Hajara Digital D

Hajara Digital D I'm here to help you build a strong online presence and master your finances.

28/02/2026

Saudiya tayi Allah wadai gameda farmak@r sansanin sojin Amurka da ir@n tayi. Shin tsorone ko rashin kishin Kai.

Yan content monetization su matso kusa. Yanzu lokaci yayi da yak**ata ace anfara ribayar kudin content monetization.Duk ...
28/02/2026

Yan content monetization su matso kusa. Yanzu lokaci yayi da yak**ata ace anfara ribayar kudin content monetization.

Duk Wanda/wacce takeda tambaya to Ina saurare kuma zan amsa daidai sanina.

Nifa siyasar bana an rabamin hankali. Inason Atiku kuma inason Kwankwaso. Har yanzu ban tsayar da gwanina ba. Ku waye gw...
27/02/2026

Nifa siyasar bana an rabamin hankali. Inason Atiku kuma inason Kwankwaso. Har yanzu ban tsayar da gwanina ba. Ku waye gwaninku a siyayyar Bana?

Tunda naga inada dubu 3 a account nawa nasan da izinin Allah hajjin bana Dani za'ayi. Duk Wanda bai tayani murna ba baza...
27/02/2026

Tunda naga inada dubu 3 a account nawa nasan da izinin Allah hajjin bana Dani za'ayi. Duk Wanda bai tayani murna ba bazai samu tsaraba.

Barkanku da safiyar yau, ina yiwa kowa fatan Alkhairi.
26/02/2026

Barkanku da safiyar yau, ina yiwa kowa fatan Alkhairi.

25/02/2026

Gaskiya baku kyauta ba ace nayi kusan shekara banhau online ba amma ba Mai iya cewa Ina wance? Ba amana.

20/08/2024

♦️AL'AJABI ♦️
(DAGANI BABU TAMBAYA)

BY
HAJARA YUSUF
(Real Hajara Yusuf)

Episode 15

Bayan jamaa sun taru ana jimamin me yasa jamaar cikin adaidaita sahun s**a ruga aguje s**a fita, acikin jamaar kuwa harda abban fati.

Bayan kowa ya leka cikin napep din kuma ba wanda yaga wani abun tsoro, abban fatine yaje gaban kaka yace haba inna babu wani abun tsoro acikin adaidaita sahun amma duk kunbi kun daga hankalinku, kaka tace Ayuba lafiyan idonka lau kuwa? Abban Fati yace Wallahi inna bakomai sai Akuya da agwagwa. Kaka ta tashi aguje taruga cikin gida tana ihu Salati, yayinda itama zee tayi hanyar gidansu da gudu, shi kuma Hamisu yana gefe jikinsa yana rawa yanata maimaita inda Rabbana no Wahala, yayinda shi Ya'u ya samu waje ya zauna ya rattaba tagumi.

Abun dai yabawa kowa mamaki, abban fati yaje wajen ya'u yace wai meke faruwa dakune kuyi mana bayani mana hankalin kowa ya kwanta. Ya'u yace abundai sai INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUUN, Wancan agwagwan da kuka gani ya bace mana acan unguwarmu mun nemeshi sama da kasa bamu samuba, sannan akuyar ta mutu tun acan muka dauka muka bawa matasa suje su jefar. To yanzu gasu nan acikin adaidaita bayan bamu taho dasu ba.

Abban fati yace yanzu akuyarda ta mutu itace zata dawo tashiga adaidaita? to shikenan yaro yanzu abunda zaayi shine bari aciresu daga adaidaitan saika samu kaje kahuta, Ya'u yace bafa rudu muka shiga ba, Wallahi abunda nafada gaskiya ne. Mallam Ayuba yace kaidai kasamu kaje kahuta yaudin gobe sai kadawo kafamin asalin abunda yafaru.

Yana fadin haka yabar wajen yanufi inda adaidaitan yake, yasa hannu yafito da akuyar da kuma agwagwar yayi cikin gida dasu.

GIDAN FATI
Fati da jibrin suna zaune a parlour duk sunyi shuru k**ar kurame, fatice tayi gyaran murya sannan tace. Da karfe nawa zamu tafine naga har yanzu kaki ka motsa. Jibrin yace bazamu jeba su zasu zo, fati tace amma dadai munje din inyaso wani lokacin sai suzo. Jabir yace nidai nagama magana. Fati tace to shikenan amma ai daka fadamin nayi musu girki kafin su iso, amma dukda haka bai baci ba, bari nadafa musu koda taliya, daga haka tashiga kitchen tayi jajjagen kayan miyanta ta soya tazuba ruwa tafito tasameshi a inda tabarshi, tana zama tace su nawane zasu zo? yace su shida, fati tace to fadamin sunayensu sai yace akwai Mama sai wacce take biye mini Hasiya, sai sautanda sai musa sai yan biyunmu kuma yan auta Hassan da Hussaini. Fati tace amma kana ganin karfe nawa zasu iya isowa, jibrin yace karfe 2:00pm daidai.

Bayan fati tagama dafa abunda zata dafa tasa a warmer ta jera komai a dining table. Karfe daya da rabi nayi Sai taje tayi wanka ta dauro Alwala tazo tafara sallah, tana sallamewa kawai sai taji guguwa yana tashi, iska tako ina k**ar zai dauke gidan nasu, ga kuwwa da kururuwa da s**a mamaye ko ina. Fati ta tashi kenan zataje falo tayiwa jibrin magana kawai sai taji guguwa ya dauketa yayi sama da ita bata ankare ba taganta awani gagarumin jeji wanda baida gabas bare yamma, ga wasu mutane masu jajayen hakora masu k**a da ifiritai sun zagayeta, sannan dukkaninsu akwai kaho a kawunansu.

Fati tayi ihu ta tashi zata gudu daya daga cikinsu ya daka mata tsawa yayinda bakinsa yake amayarda wuta. Nan take fati tafadi kasa sumammiya.

19/08/2024

♦️AL'AJABI ♦️
(DAGANI BABU TAMBAYA)
HAJARA YUSUF
BY
REAL HAJARA YUSUF

ᗴᑭIՏOᗪᗴ 14

Ya'u yana lekawa waje yaga akuyan yana shure-shuren mutuwa, ga kuma kumfa da yake fita a bakin akuyan, Hashimu yayi saurin zuwa wajen ya'u yana cewa mai gida a taimaka mana da wuka akuyarmu zata mutu.

Ya'u ya juya da sauri zaije ya dauko wukan kawai sai yaji mallam Zakiru yana cewa Akuyar nan koda an yanka bazata ciwu ba dan haka abarta ta karasa. Da mamaki kaka tace haba mallam ya zaayi mubar akuya tamutu bayan zamu iya yankawa? Zainab tayi saurin rike hannun kaka tareda fadin dan Allah kaka duk abunda mallam yafada kar muyi jayayya.

Ya'u yace hakan yak**ata ayi dan samun mafita. Yanzu dai ku shigo na kaiku gida daga baya zaa san yadda zaayi ashawo kan lamarin.

Kaka da zainab s**a shiga adaidaita sahun amma Hashimu bai shiga ba ya tsaya waige-waige, kaka ta leka waje tace kai bazaka shigo bane koyaya.

Hashimu yace agwagwar nake nema ban ganiba, k**ar wasa haka s**a nemi agwagwar nan s**a rasa, haka s**a hakura s**a shiga adaidaitan Ya'u yaja s**a nufi gida.

Sunyi kusan minti biyar suna tafiya ba wanda yayiwa wani magana sabida kowa da abunda yake sakawa acikin ranshi.

Ya'u ne ya katse shirun da cewa "Ai hajiya kaka ina mai tabbatar muku da cewa kada kudamu Wannan Matsalar takusa zuwa karshe da izinin Allah"

Zainab tayi ajiyar zuciya sannan tace to gaskiya babu abunda bashida karshe, Matsalar bamusan ya karshen zai kasance ba, ta karashe maganar tana sharan kwalla.

Kaka tace kwantar da hankalinki yarinya babu abunda zai faru. Ninan da k**e ganina nafi karfin aljanu suyimin wargi. Dan bakusan yadda nake abaya bane shiyasa kuke shakku akan abunda zan iya. Ai ina fada muku ruwane ya daki babban zakara, badan hakaba da tuni an rufe babin Wannan Aljanin.

Ahaka kaka tayita jansu da hira har s**a manta da dumbin damuwa da suke dashi, sa'annan Ya'u yace Hajiya kaka nayiwa mallam magana yace bakomai zaiyi iya kokarinsa wajen ganin ya taimaka muku.

Kaka tace MadAllah gaskiya mungode da wannan kokari da kake mana. Ya'u yace bakomai Hajiya kaka ai yiwa kaine, dan yanzu anzama daya.

Bayan sun isa kofar gida Ya'u yayi packing amma basu kaiga fita ba sai wayan Zainab yayi ringing, tana dubawa taga private number, taja tsaki zatayi rejecting kawai sai taga yayi receiving da kanshi sannan ya shiga hands free ba tareda ta taba ba.

Abu nafarko da s**a fara ji shine dariya mai k**a da gurnani, sannan s**aji wani shakakken murya mai firgitarwa yana cewa. Bamu fara dan mudaina ba, duk wanda ya shiga hanyarmu saimun kawar dashi koda kuwa wanene, wannan Gargadi ne. Ga sakonku na ajiye muku abayanku.

Suna leka boot din dukkaninsu s**a fita aguje kowa yayi nasa hanyar. Yayinda jamaa s**a taru dan ganin meke faruwa kuma me yasa s**a gigice gaba dayansu.

18/08/2024

♦️AL'AJABI♦️
(DAGANI BABU TAMBAYA)
BY
REAL HAJARA YUSUF

Episode 13

Da yake zainab tasan gidan basu wani sha wahala ba s**a isa, Da yake sammako s**ayi sunje babu kowa hakan ya basu damar Shiga. Gaban zainab ne yafadi yayinda tayi ido hudu da Mallam Zakiru. Hakan yasa takoma bayan kaka ta rakube, Mallam Zakiru ya kalleta yace Kizo nan kizauna yayi mata nuni da wata darduma dake gabansa yana fuskantarsa.
..... Jiki na rawa zainab ta tashi ta zauna a inda aka umurceta, gabanta sai faduwa yake. Mallam Zakiru yace Fadamin meke tafe daku...... Dama... Da... Zainab tak**a in ina, kaka tace to ai gani ni sai a tambayeni tunda ita takasa Magana.

Mallam Zakiru yace Nasan tabbas dole saikun dawo amma dai ina Sauraron ku ya maida hankalinsa kan kaka da ita dinma shi take kallo. Bayan kaka tayi gyaran murya sannan tafara magana ba tareda da huta ba saida ta zaiyano masa komai harda Akuya da agwagwa da s**a kawo sannan ta zaiyano masa irin Azabar da takeso ayiwa Aljaninda yake tsorata fati. Mallam yayi Shiru Sannan Yace....

Ni Mallam Zakiru ba zan iya yi muku aikin nan ba sabida yanzu wannan aikin yafi karfina. Lokacin da naso taimakonku baku bani dama dan haka yanzu saidai kuyi hakuri ni Bazan iyaba saidai ku nema awani wajen.

Kaka tace haba Mallam da girmanka yaushe zaka tsaya gaba da kananan yara dan kawai sunyi maka rashin kunya a baya haba kar ka manta d'a Nakowa ne, Mallam Zakiru yace hakane kuma ni tun tuni na yafe musu, k**a tace yauwa to godiya muke ke jeki kice hashimu ya shigo da Akuya da agwagwan. Mallam yace aikinne bazan iyaba kuje kawai. Kaka zatayi magana mallam yace wani ya shigo domin wasu sunzo a bayansu. Hakan yasa kaka da zainab tashi su fita badan sun so ba.
... Bayan sun fitane s**a tsaya a kofar gidan suna jira ko wani zaizo a adaidaita saisu samu su shiga, ana haka saiga a daidaita sahu yazo juyawar da zainab zatayi kawai sai taga Ya'u nan take taji wani farin ciki ya lullubeta. Yana yin parking zainab tace kaka wannan Shine Ya'u mai Adaidaita. Ya'u shi kuwa bai ganeta ba sabida tasa face mask. Yazo zai wuce kenan sai tayi saurin cire face mask din sannan tace sannu! Yana ganinta yaji farin ciki ya ziyarce shi bai San sanda ya saki murmushi ba Haka itama murmushin take har ya iso gabanta s**a gaisa sannan tace zaka dade ne idan ka shiga Ya'u yace da wani abune, zainab tace munaso ka kaimu gidane, Ya'u yace ay gaskiya zan dade saidai yanzu bari zan kaiku saina dawo daga baya nayi uzurina, zainab tace aa ai naga ba layi zaka iya shiga zamu jiraka idan kagama saika fito mutafi. Ya'u yayi murmushi sannan yace ba wajen Mallam nazo ba gida nadawo. Da mamaki zainab tace kana nufin kai dan mallam ne, Ya'u yace kwarai kuwa. Zainab tace sai yanzu kuwa na lura kuna k**a kuwa ba banbanci. Ya'u yace saidai niba tsoho bane, gaba dayansu s**ayi dariya. Kakace ta kwalawa zainab kira sai ananne zainab ta tuna ta zake dayawa da har ta manta dasu kaka, Ya'u ne ya tsuguna har kasa ya gaida kaka sannan yace kuzo Muje sunje sun shiga kenan sai Ya'u yaga hashimu rike da agwagwa yana Jan Akuya zai shiga. Ya'u yace baku samu ganinsa bane? Kaka tace inafa korarmu yayi, da mamaki Ya'u yace kora? Kuma Mallam din? Zainab tace ay Wallahi anan tadan bashi bayani amma taboye sauran. Yau yace kuyi hakuri yanzu zanje na rokar muku Insha Allahu zaiyi muku aikin.
... Bayan mutum na ciki yafita Ya'u ya shiga yayiwa Mallam bayani harda yadda gidan fati ya bace masa. Da farko mallam yaki amincewa amma daga baya ganin yadda Ya'u ya nace hakan ya sashi amincewa. Amma da sharadin zaiyi musu aikine kawai ba tareda ya fada musu da baki ga inda Matsalar take ba. Ya'u yace ya amince sannan ya roki Alfarma a fada masa menene Matsalar sannan yayi Alkawari bazai fada ba. Mallam bai boyewa Ya'u komai ba gameda abunda ke faruwa da fati. Ya'u ya jinjina Al'amarin sannan yayi godiya ya fita.

Su zainab suna zaman jiransa a waje shiko ya tsaya a zaure yanata sake-sake a ransa.
... Anya zai iya rike wannan Alkawari kuwa ba tareda ya fadawa zainab ba?
.... Shida yake son taimakonsu ta yaya zaayi kuma yabarsu suyita lalube acikin duhu?
... Idan ya fada yaci Amanar Mahaifinsa idan kuma ya bari fati da zainab zasu sha wahala.

Murya da hayaniyar jamaa ne yadawo dashi haiyacinsa, Yayi waje da gudu dan ganin meke faruwa.

♦️AL'AJABI ♦️(DAGANI BABU TAMBAYA) HAJARA YUSUF    BYREAL HAJARA YUSUF            ᗴᑭIՏOᗪᗴ 12𝐈𝐍𝐀 𝐖𝐀𝐃𝐀𝐍𝐃𝐀 𝐒𝐔𝐊𝐄 𝐒𝐎𝐍 𝐅𝐀𝐑𝐀 𝐒𝐀...
18/08/2024

♦️AL'AJABI ♦️
(DAGANI BABU TAMBAYA)
HAJARA YUSUF
BY
REAL HAJARA YUSUF

ᗴᑭIՏOᗪᗴ 12

𝐈𝐍𝐀 𝐖𝐀𝐃𝐀𝐍𝐃𝐀 𝐒𝐔𝐊𝐄 𝐒𝐎𝐍 𝐅𝐀𝐑𝐀 𝐒𝐀𝐍𝐀𝐀𝐑 𝐒𝐀𝐘𝐀𝐑 𝐃𝐀𝐓𝐀. 𝐆𝐀 𝐃𝐀𝐌𝐀 𝐓𝐀 𝐒𝐀𝐌𝐔.
Nakowadata.com 𝐒𝐔𝐍 𝐊𝐀𝐑𝐘𝐀 𝐅𝐀𝐑𝐀𝐒𝐇𝐈 𝐊𝐔𝐌𝐀 𝐀 𝐒𝐇𝐈𝐑𝐘𝐄 𝐒𝐔𝐊𝐄 𝐃𝐎𝐌𝐈𝐍 𝐊𝐎𝐘𝐀 𝐌𝐔𝐊𝐔 𝐘𝐀𝐃𝐃𝐀 𝐙𝐀𝐊𝐔 𝐒𝐀𝐌𝐔 𝐊𝐔 𝐀𝐊𝐀𝐋𝐋𝐀 3000 𝐊𝐔𝐋𝐋𝐔𝐌 𝐓𝐀 𝐇𝐀𝐍𝐘𝐀𝐑 𝐒𝐀𝐘𝐀𝐑𝐃𝐀 𝐃𝐀𝐓𝐀, 𝐊𝐀𝐓𝐈𝐍 𝐊𝐈𝐑𝐀, 𝐑𝐄𝐒𝐔𝐋𝐓 𝐂𝐇𝐄𝐂𝐊𝐄𝐑 (𝐖𝐀𝐄𝐂 𝐀𝐍𝐃 𝐍𝐄𝐊𝐎), 𝐍𝐄𝐏𝐀 𝐁𝐈𝐋𝐋 𝐃.𝐒

𝐑𝐄𝐆𝐈𝐒𝐓𝐄𝐑 𝐊𝐘𝐀𝐔𝐓𝐀𝐍𝐄
𝐀𝐘𝐈 𝐌𝐀𝐙𝐀 𝐀 𝐓𝐔𝐍𝐓𝐔𝐁𝐄𝐌𝐔 𝐀 𝐖𝐀𝐍𝐍𝐀𝐍 𝐋𝐀𝐘𝐈 𝐊𝐀𝐌𝐀𝐑 𝐇𝐀𝐊𝐀
08136230000

Kaka tayi saurin mikewa tadau hijabi tace tazo Muje gidan malamin ni zan bashi akuya da bakar agwagwan ya kashe min wannan tsinannen Aljani da yake bibiyar rayuwar fati kuma dukda tayi aurenma bai barta ba. To wllh ba zanyi kaffara ba dole sai ankona shi da Jinin agwagwa... Dariya ne ya kufcewa zainab batare da tayi niyyar yin dariyar ba, kaka ta galla mata harara sannan tace ke kuma dariyar me k**e? Zainab wayance tace dariyar farin ciki nake kaka yadda zakisa a wulakanta wannan azzalumin da yake so ya cutar da fati, Gaskiya kaka ke jaruma ce.

Kaka ta saki murmushi sannan tace ai badan yanzu inada tausayi ba da kuwa da kaina zan kona wannan Aljanin amma banaso na dawo da jarumtata irinna bayane shiyasa zan mika shi ga malamai. Yanzu dai tashi mutafi zainabu dan da zafi - zafi ake dukan karfe.

Sai a sannan mama tayi mgn tace Amma ni aganina da andai tsaya shi Mallam din yadawo a fada masa watakila da abunda zai iya. Kaka tayi shiru sannan tace aa Hamsatu nidai ba zanyi kunnen uwar shegu ba gameda Al'amuran fati.

Mama tace wannan gaskiya ne saidai koda da wani abunda zaa bukata kinga zai iya taimakawa. Wayar zainab ce tayi kara tana dubawa taga Ya'u dan Adaidaita sahune yake kira. Tayi saurin cewa yauwa kaka kinga wannan mai kiran shine dan Adaidaita daya kai fati amma ni ya gagara kaini.

Kaka tace to kice masa jibi yazo zai kaimu gidan fatin Da izinin Allah Bazai gaji a banza ba kuma zamu bashi duk kudinda ya bukata tunda dai yanzu ana tsadar man fetur. Kafin zainab tadau kiran har kiran ya katse. Dan haka ta ajiye wayar a gefe ta cigaba da cewa Wllh shi kanshi Ya'u abun ya kulle masa kai. Amma tunda zaa dau mataki ai shikenan komai zaizo da sauki.

Kaka tace mataki kam k**ar an daukeshi angama dan ba zance a yiwa wannan Aljani sassauci ba. Yanzu dai zainabu kije gida ki nemi izinin iyayenki kice zakiyi mini rakiya gobe da safe. Zaki kaini gidan malamin naku, yanzu zan k**a akuyata daya sannan zan aika hashimu sayen agwawan kinga kenan gobe sai tafiya.

Zainab tace to shikenan kaka Allah ya kaimu goben, saida safe mama' dukkansu s**a amsa da Allah ya kaimu. Zainab tasa kai tafita.

Bayan Mallam ya dawo saida mama tabari yayi wanka yaci abinci, sannan tayi masa bayanin dukkanin abunda ke faruwa Harda shirin kaka na komawa gidan Mallam Zakirun.

Mallam ya jinjina Al'amarin amma yayi karfin halin cewa ba komai ai ba abunda ya gagari Allah, zamu cigaba da Addua har Allah ya yaye mata. Mama tace hakane amma yanada kyau ayi Addu'ar sannan a hada da magani. Mallam yace to Allah yasa a dace,

Mama tace Ameen Ya Allah.

Zainab kuwa da taje gida zama tayi a gaban waya tana jiran Ya'u ya sake kira amma taji shuru bai kiraba. Gashi bata San dalili ba Haka kawai take jin sonyin magana dashi.

Saida dare yayi Ya'u bai kiraba sannan ta cire rai da ganin kiran shi.

Shima ta bangaren Ya'u duk abun ya dameshi ganin bata dau kiransa ba kuma bata bishi da kira ba a haka ya kwana da tunanin dalilin rashin daukar wayarsa ko binsa da kira.

A can bangaren fati kuwa tanata shiri ita a dole zasuje ganin iyayen Jibrin. Amma abun mamakin shine wani mafarki da tayi mai k**a da gaske amma tayi hakuri ta barwa zuciyarta komai.

Gari na wayewa zainab tayi shiri tun da sanyin safiya, yayinda itama kaka ta shirya dawuri tayiwa mama da mallam sallama sannan takira hashimu tace yazo suje tare.

Bayan ta fitane ta shiga gidansu zainab. Ummar zainab na ganinta tayi mata sannu da Zuwa tareda fadin cewa haba Inna ai ba saikin zoba, zainab ai jikarki ce.

Kaka tace hakane amma ai yak**ata nazo din. Bayan sun gaggaisa zainab tafito s**a nufi bakin hanya duk su ukun s**a hau a daidaita sahu sai gidan mallam Zakiru.

Buy Cheap Internet Data Plan and Airtime Recharge for Airtel, 9mobile, GLO, MTN, Pay DSTV, GOTV, PHCN.

♦️AL'AJABI♦️(DAGANI BABU TAMBAYA)    BYHajara Yusuf _REAL HAJARA YUSUF_            ᗴᑭIՏOᗪᗴ 11𝐈𝐍𝐀 𝐖𝐀𝐃𝐀𝐍𝐃𝐀 𝐒𝐔𝐊𝐄 𝐒𝐎𝐍 𝐅𝐀𝐑𝐀 𝐒...
16/08/2024

♦️AL'AJABI♦️
(DAGANI BABU TAMBAYA)
BY
Hajara Yusuf
_REAL HAJARA YUSUF_

ᗴᑭIՏOᗪᗴ 11

𝐈𝐍𝐀 𝐖𝐀𝐃𝐀𝐍𝐃𝐀 𝐒𝐔𝐊𝐄 𝐒𝐎𝐍 𝐅𝐀𝐑𝐀 𝐒𝐀𝐍𝐀𝐀𝐑 𝐒𝐀𝐘𝐀𝐑 𝐃𝐀𝐓𝐀. 𝐆𝐀 𝐃𝐀𝐌𝐀 𝐓𝐀 𝐒𝐀𝐌𝐔.
Nakowadata.com 𝐒𝐔𝐍 𝐊𝐀𝐑𝐘𝐀 𝐅𝐀𝐑𝐀𝐒𝐇𝐈 𝐊𝐔𝐌𝐀 𝐀 𝐒𝐇𝐈𝐑𝐘𝐄 𝐒𝐔𝐊𝐄 𝐃𝐎𝐌𝐈𝐍 𝐊𝐎𝐘𝐀 𝐌𝐔𝐊𝐔 𝐘𝐀𝐃𝐃𝐀 𝐙𝐀𝐊𝐔 𝐒𝐀𝐌𝐔 𝐊𝐔 𝐀𝐊𝐀𝐋𝐋𝐀 3000 𝐊𝐔𝐋𝐋𝐔𝐌 𝐓𝐀 𝐇𝐀𝐍𝐘𝐀𝐑 𝐒𝐀𝐘𝐀𝐑𝐃𝐀 𝐃𝐀𝐓𝐀, 𝐊𝐀𝐓𝐈𝐍 𝐊𝐈𝐑𝐀, 𝐑𝐄𝐒𝐔𝐋𝐓 𝐂𝐇𝐄𝐂𝐊𝐄𝐑 (𝐖𝐀𝐄𝐂 𝐀𝐍𝐃 𝐍𝐄𝐊𝐎), 𝐍𝐄𝐏𝐀 𝐁𝐈𝐋𝐋 𝐃.𝐒

𝐑𝐄𝐆𝐈𝐒𝐓𝐄𝐑 𝐊𝐘𝐀𝐔𝐓𝐀𝐍𝐄
𝐀𝐘𝐈 𝐌𝐀𝐙𝐀 𝐀 𝐓𝐔𝐍𝐓𝐔𝐁𝐄𝐌𝐔 𝐀 𝐖𝐀𝐍𝐍𝐀𝐍 𝐋𝐀𝐘𝐈 𝐊𝐀𝐌𝐀𝐑 𝐇𝐀𝐊𝐀
08136230000

Mallam yace akwai babbar musiba da zata tunkari fati matukar bata tashi tsaye ta nemawa kanta mafita ba. Musibar kuwa idan tazo ba fati kadai zata shafa ba har ni danake a matsayin kawarta saita shafemu gaba daya. Kuma... Sai zainab tayi shuru ta kasa karasa maganar.

Kaka tayi saurin cewa kuma me abu fada mana yanzu adau mataki.

Zainab tayi ajiyar zuciya sannan tace kuma wai Aljani ne mai hatsarin gaske yake bibiyar rayuwar fati dan haka zai iya bijiro mata ta kowani irin yanayi ba tare da tasani ba.

Zainab ta kalli mama sannan tace kunsan abun mamakin kuwa? Mama ta girgiza kai alamar aa. Zainab tace wallahi siffar Aljaninda mallam ya zayyana mana irinsa sak fati take gani a mafarki.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUUN Shine abunda mama da kaka suke maimaitawa, zainab tace to ba wannan ba akwai wani babban abunda ke damuna gameda wannan Al'amari kuma shine sanadiyar zuwana nan.

Duk s**ayi shuru suna sauraronta.

Dama idan zanje gidan fatine bana ganin gidan.

Gaban mamane ya yanke ya fadi nan take tafara diban gumi.

Kaka tace k**ar yaya kuma zakice bakya ganin gidan.

Zainab nan take ta kwashe labarin yadda taje bata samu ba, da kuma zuwanda tayi da Ya'u har s**a gaji s**a dawo basuga gidan ba.

Ya Allah gamu gareka, yanzu ku yarannan dan wauta dama kunsan da wannan bayani shine kuka bari ai tun tuni andau mataki amma yanzunma bai baciba, zansa shi baban nata agaba yaje har gidan nata yayi mata Addua. Subarmin jikata ta zauna lafiya a gidan mijinta.

Ran zainab yayi baki ganin har yanzu bata gane ina Matsalar takeba. Gashi tana tsoron fadan abunda ke ranta Dan gudun me zai faru. Azahiri kuwa cewa tayi hakane wllh yak**ata adau mataki dan ko wayarta sunsa ya daina shiga idan aka kira.

Kaka tace haba zainabu abu aini indai matsala ta shigo hanuna kowacce irice sai naga bayanta to bare kuma wannan karamar Matsalar.

Zainab ta lura da yadda jikin mama yayi sanyi hakan yasa ta fara tunanin watakila mama ta fahimci inda Matsalar take.

Buy Cheap Internet Data Plan and Airtime Recharge for Airtel, 9mobile, GLO, MTN, Pay DSTV, GOTV, PHCN.

Address

Maiduguri

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hajara Digital D posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share