Comrd Ahmad TV

Comrd Ahmad TV Graphic designer, content writer, Business advertiser, business planner, oil and gas marketer, long grain rice seller DM for a business deal 09031316584

HUKUMAR HISBAH TA JAHAR SOKOTO TA RUFE WASU HOTEL BIYU .Hukumar Hisbah ta jahar Sokoto Nachi gaba dakai Samame inda a ji...
06/06/2026

HUKUMAR HISBAH TA JAHAR SOKOTO TA RUFE WASU HOTEL BIYU .

Hukumar Hisbah ta jahar Sokoto Nachi gaba dakai Samame inda a jiya Juma'a 5/6/2026 jami'an na Hisbah Sun sake kai wani samame a shiyar kwanawa tare da cafke Mutun goma sha tara (19) Maza da Mata

Tare da Kulle Otal biyu (2) da s**a sabama Umarnin Hukumar. Wannan samamen ya gudana a karkashin Jagorancin Babban Kwamandan Hisbah na jahar Sokoto Malan Usman Abdullahi Jatau tare da rakkiyar Director Da'awah Imam Sirajo Abubakar, board member mal. Abdurrahman mai tawul, AC Hassan Mu'azu da AC Habibah Muhammad Karkashin OPERATION TSAFTACE BIRNIN SHEHU.

Na shirya mutuwa  Akan Al’ummata.Inji hon yahaya yari Abubakar
05/06/2026

Na shirya mutuwa Akan Al’ummata.

Inji hon yahaya yari Abubakar

APC ne s**a fara neman Peter Obi ya yiwa Tinubu Mataimaki kafin mu hade dashi, watakila lokacin yana musulmi, sai yanzu ...
05/06/2026

APC ne s**a fara neman Peter Obi ya yiwa Tinubu Mataimaki kafin mu hade dashi, watakila lokacin yana musulmi, sai yanzu da muka hadu ya zama Arne. Inji Kwankwaso

Me Zaku Ce ?

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!Allah Ya yi wa Malam Abbakar Pharmacy rasuwa a yau Juma'ah, bayan jinya da ya sha...
05/06/2026

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!

Allah Ya yi wa Malam Abbakar Pharmacy rasuwa a yau Juma'ah, bayan jinya da ya sha fama da ita.

Muna roƙon Allah ya jiƙansa da rahama, ya gafarta masa kurakuransa, ya yalwata masa kabarinsa, ya kuma bai wa iyalansa da masoyansa haƙuri da juriya.

Allah Ya sa Aljannah ce makomarsa tare da iyayenmu da malamanmu da zurriyyarmu da aminanmu da yan'uwanmu.

LABARI: Kotun Tarayya Ta Umarci Sowore Ya Fara Kare Kansa A Shari’ar Bata Sunan TinubuDaga Ayau News// Fareedah Abdullah...
05/06/2026

LABARI: Kotun Tarayya Ta Umarci Sowore Ya Fara Kare Kansa A Shari’ar Bata Sunan Tinubu

Daga Ayau News// Fareedah Abdullahi Zarma

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci ɗan siyasa kuma mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore, ya fara gabatar da kariyarsa a shari’ar bata suna da aka shigar a kansa kan zargin yin kalaman ɓatanci ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Wanda hukumar DSS ke tuhuma da wallafa kalaman da ake zargin ƙarya ne a shafukansa na X da Facebook, inda ya kira Shugaba Bola Tinubu da "mai laifi" ( criminal).

Mai shari’a, Mohammed Umar, ya yi watsi da bukatar lauyan Sowore na a dage shari’ar har bayan hutun kotu. Daga nan sai ya ba da umarnin a ci gaba da sauraron shari’ar kullum k**ar yadda doka ta tanada. Kotun ta sanya ranar 5 ga Yuni domin Sowore ya fara gabatar da hujjojin kare kansa.

Me zaku ce?

LIKE// SHARE & FOLLOW

DA DUMI-DUMI: An k**a Ifechukwu Dennis matashin da ake zargi da kwaikwayon muryar Shugaba Tinubu, inda a ciki ya yi wasu...
05/06/2026

DA DUMI-DUMI: An k**a Ifechukwu Dennis matashin da ake zargi da kwaikwayon muryar Shugaba Tinubu, inda a ciki ya yi wasu kalamai masu tada hankali da ka iya jawo shugaban kasar ya fadi zabe

Kakakin Shugaban Kasa Bayo Onanuga ya ce an k**a matashin ne a Benin bayan da Shugaban yan sanda ya yi amfani da fasahar zamani wajen ganowa da cafko matashin

Me ya k**ata ayi masa?

05/06/2026

Sheikh Isa Ali Pantami ya gama magana

DA DUMI-DUMI: Jam'iyyar APC Ta Tabbatar Da Cewa Har Yanzu MA Ne Ɗan Takararta Na Gwamna, Ta Musanta Jita-Jitar Sauya Shi...
04/06/2026

DA DUMI-DUMI: Jam'iyyar APC Ta Tabbatar Da Cewa Har Yanzu MA Ne Ɗan Takararta Na Gwamna, Ta Musanta Jita-Jitar Sauya Shi

Jam’iyyar (APC) ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta dangane da cewa wai ana shirin sauya ɗan takararta na gwamna a Jihar Bauchi, a cewarta, labari ne na ƙarya marar tushe.

A cikin wata sanarwa da Shamsuddeen Lukman Abubakar ya fitar, an tabbatar da cewa Mohammed Abdullahi Abubakar shi ne halastaccen ɗan takarar gwamna na APC a jihar, kuma babu wani mataki ko niyya da ke nuni da iyuwar sauya shi.

Sanarwar ta ce an ƙirƙiri jita-jitar ne domin tayar da hankali da kuma karkatar da hankalin magoya baya daga manufofin jam’iyya da burin ci gaba da aka gina.

Haka kuma, an yi kira ga mabiya jam’iyyar da al’ummar jihar da su yi watsi da irin waɗannan rahotanni, su kuma ci gaba da kasancewa cikin natsuwa da goyon bayan tafiyar jam’iyyar.

A ƙarshe, APC ta jaddada cewa matsayinta a kan takarar gwamna a Bauchi bai canza ba, tana mai kira da a ci gaba da tallata manufofin ɗan takarar domin ciyar da jihar gaba.

DA DUMI-DUMI: Masu zanga-zanga sun kusa shiga harabar fadar shugaban kasa duk da tulin jami’an tsaro da aka jibgeRahoton...
04/06/2026

DA DUMI-DUMI: Masu zanga-zanga sun kusa shiga harabar fadar shugaban kasa duk da tulin jami’an tsaro da aka jibge

Rahoton ICR ya nuna cewa masu zanga-zangar na cigaba da samun karin mutane da yawa wanda a yanzu haka har sun kai harabar ginin sakatariyar Gwamnatin Tarayya dake kusa da fadar Shugaban kasa ta A*o Villa, suna neman sai an sako duka mutanen Najeriya da yan bindiga ke rike da su

Sannan kuma suna son Tinubu ya sauka nan take saboda ya gaza daqile matsalar tsaro

Me zaku ce?

MAFI ƘOLOLUWAR ZALUNCIMafi ƙololuwar zalunci shi ne cin zarafin dattijo wanda har ya kai shekarun da yake da jikoki k**a...
04/06/2026

MAFI ƘOLOLUWAR ZALUNCI

Mafi ƙololuwar zalunci shi ne cin zarafin dattijo wanda har ya kai shekarun da yake da jikoki k**ar ka. Dattawa mutane ne da ya k**ata a girmama su, a tausaya musu, kuma a kare mutuncinsu a kowane hali.

A cikin wani faifan bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, an ga yadda wasu masu garkuwa da mutane ke cin zarafin waɗannan dattawa domin tilasta wa iyalansu kawo kuɗin fansa. Wannan lamarin ya nuna irin rashin tausayi da rashin imani da ke tattare da ayyukan masu aikata irin waɗannan munanan laifuka.

Hakika wannan zalunci ne mai girma kuma abin Allah wadai. Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya tarwatsa aniyarsu, ya tona ashirin su, Ya hana su cimma mugun nufinsu, Ya kuɓutar da waɗannan bayin Allah cikin ƙoshin lafiya, Ya kuma sada su da iyalansu cikin aminci da farin ciki.

Allah Ya kawo ƙarshen garkuwa da mutane da duk wani nau'in zalunci na tà'àddàncì a ƙasarmu. Amin.

Address

No 23 Liverpool Road Apapa
Lagos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Comrd Ahmad TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Comrd Ahmad TV:

Share