa gyare-gyaren da gwamnati ke yi sun fara jawo hankalin masu zuba jari, tare da ƙara inganta yanayin kasuwanci da tattalin arziki.

Haka kuma ya ce Najeriya na ci gaba da samun manyan jarin gine-gine da sauran ayyukan raya ƙasa, kuma tana ƙoƙarin zama ƙasa mai jan hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

Bagudu ya ce yana da muhimmanci a riƙa bayyana nasarorin Najeriya ga duniya, domin dimokuraɗiyyar ƙasar da sauye-sauyen tattalin arzikinta na zama abin koyi ga sauran ƙasashe.

A ƙarshe, bangarorin biyu sun tabbatar da aniyarsu ta ci gaba da haɗin gwiwa wajen bunƙasa tattalin arziki, samar wa matasa damar aiki, da ƙarfafa dangantakar Najeriya da Kanada.

Ciroman Koko Media Team
29/07/2026

29/07/2026
ZIYARAR BANGIRMA DA NEMAN GOYON BAYA DOMIN ƘARFAFA NASARAR JAM'IYYAR APC A YANKIN KOKO-BESSE GABANIN ZAƁEN 2027Dan takar...
24/07/2026

ZIYARAR BANGIRMA DA NEMAN GOYON BAYA DOMIN ƘARFAFA NASARAR JAM'IYYAR APC A YANKIN KOKO-BESSE GABANIN ZAƁEN 2027

Dan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Kebbi mai wakiltar Koko-Besse a ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Hon. Abdurrahman Mamuda Wafa Koko (Giwa), tare da tawagarsa, sun kai ziyarar bangirma da neman shawarwari ga Mai Girma Ciroman Koko, Alhaji Shehu Mohammed Bello Koko (Shehu Fari) a Babban Birnin Tarayya, Abuja, ranar Alhamis, 23 ga Yuli, 2026.

wannan ziyara don neman shawarwari tare da neman ci gaba da samun goyon baya da gudummawar Mai Girma Ciroman Koko, wanda ya kasance daya daga cikin manyan jiga-jigan APC da s**a taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarorin da Jam'iyyar APC ta samu a yankin Koko-Besse da maiyama a zabukan da s**a gabata.

A yayin tattaunawar, an yi nazari kan muhimman dabarun da za su ƙara ƙarfafa haɗin kai a tsakanin shugabanni, magoya baya da mambobin jam'iyya, domin tabbatar da cewa Jam'iyyar APC ta samu nasara a babban zaɓen shekarar 2027.

Tawagar ta kuma roƙi Mai Girma Ciroman Koko da ya ci gaba da ba da irin gudummawa, shawarwari da goyon bayan da ya saba bai wa Jam'iyyar APC da 'yan takarar Jam'iyyar APC daga matakai daban-daban a yankin Koko-Besse domin samun nasara a zaɓe mai zuwa.

A nasa jawabin, Mai Girma Ciroman Koko, Alhaji Shehu Mohammed Bello Koko (Shehu Fari) ya tabbatar da cewa zai ci gaba da bai wa Jam'iyyar APC da dukkan 'yan takararta goyon baya da gudummawar da za ta taimaka wajen samun gagarumar nasara a zaɓen shekarar 2027.

Ya bayyana cewa wannan matsaya ta samo asali ne daga gamsuwarsa da irin ayyukan alheri, ci gaba da sauye-sauyen da Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu) ke aiwatarwa domin inganta rayuwar al'ummar jihar. Saboda haka, ya bayyana aniyarsa ta yin duk mai yiwuwa domin ganin Gwamnan ya samu damar komawa kan mulki a karo na biyu, tare da tabbatar da nasarar dukkan 'yan takarar Jam'iyyar APC domin su ci gaba da tafiyar da manufofin ci gaba da s**a amfani al'ummar Jihar Kebbi.

Haka kuma, an tattauna muhimmancin bai wa matasa dama a harkokin siyasa, tare da ƙarfafa su su shiga a dama da su wajen jagoranci da ayyukan jam'iyya. An jaddada cewa matasa su ne ginshiƙin nasarar kowace jam'iyya, kuma haɗin kansu, jajircewarsu da kishinsu za su taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar APC a zaɓen shekarar 2027.

A ƙarshe, tawagar ta yaba da kyakkyawar tarbo, shawarwari masu amfani da kuma jajircewar Mai Girma Ciroman Koko wajen haɗa kan al'umma da ci gaba da tallafa wa Jama'a da APC. Sun bayyana cewa irin wannan haɗin kai da goyon baya zai zama babban ginshiƙi na samun nasarar jam'iyyar da dukkan 'yan takararta a babban zaɓen shekarar 2027.

Haɗin Kai, Goyon Baya da Kyakkyawan Tsari Su Ne Mabuɗin Nasarar APC a Koko-Besse da Jihar Kebbi a 2027.

Ciroman Koko Media Team
24/07/2026

A MADADIN MAI GIRMA SARKIN KOKO, ALHAJI MOHAMMED BELLO KOKO II, DA DAUKACIN AL'UMMAR MASARAUTAR KOKO, ANA MIƘA SAƘON TAY...
22/07/2026

A MADADIN MAI GIRMA SARKIN KOKO, ALHAJI MOHAMMED BELLO KOKO II, DA DAUKACIN AL'UMMAR MASARAUTAR KOKO, ANA MIƘA SAƘON TAYA MURNA GA CP DANBABA MOHAMMED BISA SAMUN MUƘAMIN COMMISSIONER OF POLICE (CP)

Da sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Ƙai.

Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, tare da daukacin al'ummar Masarautar Koko, suna miƙa saƙon taya murna ta musamman ga ɗaya daga cikin fitattun 'ya 'yan Al'ummar Masarautar Koko, CP Danbaba Mohammed bisa wannan babban matsayi da Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙaddara masa na zama Commissioner of Police (CP) a Rundunar 'Yan Sandan Najeriya.

Wannan ɗaukaka ba ta tsaya a gare ka kaɗai ba; ɗaukaka ce ga iyalanka, Masarautar Koko, Jihar Kebbi da kuma ƙasa baki ɗaya. Haƙiƙa, wannan ci gaba ya tabbatar da cewa ƙwazo, jajircewa, biyayya ga doka da riƙon amana su ne ginshiƙan samun nasara.

Mai Girma Sarkin Koko yana addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara maka lafiya, hikima, basira da ƙarfin guiwa domin gudanar da wannan babban nauyi cikin adalci, gaskiya da kishin ƙasa. Allah Ya sanya wannan matsayi ya zama sanadin ƙarin ɗaukaka da nasarori a rayuwarka.

A madadin Masarautar Koko baki ɗaya, muna kuma bayyana matuƙar godiya da yabawa gare ka bisa irin gudummawar da kake bayarwa wajen taimakawa matasan Masarautar Koko su samu shiga cikin Rundunar 'Yan Sandan Najeriya. Wannan kyakkyawan aiki da kake yi ya nuna ƙaunarka ga al'ummarka da kuma kishinka na ganin matasa sun samu aikin yi da kyakkyawar makoma.

Jama'a basu mantawa da waɗanda aka share musu hanya zuwa ga ci gaba. Saboda haka, Masarautar Koko tana alfahari da kai, kuma tana yabawa tare da godiya bisa wannan gagarumar gudummawa da kake ci gaba da bayarwa.

Muna roƙon Allah (SWT) Ya ci gaba da tsare ka, da daukaka, Ya ba ka ikon ci gaba da yi wa Najeriya, jahar kebbi da al'umma hidima cikin gaskiya, adalci da riƙon amana.

Muna sake taya ka murna, muna yi maka fatan alheri da ƙarin nasarori a gaba. Allah Ya ƙara ɗaukaka da arziki. Amin.

Allah Ya kiyaye Mai Girma Sarkin Koko, Ya ɗaukaka Masarautar Koko da jahar kebbi Ya kuma ci gaba da baka nasara. Ameen

Masarautar Sarkin Koko
22/07/2026

HAKIMAI, MALAMAI DA LIMAMAN MASARAUTAR KOKO SUN GUDANAR DA ADDU'AR CIKA SHEKARA UKU DA RASUWAR MARIGAYI MAI GIRMA SARKIN...
21/07/2026

HAKIMAI, MALAMAI DA LIMAMAN MASARAUTAR KOKO SUN GUDANAR DA ADDU'AR CIKA SHEKARA UKU DA RASUWAR MARIGAYI MAI GIRMA SARKIN KOKO, MALAM MOHAMMADU BELLO KOKO NA I

A yau, 21 ga Yuli, 2026, ya cika shekaru uku da rasuwar Marigayi Mai Girma Sarkin Koko, Malam Mohammadu Bello Koko Na I, wanda ya rasu a ranar 21 ga Yuli, 2023.

Domin tunawa da wannan rana, Hakimai, Malamai da Limaman Masarautar Koko sun gudanar da addu'o'i na musamman, suna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki da Ya gafarta masa kurakuransa, Ya yalwata masa rahama, Ya sanya kabarinsa ya zama lambu daga cikin lambunan Aljanna, Ya haskaka masa kabari, Ya kuma ba shi matsayi mafi girma a Aljannatul Firdausi.

Haka kuma, an yi addu'ar Allah Ya ba iyalansa, Masarautar Koko da al'ummar Musulmi baki ɗaya haƙurin jure rashinsa, Ya kuma ci gaba da ɗaukaka Masarautar Koko cikin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba.

Allah Ya jiƙan Marigayi Mai Girma Sarkin Koko, Malam Mohammadu Bello Koko Na I. Allah Ya gafarta masa, Ya karɓi kyawawan ayyukansa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya jiƙan dukkan Musulman da s**a riga mu gidan gaskiya. Amin Ya Rabbal 'Alamin.

Masarautar Mai Girma Sarkin Koko
21/07/2026

Yau 21/07/2026 Shekara Uku kenan da rasuwar Mai girma Sarkin Koko Malam Mohammadu Bello Koko, Muna rokon Allah ya Jikans...
21/07/2026

Yau 21/07/2026 Shekara Uku kenan da rasuwar Mai girma Sarkin Koko Malam Mohammadu Bello Koko, Muna rokon Allah ya Jikansa da rahama Allah ya kyautata makomar sa Amin.

19/07/2026

😂😂😂😂Hadarin Doki Masifa ne

17/07/2026

Let's Go Active

Address

Koko

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SalihuAbdullahi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share