HIZKILU UMAR SULAIMAN

HIZKILU UMAR SULAIMAN Lalle yan uwa munbude wannan shafinne dan taimakon kammu da yan uwammu musamman akan abunda yashafi

Anemi ilimin addini shine garkuwaFarillan alwala guda 7 ne1.niyya.2.wanke fiska.3.wanke hannu zuwa guwar hannu.4.shafar ...
06/08/2025

Anemi ilimin addini shine garkuwa
Farillan alwala guda 7 ne

1.niyya.
2.wanke fiska.
3.wanke hannu zuwa guwar hannu.
4.shafar kayi.
5.wanke kafa zuwa idon sawu.
6.cuccudawa.
7.gaggautawa.

In Allah yayarda zan kawo muku sunnoni da musta habbai

Ina yiwa kowa fatan alkhairi

*Karka sake Maƙotanka su yi maka mummunan shaida akan waɗannan abubuwan:*1- *Kar ka sake ayi maka shaidar rashin yin sal...
23/07/2025

*Karka sake Maƙotanka su yi maka mummunan shaida akan waɗannan abubuwan:*

1- *Kar ka sake ayi maka shaidar rashin yin sallah ko ƙin zuwa masallaci matukar kana da lafiya*

2- *Kar ka sake ayi maka shaidar baka yiwa mutane sallama ko in sun yi maka baka amsawa*

3- *Duk rintsi duk wuya kar a sameka da laifin ƙin zuwa ta'aziyya, ko rashin duba maƙocinka yayin da bashi da lafiya*

4- *kar ka sake a kamaka da laifin zubawa maƙocinka kwata a ƙofar gidansa*

5- *Ka yi iyaka ƙoƙarinka wajan barin matarka zuwa dubiya ko barkar suna a keɓantaccan lokacin da ka zaɓa mata*

6- *karka sake ka ci kuɗin maƙocinka, ko a yi maka shaidar zalunci*

7- *kar ka sake maƙocinka ya tambayeka wani abu ka hana shi matukar kana da shi ko yaya ya ke*

8_*ka zamanto mai nuna damuwarka yayin da maƙocinka ya ke cikin wani mawuyacin hali, karka koma gefe kana tseguminsa*

9- *kar ka sake ayi maka shaidar mai nuna fariya ko nuna cewa ka fi kowa ilmi, kuɗi, matsayi, ko mukami*

10. *Kar ka sake ka kwana cikin koshi yayin da maƙocinka ke cikin yunwa*

*Ya Allah ka sanya mu cikin salihan bayinka karka sanya mu cikin gafalallu.

Da farko dai, Muna Mika Ta’aziyya ga yan uwan da Abokanan Arziki da ilahirin Mutanen Arewa a bisa Waenda wannan Ibtila’i...
28/03/2025

Da farko dai, Muna Mika Ta’aziyya ga yan uwan da Abokanan Arziki da ilahirin Mutanen Arewa a bisa Waenda wannan Ibtila’in Kisan Gilla a Faru dasu a Wani Gari a Edo State.

Nayi Mutukar Girgiza, Zuciyata ta kasa Ganin wannan Kisan Gillan da wasu bara gurbi mutanen kuma fa Yan Nigeria ne, waenda zuciyansu ya kekashe, wa’enda talauci yayi musu katutu a zuciyansu , saboda kwai kishi na jahilci akan su yan Arewa ne!

Na tsani Nuna Kabilanci ko na bangaren yare, Ko na Addini ko kuma Jinsi, ko kuma na Gari, wannan Abun ba karamin koma baya yake jawo wa a harka rayuwa da cigaba ba.

Wannan kisan Gillan ya wuce misali, ya firgitani, kuma nashiga dimuwa matuka! Kuma insha Allah muna magana da Manya manya Hukumomi, Kungoyoyin Kare hakkin bil’adam da kuma wasu masu kishin Arewa don samun matsaya akan wannan ibtila’in.

Haka kawai K**a Mutum da Ran shi, ka daure shi, ka saka shi cikin taya, ka zuba mishi petroluem ko kalanzir, ka Ketta masa wuta, kuma kashe shi , kana kallonsa yana ihu yana kuka kaikuma kana mishi Dariya har sai kaga ranshi ya fita, batare da wata Dalili ba kuma kai ba Hukuma ba!

Kai wannan Abu yayi muni!
Insha Allah sai mun bi kadin hakkin waenaan bayin Allah.

Muna Kira ga Jami’an tsaro da gaggauta Kamo waenda s**ayi wannan Kisan Gillan don girban Abunda s**a aikata.
Daga

23/10/2024

Izala da ɗarika

Address

Maiduguri

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HIZKILU UMAR SULAIMAN posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to HIZKILU UMAR SULAIMAN:

Share

Category