26/04/2025
DA DUMI-DUMI: Mafarauta da Manoma Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Ba Su Damar Korar ’Yan Bindiga da ’Yan Boko Haram Daga Daji
Kungiyoyin Mafarauta da manoma a Najeriya sun roki gwamnatin tarayya da ta amince da su a hukumance domin su fuskanci ‘yan ta’adda da sauran bata-gari da s**a fake a dazuka, tare da kawar da su gaba ɗaya.
Masu farauta da ke karkashin ƙungiyoyi irinsu Nigerian Forest Security Service (NFSS), Professional Hunters Association of Nigeria, Agbekoya Farmers’ Society of Nigeria, da Oodua Peoples Congress, sun bayyana cewa suna da ilimi, horo, ƙwarewa, da kuma ƙarfin ruhi da ake bukata domin fafatawa da ‘yan ta’adda cikin dazuka.
Joshua Osatimehin, Babban Kwamandan NFSS, ya bayyana cewa tabarbarewar tsaron dazuka babban barazana ne ga zaman lafiya da ci gaban ƙasa, yana mai jaddada cewa kamata yayi a ba su cikakken goyon bayan gwamnati domin su tunkari matsalar da gaggawa.
Ya ce, “Mun san dazukan ƙasar nan, wasu daga cikin jami’anmu ma a cikin daji suke zaune. Amma ba za mu iya kai farmaki kan bata-gari ba tare da cikakken izinin gwamnati ba, domin gudun kada a tuhume mu da laifukan keta haddin bil’adama.”
Ya ƙara da cewa, “Da zarar gwamnati ta ba mu damar da muke bukata, za mu iya amfani da dukkan dabaru da kayan aiki — na zahiri da na ruhaniya — wajen kawar da ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane, domin a gaskiya adadin su ƙalilan ne idan aka kwatanta da yawan al’ummar Najeriya.”
Osatimehin ya jaddada cewa da zarar gwamnati ta samar da kayayyakin aiki da kayan tsaro da s**a dace a matakin su, dazuka za su fi samun kariya kuma kashe-kashen da ake fama da su za su ragu sosai.
“Irin wannan kariya daga mu zai zama garkuwa ta farko kafin isowar rundunar soja ko ’yan sanda wajen shawo kan lamarin,” inji shi.
KBC Hausa