Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa

Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa, Fatima Dahiru funtuwa@gmail. com, Lagos.

Sunana Fatima Dahiru Funtuwa, an haifeni a 1997, tun tasowata inada sha'awar rubutu, ina godiya ga Allah da yayini a marubuciya, Allah ya 'kara mani fasaha da juriya tare da sauran marubuta, ya kuma cika mana burinmu na Al-kairi

21/11/2025

Yana da kyau mu fara tantance yadda ake rarrabe kalma da kalma sannan mu fara rubutu.

Idan mutum ya yi
rubutu ya fara karanta shi kafin ya yi Posting, saboda mai karantawa ya samu sau'kin fahimtar me aka rubuta.
Wad'annan wasu daga cikin 'ka'idojin rubutu ne, a tawa 'yar fahimtarπŸ˜‚ , wad'anda yana da kyau mu fahimci yadda ake rubuta su.
πŸ‘‡

acikin ❌ a cikin βœ”οΈ

yanadam fare❌ yana damfare βœ”οΈ

gir mamawa❌girmamawa βœ”οΈ

tare dasara masa ❌tare da sara mashi βœ”οΈ

nandanan❌nan da nan βœ”οΈ

yace❌ ya ce βœ”οΈ

atayarda Sallah❌ a tayar da sallah βœ”οΈ

dakyar tamike tafita ❌da kyar ta mi'ke ta fita βœ”οΈ

yanazaune❌ yana zaune βœ”οΈ

kaitsaye ❌ kai tsaye βœ”οΈ

s**anufi part d'in marwan tundaga❌ s**a nufi part d'in marwan tun daga βœ”οΈ

karage damuwa ❌ka rage damuwa βœ”οΈ

kasan yanayi ciyon ka ❌
ka san yanayin ciwon ka βœ”οΈ

Yanacikin ❌yana cikin βœ”οΈ

Slm ❌ Assalamu alaikumβœ”οΈ

Wlh❌ wallahiβœ”οΈ

Gdy❌ godiyaβœ”οΈ

shine❌ shi neβœ”οΈ

wacca❌ wacceβœ”οΈ

yacce ❌yaddaβœ”οΈ

ah ah❌ βœ”οΈa'a

nagode ❌na godeβœ”οΈ

itace❌ ita ceβœ”οΈ

20/11/2025

Big shout-out to my newest top fans! Haulat Harun, Sumayya Lawal, Farida Saadu, Rumaisa Ahmad, Shatuu Abdullahi Sidy, Karima Ibrahim Nakarkara, Pricess Nuri Khaleel, Mamee Sallau, Ltz Nusaiba Muhammad Abdullahi, Aslamiyya Musa, Fatima Adamu, Mareesah Ummar, Habibi shaibu , Ummu Rukayyat, Husnatullah Magaji, Khamis Ameera, Aisha Umar, Sameerah Ahmad, Ummakursum Abubakar, Abubakar Maryam, Hajarah kanwata, Aisha Mustapha, Maman Bashir Aminu, Maryam Boddi, Maman al ameen, Kausar Musa, Halimat Sadiya Uma Re, Medukan Marar Mata, Maryam Lawal, Fatima Hussaini, Fatima Zahara, Muhammad Aisha, Maman Zara, Lourert Louwerl, Ummih Haruna Dalwa, Suleiman Aisha, Benaxir gimba gani, Abdussalam Hussain, Ummu Hydar, Asma'u Ismail Muhammad, Fatima hussaini m dala, Rukayya A Yusuf, Bilkisu Ibrahim, Nafsee Lawal, Mareesah Umar, Ummuh Nihila, Zainab Ibrahim, Shamsu Yakubu, Zahra Teema Isah, Mudassir Dahiru

20/11/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Nusaiba Garba Kanwa, Asmaa'u Ahmad, Ummun Areef, Salisu Balkisu, Maman Najla, Maman Khaleel, Jiddarh Suleiman, Husee Bileesing, Katiy Muhammad, Ummu Maryam, Hauwa Baba, Tymer's Henna, Khadija Lawal

: πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    58   09042512952         Ya ce "Allah...
20/11/2025

: πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 58

09042512952


Ya ce "Allah dai ya kiyaye, Aiku matanne da anyi maku zancen kishiya shikenan yanzun mutum ya' bata shirin shi."

Ta ce "A'a ka daina yin jam'i, ni ka ta'ba ganin na yi?"

Ya ce "To na ta'ba zo maki da zancen kishiyar ne?"

Ta ce "Haba ai kasan ni ba abinda zai faru."

Ya ce a'a ai ba'a san maci tuwo ba sai miya ta 'kare. "

Tayi dariya tare da fad'in "Ai dai ya k**ata ka shaide ni."

Ya ce "Taya za'ayi in shaide ki? Tunda ban ta'ba zo maki da zancen 'kara auren ba, amma ba komai, wata rana koda wasa ne zan tone ki da zancen kishiya, inga yadda zakiyi."

Ta ce "To ai ka riga kace tono na zakayi, kaga daka fad'a dama na sani, don haka ya za'ayi in tada hankali na, tunda na san wasa kake."

Sukasa dariya baki d'ayan su.

🍚🍚🍚🍚🍚KATSINA TA DIKKO 'DAKIN KARA 🍚🍚🍚🍚🍚

Ko da ta je wurin su H-Amina sai da hankalin ta yayi mummunan tashi, saboda ta same su a wani Irin yanayi, sunyi ramar da basu ta'ba yin Irin ta ba, ga bugu, duk an farfasa masu jiki, fuskar su duk ta kumbura, sunyi wani zuru-zuru, duk wanda ya gansu dole ya tausaya masu, bata san lokacin da hawaye s**a zubo mata ba, sai da ta dake sannan ta ce

"H-Amina me yasa kika kashe kishiyar ki?"

H-Amina ta d'ago da idanun ta, wad'anda har sun 'kan'kance saboda azabar kuka.

Ta ce "Bani na kashe ta ba."

Barrister Haseenat ta ce "To yaya akayi?"

Ta ce "Zargi ne kawai akeyi, Al-halin ni da naje gidan ma ko ganin ta banyi ba, kuma lokacin da aka kashe ta ni na riga na kai kano, ban san yadda akayi ba."

Barrister Haseenat ta ce "Kin tabbatar ba ke kika kashe taba?"

"Bani na kashe ta ba, kuma ban san wanda ya kashe ta ba, tunda ni bamma ta'ba zuwa garin ba sai wannan ranar, ballan tana in san ala'kar ta da mutane."

Barrister Haseenat ta ce "Da kika shiga gidan me yasa baki ganta ba?"

"Sabo da mujin ta ya rufe 'kofar, ko falon ma bai bari na shiga ba, har nabar gidan, kuma bayan na tafi shima ya biyo ni a baya, ni lokacin na isa kano, shi kuma ya kusa kaiwa, aka kira shi a waya aka sanar da shi cewa yaje an tarar da gawar matar shi a cikin d'akin ta, daga haka ni bansan komai ba. "

Barrister Haseenat ta ce "Kin tabbatar abinda kika fad'a min gaskiya ne?"

H-Amina ta ce "Iya kar gaskiya ta na fad'a maki."

Barrister Haseenat ta ce "Idan har aka samu akasin haka, to ni babu yadda za'ayi in iya fitar dake, ma'ana in dai ke kika kashe ta, to dole gaskiya zatayi halin ta."

H-Amina ta ce "Wallahi ba ni na kashe ta ba😭😭😭."

Dai-dai nan kuka ya kwace mata.

Barrister Haseenat tayi waje, don bazata iya ci gaba da ganin yanayin da Amina take ciki ba.



COURT

Ranar litinin biyu ga watan February aka fara shari'ar H-Amina Mansur.

Kamar yadda aka saba, ko wace ranar Monday courtu tana cika ma'kil da jama'a.

Haka aka fito dasu duk sun fita k**annin su.

Bayan an natsu, maga takardar kotun ya kira sunan shari'ar da z'a fara yi a yanzun, sannan lauyoyi s**a gabatar da kansu k**ar haka.

"Sunana Barrister Abubakar Ibrahim, ni lawyer ne daga hukumar kare ha'k'kin d'an Adam, na tsaya ne a wurin nan domin kwato ma iyalan marigayiya ha'k'kin su na kisan 'yar su da akayi."

Daga d'aya ' bangaren kuma ta ce

"Sunana Barrister Haseenat, ni lawyer ce wadda nake kare wadda ake zargi da kisan marigayiya Mariya."

Sannan gaba d'ayan su s**a zauna.

Al-'kali ya ce "Daga ' bangaren kare ha'k'kin 'Dan Adam, ko zaka sanar damu dalilin da yasa kuke zargin H-Amina da cewa ita ta kashe kishiyar ta?"

Barrister Abubakar ya sake mi'kewa tsaye, sannan yayi godiya ga Al-'kali ya ci gaba da cewa

"Ranar Ashirin da uku ga watan January, H-Amina da 'kawar ta sun shiga gidan marigayiyar da tashin hankali mai tsanani, wanda daga 'karshe har ita H-Aminar tayi ikirarin cewa :Lallai bata fita gidan sai taga gawar ta, kuma hakan ta fad'e shine a bainar jama'a, bayan kuma ta bar gidan da wasu awanni, sai aka tarar da gawar mamaciyar a d'akin ta, inda aka kashe ta da wu'ka, ta hanyar caka mata ita a 'kafon zuciya, don haka muke neman wannan kotu mai adalci da ta d'auki matakin daya dace akan wannan mata, na gode. "

Zuwa can sai Al-'kali ya ce "Ko Lawyer wadda ake zargi tana da abin cewa?"

Sai ita ma ta mi'ke bayan Barrister Abubakar ya zauna.

"Kwarai kuwa ya mai shari' a, Maganar cewa H-Amina ta ambaci zata kashe Mariya, wannan ba abin mamaki bane, domin kuwa kowa yasan zafin kishi ga d'iya mace, a yayin da Irin abinda ya faru ga H-Amina ya faru gare ta, zata iya fad'in ko wace Irin kalma ce a yayin da take cikin 'bacin rai, harma abinda ba zaka iya aikatawa ba.

Ta fad'i kalmar kisa ne badon zata iya aikatawa ba, sai don zafin kishin da take ciki a wannan lokacin, sai kuma

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    57   09042512952            πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’BIRNI...
17/11/2025

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 57

09042512952



πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’BIRNIN TARAIYA ABUJA πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’

Bata sha wahala ba ta gane gidan, kuma tayi sa'a ta same ta a gida.

Bayan sun zauna.

Ta ce "Ashe Yau babbar ba'kuwa gareni, ya hanya?"

Asiya ta ce "lafiya lau."

Barrister tasa aka kawo mata abinci da lemo mai sanyi, ta ce "Lallai kinsha hanya, ya maman taki?"

Asiya tayi shiru, sannan ta ce "Dama dalilin tane nazo."

Barrister Haseenat ta ce "Gaskiya shiyasa na ganki a cikin wani Irin yanayi, hala babu lafiya ko?"

Asiya ta d'aga kai alamar e.

Barrister Haseenat ta 'kara tsaida hankalin ta wuri guda tana kallon Asiya, tare da sauraron maganganun da zasu fito daga bakin ta.

Asiya ta ce " Daddyn mune ya' kara aure................................................................................................................

Asiya ta gama fad'a mata abinda ya faru, kaf! Bata 'boye mata komai ba, bayan ta gama ta fashe da kuka.

Barrister Haseenat ta ce "Kiyi ha'kuri, in Allah ya yarda komai zaizo da sau'ki, ba zaku rasa mommy ku ba, zata fito da izinin Allah, ku dai ku tayata da Addu'a, ranar Monday kikace za'a shiga shari'ar ko?"

Asiya ta ce "E.

" To shikenan Allah ya kaimu, Katsina ne aiko? "

Asiya ta ce " Can ne."

Barrister ta ce " To shikenan kina iya zama nan wuri na, ranar juma'a (Jibi kenan) saimu tafi, dama ai bada mota kikazo ba ko? "

Ta ce " E, ta jirgi nazo."

Barrister ta ce " To shikenan sai mubi jirgin ranar juma'a, mu tafi, kinga zuwa Asabar da Lahadi harna kimtsa.

Ta ce "To shikenan nagode."

Barrister Haseenat ta ce "Ai ba komai yima kai ne, duk wani matsayi dana kai a yanzun maman ki ce sila, bazan ta'ba mantawa da ita ba, kuma zanyi bakin 'ko'karina don ganin ta fita, Allah ya shege mana gaba."

Misalin' karfe Tara na dare, Barrister Haseenat na zaune tare da mai gidan ta Barrister Kabir Ma'karfi, suna kallon tashar NTA News.

Haseenat ta ce " Niko Oga akwai maganar da nake so muyi da kai tun d'azun, amma na bari ne ka kimtsa tukunna."

Ya ce "Ina jinki."

Ta taso daga inda take zaune ta dawo Daf! Dashi ta zauna, sannan ta ce " 'kawa ta da nake yawan baka labarin ta, H-Amina ta Kano?"

Ya ce "Oky na gane ta."

Ta ce "To shine wani iftila'in rayuwa ya same ta, mai gidan ta ne ya 'kara aure bai sanar da ita ba, har saida akazo har gida aka gaya mata, to ranta ya' baci sosai, sai taje har gidan da aka ce mata yayi auren, ta same shi tayi fad'anta son ranta, har tana cewa saita kashe Amaryar, to bayan ta gama fad'an nata ta dawo gida, sai akaje aka samu gawar Amaryar, to shine akazo aka tafi da ita, akan zargin ita ta kashe ta, daga ita har wadda tazo ta sanar da ita karin auren mujin nata suna hannu, ranar litinin d'innan za'a shiga shari'ar.

To amma ni Oga abinda yake bani mamaki, TAYA ZA'AYI AMINA TA IYA KASHE MUTUM? Matar dana sani da tausayi, wadda ko wata halitta taga mutum zai kashe, sai tace me tayi maka? To amma tayaya ita zata iya kashe mutum? "

Barrister Kabir ya ce " Aiku mata wani lokacin halin ku yana iya canzawa daga yadda aka sanku, musamman idan aka zo maku da zancan kishiya, gaba d'aya idanun ku rufewa sukeyi, nan take sai aga hali ya canza."

Umhhh! Oga wasu matan dai, amma duk da haka ai kasan baiyi mata adalci ba, a 'kalla daya sanar da ita kafin yayi auren, da hakan bata faru ba, amma sai ya 'boye mata."

Barrister ya ce "To kika sani ko yana tsoron ya sanar da ita ne gudun tashin hankali?"

Ta ce "To ai kuma ga abinda rashin sanarwar ya haifar, in kasan kana tsoron abu me zaisa kayi shi? Kuma dole nefa sai namij ya zama jajurtacce a cikin gidan shi, ya nuna komai baifi 'karfin shi ba, amma yanzun ina amfanin wannan?"

Ya ce "Allah dai ya kiyaye, Aiku matanne da anyi maku zancen kishiya shikenan yanzun mutum ya' bata shirin shi."

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    56   09042512952      Ta ce  "Asiya Mom...
16/11/2025

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 56

09042512952

Ta ce "Asiya Mommyn ki mutuniyar kirkice, mai tausayi, musamman idan ta lura da mutum baya da shi, Asiya nayi karatu, amma kashi saba'in cikin d'ari 70/100 na hidimar karatu na Mommyn ki ita ta d'auka, har nakai matsayin da nake a yanzun, domin ita Amina 'yar kasuwa ce, ni kuma karatu nake so inyi, ' kawata ce sosai wadda tayimin abinda ko d'an uwa nane iyakar abinda zai yi min kenan, karatu dai har na 'kasar waje da nayi ita ta d'auki nauyi, da kud'inta nayi wannan karatun, ni ban ta'ba ganin 'kawa ma Irin wannan ba.

Idan inayi mata godiya sai ta ce min: Ai taimakon kai ne, wata rana kema zaki iya tai makona ta inda ban zata ba, kuma ko baki taimake ni ba, idan kika taimaki' kasa ta ai kin gama min komai.

Asiya ki d'auki hali Irin na maman ki. "

NA ce " Mommy na mutuniyar kirkice, to da kikayi karatun wane aiki k**e yi yanzun? "

Ta ce "Aikin lowyer, tare da kuma muji na Barrister Kabir Ma'karfi, wanda shi tsofon lowyer ne, kuma mai yin nasara a mafi yawa daga case d'in da yasa gaba, wanda hakan yasa mutane da yawa suke son aikin shi sosai, domin ko ni idan na had'u da cese me rikitarwa, saina had'a da neman taimakon shi. "

NA ce" Lallai Mommyn mu nima in Allah ya yarda zanyi hali Irin nata, sai idan....................

******************************

AL-Amin ya katse ta da cewa "Ina ne wannan 'kawar Mommyn take?"

Asiya ta ce "Ta fad'a mani cewa tana zaune ne a Abuja."

Alhaji Mansur ya ce "Yaya Sunan ta."

Asiya ta ce "BARRISTER HASEENAT, Daddy ka bani dama inje Abuja in sanar da ita halin da Mommy take ciki."

AL-Amin ya ce "Kinsan gidan ta ne?"

Asiya ta ce "Mommy ta ta'ba zuwa dani, sau d'aya amma Insha Allahu zan gane."

πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’BIRNIN TARAIYA ABUJA πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’πŸ’

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    5509042512952      Asiya ta ce "Daddy k...
16/11/2025

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 55

09042512952

Asiya ta ce "Daddy kasan zafin kishi Irin na mommyn mu, amma me yasa zakayi aure bata sani ba? A 'kalla inda ta sani Daddy abin zaizo da sau'ki, yanzun shikenan Daddy mun rasa mommy kenan? 😭😭😭."

Dai-dai nan ta fashe da kuka.

AL-Amin ya ce "Daddy ina mafita?"

Daddy ya d'ago kan shi ya ce "Nima ita d'in nake tunani, domin kuwa rana ita yau za'a fara shari'ar su, ina ne zamu samu kwararren lowyer wanda zai tsaya mana a wannan shari'ar? Domin kuwa LALLAI CASE 'DINNAN BA MAI IYA WARWARE SHI SAI WANDA YASAN AIKIN SHI, shine nake tunanin wane lowyer ne zan tunkara? "

Asiya ta d'ago kanta cikin sauri ta kalli Daddy ta ce " Akwai. "

Gaba d'ayan su s**a maida hankalin su a kanta.

Ta ce "Wata ranar Juma'a, Mommy tayi ba'kuwa, lokacin banyi aure ba, ina cikin d'aki na, naji ta kwala min kira

******************************

" Asiya!

Cikin sauri na tafo wurin ta, tare da fad'in " Gani Mommy."

Ta ce " Sarkin zaman d'aki, kizo ga wata maman taki nan ku gaisa."

Cikin fara'a nace "Sannu da zuwa Mommy."

Itama ta amsa min cike da kulawa, sannan ta ce "Ashe kinada budurwa haka?"

Mommy tayi dariya ta ce "Akwai ma yayan ta ya fita ne, sunan shi Aminu."

Ta ce "Masha Allah kice na kusan dawowa biki."

Sukasa dariya, ni kuma saina juya zan koma d'aki na.

Mommy ta ce "Zo ki zauna kafin in dawo, ta mi'ke tsaye, tare da fad'in "Naji Daddyn ku ya shigo, bari naje wurin shi."

Lokacin da mommy ta tafi ni kuma na zauna, kawai sai muka fara fira da ba'kuwar tata, anan take tambayar matakin karatuna ni kuma ina bata amsa.

Ta ce "Asiya Mommyn ki mutuniyar kirkice, mai tausayi, musamman idan ta lura da mutum baya da shi, Asiya nayi karatu, amma kashi saba'in cikin d'ari 70/100 na hidimar karatu na Mommyn ki ita ta d'auka, har nakai matsayin da nake a yanzun,

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    5409042512952             Ta ce  "Docto...
16/11/2025

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 54

09042512952



Ta ce "Doctor kayimin addu'ar in mutu kawai! Domin kona fito wani tashin hankalin zan fuskanta a wurin ka! Ni ina nan ina tsare maka kaina, kai kana can kana cin amana ta!"

Sai hawaye sharrr! A idanun ta.

Don haka kaje kawai kaci gaba da yimin addu'ar mutuwa.........

Dai-dai nan wata 'yar sanda ta le'ko, ta ce " "Malam lokacin ka fa ya' 'kare. "

Don haka cikin sauri ya fita, Halima ta 'kara
fashewa da kuka.

Alhaji mansur ma yazo wurin su, ya kuma tausaya masu sosai, don saida ma aka fitar dashi daga wurin, don kuka yakeyi sosai.

Mahaifiyar ta H-Asamau da mahaifin ta duk sun zo, a binda s**a fad'a mata shine "Duk runtsi kada ku amsa laifin da baku kuka aikata shi ba, domin komin daren dad'ewa gaskiya zata baiyana, idan kuka amsa laifin da baku ku kayi ba, to za'a yanke maku hukuncin da bai k**acekuba, ha'ki'ka kun shiga rayuwa mai wahala, amma ku zama masu juriya da mi'ka Al-amarin ku ga Allah, lallai zai kawo maku mafita, tabbas zaku sha wahala! Amma ku jure, ku shanye duk wata wahala da za'a baku, mu kuma zamu taya ku da Addu'a."

Haka s**a rabu kowa na kuka.

Washe gari tunda safe, aka saka su a mota aka wuce dasu katsina, ba tare kuma da 'bata lokaci ba aka wuce da case d'insu courte domin tabbatar dayin bincike.

Domin iyayen ta ne s**ace basu yarda ba, lallai 'yarsu sharri akayi mata, ba zata ta'ba iya aikata hakan ba, to don haka aka mi'ka AL-amarin zuwa Courtu.

A Kano kuwa Alhaji Mansur ne zaune a cikin falon H-Amina, yayi tagumi da hannayen shi guda biyu,, sannan gaba d'aya' ya'yanshi na zaune a falon.

AL-Amin ya ce "Abbah me yasa kayi mana haka? Gashinan duk ka sanya mu cikin wani Irin yanayi, wanda ko a mafarki bamu ta'ba shiga Irin shi ba."

Asiya ta ce "Daddy kasan zafin kishi Irin na mommyn mu, amma me yasa zakayi aure bata sani ba? A 'kalla inda ta

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    5309042512952        Suna isa Station d...
16/11/2025

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 53

09042512952

Suna isa Station d'in s**a iza 'keyar ta bayan sel, inda 'kawar tata take, sannan cikin hanzari 'yar sandar ta dawo opice ogan su.

Ta ce "Sir an shigo da ita, tana bayan kanta."

Ya ce "OK yanzun zan had'a files d'insu a wuce dasu Katsina, kuma sune kad'ai wad'anda ake zargi da kisan?"

Ta ce "Sune kad'ai Sir."

Ya ce "Yayi kyau, bazan ta'ba wannan cese d'in ba, amma ku shirya zuwa gobe sai a wuce dasu."

Ta ce OK Sir, tare da sara mai.

Shi kuma sai ya mi'ke ya nufi bayan kantar, yayi tsaye yana kallon su d'aya-bayan-d'aya, kimanin mintuna biyu, sannan ya girgiza kai ya wuce.

A wannan lokacin kuwa idanun kowa yayi jawur k**ar gauta, don sunyi kukan gami da yin nadama har ba iyaka.

Halima ta ce "Hajiya duk ni naja maki wannan abu, don da banje na sanar dake ba, da hakan bata faru ba."

H-Amina ta ce "A'ah kibar d'ora laifin a kanki, domin kuwa ni na fiki ganin laifi na, dana kasa sai-sai-ta kalamaina a yayin da nake fad'a a gidan ta, sannan kuma da nasan yarinyar nan kwanan ta sun kusa 'karewa, da banma wahalar da kaina a kanta ba, Allah shiya jarrabemu da wannan Al-amari, kuma shine kad'ai zai iya fidda mu. "

Doctor Ahmed yazo, don ya 'kara ganin ta, ta bashi tausayi sosai a yanayin daya ganta, bai san lokacin daya zubda hawaye ba.

Ita kuwa rad'ad'i biyu ne a zuciyar ta, idan ta kalle shi tana yimai kallon wanda yaci amanar ta, shiyasa koda yazo ma sai taji k**ar ya 'kara mata wata azabar ne.

Ya ce "Allah ya kiyaye Halima, Allah kuma ya fitar da ku, domin nasan duk zargi ne, kuma wata rana zaku fita, Allah ya baiyanar da gaskiya."

Ita dai bata ce mai komai ba, don ita zafin kishin da take ciki ma yafi u'kubar da take ciki yanzun.

Ya ce "Don Allah idan kin fito ki gyara halin ki."

Ta ce "Doctor kayimin addu'ar in mutu kawai! Domin

13/11/2025

IDAN WANI YAYI RAWA AKA BASHI KU'DI, WANI IDAN YAYI DUKA ZAISHA.

Bar ganin AM YERIMA ya samu wannan nasarar, kar kayi tunanin cewa idan wani ya aikata Irin haka zai tsira.

Zata iya yuwuwa Yarima yanada wani jigo na kusa dashi a gomnatance, wanda dama ta'bashi ba abune mai sau'ki ba, ko kuma Asali d'an wani ne.

Za kuma ta iya yuwuwa nasara ce da wata hikima daga lillahi.

Koma dai menene munayi mashi fatan Al-kairi, Allah kuma ya tsare shi akan sharrin ma'kiya, idan har abinda yayi akan gaskiya ne.

Amma nayi imani harga Allah wani idan ya aikata, daga wajen da akayi a bin, ba za'a d'aga maganar ba, ballan tana har wasu ma, su saka baki, mutum ya jama kanshi d'auri kenan har iyakar rayuwar shi, da 'kas'kanci, ba kuma za'a ta'ba jin labarin ba, shikenan yayima' yan uwanshi da iyayen shi asara.

Kada kace wannan yayi nima bari in zama (Jan wuya) in aikata Irin abinda yayi, wata 'kila ya zame maka rabon wahala.

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    5209042512952       Kwana biyu gawar ta...
13/11/2025

πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 52

09042512952

Kwana biyu gawar tayi a hannun likitoci, sannan s**a badata don ayi mata sutura.

Alhaji Sa'adu na zaune bisa kujera, shi kuma Alhaji Mansur yana zaune kan gado, ya mi'ke' kafafun shi, yake cewa "Sa'adu wallahi dana san abinda 'karin auren nan zai jawo min kenan da banyi ba, yanzun dai na rasa Amaryar, kuma Itama uwar gidan tana neman su'buce mani, wannan wace Irin rayuwa ce?"

Alhaji Sa'adu ya ce ' kaddara ce, wadda kuma bakada ikon da zaka kauce mata, sai dai wannan mata taka tayi kuskure."

Alhaji Mansur ya ce "Yanzun kaima kana zargin cewa H-Amina ce ta kashe ta?"

Ya ce "Yaya aiba zargi nake ba, magana ce gatanan tabbatacciya!! Ba'kin ciki na d'aya 'ya'yan da kuka haifa da ita, ta bar masu abin kunya!"

Alhaji Mansur ya ce "Sa'adu ka daina wannan zargin ba gaskiya bane, H-Amina ba zata iya aikata kisa ba, ni nafi kowa sanin halin ta."

"Haba yaya ya zaka ri'ka saurin kare ta, bacin zafin kishin ta ya riga ya d'ebe ta, ta aikata mummunan aikin da zata dawo tayi danasani!! Haba yaya k**a daina wannan maganar Allah dai ya kiyaye gaba kawai."

Anzo an tafi da Halima station, k**ar yadda aka d'auki H-Amina, Doctor Ahmed ya tausaya mata sosai, kuma yayi juyayin wannan lamari, duk da yasan duk tsiya zata dawo, domin zargine ake yi masu, kuma komin daren dad'ewa gaskiya zata baiyana, don har cikin zuciyar shi bai yarda cewa za'a iya had'a baki da matar shi ayi kisan kai ba (Koko don dai baiga Irin tashin hankalin da s**aje s**ayi a gidan mamaciyar bane oho?) Amma koba komai anyi maganin gulag cc Irin ta Halima, gobe ma ta 'kara.

Duk da yasan zafi Irin na sha'anin kisa, amma sai bai d'auki a bin cewa zai yi wani zafi ba, kawai dai bincikene za'aje ayi a dawo.

wannan kenan.

Suna isa Station d'in s**a iza 'keyar ta bayan sel, inda 'kawar tata take, sannan cikin hanzari 'yar sandar

fateema: πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“                          NAFATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA  Page    5109042512952      Ai bata san...
12/11/2025

fateema: πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“ RUĎANI πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“πŸŽ“

NA

FATIMA ĎAHIRU FUNTUWA BINTA

Page 51

09042512952

Ai bata san lokacin da ta diro 'kasa da gwowoyinta ba, ta dur'kushe a gaban shi, tana bubbuga' kafafun shi ta ce "Don Allah Doctor in barci nake yi ka ta she ni, Doctor mafarki nakeyi ko? Don Allah ka tada ni! Wallahi 'kwa'kwalwa ta bazata iya d'auka ba! Doctor me kake cewa ne?"

Ya ce "A'ah! Halima meye hakane wai? To ki bud'e idon ki sosai, ba mafarki k**e ba, nine dai k**e gani, kuma na 'kara aure kimanin watanni hud'u da s**a wuce."

Ta ce "Doctor da matar ka fa kace kake waya, harna tsaya ma ina sauraron ka!! Ni na d'auka ma da wata karuwa can, ka samu kuke waya, in tashi inyi fad'a na in ha'kura! Don nasan duk tsiya wata rana zata rabu da kai, ko kuma inyi yadda zanyi in rabaka da ita! Amma sai ka bud'e baki kacemin matar ka! Na shiga uku πŸ™†β€β™‚οΈπŸ™†β€β™€οΈ Doctor me kake nufi? "

Ya ce" Subuhanallahi! Halima ya zaki zarge ni da karuwa? Mata ta ce, k**ar yadda na aure ki fa, A'ah! Ni ki daina had'a ni da karuwa gaskiya."

"Doctor ka 'kara aure? Ka sakani a cikin kunyar duniya! Ni gara ma a kashe ni in huta!!!"

Ya ce "Halima ki dubi' kalu-balan da k**e ciki a kan kisan yarinyar nan, ba wannan shirmen ba!"

Ta ce "Yo aini abinda kazo min dashi ya fiyemin wannan case d'in zama tashin hankali!! Ni! Kamar ni πŸ€·β€β™€οΈ!!! Kishiya!!! πŸ‘©β€β€οΈβ€πŸ’‹β€πŸ‘© Doctor akwai matsala!!"

Ya ce "A wurin ki ko?"

Ta 'kara kallon shi sosai, Ta ce "Yo bak**a damu ba."

Ya ce "To damuwar me zanyi?"

Haka ta kwana kuka a wannan daren, don a rayuwar ta bata ta'ba gain ba'kin dare Irin wannan ba.

A Asibitin kuwa ruwa aketa' kara ma Alhaji Mansur da Mama Jummai, ko wannen su yana cikin wani yanayi, domin kuwa Alhaji Mansur sambatu kawai yake, wani lokacin ma sai an rirri'ke shi.

'Kanin shi Alhaji Sa'adu shine yazo yake jinyar shi.

Kwana biyu gawar tayi a hannun likitoci, sannan s

Address

Fatima Dahiru Funtuwa@gmail. Com
Lagos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Littafin Abokin fira Na Fatima Dahiru Funtuwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share