
29/07/2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Ta Shiga Cikin Sha’anin Aurensu !
Wani matashi mai shekaru 27 mai suna Yayu Musa, ya shiga hannun rundunar sa-kai bayan da ya hallaka surukarsa, Atayi Abdul, a garin Olla, ƙaramar hukumar Omala, jihar Kogi.
Rahotanni daga mazauna yankin sun bayyana cewa lamarin ya faru da misalin ƙarfe 8 na dare a ranar Juma’a.
Wanda ake zargin ya yaudari surukarsa da zargin cewa wasu na girbin amfanin gonarta, lamarin da ya sa ta bi shi zuwa gona, inda ya cukume ta har ya kashe ta.
Bidiyon da rundunar sa-kai ta ɗauka ya nuna yadda aka sami gawar matar da raunuka da dama a jikinta, alamar cewa an sare ta bayan an kashe ta.
An k**a wanda ake zargin a wani gari dake makwabtaka da su bayan rundunar sa-kai ta ƙaddamar da farautarsa. A cikin bidiyon da aka ɗauka, Yayu Musa ya amsa cewa ya aikata kisan saboda fushin da ya ji game da yunƙurin surukarsa na ba wani namiji matarsa, Umi Idris, domin rashin samun ciki.