Borno Media Stalwart

  • Home
  • Borno Media Stalwart

Borno Media Stalwart Borno Media Stalwart (BMS), is a media platform form that will give up latest update across the state and Nigeria at large.

I will to formally inform our esteem follower of this great media platform (BMS), I will like to seize this avenue and i...
17/07/2025

I will to formally inform our esteem follower of this great media platform (BMS), I will like to seize this avenue and inform my resignation from People Democratic Party (PDP) to join the national coalition Africa Democratic Congress (ADC) after thorough consultation to follow the footsteps of our leader H.E Alhaji Atiku Abubakar.

Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Sen Aminu Waziri Tambuwal. Ya fice Daga Jam'iyyar PDP Ya koma ADC Kamar Yadda Wata Majiya Ta...
03/07/2025

Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Sen Aminu Waziri Tambuwal. Ya fice Daga Jam'iyyar PDP Ya koma ADC Kamar Yadda Wata Majiya Ta kusa Dashi Ta bayyana

Loading...
02/07/2025

Loading...

Aregbesola Yazama Sabon Sakataren Jam'iyyar ADC wanda Ta kasance Kawancen Jam’iyyu Masu Adawa Domin Tunkarar Tinubu A 20...
02/07/2025

Aregbesola Yazama Sabon Sakataren Jam'iyyar ADC wanda Ta kasance Kawancen Jam’iyyu Masu Adawa Domin Tunkarar Tinubu A 2027.

A wani babban taron da ya tara fitattun ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban na adawa a birnin Abuja, kawancen jam’iyyu masu adawa a Najeriya sun amince da ɗaukar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a matsayin sabon dandalin siyasa da za su yi amfani da shi wajen fuskantar manyan zaɓuka masu zuwa, ciki har da na 2027.

A yayin taron da aka gudanar ranar Talata, an sanar da Sanata David Mark, tsohon shugaban majalisar dattawa, a matsayin shugaban riko na ƙasa na sabon dandalin siyasar, yayin da Ogbeni Rauf Aregbesola, tsohon gwamnan jihar Osun, ya samu mukamin sakataren riko na ƙasa.

Hakazalika, an naɗa Bolaji Abdullahi, tsohon ministan wasanni a Najeriya, a matsayin mai magana da yawun kawancen.

Wata majiya ta tabbatar wa da KBC News cewa za a gudanar da wani taron kara jaddada wannan mataki a ranar Laraba, inda ake sa ran za a bayyana cikakkun matakan da za a bi wajen tabbatar da wannan sauyin siyasa.

A nasa jawabin karɓar wannan muƙami, Aregbesola ya jaddada cewa ya zama dole jam’iyyar ADC ta bambanta kanta da sauran jam’iyyu ta hanyar ɗorewa kan akida da tsayayyen tsari na siyasa.

Matakin na naɗin David Mark da Aregbesola na zuwa ne a daidai lokacin da siyasar Najeriya ke shiga wani sabon salo, musamman duba da yadda jama’a ke bayyana gajiyarsu da tsofaffin jam’iyyu da gazawar su wajen kawo sauyi mai ma’ana.

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDPTsohon shugaban majalisar dattawa na Najeriya, ...
02/07/2025

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tsohon shugaban majalisar dattawa na Najeriya, Sanata David Alechenu Bonaventure Mark, ya bayyana hukuncinsa na ficewa daga jam’iyyar adawa ta Peoples Democratic Party (PDP), wadda ya shafe fiye da shekaru 26 yana yi wa hidima.

A wata wasika da ya aikawa shugaban gundumar jam’iyyar PDP na Otukpo, karamar hukumar da ya fito a jihar Benue, David Mark ya tabbatar da barinsa jam’iyyar nan take. Wasikar mai dauke da kwanan wata 27 ga Yuni ta bayyana ne jim kadan bayan da wata kawancen jam’iyyu masu adawa s**a ayyana African Democratic Congress (ADC) a matsayin sabon dandamalin siyasar su tare da nada David Mark a matsayin shugaban kawancen.

A cikin wasikar, Sanata Mark ya jaddada cewa ya dauki lokaci mai tsawo yana marawa PDP baya, tun daga kafuwarta zuwa faduwar ta a 2015, inda ya zama daya daga cikin ‘yan jam’iyyar da s**a nace a cikinta duk da koma bayan da ta fuskanta.

“Kamar yadda kuka sani, shekaru da dama kenan ina cikin wannan jam’iyya ina kuma jajircewa wajen ganin ta ci gaba da tafiya bisa akida da nagarta,” in ji shi a cikin wasikar.

“Ko da lokacin da mafi yawan jiga-jigan jam’iyyar s**a fice bayan faduwar mu a zaben shugaban kasa na 2015, na dauki alkawari cewa zan kasance mutum na karshe da zai tsaya tsayin daka a PDP.”

Ya kara da cewa kokarinsa wajen sake gina jam’iyyar, sasanta bangarori, da kuma maido da martabarta ya taimaka kwarai wajen dawo da PDP cikin sahun manyan jam’iyyun da ke da tasiri a Najeriya.

Ficewar David Mark daga PDP dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake fargabar rikice-rikice a cikin jam’iyyar, musamman duba da yadda wasu tsofaffin jiga-jiganta ke komawa wasu sabbin hadin gwiwar siyasa kafin babban zaben 2027.

Jam'iyya PDP a Kebbi ta yi zama kan zaben 2027.Shugabannin jam'iyyar sun amince su shiga hadakar 'yan adawa don kayar da...
29/06/2025

Jam'iyya PDP a Kebbi ta yi zama kan zaben 2027.

Shugabannin jam'iyyar sun amince su shiga hadakar 'yan adawa don kayar da APC a 2027.

PDP ta zargi APC da jefa mutane cikin talauci, ta ce dole a hada karfi don sauya gwamnati.

29/06/2025

Atiku 2027 insha Allah

29/06/2025

Tinubu yayiwa yan Borno
Subtraction method

YANZU-YANZU: Saudi Arebiya ta amince da a binne Alhaji Aminu Alhassan Dantata a Madinah.Wani jikan sa, Sanusi Dantata ne...
29/06/2025

YANZU-YANZU: Saudi Arebiya ta amince da a binne Alhaji Aminu Alhassan Dantata a Madinah.

Wani jikan sa, Sanusi Dantata ne ya bayyana hakan a shafinsa na X, inda ya ce tuni shirye-shirye sun yi nisa wajen binne shi.

A cewar Sanusi, a gobe Litinin za a yi wa gawar ta marigayi Dantata sallah a masallacin Ma'aiki (SAW) sannan a binne shi.

Ameen
07/03/2025

Ameen

28/02/2025
Nasir El-Rufai ya koka yadda ba a yaba wa Atiku Abubakar game da ci gaban da ya samar.
22/02/2025

Nasir El-Rufai ya koka yadda ba a yaba wa Atiku Abubakar game da ci gaban da ya samar.

Address


Telephone

+2348066778347

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Borno Media Stalwart posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Borno Media Stalwart:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share