AID Multimedia Hausa

AID Multimedia Hausa Media and Multimedia Services

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Ta Shiga Cikin Sha’anin Aurensu !Wani matashi mai shekaru 27 mai suna Yayu Musa, ya sh...
29/07/2025

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Ta Shiga Cikin Sha’anin Aurensu !

Wani matashi mai shekaru 27 mai suna Yayu Musa, ya shiga hannun rundunar sa-kai bayan da ya hallaka surukarsa, Atayi Abdul, a garin Olla, ƙaramar hukumar Omala, jihar Kogi.

Rahotanni daga mazauna yankin sun bayyana cewa lamarin ya faru da misalin ƙarfe 8 na dare a ranar Juma’a.

Wanda ake zargin ya yaudari surukarsa da zargin cewa wasu na girbin amfanin gonarta, lamarin da ya sa ta bi shi zuwa gona, inda ya cukume ta har ya kashe ta.

Bidiyon da rundunar sa-kai ta ɗauka ya nuna yadda aka sami gawar matar da raunuka da dama a jikinta, alamar cewa an sare ta bayan an kashe ta.

An k**a wanda ake zargin a wani gari dake makwabtaka da su bayan rundunar sa-kai ta ƙaddamar da farautarsa. A cikin bidiyon da aka ɗauka, Yayu Musa ya amsa cewa ya aikata kisan saboda fushin da ya ji game da yunƙurin surukarsa na ba wani namiji matarsa, Umi Idris, domin rashin samun ciki.

Tinubu ya cika dukkannin alkawurran da ya yiwa yankin Arewa, inji kungiyar Gwamnonin Arewa.Me za ku ce ?
29/07/2025

Tinubu ya cika dukkannin alkawurran da ya yiwa yankin Arewa, inji kungiyar Gwamnonin Arewa.

Me za ku ce ?

Tsegumi! A kuke kalon wannan hadin na PDP a 2027?
29/07/2025

Tsegumi!

A kuke kalon wannan hadin na PDP a 2027?

Mutanen Barno sai son barka yayin da gwamnan jihar Baba Gana Umara Zulum ya Gina masu katafaren asibiti mai gadon marasa...
29/07/2025

Mutanen Barno sai son barka yayin da gwamnan jihar Baba Gana Umara Zulum ya Gina masu katafaren asibiti mai gadon marasa lafiya 150, asibiti na zamani mai wutar sola da kayan aiki na zamani.

Shin wai da gwamnan Barno da na Kano wa yafi aiki ne?

Shugabannin Arewa na taron tunawa da Sardauna A yanzu haka a dakin taro a Arewa Hausa, dake Kaduna inda aka fara gagarum...
29/07/2025

Shugabannin Arewa na taron tunawa da Sardauna

A yanzu haka a dakin taro a Arewa Hausa, dake Kaduna inda aka fara gagarumin taro na Kara wa Juna Sani karkashin Gidauniyar Tunawa da Sardauna. Taron ya tara manyan jami’an gwamnati daga shiyyoyin Arewa domin amsa tambayoyi game da ayyukan Gwamnatin Tinubu cikin shekaru biyu da s**a gabata, musamman a Arewa.

A yayin zaman, za a yi tattaunawa mai zurfi kan tsaron Arewa, bunkasar tattalin arziki, da inganta rayuwar al’umma ta hanyar shirye-shirye da tsare-tsaren gwamnati.

Tunawa da Sardauna ya k**ata shugabannin Arewa suyi ko kuma koyi da shi?

Yan matan Super Falcons da s**a lashe Gasar Kofin Afrika na Mata sun samu kyautar na dala $100,000 sama da 150millions N...
29/07/2025

Yan matan Super Falcons da s**a lashe Gasar Kofin Afrika na Mata sun samu kyautar na dala $100,000 sama da 150millions Naira kowacce 'yar wasa.

Yayin da kowanne Coach da ma'aikatan da Staffs s**a samu dala $50,000. Kimanin 75million. Bugu da ƙari, kowanne ɗan ƙungiyar zai samu gida mai ɗaki uku a ƙarƙashin shirin gidaje na gwamnatin "Renewed Hope Housing Scheme".

Amma waɗannan sojojin da s**a ji rauni har s**a zama nakasassu na har abada, ba su cancanci ko dala $100 ba. Wannan yana nuna mana yadda gwamnatinmu ta damu da harkar Tsaro.

Shin haka kuke gani ya dace da jaruman sojoji da ke sadaukar da rayuwarsu saboda ƙasar nan?

Mu faɗi gaskiya ko da sau ɗaya ne.

Daga Musa TG Muhammad

Ban ga rubutun Sheriff Almuhajir a kan daruruwan talakawan Zamfara da ke hannun 'yan bindiga ba, suma talaucinsu sa saka...
29/07/2025

Ban ga rubutun Sheriff Almuhajir a kan daruruwan talakawan Zamfara da ke hannun 'yan bindiga ba, suma talaucinsu sa sakacinsu ne k**ar yadda ya ke fada ya jefa su cikin wannan hali?

Mutum yana cikin gwamnati ba shi da aiki sai aibata talakawan Arewa, yana maganar su s**a daura wa kansu talauci, yana kwatantasu da na Kudu, bayan bai taba zuwa Kudu yayi rayuwa a can ba, kuma a haka wai Dafta ne?

Daga Ibrahim Dalib Abbas

Kamfanin dillancin labaran Nijar (ANP) ya ruwaito cewa ƙasashen biyu sun sanya hannu a yarjejeniyar ce ranar Litinin yay...
29/07/2025

Kamfanin dillancin labaran Nijar (ANP) ya ruwaito cewa ƙasashen biyu sun sanya hannu a yarjejeniyar ce ranar Litinin yayin ganawar shugaban Nijar, Janar Abdourahamane Tiani, da wata tawagar Rasha ƙarƙashin jagorancin ministan mak**ashi, Mista Sergei Tsivilev.

Yaushe kuke ganin itama Nigeria za ra yi wannan yunkuri ?

Makarantar G.S.S Kurna Asabe da ke Kano kenan.Hotuna daga Abdulwahab Magaji
29/07/2025

Makarantar G.S.S Kurna Asabe da ke Kano kenan.

Hotuna daga Abdulwahab Magaji

Hukumar dake yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta k**a Mutane 11 kan Haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a jihar Akwa I...
29/07/2025

Hukumar dake yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta k**a Mutane 11 kan Haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a jihar Akwa Ibom.

Omoyele Sowore yayi zargin Ganduje ya gina otel na biliyoyin nairori da kudin al'ummar Kano a Abuja.
29/07/2025

Omoyele Sowore yayi zargin Ganduje ya gina otel na biliyoyin nairori da kudin al'ummar Kano a Abuja.

Gwamnatin Kano ta shiga taitayinta ta Sako Shaikh Abduljabbar domin siyasa ce ta sa aka k**a shi, cewar Young Shaikh.
29/07/2025

Gwamnatin Kano ta shiga taitayinta ta Sako Shaikh Abduljabbar domin siyasa ce ta sa aka k**a shi, cewar Young Shaikh.

Address

Festac Town

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AID Multimedia Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AID Multimedia Hausa:

Share