Comrd Ahmad TV

Comrd Ahmad TV Graphic designer, content writer, Business advertiser, business planner, oil and gas marketer, long grain rice seller DM for a business deal 09031316584

Matar Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo Dake Kano Ta RasuAllah ya yi wa amaryar Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano,...
09/09/2026

Matar Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo Dake Kano Ta Rasu

Allah ya yi wa amaryar Shugaban Karamar Hukumar Kabo ta Jihar Kano, Hon. Lawan Najume, Hajiya Maimuna wadda aka fi sani da Hajjo, rasuwa.

Lawan Najume ne ya tabbatar da rasuwar matarsa a wani saƙon da ya wallafa a shafinsa. na Facebook

Najume ya bayyana cewa, marigayiyar ta rasu ne bayan ta yi fama da rashin lafiya.
Hajiya Maimuna ta rasu ne a ƙasar Masar ranar Talata 8 ga Satumba, 2026.

Tuni shugaban ƙaramar hukumar ya soma karɓar saƙonnin taʼaziyya kan rashinta

Daga Mukhtar Lawan Liver Gwarzo

Night Update 🌧️🌧️🌧️ 🌧️ Ga jerin garuruwan da zasu samu ruwan sama a wannan daren Insha-Allah 👇 👏 Kuyi mana like da share...
08/09/2026

Night Update 🌧️🌧️🌧️

🌧️ Ga jerin garuruwan da zasu samu ruwan sama a wannan daren Insha-Allah 👇

👏 Kuyi mana like da share domin sauran jama'a su amfana.

🌧️ Daga cikin su akwai 👇

Maiduguri
Gombi
Dikwa
Mubi
Damboa

Michika
Song
Hong
Yola
Fufore

Hadejia
Jahun
Gumel
Ringim
Babura

Kazaure
Dutse
Guri
Kano
Mai Gatari

Mayo Belwa
Kumo
Gombe
Dukku
Potiskum

Damaturu
Gulani
Fika
Gassol
Machina

Kaduna
Zaria
Soba
Lere
Makarfi

Kagarko
Abuja
Rano
Suleja
Funtua

Kontagora
Gusau
Maru
Bida
Rijau

Birnin Kebbi
Mariga
Sakaba
Argungu
Mashegu

Bukkuyum
Mafara
Kebbe
Gummi
Doguwa

Etc...

📡 Kuci gaba da bibiyar shafina domin samun sahihin hasashen yanayi akai akai ⛈️

Like
Follow & Share

Usama Hamisu Hasashe ✍️

🗓️ Tuesday 8th September 2026

Acikin Daren Nan yan takarar gwamnan a jam'iyyar ADC Sun ziyarci Atiku Abubakar a A gidansa Dake Abuja A cikin Harda Tso...
08/09/2026

Acikin Daren Nan yan takarar gwamnan a jam'iyyar ADC Sun ziyarci Atiku Abubakar a A gidansa Dake Abuja A cikin Harda Tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami da Maniru Muhammad Daniya

Dallatun Sokoto Ya Miƙa Gagarumin Tallafi Ga Kwamitin Zakka Da WaƙafiMaigirma MD Murtala Abdulkadir Dan Iya (Dallatun So...
08/09/2026

Dallatun Sokoto Ya Miƙa Gagarumin Tallafi Ga Kwamitin Zakka Da Waƙafi

Maigirma MD Murtala Abdulkadir Dan Iya (Dallatun Sokoto), ya yi abinda ya saba na bada tallafin da yake badawa ga kowace gunduma duk bayan watanni shida, inda ya bada buhun shinkafa dubu goma sha biyu da ɗari uku da hamsin, atamfa dubu goma sha biyu, kaftani da babbar riga ga kowane uban kasa guda 87, motoci guda biyar zuwa ga Zakkah da wakafi.

Haka zalika ya baiwa kowane Ubankasa naira dubu hamsin.

Daga Wazeerin Wamakko

Ƴan bambaɗanci da su ka kewaye Buhari ne su ka ci amanar sa - Tsohon shugaban DSSTsohon Darakta-Janar na Hukumar Tsaro t...
08/09/2026

Ƴan bambaɗanci da su ka kewaye Buhari ne su ka ci amanar sa - Tsohon shugaban DSS

Tsohon Darakta-Janar na Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), Lawal Daura, ya ce gwamnatin marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ta fuskanci matsaloli ne saboda wasu mutanen da ya amince da su sun kasa riƙe amanar ya basu.

Daura ya ce abin da ya faru a gwamnatin Buhari ya nuna haɗarin baiwa alaƙar mutum da amana fifiko wajen nada mutane muk**an gwamnati, ba tare da la’akari sosai da ƙwarewarsu ba.

Daily Trust ta rawaito cewa tsohon shugaban DSS din ya bayyana hakan ne a wata hira da shirin Politics Today na Channels Television da aka watsa a ranar Litinin.

A cewarsa, Buhari ya kewaye kansa da mutanen da ya amince da su, amma daga baya wasu daga cikinsu su ka ci amanar sa.

Daura ya bayyana cewa kasancewarsa kusa da Buhari ya samo asali ne daga nauyin aikinsa na shugaban hukumar leƙen asiri ta ƙasa, ba wai saboda yana cikin wani gungun masu iko a gwamnatin ba.

Ya kuma kare tsohon shugaban ƙasar daga masu cewa gwamnatin Buhari ita ce mafi muni a tarihin siyasar Najeriya, inda ya bukaci masu s**ar gwamnatin da su duba tarihin ƙasar daga shekarar 1995 zuwa lokacin da Buhari ya bar mulki a 2023 domin tantance waɗanne shekaru ne s**a fi muni.

Daura ya shawarci gwamnatocin da za su zo nan gaba da su raba aminci da alaƙar mutum da kuma ƙwarewar da ake buƙata wajen riƙe mukamin gwamnati.

Gwamnatin Katsina Ta Kai Samame Wajen Siyar Da Sinadarin KwamusoGwamnatin Jihar Katsina ta fara kai samame wuraren da ak...
08/09/2026

Gwamnatin Katsina Ta Kai Samame Wajen Siyar Da Sinadarin Kwamuso

Gwamnatin Jihar Katsina ta fara kai samame wuraren da ake zargin ana safarar da siyar da sinadarin Kwamuso, wanda ake amfani da shi wajen kula da yara marasa lafiya a jihar.

Samamen, wanda Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Katsina ta gudanar tare da haɗin gwiwar hukumomin lafiya na matakin farko da jami’an tsaro, ya gudana ranar Litinin, 7 ga Satumba 2026.

A yayin samamen, jami’an sun k**a mutane shida a wani asibitin Baƙin da ke Ƙaramar Hukumar Mashi, yayin da aka k**a wasu mutane biyu a cikin garin Katsina, bisa zargin hannu wajen safarar da siyar da sinadarin.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala samamen, shugaban kwamitin da Kwamishinan Lafiya na jihar ya kafa, Hon. Musa Adamu Funtua, ya ce safarar sinadarin Kwamuso babban laifi ne da ke jefa rayuwar yara marasa lafiya cikin haɗari.

“Wannan abu ba kishin ƙasa ba ne, ba tausayi ba ne, kuma ba tsoron Allah ba ne. Ana ba da Kwamuso ne domin yara marasa lafiya, don haka duk wanda ke yin wannan ta’asa yana cutar da al’umma,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar na kashe makudan kuɗaɗe wajen samar da ingantaccen kiwon lafiya, musamman kula da yara, don haka ba za ta bari wasu mutane su yi amfani da kayan aikin lafiya domin cin moriyar kansu ba.

“Duk wanda ke da hannu cikin irin waɗannan laifuka, idan ya shiga hannu, zai fuskanci hukuncin hukuma,” in ji shi.

Shi ma Sakataren kwamitin binciken, Dr. Umar Bello Bindawa, ya bayyana cewa samamen na daga cikin matakan farko da kwamitin zai ɗauka domin gano dillalan da ke safarar sinadarin zuwa wuraren da ake siyar da shi ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce mutanen da aka k**a za a miƙa su ga hukumomin da s**a dace domin gudanar da bincike da ɗaukar matakin da ya dace.

Dr. Bindawa ya yi kira ga masu safarar Kwamuso da su dakatar da harkar kafin su faɗa hannun jami’an tsaro, yana mai cewa duk wanda aka k**a zai fuskanci hukuma.

Samamen ya samu halartar ƙungiyoyi da hukumomin da ke da ruwa da tsaki a harkar lafiya, ciki har da masu kula da harkar abinci mai gina jiki (Nutrition) da sauran masu ruwa da tsaki.

Allah Dai Ya Ba Mu Mazajen Aure Kawai, Don Wallahi Harkar Fim Ɗin Hausa Ba Sana'a Ba Ce, Saboda Na Yi Mamakin Yadda Ƴan ...
08/09/2026

Allah Dai Ya Ba Mu Mazajen Aure Kawai, Don Wallahi Harkar Fim Ɗin Hausa Ba Sana'a Ba Ce, Saboda Na Yi Mamakin Yadda Ƴan Fim Ba Su Halarci Jana'izar Zee Diamond Ba, Inji Wannan Jaruma

Jarumar ta ƙara da cewa ƴan fim ɗin da s**a halarci jana'izar ba su wuce mutum biyar ba, k**ar Yusuf Lazio, Darakta Gidaje da Najib marubuci. Sai kuma a mata su uku ne.

Jarumar ta ce duk da cewa marigayiyar ta yi jama'a, amma idan ta ƴan fim ne da saidai ta ruɓe a gida, domin tun wajen ƙarfe 12 na rana s**a je gidan rasuwar, amma sai wajen ƙarfe uku aka yi jana'izarta.

Ta ce a yau ta ƙara tsanar masana'antar fim domin ana amfani da su ne a masana'antar a lokacin da suke da lafiya.

Matatar Man Dangote ta ƙaddamar da hannun jari na IPO na Naira tiriliyan 2.15 kan Naira 525 ga kowane hannun jariMatatar...
08/09/2026

Matatar Man Dangote ta ƙaddamar da hannun jari na IPO na Naira tiriliyan 2.15 kan Naira 525 ga kowane hannun jari

Matatar man Dangote ta ƙaddamar da wani shirin sayar da hannun jari karo na farko ga al'umma , wanda ta yi wa laƙabi da IPO na Naira tiriliyan 2.15, domin tara jari don faɗaɗa ayyukan.ta tare da bai wa al'umma damar mallakar hannun jari a kamfanin.

Babban Daraktan Kamfanin, Alhaji Aliko Dangote, ya ce hannun jarin zai bai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka damar sayen hannun jari a matatar mai ƙarfin tace ganga dubu 700,000 a kowace rana.

Shirin ya ƙunshi hannun jari guda biliyan 4.1, inda za a sayar da kowane hannun jari kan Naira 525, yayin da mafi ƙarancin adadin da mutum zai iya saya shi ne hannun jari 10, wanda darajarsa ta kai Naira 5,250.

“Wannan IPO ne na jama'a. Babu wani bambanci kan wanda zai iya mallakar hannun jarin,” in ji Dangote.

A cewarsa, matatar man, wacce ke yankin Lekki Free Zone na da ƙarfin tace ganga 700,000 a kowace rana.

Dangote ya ce wannan IPO, wanda shi ne karon farko da matatar ta fara sayar da hannun jari ga jama'a tun bayan ƙaddamar da ita a shekarar 2023, shi ne mafi girma a Afirka.

Ya bayyana cewa wannan mataki zai bai wa mutane da dama damar shiga cikin ci gaban kamfanin.

Ana sa ran shirin zai samar da ƙarin jari domin shirin faɗaɗa matatar, tare da ƙara yawan masu hannun jari a kamfanin.

2027: Obi da Makinde sun yi kira ga haɗin kan ’yan NajeriyaƊan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi ...
08/09/2026

2027: Obi da Makinde sun yi kira ga haɗin kan ’yan Najeriya

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya yi kira ga shugabannin siyasa da ’yan Najeriya da su haɗa kai domin ceto ƙasar daga matsalolin talauci, yunwa da rashin tsaro gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Obi ya yi wannan kiran ne a Abuja a yau ranar Litinin, yayin da ya halarci buɗe ofishin yaƙin neman zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasa na Allied Peoples Movement (APM), kuma Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde.

Tsohon Gwamnan Jihar Anambra ya ce Makinde ya cancanci tsayawa takarar shugaban ƙasa, yana mai cewa duk wanda ’yan Najeriya s**a zaɓa ta hanyar sahihin zaɓe mai inganci, ya k**ata kowa ya mara masa baya domin gina ƙasa mafi inganci.

Obi ya ce bai k**ata siyasa ta ci gaba da kasancewa hanyar faɗa da rarrabuwar kai ba, maimakon haka, ya k**ata a mayar da hankali wajen ciyar da ’yan ƙasa da kuma fitar da su daga talauci.

Obi ya kuma bayyana cewa manufarsu ita ce samar da Najeriya da kowane ɗan ƙasa zai samu damar samun ingantacciyar rayuwa, tare da tabbatar da cewa ɗan talaka ma zai iya zama wani babban mutum ba tare da sai ya san wani mai ƙarfi ba.

A halin yanzu, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, na daga cikin ’yan siyasar da s**a ayyana aniyarsu ta neman shugabancin Najeriya a zaɓen 2027.

Jaruman fim din Labarina da su ka rasu. 1Umar Maikudi Cashman ya rasu a ranar Laraba da dare na 21 ga watan Mayu na shek...
08/09/2026

Jaruman fim din Labarina da su ka rasu.

1
Umar Maikudi Cashman ya rasu a ranar Laraba da dare na 21 ga watan Mayu na shekarar 2025 a Zariya, kuma an yi jana'izar sa a Zariya a ranar Alhamis da safe.

2
Maijidda Muhammad Kontagora wato Fulani ta rasu a ranar Alhamis, 25 ga watan Disambar shekarar 2025 a wani Asibiti a Sokoto da yamma. Kuma an yi jana'izar ta a garin su na Kontagora bayan Sallahr Juma'a a kofar Sarkin Sudan na Kontagora.

3
Zainab Abdullahi (Diamond) wato Talatuwa Maman Bintalo a Labarina, ta rasu a ranar Litinin da asuba, 7 ga watan Satumbar shekarar 2026 a Zariya bayan fama da doguwar jinya, kuma an yi jana'izar ta a Zariyan a ranar da ta rasu ɗin.

Da fatan Allah Ya jikan su da rahamarSa, Ya sa aljanna ce makoma gare su gaba ɗaya.

Allah Yai musu rahma.

Ahmad Nagudu
Media Manager
Saira Movies

Address

No 23 Liverpool Road Apapa
Lagos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Comrd Ahmad TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Comrd Ahmad TV:

Shortcuts

Share