AID Multimedia Hausa

AID Multimedia Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AID Multimedia Hausa, Media/News Company, Lagos.
(1)

Media and Multimedia Services
subscribe to our YouTube channel and follow us on TikTok
https://youtube.com/?si=H493doKrrjk9e5R5
https://www.tiktok.com/?_t=ZS-90UuETg8b0q&_r=1

A Kano  an ƙi sakin motar Luxurious Bus da ake zargin an yi safarar ƙwaya ta rabin Naira Biliyan da ita Hukumar Task For...
07/09/2026

A Kano an ƙi sakin motar Luxurious Bus da ake zargin an yi safarar ƙwaya ta rabin Naira Biliyan da ita

Hukumar Task Force ta Kano mai yaƙi da shaye-shaye da safarar miyagun ƙwayoyi ta ce ba za a saki wata babbar motar bas da aka kwace bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi ba har sai an kammala bincike.

Wannan na zuwa ne bayan rahotannin da s**a bayyana cewa akwai yunkurin hook Naira miliyan 500 a cikinta ko kuma suna da alaƙa da ita.

Shugaban Task Force ɗin, Muhuyi Magaji, ya ce binciken lamarin na ci gaba da gudana, kuma za a bi matakan da doka ta tanada kafin yanke hukunci kan makomar motar da mutanen da ake zargi da hannu a lamarin.

Rahotanni sun ce an k**a mutane shida a yayin samamen da Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta gudanar a kan hanyar Zariya zuwa Kano.

Mutanen da NDLEA ta bayyana sun haɗa da:

🔹 Okodili Ibeabuchi, mai shekara 60
🔹 Onyeka Vincent, mai shekara 47
🔹 Nwanko Wisdom, mai shekara 36
🔹 Success Chigozie, mai shekara 30
🔹 Emmanuel Jude, mai shekara 27
🔹 Chinedu Peter , mai shekara 39

NDLEA ta ce an kwato kwayoyin Tramadol, Rohypnol da sauran opioids guda 728,958,tare da gram 360 na co***ne, gram 99.8 na methamphetamine, kwalaben codeine guda 50 da kuma kilogram 2.7 na *Loud*, wani nau'in cannabis na roba.

Task Force ɗin ta ce za a ci gaba da binciken mallakar motar, direbobi da sauran mutanen da ke da alaƙa da lamarin, kafin a ɗauki matakin da ya dace.

Wani matakin doka yafi dacewa a dauka kan motocin da ake safarar miyagun kwayoyi da su?

Tsegumi! Hoton Shaihin Malami Makaranci kuma mahaddacin Alkur'ani mai girma da ake wa lakabi da Malam mai aunaka aunaka ...
05/09/2026

Tsegumi!

Hoton Shaihin Malami Makaranci kuma mahaddacin Alkur'ani mai girma da ake wa lakabi da Malam mai aunaka aunaka akan gadan ahba'i na taron siyasa a Kano na daukar hamkali a soshiya midiya

Yayin da wasu ke cewa tawali'une ya sanya shaihin Malamin zaman dirshen a gadon ahba'i, wasu na cewa ya kaskantar da kanshi ne ya halarci taron siyasar da ba a karrama shi a ba shi wajen zama ba.

Ya kuke kalon wannan batun.

Matar shaharren lauyan nan na Kano Abba Hikima  ta shiga rikicinsa da 'yar gwagwarmaya Zainab Nasir Ahmad da ke yi wa ka...
05/09/2026

Matar shaharren lauyan nan na Kano Abba Hikima ta shiga rikicinsa da 'yar gwagwarmaya Zainab Nasir Ahmad da ke yi wa kanta lakabi da jagorar talakawan Kano, kana mai bai wa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf shawara kan al'amuran matasa a jihar.

Matar lauyan wanda ya ce ita ma lauya ce, ta shiga jerin lauyoyinsa wajen maka Zainab Nasir a kotu, bisa zargin bata sunan mijinta k**ar yadda Barista Abba Hikima ya wallafa a shafinsa na Facebook k**ar haka;

Lauyoyi da dama, cikinsu har da matata, sun yi nisa wajen daukar matakin doka akan wannan case. Da farko sun nemi gina case din akan innuendo sun tattara hujjoji na nesa da kusa saboda tabbatar da bata suna ko kazafi ta hanyar shagube yafi wahala. Amma bayan fitar da screenshot da ta yi jiya, sai lauyoyin s**a ce “shikenan ma komai ya fito fili”. An samu hujjojin mafiya saukin tabbatarwa kuma an kara samun wasu gabobin ma na yin shariar.

Amma bayan abunda ya faru tsakanin jiya zuwa yau, da abunda Allah Ta’ala yayi min, babu abunda ya dace dani sai na cika da godiyar Allah, kuma na kwatanta shiriyar Annabi Sallahu Ta’ala alaiHi wa aaliHi wa sallam wanda yanzu haka nake gaban shi a Madinar sa SAW.

Wallahi akwai yadda zan yi da Zainab, kuma cikin sauki. Sannan babu wani minister, kwamishina ko gwamna da zai iya kareta daga girbar abunda ta yi min. Amma ina fahimtar idan na dauki wani mataki bayan abunda Allah yayi min to ban gode ba. Domin kudi, mulki ko wani abun duniya ba zai iya siya min wannan shaidar kuka min ba. Ba don hali na Allah ya min abunda yayi min ba. Rahamarsa ce kawai SWT. Da yaso, sai ya bari abunda mutane da dama s**a zauna s**a shirya, ciki har da mutanen da nake kaddarawa, ya same ni. Misali, zan iya duba waya ta ya zama ba ni da record din abunda ya faru. Ko ma sauran abubuwan da zasu iya faruwa ya zama da gaskiyar taka amma taki karbuwa.

Wallahi da nashiga masjidin Nabawy kasa karasawa wajen qubbatul khadara’i nayi saboda tuhumar kaina da nake tayi. Nasan duk abunda ya samu mutum mara kyau daga abun hannayensa s**a jawo ne. Amma ina ta tuna hadithin Annabi Sallahu alaihi wa sallam da yake cewa Sayyiduna Ibn Abbas:

يَا غُلَامُ، إِنِّي أُعَلِّمُكَ كَلِمَاتٍ:

احْفَظِ اللَّهَ يَحْفَظْكَ،

احْفَظِ اللَّهَ تَجِدْهُ تُجَاهَكَ

Ina jin Allah ba zai bari na tabe ba. Musamman tunda ya bari na ziyarci AnnabinSa SAWAW a dai dai lokacin da wannan abu yake faruwa.

Duk da bana jin na cika bukatar wannan kiyayewa ta Allah domin cancantar kariyarSa. Ina ta maimaita:

ۚ وَلَوْ أَنَّهُمْ إِذ ظَّلَمُوا أَنفُسَهُمْ جَاءُوكَ فَاسْتَغْفَرُوا اللَّهَ وَاسْتَغْفَرَ لَهُمُ الرَّسُولُ لَوَجَدُوا اللَّهَ تَوَّابًا رَّحِيمًا

Gashi kuwa rahamar Allah ta riske ni. Alhamdulillah.

Saboda haka na yanke shawarar barin wannan case saboda Allah. Babu wani redress da kotu zata bani da ya wuce wanda Allah ya min. Babu wani hukunci da za’a yi mata da ya kai abunda ya faru yanzu.

Allah ya karawa Annabi SAWAW wasila da fadhila.

Nagode muku da kuka shiga al’amarina.

Kuma na koyi babban darasi.

Allah ya sa mu gama lafiya.

Ameen.

Abba Hikima
5/09/2026
Madinatul Munawwara

Rikicin da ya barke tsakanin Abba Hikima da Zainab Nasir a soshiyal midiya nada alaka da siyasar Kano, kuma tun bayan barkewar rikicin, lauyan ya tafi Saudiya Umara.

Sai jiya na fara ganin clips din hirar wani matashin bafulatani da ya zargi Sen Buba da cewa yana financing banditry. Hi...
04/09/2026

Sai jiya na fara ganin clips din hirar wani matashin bafulatani da ya zargi Sen Buba da cewa yana financing banditry. Hirar ta kai wajen episodes 8 a page din D English Alhaji- wanda shima sai a jiyan na fara sanin page din. Bayannan kuma na kalli videos na malaman addini da social media influencers da dama da suke bada kariya ga Senator Buba.

Akwai hakki akan mahukunta da su zama transparent wajen bincike da tabbatar da ainihin menene gaskiyar wannan lamari. Suma malaman addini yak**ata su zare kansu daga cikin wannan al’amari su bar jamian tsaro da s**a kware su tantance komai kafin su dau matsaya. Idan abu ya shafi security yana bukatar samun bayanai masu yawa- wasunsu kuma na sirri ne.

Komai darajar mutum bai kai rayukan da ake rasawa ba. Komai mutum zai baka bai kai darajar zaman lafiya ba. Dubban mutane sun shiga cikin kunci saboda wannan lamari. Muna fatan wannan kadiya ya zama sanadin gano tushen wannan matsala ta tabarbarewar tsaro a yankunnanmu na Arewa.

Hakki ne akanmu duka mu nemi hukuma tayi transparent bincike- idan Buba ne da gaskiya ta wanke shi- idan kuma yana da hannu ta hukunta shi.

Ra'ayin Dr Ibrahim Musa

Ya kuke kalon zargin da ake yi wa wasu gaggan 'yan siyasa da ke cikin gwamnati da hannu wajen taimakon 'yan ta'adda da ta'addanci?

Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Sarkin Gumel,Ya Jinjinawa Shekaru 46 Na Mulkin Sarkin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ba...
04/09/2026

Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Sarkin Gumel,Ya Jinjinawa Shekaru 46 Na Mulkin Sarkin

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhininsa bisa rasuwar Sarkin Gumel, Mai Martaba Alhaji Dr. Ahmed Muhammad Sani II, CON, wanda ya rasu a ranar Alhamis, 3 ga Satumba, 2026, a birnin Alkahira na ƙasar Masar.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis, Shugaba Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Gumel, gwamnati da al’ummar Jihar Jigawa, da kuma daukacin masarautun gargajiya na Najeriya.

Shugaban Ƙasan ya bayyana rasuwar Sarkin Gumel a matsayin ƙarshen wani muhimmin tarihi, yana mai cewa marigayin ya hau gadon sarautar Gumel a ranar 16 ga Disamba, 1980, inda ya yi kusan shekaru 46 yana mulki a matsayin sarki na 16 na masarautar.

Ya ce tsawon shekarun mulkinsa sun sanya marigayin cikin sarakunan gargajiya na farko da s**a fi dadewa kan karagar mulki kuma s**a fi samun girmamawa a Najeriya.

Shugaba Tinubu ya kuma bayyana marigayin a matsayin ƙwararren malami, ma’aikacin gwamnati kuma ɗan kishin ƙasa, wanda gudummawarsa ga al’umma ta wuce iyakokin fada.

Kafin ya zama sarki, Alhaji Ahmed Muhammad Sani II ya yi aiki a Hukumar Native Authority ta Gumel, Hukumar Shige da Fice ta Najeriya, sannan ya kasance babban jami’i a Ofishin Gundumar Kazaure.

Tsakanin shekarar 1978 zuwa 1980, ya kasance Kwamishinan Yaɗa Labarai, Harkokin Cikin Gida da Al’adu na tsohuwar Jihar Kano.

A lokacin da yake wannan matsayi ne aka kafa jaridar Triumph Newspaper, tashar talabijin ta CTV 67 wadda daga baya ta zama ARTV, tare da faɗaɗa ayyukan Radio Kano. Wadannan kafafen yaɗa labarai na daga cikin muhimman cibiyoyin yaɗa bayanai a Arewacin Najeriya har zuwa yau.

Shugaba Tinubu ya ce a lokacin da yake kan karagar sarautar Gumel, Alhaji Sani II ya sauya masarautar zuwa abin koyi wajen samar da zaman lafiya da ci gaba.

Ya bayyana shi a matsayin uba ga kowa, mai hikima da kuma mai kula da al’adun al’umma, wanda ya sadaukar da tsawon mulkinsa wajen inganta ilimi, karatun addinin Musulunci, haɗin kan al’ummomi daban-daban da kuma kare al’adun masarautar Gumel, wadda na daga cikin tsofaffin masarautun Arewacin Najeriya.

Shugaban Ƙasan ya ce a Jihar Jigawa, salon jagorancin marigayin mai natsuwa, taka-tsantsan da kuma haɗa kan jama’a ya taimaka wajen samar da kwanciyar hankali a tsawon shekarun da jihar ta fuskanci sauye-sauyen siyasa da matsalolin tsaro.

Ya ƙara da cewa marigayin ya kasance abokin hulɗa na gari wajen samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma, tare da fifita jin daɗin jama’arsa a kan komai.

Shugaba Tinubu ya ce Najeriya ta yi babban rashi na wani fitaccen shugaban gargajiya, wanda za a yi kewar shawarwarinsa masu hikima, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke ci gaba da dogaro da tasirin shugabannin gargajiya wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa.

Shugaban Ƙasan ya roƙi Allah Ya gafarta wa marigayin kurakuransa, Ya karɓi kyawawan ayyukansa, Ya kuma ba shi Aljannar Firdausi.

Ya kuma roƙi Allah Ya bai wa iyalan marigayin, Masarautar Gumel da al’ummar Jihar Jigawa ƙarfin jure wannan babban rashi da ba za a iya maye gurbinsa ba.

Jajurtaccen sojan nan mai da'awar Musulunci, Adam Ashaka na cigiyar miji ga wata budurwa 'yar gidan masu bautar Dodo da ...
03/09/2026

Jajurtaccen sojan nan mai da'awar Musulunci, Adam Ashaka na cigiyar miji ga wata budurwa 'yar gidan masu bautar Dodo da ta Musulumta

Shaikh Adam Ashaka ya ce,

"Iyayen ta Suna bautan Dodo ta karbi addinin MUSULUNCI tace insama mata miji wannan Zai koya mata addinin MUSULUNCI ya kula da ita ya rita amama Duk wanda Zai iya aure ta fisabilillahi yamin magana insha ALLAHU Zamu bashi ita fisabilillahi amman da Sharadin Zakayi Hakuri da Halayen da dabi'u ta kafun ta Saba don ba taba rayuwa Cikin jama'a tunda aka Haife ta acjeji take"

Game bukata yayi mana DM sai mu hada shi da Adam Ashaka.

Yanzu Yanzu:Kamfanin Sufuri Na Uber Ya Sanar Da Ficewarsa a Najeriya Bayan Shekaru 12 Yana AikiKamfanin safarar fasinjoj...
02/09/2026

Yanzu Yanzu:Kamfanin Sufuri Na Uber Ya Sanar Da Ficewarsa a Najeriya Bayan Shekaru 12 Yana Aiki

Kamfanin safarar fasinjoji ta manhaja, Uber, ya sanar da dakatar da ayyukansa a Najeriya daga yau, 2 ga Satumba, 2026, bayan shafe shekaru 12 yana gudanar da harkokinsa a kasar.

Uber ta ce ta dauki matakin ne bayan gudanar da cikakken nazari kan harkokin kasuwancinta, inda ta bayyana cewa shawarar ta shafi Najeriya da Uganda, ba sauran kasashen Afirka da take aiki ba.

Kamfanin ya fara aiki a Najeriya ne a Lagos a shekarar 2014, inda daga bisani ya zama daya daga cikin manyan kamfanonin da s**a sauya tsarin zirga-zirgar jama'a ta hanyar amfani da manhajojin zamani.

Uber ta gode wa miliyoyin masu amfani da manhajar da direbobin da s**a yi aiki da ita tsawon shekaru, tare da neman afuwar wadanda dakatarwar ayyukan za ta kawo wa cikas.

Kamfanin ya kuma ce zai tallafa wa direbobi, fasinjoji da ma'aikatansa na cikin gida yayin mika mulki, yayin da aka sanya ranar 23 ga Satumba, 2026 a matsayin wa'adin gabatar da tambayoyi ko bukatun karshe da s**a shafi asusun masu amfani.

Ficewar Uber na zuwa ne a lokacin da bangaren safarar fasinjoji ta manhaja a Najeriya ke fuskantar gasa mai tsanani daga kamfanoni irin su Bolt da inDrive, tare da hauhawar farashin man fetur da kudin kula da motoci.

Me kuke ganin wannan ficewar Uber za ta haifar wa direbobi da fasinjojin Najeriya?

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin sama wa ƙwararrun ’yan Nijeriya aiki a ƙasashen wajeGwamnatin Tarayya ta ƙaddama...
01/09/2026

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin sama wa ƙwararrun ’yan Nijeriya aiki a ƙasashen waje

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani shiri mai suna “Hire from Nigeria” (wato 'A ɗauki ma'aikata daga Nijeriya') domin bai wa ’yan ƙasar nan damar yi wa kamfanoni da masu ɗaukar ma’aikata na ƙasashen waje aiki.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wani taron manema labarai da aka yi a ofishin sa a Abuja.

Ya ce: “Ƙaddamar da wannan shiri wani muhimmin mataki ne a ƙoƙarin da Nijeriya take yi na sanya ɗaya daga cikin manyan kadarorin ƙasar mu, wato mutanen mu, a sahun gaba wajen hulɗar tattalin arzikin mu da duniya.”

Ya ce yawan matasan Nijeriya, da ɗimbin ƙwararrun ma’aikatan ta da kuma bunƙasar fasahar zamani sun ba ƙasar damar yin gogayya da sauran ƙasashe a fagen tattalin arzikin duniya.

Idris ya ce: “Makomar tattalin arzikin Nijeriya za ta ƙara dogara ne kan ƙwarewa, ƙirƙire-ƙirƙire, fasaha da kuma ƙwazon jama’ar mu. A shirye Nijeriya take ta yi gogayya a fagen duniya. A shirye ƙwararrun ’yan Nijeriya suke su yi aiki, kuma ya k**ata duniya ta mayar da hankali kan Nijeriya."

Ya ƙara da cewa gangamin ya haɗa ma’aikatun tarayya na Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari da na Ilimi, NATEP, iDICE da kamfanoni masu zaman kan su domin haɗa ƙwararrun ’yan Nijeriya da masu neman ƙwararrun ma’aikata a duniya.

Ya ce shirin ya yi daidai da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma burin Gwamnatin Tarayya na samar da guraben aiki miliyan ɗaya ta hanyar fitar da ayyuka zuwa ƙasashen waje.

“Ba sai matashi ɗan Nijeriya ya bar ƙasar ba kafin ya samu damar shiga harkokin tattalin arzikin duniya. Idan aka ba shi ƙwarewar da ta dace, ababen more rayuwa, ƙa’idojin sana’a da damar shiga kasuwanni, ’yan Nijeriya za su iya rayuwa, su yi aiki kuma su samu kuɗi a nan gida, yayin da suke samar da ayyuka ga abokan ciniki da masu ɗaukar ma’aikata a faɗin duniya,” inji shi.

Shi kuma Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa, ya ce ma’aikatar sa tana inganta ƙwarewar ’yan Nijeriya ta hanyar inganta tsarin koyarwa, koyar da sana’o’i da dabarun fasahar zamani, da kuma horar da su bisa buƙatun masana’antu.

“Manufar Ma’aikatar Ilimi ita ce, a duk inda ake neman ma’aikata a duniya, muna son ’yan Nijeriya su samu horo, su samu takardar shaidar ƙwarewa kuma su kasance a shirye don a ɗauke su aiki,” inji shi.

A nata ɓangaren, Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Jumoke Oduwole, ta ce gangamin zai taimaka wajen samar da ayyukan yi ga matasan Nijeriya, da ƙara fitar da ayyuka zuwa ƙasashen waje da jawo zuba jari.

“Shirin ‘Hire from Nigeria’ ya wuce kamfen na wayar da kai kawai; shiri ne na ƙasa da aka tsara domin bunƙasa tattalin arziki,” inji Oduwole.

Ta ce za a gabatar da kamfen ɗin a taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 81, inda Nijeriya za ta bayyana fa’idar ɗaukar ’yan Nijeriya aiki ga masu ɗaukar ma’aikata na duniya.

Tun da farko, Babbar Mataimakiya ta Musamman kan Sadarwa ta Dabaru da NATEP, Misis Olajumoke Dan-Okayi, ta ce shirin zai magance matsalolin da ke hana ƙwararrun ’yan Nijeriya samun damar aiki a duniya.

Ta ce: “Ba ƙwarewa ce matsalar ba, kuma ba buri ba ne. Matsalar ita ce yadda za a gano ƙwararrun ’yan Nijeriya, amincewa da su da kuma samun damar shiga kasuwannin duniya. Don haka, shirin ‘Hire from Nigeria’ yana da ayyuka uku masu sauƙi: ya sauƙaƙa wa duniya gano Nijeriya, ya sauƙaƙa amincewa da ƙwararrun ’yan Nijeriya, sannan ya sauƙaƙa ɗaukar ’yan Nijeriya aiki.”

Ana sa ran kamfen ɗin zai haɗa ƙwararrun ’yan Nijeriya da masu ɗaukar ma’aikata, kamfanoni masu neman ma’aikata, masu zuba jari da kasuwannin ƙasashen waje.

Abun Takaici Ne Yadda Jikan Wanda Ya Kafa Kungiyar Izala Ya Zama Kirista, Cewar Jajurtaccan Soja Mai Da'awa, Adam Ashaka...
01/09/2026

Abun Takaici Ne Yadda Jikan Wanda Ya Kafa Kungiyar Izala Ya Zama Kirista, Cewar Jajurtaccan Soja Mai Da'awa, Adam Ashaka

Shaikh Adam Ashaka ya ce;

"Babban abun takaici wannan yaron A' Cikin yayan Malam Nura khalid wannan yaron Shine mai Sunan Marigayi Sheikh Ibrahim bawa Mai Shikafa kunsan Malam Nura khalid yana Auren yar marigayi Sheikh Ibrahim bawa Mai Shinkafa ta Cikin Sa gaskiya inci amanar Malam, dama Sauran Al'ummar Musulmai baki daya Yau' awayi gari wai jikan Sheikh Ibrahim bawa Mai Shinkafa ne ya koma CHRISTIAN ✝️"

Zagayen Maulidi A Kwaryar Birnin KanoDaman haka kanawa ke himma a Maulidin fiyayyen halitta?
01/09/2026

Zagayen Maulidi A Kwaryar Birnin Kano

Daman haka kanawa ke himma a Maulidin fiyayyen halitta?

Address

Lagos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AID Multimedia Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AID Multimedia Hausa:

Shortcuts

Share