Ɗaliban Yankin Gabas

Ɗaliban Yankin Gabas Preaching and propagation

MATSAYI DA DARAJA WANDA KE CIKIN GIDAN (SAYYEEDA-ZAHRA) ALAIHASSALAM. ACIKIN AL-QUR'ANI. DA KUMA HADISAN ANNABI MUHAMMAD...
06/11/2025

MATSAYI DA DARAJA WANDA KE CIKIN GIDAN (SAYYEEDA-ZAHRA) ALAIHASSALAM.

ACIKIN AL-QUR'ANI. DA KUMA HADISAN ANNABI MUHAMMAD SALLALLAHU-ALAIHI WA'ALIHI WASSALLAM.

فِي بُيُوتٍ أَذِنَ اللَّهُ أَن تُرْفَعَ وَيُذْكَرَ فِيهَا اسْمُهُ يُسَبِّحُ لَهُ فِيهَا بِالْغُدُوِّ وَالْآصَالِ

Gidan da hatta ( Manzon ) Allah baya shiga sabili da matsayin gidan sai ya naimi izini a gurin masu gidan wato ( Sayyeeda-Zahra ) da ( Imam Aliyu ) gidan da ba'a shiga sai an kira sunan Allah da naiman iz'nin masu gidan sabili da darajan su.

Wannan aya da mukawo a sama tana magana ne akan daraja da matsayi na gidan Annabawan Allah Subhanahu-Wata'ala.

Daga ciki kuwa harda gidan ( Sayyeeda-Zahra ) salamullahi alaiha.

Sabili da akawi hadisi da yake nuni akan cewa akaw gidan (Sayyeed Zahra ) Acikin hadisin kuma daga (Manzon) Rahma ne kai tsaye.

Watarana a massallaci wani mutum ya mike a masallaci ya tambayi (Manzon - Rahama) cewa ayannan da ta sauka wato.

( Fhi-Bhuyutin----zuwa karken ayan)

Yake tambayan (Manzon) rahama ana magana akan wani gidane ?

Sai (Manzon) rahama yace dashi gidan Annabawa ake nufi.

Sai shi kuma ( Abubakar ) ya miqe ya tambaya? cewa ya ( Rasulullah ) daga cikin gidajen da ayan nan taka sauka akwai wancan gidan sai yayi nuni da gidan da Imam ( Aliyu Da Sayyeeda ) suke zaune.

Sai Manzon Allah ya amsama (Abubakar) da cewa yana cikin mafi girman gidan da ayan ta sauka akansu.

Amma duk da matsayi da daraja na wannan gidan wanda ba'a shiga sai ankira sunan Allah da ( Manzon ) Allah a ciki.

Shine gidan da hatta (manzon) Allah baya shiga kai tsaye sai ya kira sunan Allah da masu gidan.

Amma ahaka a samu (Abubakar) bayan kwacen Khalifan cin Manzon Allah da ayi a basa ahaka bai bariba saida ya tura ( Umar Ɗan Khaɗɗab ) gidan ƴar ( Manzon Allah ) dashi da rundunan sa domin suje su ɗaƙƙo Imam ( Aliyu Da Sayyeeda Zahra ) akan wai sai sunyi bai'a ya zuwa khalifancin da aka bama ( Abubakar )

A lokacin da ( Ummar ) ya isa gidan(Sayyeeda Zahra) yana zuwa ya k**a kira da ƙarfi cewa yake ƴar gidan ( Manzon - Allah) Imma kizo dake da mijinki kumiƙa wuya da shugabancin khalifa ( Abubakar ) Ko kuma wallahi sai mun ƙona wannan gidan naki

Wani acikin rundunar ( Ummar ) yaji maganan tayi girma sosai yace ya kai ( Umar ) gidannan da kake cewa ko sufito sumiƙa wuya ko muƙonashi akwai fa ƴar'( Manzon) Allah a gidan fa yace eh, yasani koda itan sai me....

Wa'iya zubillah kaduba girman wannan maganan fa

Daganan sai ( Sayyeeda-Zahra ) ta taso domin ta buɗe ƙofan da taji buga ƙofan yayi yawa.

Tana zuwa bakin ƙofan sai wani ya buga ƙofan da ƙarfi harta bugi ƙirjin ta sannan ta faɗo mata akan awazunta ya 😭😭😭😭 ( Sayyeeda-Zahra )

Daganan ta faɗi daman akwai cikin ɗanta wanda za'ahaifa wanda aka saka masa suna ( MUHSIN ) wah'musibatah, ya ( Zahra )😭😭😭😭

Daganan basubarta haka ba akwai wani la'anan nen Allah wanda ake kiransa da ( Ƙumfuz ) wanda yayita dukanta a ƙirji har'sai da tayi shahada.😭😭😭😭

Wannan hadisi ya zone a littafi wanda ake kira daga ( Ibn - Ƙhutaiba ) ( Al-Imamah-Wassiyasah )

Allah Subhanahu-Wata'ala Ya Tabbatar Damu A Cikin Masu Wulaya Da Manzon Allah Da Iyalangidansa.

Daga : Khalid Ahmad Kudan Turiyya

08/10/2025

Tambaya : Shin Da ( JIHADIL-ASGAHAR ) Wato Jihadi Wanda Ake Fita Domin Tabbatar Da Addinin Allah Subhanahu-Wata'ala

DA Kuma ( JIHADIL-AKHBAR ) Wato Yaƙi Da Zuciyanka Wajan Hanata Saɓon Allah Subhanahu-Wata'ala Wannene Yafi Girma Da Kuma Wuya Da Lada ?

Amsa : Itace ( JIHADIL-AKHBAR ) Wato Ƙoƙari Wajan Hana Zuciya Saɓon Allah Subhanahu-Wata'ala Yafi Wuya Da Kuma Lada

Sabili Da (JIHADIL-AKHBAR) Shine Mutum Zai Kare Kansa Ne Daga Biyema Sha'awa, Da Kuma Hana Kansa Saurin Fushi,

Sannan Kuma Mutum Zai Tsarkake Zuciyan Sa Ga Dukkan Saɓo Da Allah Subhanahu-Wata'ala Bayaso Mutum Ya Daure Ya Hana Kansa Aikatawa

Kaman Irin Gulma, Da Shaye Shaye, Da Zinace Zinace, Da Hana Kansa Ƙarya, Da Sauran Dukkan Munanan Ayyuka Da Basu Da Kyau Wanda Allah Subhanahu-Wata'ala Ya Haramta Gabaki Ɗaya

Wannan Kuma Ba Ƙaramin Aiki Bane A Gurin Ɗan Adam Ba Kuma Kowa Yake Iya Aikata Hakan Ba

Amma Yaƙi Kowa Idan Takai Ta Kawo Kowama Yana Iya Fita Sabili Da Idan Rashin Fita Aga Zaisa A Rasa Kowa

Allah Subhanahu-Wata'ala Ya Bamu Ikon Gyaran Zukatanmu Da Kuma Kaucema Dukka Aiki Na Saɓon Allah Subhanahu-Wata'ala

01/09/2025

Hukunce-hukuncen shari'a zama 10
Hukuncin shakka a kan ruwa.
Tare da Sheikh Muhammad Ishaq's Danmaigauta

20/08/2025

( المعاد الجسماني )

CIGABA DA

DARASI AKAN( AL-MA'ADULJISMANI ) YANDA ZA'A TASHI MUTUM BAYAN YA MUTU KO KUMA YAYI SHAHADA

RANAN LAHIRA DA RANSA K**AN YADDA YAKE KAFIN YA MUTU KO KUMA YAYI SHAHADA

DOMIN A SA K**A KOWA DA LADAN ABUN DA YA AIKATA A DUNIYA

DA KUMA AMFANIN RANAN TASHIN AL-ƘIYAMA A GURIN ƊAN ADAM

DAGA : Khalid Ahmad Kudan Khalid Ahmad Kudan Turiyya

20/08/2025

( المعاد الجسماني )

CIGABA DA

DARASI AKAN( AL-MA'ADULJISMANI ) YANDA ZA'A TASHI MUTUM BAYAN YA MUTU KO KUMA YAYI SHAHADA

RANAN LAHIRA DA RANSA K**AN YADDA YAKE KAFIN YA MUTU KO KUMA YAYI SHAHADA

DOMIN A SA K**A KOWA DA LADAN ABUN DA YA AIKATA A DUNIYA

DA KUMA AMFANIN RANAN TASHIN AL-ƘIYAMA A GURIN ƊAN ADAM

DAGA : Khalid Ahmad Kudan Turiyya

17/08/2025

Hukunce-hukuncen shari'a zama na tara (9)
hukuncin ruwa, bayani a kan ma'anar kur da ma'aunansa a shari'a.



Tare da Sheikh Muhammad Ishaq's Danmaigauta

07/08/2025

( المعاد الجسماني )

DARASI AKAN( AL-MA'ADULJISMANI ) YANDA ZA'A TASHI MUTUM BAYAN YA MUTU KO KUMA YAYI SHAHADA

RANAN LAHIRA DA RANSA K**AN YADDA YAKE KAFIN YA MUTU KO KUMA YAYI SHAHADA

DOMIN A SA K**A KOWA DA LADAN ABUN DA YA AIKATA A DUNIYA

DA KUMA AMFANIN RANAN TASHIN AL-ƘIYAMA A GURIN ƊAN ADAM

DAGA : Khalid Ahmad Kudan Turiyya

06/08/2025

KARATUN LITTAFIN AQA'IDUNA
ZAMA NA BIYU.

(1)ME AKE NUFI DA AQIDA?

(2)SHIN YA HALASTA MUKALAFI YA YI TAKALIDI DA IYAYENSA KO MALAMANSA A AQIDA BA TARE DA GAMSASHEN DALILI BA?
TARE DA SHEIKH Usama Amin

06/08/2025
YANCI A TSAKANIN MUSLUNCI DA LIBERALISMliberalism: Wani motsi ne da aka samar da shi a kasashen yamma, a karahen karni g...
06/08/2025

YANCI A TSAKANIN MUSLUNCI DA LIBERALISM

liberalism: Wani motsi ne da aka samar da shi a kasashen yamma, a karahen karni goma sha shida miladiyya, domin tabbatar yancin mutum a karan kansa, ba tare da la'akari da sauran al'umma a zamantakewa ba. Shiyasa ma ake ce mata falsafar yanci.

Menene bambanci tsakanin 'yanci a Mahangar Musulunci da 'yanci a Mahangar liberalism?

Amsa:
Akwai bambanci na asali tsakanin ma'anar 'yanci a mahangar Musulunci da ma' anar yanci a mahagar liberalism din yammacin Turai. Wannan bambanci ya samo asali ne daga maganar da kowane bangare yake kallon duniya, wato bambanci a abin da ke cewa ru'uya kauniyya.¹ Alal misali, ‘Yancin fadin albarkacin baki, a liberalism ana kallonsa a matsayin cikakken hakki wanda ba shi sharadi ko iyaka, wato kana da yancin ka fadi komai a kan komai, ko da kuwa ya kai ga cin mutuncin addinai ko yada hargitsi a cikin al'umma. Wanda a karkashin wannan ne ma'abota wannan maganar ta liberalism suke cin mutunci ga addinin musulunci, da ma Manzon muslunci (s a w w). A Musulunci kuwa, ƴanci yana da sharadi da iyakokin, daga ciki akwai rashin sabawa dokokin addini da rashin haddasa fitina, da rashin sabawa dokokin zamantakewa, da rashin sabawa kyawawan dabi'un da al'umma s**a yarda da su.

'YANCIN MUTUM DA 'YANCIN ZAMNTAKEWA
A Muslunci ba wai ana fahimtar 'Yanci bane a matsayin 'yancin kai kadai ba ne, a a, yanci ya kunshi yancin rayuwa a cikin al' umma. Wannan yana nufin cewa al'umma tana da hakkin kare kanta daga ayyukan da za su cutar da kimarta da kwanciyar hankalin ta bangaren aminci da kyawawan dabi'u. Don haka, za mu ga a musulunci akwai iyakoki a da sharudda da hani ma, a kan wasu ayyuka da za su cutar da al’umma gaba daya, k**ar haramcin alfasha da nuna munanan ayyuka a bainar jama’a.
Wannan saɓanin 'yancin kai na yammacin Turai, na liberalism, inda aka mayar da hankali ga mutum a matsayin mai cin gashin kansa, kuma ana daukar 'yancin kai a matsayin abin da ya fi muhimmanci giye da yancin al' umma, koda kuwa yancin kai ya ci karo da bukatun al'umma gaba daya. Wannan ya haifar da yaduwar tsarin zamantakewa wanda ke fifita mutum a karan kansa sama da iyali da kyawawan dabi'un jama'a, wanda ya haifar da rushewar al'adun gargajiya da yawa.

Manufar 'yanci a Musulunci ita ce kaiwa zuwa ga bauta ga Allah (s w t), da bin tafarkin k**ala ta ruhi da dabi'a. Mutum yana da ’yancin zaɓi a karan kansa, amma wannan ’yancin ba haka aka sake shi ba ba tare da iyakoki, a’a, wannan zabin an baiwa mutum ne domin ya zabi abin da yake daidai kuma ya lizimci gaskiya. Don haka, a cikin Musulunci ne akwai "'yanci na haƙiƙa," wanda ke nufin 'yantuwa daga bautar kai, da sha'awa, da buƙatun abin duniya.
Amama a cikin liberalism kuwa, 'yanci kai shi ne manufa a karan kansa, wato manufar farko ita ce mutum ya sami 'yancin yin duk abin da ya ga dama, matukar bai keta 'yancin daidaiku irinsa ba k**ar yadda doka ta tanada. Wannan yana kai mutane zuwa ga abin da ake cewa nisbiyyatul-akhlaƙ², saboda abin da aka yarda da shi a yau, yana iya zama abin da ba a yarda da shi ba a gobe, kuma abin da ba a yarda da shi ba a yau, ana iya yarda da shi a gobe, ya danganta da ci gaban al'umma.

IYAKOKIN 'YANCI A MUSULUNCI
'Yanci na karkashin tsarin shari'a ne, wanda ke bayyana abin da ya halatta da wanda bai halatta ba. Akwai hane-hane na addini da na kyawawan ɗabi’a da ke kare al’umma daga karkacewa da asara.

Don haka Musulunci bai hana mutane yin tunani da warwara ko kawo sabon abu ba, sai dai ya haramta keta alfarmar abubuwa masu kima da tsarki, kuma ya haramta yada ilhadi, ko cutar da al'umma da sunan 'yanci. Amma a liberalism, iyakokin 'yanci suna ƙayyade ne dokokin mutum, waɗanda ke canzawa bisa ga yanayin siyasa da zamantakewa. A wasu kasashen, ana samun cikakken 'yancin yada ilhadi da cin mutuncin addinai, da kuma 'yancin bayyana ra'ayin aikata alfasha a bayyane kuma mara iyaka, wanda ke haifar da wargaza dabi'un iyali da zamantakewa.

https://t.me/muhammadishaq45
Muhammad Ishaq's Danmaigauta

06/08/2025

Celebrating my 2nd year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉

Address

Kano Abuja Road
Kudan

Telephone

+9647852525516

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ɗaliban Yankin Gabas posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ɗaliban Yankin Gabas:

Share