AID Multimedia Hausa

AID Multimedia Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AID Multimedia Hausa, Media/News Company, Lagos.
(1)

Media and Multimedia Services
subscribe to our YouTube channel and follow us on TikTok
https://youtube.com/?si=H493doKrrjk9e5R5
https://www.tiktok.com/?_t=ZS-90UuETg8b0q&_r=1

Wani Kwastam da ya sanya labule da  mata uku a Hotel a Katsina, ya sheka BarzahuJami'in hukumar hana fasakwabri ta kasa ...
16/10/2025

Wani Kwastam da ya sanya labule da mata uku a Hotel a Katsina, ya sheka Barzahu

Jami'in hukumar hana fasakwabri ta kasa wato Kwastam mai mukamin ASC, Lawal Tukur, ya rasu bayan ya k**a daki a hotel ya kuma saki labule da mata uku,

Rahitanni sun ce an gano gawar Lawal Tukur ne a dakin hotel din Murjani da ke kwaryar birnin Katsina bayan ya shiga dakin ya kuma saki labule da mata uku da s**a hadar da Khadija Ali, Aisha Lawal, da Hafsat Yusuf.

Jam'iyyar ADC ta zargi shugaba Tinubu da son maida Nijeriya amfani da jam’iyya guda.
16/10/2025

Jam'iyyar ADC ta zargi shugaba Tinubu da son maida Nijeriya amfani da jam’iyya guda.

Jajurtaccen sojan Najeriya nan mai da awar addinin Islama Adam Ashaka,lokacin da ya shiga wani cocinya hau munbarin coci...
16/10/2025

Jajurtaccen sojan Najeriya nan mai da awar addinin Islama Adam Ashaka,lokacin da ya shiga wani cocinya hau munbarin cocin don yin kira zuwa Musulunci.

Adam Ashaka ya shahara wajen musulumtar da Maguzawa masu bautar doddani, da Kiristoci da sauran mabiya addinai zuwa Musulunci, ya kuma shahara da s**ar manyan Malaman Musulunci masu amfani da addini ko kungiyanci don cimma manufar siyasa, inda yake jadadda akidar shi na a zabi shugabanni masu adalci ga talakawa ba tare da anyi la'akari da addininsu ba, yana kan akidar cewa zai zaɓi Kirista a matsayin shugaba muddin zai yi ma talakawa adalci akan Musulmi da zai zalunce su.

Rikici ya kaure tsakanin 'yan Arewa mazauna Legas kan wanda zai jagoranci tallar Shugaba Tinubu a cikinsu a lokacin yaki...
15/10/2025

Rikici ya kaure tsakanin 'yan Arewa mazauna Legas kan wanda zai jagoranci tallar Shugaba Tinubu a cikinsu a lokacin yakin babban zaben 2027.

Rikicin wanda ya kaure a kafafen soshiyal midiya tsakanin magoya bayan wasu gaggan jagorarin siyasar 'yan Arewa a Legas dama kudancin Najeriya, inda s**a yi ta yi musayar yawu, ko wani bangare na kare gwaninsa.

Zamu kawo maku cikekken rahoto.

Yabon Gwani!  Prince Hadi Sani zakaran gwajin dafi na 'yan Arewa a KuduMalam Hadi Sani, Mai bai wa gwamnan jihar Ogun Da...
15/10/2025

Yabon Gwani!

Prince Hadi Sani zakaran gwajin dafi na 'yan Arewa a Kudu

Malam Hadi Sani, Mai bai wa gwamnan jihar Ogun Dapo Abiodun shawara kan al'amuran baki a jihar ya ciri tuta duba da hidimtawa al'umma da yake ba dare ba rana.

Cikin kasa da shekaru 7 da yayi a wannan mukamin ya Samar wa matasan Arewa da dama ayyukan yi na gwamnati a matakin karamar hukuma, da jiha da kuma aiki a mataki na gwamnatin tarayya, inda da yawansu ke aiki a ma'aikatun gwamnati jihar Ogun, da na kananan humumomi a jihar, da kuma masu aiki a asibitoci na gwamnatin tarayya a matsayin manyan jami'an kiwon lafiya.

Malam Hadi Sani ya kasance mai yawan yi wa makarantun Islamiyya hidima ta hanyar gayaran gininsu, da kuma sabunta su tare da tallafa wa dalibai da kayan karatu.

Ya kasance mai shiga sha'anin matasa masu karamin karfi, inda yake kokarin gaske wajen taimakon matasa masu tukin babur ko 'yan acaba domin ganin sun sami walwalah, wani dan acaba ya shaida wa AID Multimedia Hausa yadda aka taba k**a shi, aka karbe masa babur, ya daga waya ya kira Hadi Sani, ya ce nan take sai ga mai bai wa gwamna shawara yazo har inda yake ya shiga tsakani aka mai do masa da babur din shi, ya ce abun ya ba shi mamaki, ya bai wa jami'an da s**a k**a shi mamaki, ya ce ko yanzu na kira lambar shi zai dauka.

Bugu da kari Malam Hadi Sani Yayi kokari sossai wajen shiga tsakani don magance rikicin Fulani Makiyaya da manoma a jihar, lamarin da ya kawo zaman lafiya mai daurewa a wannan fannin, wanda hakan ne ya sanya shi ya koma makaranta yake karantar fannin sasanci da tabbatar da tsaro a matakin karatu na digirin digirgir (Dr) a Jami'ar Ibadan bayan yayi digirinsa na farko da na biyu a ABU Zariya.

Ganin irin yabon da Malam Hadi Sani ke samu ne daga al'ummomin da yake wakilta hakan ne yasa muma muka kawo yabonsa, domin yabon gwani ya zama dole.

Ba Hadi Sani ne farkon wanda ya fara rike mukami tsakanin 'yan Arewa mazauna kudu ba, anyi wasu da dama kafin shi, wadanda s**a rike mukamin da yafi na shi ma, amma dai idan muka yi ta mahaukaci, zamu ce ba a yi wani dan Arewa a Kudu da ya sami damar gwamnati ya amfanar da al'umma tamkar Hadi Sani ba, idan kuma akwai, gareku 'yan Arewa mazauna Kudu, ku kawo, waye naku gwanin?

Me yayi wa al'umma?

Hoto:lawal Abdullahi Matazu

15/10/2025

'Yan Arewa 'Yan Kasuwar Alaba Rago Na Cikin Firgici Da Fargaba Yayin Da Mahukunta A Legas Ke Yunkurin Rushe Kasuwar Gaba Dayanta

Labarai Cikin Hotuna:Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, tare da Kwamishinonin Yada Labarai na jihohi...
15/10/2025

Labarai Cikin Hotuna:Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, tare da Kwamishinonin Yada Labarai na jihohin da jam’iyyar APC ke mulki, a yayin ziyarar gani da ido da s**a kai a Ginin Wutar Lantarki na Gaggawa mai Amfani da Iskar Gas na Maiduguri (Maiduguri Emergency Gas Power Plant), wanda Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL) ke ginawa.

Ziyarar ta gudana ne a yau Laraba a Maiduguri, tashar zata samar da ƙarfin wutar lantarki har megawatt 50, wacce za ta inganta samar da wutar lantarki a Jihar Borno da kewaye.

Ikon Allah:An yi auren wata Amarya mai gemu a Nijar
15/10/2025

Ikon Allah:An yi auren wata Amarya mai gemu a Nijar

Naira miliyan 10 aka bai wa Baban Bilyaminu, ya ce ya yafe jinin Dansa wanda bai san ciwonsa ba, bai san cinsa da shan s...
15/10/2025

Naira miliyan 10 aka bai wa Baban Bilyaminu, ya ce ya yafe jinin Dansa wanda bai san ciwonsa ba, bai san cinsa da shan sa ba, tun yana jariri, cewar jajurtaccen Lauya, AUDU BULAMA BUKARTI

Wanda ya ce;

Tabbas mutumin da ya fito jiya ya ce ya yafe wa Maryam Sanda shi ne baban Bilyaminu. Amma na tattauna da dangin mahaifiyar Bilyaminu, waɗanda Bilyaminu ya girma a hannunsu tun daga ranar da mahaifiyarsa ta dawo gida wankansa. Ga abinda su ka ce:

1. Sun ce baban Bilyaminu bai sake zuwa ya duba ɗansa ba tun daga ta'aziyyar rasuwar mahaifiyar Bilyaminu a gidan iyayenta da ya je bayan ta gama wakan Bilyaminu a 1981.

2. Sun ce bai taɓa sanin ci, ko sha, ko sutura, ko jinya, ko karatun Bilyaminu ba.

3. Sun ce akwai lokacin da kakar Bilyaminu ta tura shi hutu gurin baban lokacin yana firamare domin su san juna, a kuma kai shi wurin kakanninsa na gefen uba a Ƙaramar Hukumar Isa ta Jihar Sokoto, amma uban ya sa shi a mota dawo da shi Birnin Kebbi gurin iyayen kakar tasa a ranar da ya je gurinsa.

4. Sun ce baban Bilyaminu ya yi aiki na misalin tsawon shekara biyu a garin Birnin Kebbi, inda Bilyaminu ya girma, amma bai taɓa leƙa gidan kakar Bilyaminu idan ya girma ba, ya duba yaron ba. Hasali ma, ɓuya ya ke yi domin ba ya so a san cewa ya na garin.

5. Sun ce bai halarci ɗaurin auren Bilyaminu na farko ko na biyun da a ka yi da Maryam Sanda ba. Ko tambayar auren bai je ba.

6. Sun ce baban bai je ko jana'izar ko ta'aziyyar Bilyaminu ba.

7. Sun ce bai taɓa halartar Kotu domin bibiyar Shari'ar kisan Bilyaminu ba.

8. Sun ce sam bai tuntuɓe su ba kafin ya fito ya yi wannan maganar kuma ba wanda ya tuntuɓe su game da yafe wa Maryam Sanda, kuma su ba su yafe ba.

9. Su na zargin cewa miliyan goma uwar Maryam Sanda ta ba wa uban domin ya saryantar da jinin Bilyaminu.

Don uba dai mutumin nan shi ne uban Bilyaminu tun da haka Shari'ah ta ce. Amma abin mamaki ne don mutumin da bai san ciwonka ko kaɗan ba ya ce ya yafe jininka? Ai ko a kwalarsa. Shin uba shi kaɗai zai iya yafe jinin ɗa a Shari'ar musulunci ko kuwa sai dukkanin awliyāʾ al-dam (wakilan jini) sun amince?

Wata shari'ar sai a lahira.
Daga shafin Audu Bulama Bukarti.

Sau nawa kuke wanke Hannu a kowace rana ?
15/10/2025

Sau nawa kuke wanke Hannu a kowace rana ?

Tsohon Firaministan kasar Kenya Raila Odinga ya rasuA cewar sanarwar da shugaban kasar William Ruto ya wallafa a shafins...
15/10/2025

Tsohon Firaministan kasar Kenya Raila Odinga ya rasu

A cewar sanarwar da shugaban kasar William Ruto ya wallafa a shafinsa na Facebook, Odinga ya mutu ne a ƙasar Indiya inda yake jinya.

Sanata mai wakiltar Bauchi ta Arewa, Kaila Samaila, ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC.
15/10/2025

Sanata mai wakiltar Bauchi ta Arewa, Kaila Samaila, ya bar jam’iyyar PDP ya koma APC.

Address

Lagos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AID Multimedia Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AID Multimedia Hausa:

Share