KTG Hausa News

KTG Hausa News Ingantattun Labarai wanda s**a inganta na gaskiya.

2027: Idan Tinubu ya bani takarar mataimakin shugaban ƙasa  da gudu zan karɓa - Barau Jibrin Mataimakin Shugaban Majalis...
26/06/2025

2027: Idan Tinubu ya bani takarar mataimakin shugaban ƙasa da gudu zan karɓa - Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya bayyana cewa ko da yake ba ya son ya shiga cikin muhawarar wanda zai iya zama abokin takarar Shugaba Bola Tinubu a 2027, zai karɓi kowane nau’in aiki da Shugaban ƙasa zai danka masa cikin farin ciki da biyayya.

Yayin wani taron manema labarai da aka shirya dangane da shirin jin ra’ayoyin jama’a a shiyyoyi daban-daban da Kwamitin Majalisar Dattawa kan Sauya Kundin Tsarin Mulki , Barau ya ce: “Duk abin da Shugaba ya bukace ni da in yi, zan yi shi dari bisa dari ”

Wannan bayani na zuwa ne bayan wata magana da ya yi a ranar Talata, inda ya shawarci wata ƙungiya da ke goyon bayan kudurin sa ya zama mataimakin shugaban kasa a 2027 da su maida hankali wajen goyon bayan shirye-shiryen gwamnati maimakon batun siyasa.

“Lokacin siyasa zai zo, amma yanzu lokacin shugabanci ne.”

Barau ya bayyana Shugaba Tinubu a matsayin uban gidansa na siyasa wanda yake da cikakkiyar biyayya a gare shi.

Da A Ce Tinubu Ba Shugaban Kasa Ba Ne, Da Yanzu Ana Kan T**i Tare Da Shi Ana Zanga-Źànga Saboda Tsadar Rayuwa, Inji Sana...
25/06/2025

Da A Ce Tinubu Ba Shugaban Kasa Ba Ne, Da Yanzu Ana Kan T**i Tare Da Shi Ana Zanga-Źànga Saboda Tsadar Rayuwa, Inji Sanata Ndume

Me za ku ce?

Yanzu-Yanzu Gwamnatin jahar Adamawa ta cire Atiku Abubakar a matsayin Wazirin Adamawa
24/06/2025

Yanzu-Yanzu Gwamnatin jahar Adamawa ta cire Atiku Abubakar a matsayin Wazirin Adamawa

SDP ta dakatar da Shugaban Jam’iyya Shehu Gabam, da Shugaban Matasa na ƙasaKwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na Jam’iyyar...
24/06/2025

SDP ta dakatar da Shugaban Jam’iyya Shehu Gabam, da Shugaban Matasa na ƙasa

Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) ya amince da dakatar da Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Shehu Gabam, tare da wasu membobin kwamitin – Nnadi Clarkson, mai kula da binciken kuɗi, da Chukwuma Uchechukwu, shugaban matasa na ƙasa – bisa zargin aikata babban laifin almundahana da karkatar da kuɗin jam’iyya.

Sanarwar dakatarwar na kunshe ne a cikin wata takarda da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa, Araba Rufus Aiyenigba, ya fitar, kuma aka isar da ita ga Vanguard.

Sanarwar ta ce:

> “Wannan matakin ya biyo bayan wasu matsayai da mambobin kwamitin gudanarwa s**a cimma, inda aka gabatar da tabbatattun hujjoji da ke haɗa waɗannan jami’ai da wasu manyan harkokin kuɗi da aka gudanar ba bisa ka’ida ba, amfani da kuɗin jam’iyya don amfanin kansu, da kuma fitar da kuɗaɗe daga asusun jam’iyya ba tare da izini daga kwamitin ba.”

An gano cewa wannan matsala ta fara bayyana ne lokacin da aka gano cewa Shugaban Jam’iyya na Ƙasa, Shehu Gabam, ya tura bayanan kuɗi na bogi zuwa INEC ba tare da amincewar kwamitin ba, a matsayin abin da ake buƙata daga kowace jam’iyya.

> “Wani taƙaitaccen bayani na asusun kuɗin da ake zargi da damfara ma an buga shi a jaridu. Bayan kwamitin ya samu labarin haka, sai ya yanke shawarar mika rahoton wannan damfara ga hukumomin tsaro.”

Kwamitin ya bayyana cewa wannan mataki na dakatar da Shehu Gabam da sauran jami’an da ake zargi zai nuna wa jama’a cewa jam’iyyar SDP wadda ake darajata a matsayin jam’iyyar da ke da tsabta da kishin ƙasa, ba za ta lamunci cin hanci da amfani da ofishi wajen cutar da jam’iyya ba.

> “Wannan dakatarwa za ta ba da dama waajen gudanar da cikakken bincike. Dole ne mu kare amintattun halayenmu a matsayin jam’iyya a kowane lokaci.”

> “An kafa kwamitin bincike na wucin gadi domin yin nazari da tantance dukkanin bayanan kuɗi, tare da bayar da shawarar matakai na ladabtarwa ko shari’a idan ya zama dole.”

Sai Tinubu ya yi sa'a ma zai zo na uku a zaɓen 2027— In ji El-RufaiTsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya...
24/06/2025

Sai Tinubu ya yi sa'a ma zai zo na uku a zaɓen 2027— In ji El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ba ya damu da yawan sauya sheƙa da ake yi zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

A wata hira da aka yi da shi kai tsaye a shirin Arise TV a daren Litinin, El-Rufai ya ce shugaban ƙasa mai ci yana ɗaukar matsayin cewa tuni an gama da dawowar sa karo na biyu, ganin yadda wasu gwamnoni daga jam’iyyun adawa ke sauya sheƙa zuwa APC.

Sai dai ya bayyana cewa: "Tinubu ba zai ci zaɓe ba. A gaskiya, zai yi sa’a idan ma ya zo na uku."

Tsohon gwamnan ya zargi gwamnatin Tinubu da halin ko in kula dangane da matsanancin halin tsaro da ƙasar ke ciki, yana mai bayyana cewa an cire naira biliyan 100 daga Asusun Tarayya cikin watanni 15 da s**a gabata ba tare da amincewar jihohi ko majalisar dokoki ba.

Ya ce: "Tun cikin watanni 15 da s**a wuce, ana cire biliyan 100 daga Asusun Tarayya ana tura wa hukumomin tsaro. Amma me ya sauya?

A shekarar 2024, an sace sama da mutane miliyan 2.2, an kashe mutum 615,000. Nigeria na cikin yaƙi ne? Wannan adadi ya fi na shekaru 8 na Buhari muni. Kuma duk wannan ƙididdiga daga Hukumar Kididdiga ta Ƙasa ce, ba ta wani waje ba.

Wannan kuɗi ne da aka ɗauka daga Asusun Tarayya ba tare da amincewar Majalisar Tarayya ba. Wannan saba doka ne, kuma abin a tsige shugaban ƙasa ne, amma har yanzu ana cigaba da hakan.

Ina wannan naira tiriliyan 1.5 ta tafi? Me ya sa matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara? Me ya sa gwamnati ke buƙatar al’umma su kare kansu?”

DA DUMI-DUMI: Amvrka tace ba zata mayar wa 1ran martani kan h@rin da ta kaiwa sansanin sojojin ta a Qatar ba - inji Dona...
23/06/2025

DA DUMI-DUMI: Amvrka tace ba zata mayar wa 1ran martani kan h@rin da ta kaiwa sansanin sojojin ta a Qatar ba - inji Donald Trump.

Me za ku ce?

~ A YAU

Shugaban Al'ummar  Palasɗinu, Mahmoud Abbas, ya yi Allah-wadai da harin da Iran ta kai sansanin sojin Amurka na Al-Udeid...
23/06/2025

Shugaban Al'ummar Palasɗinu, Mahmoud Abbas, ya yi Allah-wadai da harin da Iran ta kai sansanin sojin Amurka na Al-Udeid da ke ƙasar Qatar.

📸— Abdul Journalist 1

Gwamnatin Tarayya Ta Bada Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Ba Matafiya Gwamna...
23/06/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Bada Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Ba Matafiya

Gwamnatin Tarayya ta bada tabbacin cewa Babban Birnin Tarayya Abuja yana da tsaro ga mazauna cikin sa da baƙi da kuma jakadun ƙasashen waje.

Wannan tabbacin na zuwa ne bayan da Ofishin Jakadancin Amurka da ke Nijeriya ya fitar da wata sabuwar sanarwa kan tsaro, inda ya hana tafiye-tafiyen ma’aikatan sa da iyalan su zuwa wuraren soja ko wasu gine-ginen gwamnati a Abuja, in ba don ayyuka na hukuma ba.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Gwamnatin Tarayya ta amince da haƙƙin kowane ofishin jakadanci na fitar da irin wannan gargaɗi ga 'yan ƙasar sa, sai dai ya jaddada cewa babu wani haɗari na kai-tsaye a Abuja.

Ya ce: “Duk da cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da haƙƙin ofisoshin jakadanci na ƙasashen waje, ciki har da na Amurka, na fitar da gargaɗin tafiye-tafiye ga 'yan ƙasar su, yana da muhimmanci a faɗa a fili cewa Abuja tana da tsaro ga 'yan ƙasa da mazauna da kuma baƙi baki ɗaya.”

Ya bayyana cewa hukumomin tsaro a Nijeriya suna aiki tuƙuru dare da rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a, ya ƙara da cewa tsarin tsaro a Abuja yana aiki yadda ya kamata tare da nasarori masu yawa wajen gano duk wata barazana da kuma daƙile ta kafin ta faru.

Ministan ya ƙara da cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ba ya nuni da wata barazana kai-tsaye ga Abuja, illa ya dogara ne da al’amuran tsaro na duniya gaba ɗaya.

Ya ce: “Mun fahimci cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ya ta’allaƙa ne da wasu abubuwan da ke faruwa a duniya gaba ɗaya, ba wai yana nuna wata barazana kai-tsaye ko ta gaggawa a cikin Babban Birnin Tarayya ba.

"Sai dai muna sake jaddadawa ga dukkan ofisoshin jakadanci, da masu zuba jari da abokan cigaba, da jama’a gaba ɗaya cewa babu wani dalilin fargaba."

Ya kuma bayyana ƙudirin gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a birnin tarayya, yana mai cewa: “Gwamnat

YANZU-YANZU: Shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong-un, yayi tir da matakin Amurka akan Iran, tare da tura sakon gargadi ga ...
23/06/2025

YANZU-YANZU: Shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong-un, yayi tir da matakin Amurka akan Iran, tare da tura sakon gargadi ga Amurka akan dakatar da shiga yakin kai tsaye.

📸 — Abdul Journalist 1

YANZU-YANZU: 'Yar majalisar wakilai, AOC (Alexandria Ocasio-Cortez), ta nemi a tslge Donald Trump saboda yanke shawarar ...
22/06/2025

YANZU-YANZU: 'Yar majalisar wakilai, AOC (Alexandria Ocasio-Cortez), ta nemi a tslge Donald Trump saboda yanke shawarar kai h@ri kan 1ran ba tare da amincewar mafi rinjayen majalisa ba.

~ ATP HAUSA

YANZU-YANZU: Duniya ta doshi yáƙln dúniya na uku, Inji Putin. Shugaban Ƙasar Rasha Vladimir Putin ya sanar a yau Lahadi ...
22/06/2025

YANZU-YANZU: Duniya ta doshi yáƙln dúniya na uku, Inji Putin.

Shugaban Ƙasar Rasha Vladimir Putin ya sanar a yau Lahadi cewa duniya na dosan yáƙln dúniya na uku, inda ya bayyana cewa wannan magana da ya ke da gaske ya ke yi ta.

Putin wanda ya sanar da hakan a shafinsa na Twitter da safiyar nan, ya ce ya gargaɗi da kada ta ɗauki matakin soji kan Íran amma ta ƙi jin maganarsa. Ya na mai cewa, “bari mu zuba ido mu gani, domin Íran ba za ta ƙyale dakarun Amurka da ke yankin Gabas ta Tsakiya ba”.

Vladimir Putin ya gargaɗi duniya a na gab da shiga yàƙin dúniya na uku, domin harin Amurka kan Íran shi ne mafari.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Arc. Namadi Sambo, ya bayyana cewar idan akwai wani shugaba da ke da ƙwarewa da ƙarfin ...
19/06/2025

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Arc. Namadi Sambo, ya bayyana cewar idan akwai wani shugaba da ke da ƙwarewa da ƙarfin gwiwar da zai iya warware matsalar wutar lantarki da ke addabar Najeriya tsawon shekaru, to ba wanda ya fi dacewa da wannan aiki kamar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a wajen bude katafaren Asibiti da Gwamann Kaduna Ya Gina ya sanya sunan Shugaba Tunubu. ya nuna goyon bayansa kan kokarin da Shugaba Tinubu ke yi wajen gyara muhimman sassa na tattalin arzikin ƙasa, musamman fannin makamashi.

A cewar Sambo:

“Shugaba Tinubu ya nuna kwazo da jajircewa tun kafin ya hau mulki. Yana da hangen nesa da kwarewa wajen jagorantar sauyi, musamman a bangaren wutar lantarki wanda ya daɗe yana zama kalubale ga Najeriya. Ina da yakinin cewa idan akwai wanda zai iya magance wannan matsala, to ba shi ba ne, sai Tinubu.”

KBC Hausa

Address

Kano, Road Azare, Bauchi, State
Liman Katagum
08160438660

Telephone

+2347067658337

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KTG Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KTG Hausa News:

Share