15/10/2025
Yabon Gwani!
Prince Hadi Sani zakaran gwajin dafi na 'yan Arewa a Kudu
Malam Hadi Sani, Mai bai wa gwamnan jihar Ogun Dapo Abiodun shawara kan al'amuran baki a jihar ya ciri tuta duba da hidimtawa al'umma da yake ba dare ba rana.
Cikin kasa da shekaru 7 da yayi a wannan mukamin ya Samar wa matasan Arewa da dama ayyukan yi na gwamnati a matakin karamar hukuma, da jiha da kuma aiki a mataki na gwamnatin tarayya, inda da yawansu ke aiki a ma'aikatun gwamnati jihar Ogun, da na kananan humumomi a jihar, da kuma masu aiki a asibitoci na gwamnatin tarayya a matsayin manyan jami'an kiwon lafiya.
Malam Hadi Sani ya kasance mai yawan yi wa makarantun Islamiyya hidima ta hanyar gayaran gininsu, da kuma sabunta su tare da tallafa wa dalibai da kayan karatu.
Ya kasance mai shiga sha'anin matasa masu karamin karfi, inda yake kokarin gaske wajen taimakon matasa masu tukin babur ko 'yan acaba domin ganin sun sami walwalah, wani dan acaba ya shaida wa AID Multimedia Hausa yadda aka taba k**a shi, aka karbe masa babur, ya daga waya ya kira Hadi Sani, ya ce nan take sai ga mai bai wa gwamna shawara yazo har inda yake ya shiga tsakani aka mai do masa da babur din shi, ya ce abun ya ba shi mamaki, ya bai wa jami'an da s**a k**a shi mamaki, ya ce ko yanzu na kira lambar shi zai dauka.
Bugu da kari Malam Hadi Sani Yayi kokari sossai wajen shiga tsakani don magance rikicin Fulani Makiyaya da manoma a jihar, lamarin da ya kawo zaman lafiya mai daurewa a wannan fannin, wanda hakan ne ya sanya shi ya koma makaranta yake karantar fannin sasanci da tabbatar da tsaro a matakin karatu na digirin digirgir (Dr) a Jami'ar Ibadan bayan yayi digirinsa na farko da na biyu a ABU Zariya.
Ganin irin yabon da Malam Hadi Sani ke samu ne daga al'ummomin da yake wakilta hakan ne yasa muma muka kawo yabonsa, domin yabon gwani ya zama dole.
Ba Hadi Sani ne farkon wanda ya fara rike mukami tsakanin 'yan Arewa mazauna kudu ba, anyi wasu da dama kafin shi, wadanda s**a rike mukamin da yafi na shi ma, amma dai idan muka yi ta mahaukaci, zamu ce ba a yi wani dan Arewa a Kudu da ya sami damar gwamnati ya amfanar da al'umma tamkar Hadi Sani ba, idan kuma akwai, gareku 'yan Arewa mazauna Kudu, ku kawo, waye naku gwanin?
Me yayi wa al'umma?
Hoto:lawal Abdullahi Matazu