AL-Rayyan24

AL-Rayyan24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AL-Rayyan24, Media/News Company, Maiduguri.

20/04/2023

Rikici ya barke a gidan kitso wata taga Hoton Mijinta a screen Saver .😂😂😂

17/03/2023

Gobe ne fa💪

09/07/2022

Masu bibiyarmu ku turo mana hotunan shigar Sallarku insha Allahu za mu tayaku fatan Alkairi.

Mu je zuwa.....

03/07/2022

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah yayi wa Nura Mustapha Waye (Director IZZAR SO series) rasuwa. Za'a yi Jana'izarsa da Karfe 11 na Safennan A Gidansa dake Goron Dutse Primary Insha Allah.

Muna Addu'ar Allah ya jikansa ya gafarta masa kurakuransa yasa Aljanna ce makomarsa. Idan tamu tazo Allah yasa mu cika da kyau da imani.

R.I.J.F 😭 😭 😭 😭

04-12-1443
03-07-2022

Shugaban Majalisar Dattijan Nigeria Sanata Ahmad Lawan yace rashin samun Tikitin tsayawa Takarar kujerar sa ta Sanata za...
17/06/2022

Shugaban Majalisar Dattijan Nigeria Sanata Ahmad Lawan yace rashin samun Tikitin tsayawa Takarar kujerar sa ta Sanata zai iya sawa ya fice daga Jam iyar APC izuwa PDP.

ASUWAJI BALO AHMED TINUBU, YANA GIRBAR ABINDA YA SHUKA A YANZU. Tinubu Ya gina mutane da dama a gwamnatance, shiyasa yan...
09/06/2022

ASUWAJI BALO AHMED TINUBU, YANA GIRBAR ABINDA YA SHUKA A YANZU.

Tinubu Ya gina mutane da dama a gwamnatance, shiyasa yanzu yake girbar abinda ya shuka..

Yaran da Tinubu ya gina a gwamnatance su s**a taimakesa ya ci narasa a zaben fidda gwani da APC ta gabatar a jiya.

Wannan da rasi ne babba ga yan siyasa masu bukatar cigaba a siyasar su.

Muddin dan siyasa ya gina mutane a gwamnati, a kwana a tashi wataran zasu saka masa da abinda ya musu na alkairin, Kamar yadda Tinubu yayi kuma yaga ranar hakan.

Shiyasa masu iya magana s**a ce duk abinda ka shuka shi zaka girba.

SHAWARA:
Yan Siyasa Ku gina yaranku dan wataran zasu muku rana, a lokacin da kuke bukata.

09/06/2022
[YUSUF FINANCE]

08/06/2022

Yanzu-yanzu!

Insha Allahu sai na shiga Villa a matsayin shugaban kasa 2023~Inji Tinubu

08/06/2022

1 Tinubu 👉 1,271
2 Ameachi 👉 316
3 Osinbajo 👉 235
4 Lawan 👉 152
5 Bello 👉 47
6 Umahi 👉 38
7 Yerima 👉 4
8 Onu 👉 1
9 Nwajiuba 👉 1
10 Bakare 👉 0
11 Rochas 👉 0
12 Mokelu 👉 0
13 Rich 👉 0
14 Ayade 👉 0

Buhari ya roƙi 'yan Najeriya 'kada ku ƙyale PDP ta mayar da Najeriya baya'Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi kira ...
08/06/2022

Buhari ya roƙi 'yan Najeriya 'kada ku ƙyale PDP ta mayar da Najeriya baya'

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi kira ga 'yan Najeriya su tabbata ba su bar jam'iyyar adawa ta PDP "ta mayar da ƙasa baya ba".

Da yake jawabi a wurin zaɓen ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyarsu ta APC, Buhari ya ce APC ta sauya Najeriya ta hanyar gudanar da ayyukan raya ƙasa.

"Wajibi ne mu zaɓi masu adalci 'yan kishin ƙasa da ke da aƙidar haɗa kan ƙasarmu...don ciyar da ita gaba.

"Bai k**ata mu ƙyale PDP ta mayar da Najeriya baya ba."

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoton PDP ba ta mayar da martani ba, wadda tuni ta zaɓi Atiku Abubakar a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a babban zaɓe na 2023.

YUSUF FINANCE

07/06/2022

Yanzu haka dai wakilai waso 'deligates' sun shirya don fara kada kuri'un fitar da takara daya da zai yi wa APC takarar shugaban kasa a zaben 2023.

Amma ya kuke ganin matsayar Shugaba Buhari na kin bayyana dan takarar da yake so?

07/06/2022

Yanzu Yanzu:
Ajali ya zo da karan kwana; Wani daliget Dan jihar jigawa ya mutu a wurin taron APC a Abuja."

07/06/2022

BREAKING NEWS

South West APC Leaders In Closed Door Meeting To Choose One Aspirant For The Region.

02/06/2022

YANZU-YANZU

Gidan mai na AA-Rano dake Bamfai jihar Kano, ya k**a da wuta. Muna addu'a Allah ya mayar masa da alkhairi. Amin.

Reporter Sadiq Alhaji Kolo

25/05/2022

DA DUMI-DUMINSA| muna son masu kishin Arewa comment da Miliyan daya share 1 million a 24 hours muje zuwa

24/05/2022

JUSTICE4FATIMA
JUSTICE4 HER CHILDREN

17/04/2022

DA DUMI DUMI: Musulmi za su yi azumi har sau biyu a shekarar 2030

Masu ilmin taurari sun ce a shekarar 2030 mai zuwa, Musulmin duniya za su yi azumin watan Ramadan har sau biyu.

Azumi na farko a watan Janairu, na biyu kuma a karshen watan Disambar shekarar, yanayin da tun 1997 ba a taba gamuwa da shi ba.

BBC ta ruwaito Babban dalilin aukuwar haka shi ne bambancin da ke tsakanin shekarar Musulunci da ake lissaftawa da bayyanar wata, da kuma shekarar nasara wadda aka danganta da kwanakin da duniya ke dauka kafin ta zagaya rana.

Sannan wannan yanayin a aukuwa ne sau daya cikin shekara 30 saboda shekarar Hijira ba ta kai tsawon ta nasara da kwanaki 11 ba, k**ar yadda Khaled al-Zaqaq, wani mai nazarin taurari dan kasar Saudiyya ya bayyana a Twitter.

Tsawon shekara guda ta Hijira kwana 354 ne, inda shekarar nasara kuwa ke da kwana 365.

Rahoton BBC Hausa

11/04/2022

SIYASA BADA GABABA:

A JAHAR BORNO
1-Zullum Yana layin, Osibanjo.
2-Kashim Shatima Yana layin, Tinubu.
3-Sanata Ali Ndume Yana layin. Amechi.

Daga YUSUF FINANCE

11/04/2022

Yanzu-Yanzu: Bola Ahmed Tinubu Mai neman Shugaban cin Nigeria, Yace Osinbajo Ba Dan sa Bane.

11/04/2022

KANZON_KUREGE:;
Zan Dora Daga Inda Shugaba Muhammadu Buhari Ya Tsaya

inji Professor Yemi Osinbajo yayin yadda ya kaddamar da takarar shugabancin Najeriya.

10/04/2022

Shin har yanzu ba a san maci tuwo ba kenan?

Man city ko Liverpool wa zai dauki firimiyar bana?

YAYIN DA: Shugaban Jamiyyar Apc a Najeriya Sanata Abdullahi Adamu Yayinda Yake Jagorantar Wasu Daga Cikin Sanatotin Naje...
08/04/2022

YAYIN DA: Shugaban Jamiyyar Apc a Najeriya Sanata Abdullahi Adamu

Yayinda Yake Jagorantar Wasu Daga Cikin Sanatotin Najeriya Yayin Sallar La'asar A Yau Jumma ah

Me Zakuce akai

Jam'iyyar APC ta fitarda kudin sayen fom din takarar muk**ai daban-daban a zaben shekara ta 2023.1. 'Yan Majalisun Jihoh...
06/04/2022

Jam'iyyar APC ta fitarda kudin sayen fom din takarar muk**ai daban-daban a zaben shekara ta 2023.

1. 'Yan Majalisun Jihohi (House of Assembly) - Naira Miliyan 2

2. 'Yan Majalisun Wakilai (House of Reps.) - Naira Miliyan 5

3. 'Yan Majalisun Dattawa (Senate) - Naira Miliyan 10

4. Gwamnoni jihohi (Governorship) - Naira Miliyan 30

5. Shugaban Ƙasa (President) - Naira Miliyan 50

A Cikin Waɗannan Ƴan Siyasar Najeriyar, Wa Ku Ke Fatan Ganin Ya Ɗare Wannan Kujerar Ta Shugaban Ƙasa A Zaɓen 2023 ?Daga ...
05/04/2022

A Cikin Waɗannan Ƴan Siyasar Najeriyar, Wa Ku Ke Fatan Ganin Ya Ɗare Wannan Kujerar Ta Shugaban Ƙasa A Zaɓen 2023 ?

Daga

1 - Atiku Abubakar

2 - Sanata Bala Muhammad

3 - Rabi'u Musa Kwankwaso

4 - Bola Ahmad Tinubu

5 - Prof Yemi Osinbajo

6 - Aminu Waziri Tambuwal.

7 - Malam Nasiru El-rufa'i

8 - Babagana Umara Zulum

9 - Yahaya Bello

10 - Sheikh Isah Ali Pantami

Muna Dakon Ra'ayoyin Ku!!

04/04/2022

: Mafarauta 4 sun mutu, 7 sun jikkata bayan sun taka wani abun fashewa da aka birne a wani yanki a jahar Borno.

Ministan Sadarwa Shiek Professor Isa Ali Pantami ne ya bayar da umarnin  rufe layukan wayar da ba a masu rijista da hada...
04/04/2022

Ministan Sadarwa Shiek Professor Isa Ali Pantami ne ya bayar da umarnin rufe layukan wayar da ba a masu rijista da hada su da lambar zama dan kasa ba (NIN) daga yau Litinin 4 ga watan Afrilun 2022.

Shin kuna ganin wannan yunkuri zai kawo sauyi cikin kasar musamman a bangaren tsaro?

Daga

04/04/2022

SALLAR JANA'IZA: Daga Garin Fataskum Dake Jihar Yobe Sheikh Sani Yahaya Jingir Yayiwa Sheikh Ustaz Muhammad Sambo Sallar Jana'iza

Sheikh Mohammed Surajo Ya Rasu Ne Sak**akon Hadari Daya Rutsa Dashi Yayinda Yake Kan Hanyarsa Ta Zuwa Tafsiri A Jihar Yobe Allah Yajikansa Da Rahamarsa Amin Amin .

04/04/2022

Yanzu Yanzu:
A wani Fyafayin Video,

Shugaban kasar janhuriyar Niger Bazoum, ya ce yawan haihuwa ba tare da kulawa da yaran ba yana ci mai tuwo a kwarya.

04/04/2022

Yanzu Yanzu:

‘Yan Sanda Sun Damke Wasu Da Ake Zargin Barayin Baburan Adaidaita Sahun Ne A Jihar Rivers.

04/04/2022

DA DUMI DUMI:

Kwamitin Masalacin Apo Dake Abuja Ya Janye Dakatarwar Da S**a Yi Wa Sheik Nuru Khalid Daga Limanci.

04/04/2022

Ina Mutanenmu Atashi Ayi Sahur Kar a makara fa😇

02/04/2022

Karfe 6:30 Aka Sha Ruwa A Jahar Yobe......Inda Kuke Fa???

02/04/2022

Day 1

01/04/2022

DA DUMI DUMI !!
Yanzu Yanzu. Mai Martaba Sarkin Musulmai Na Nigeria Ya sanar da Ganin Watan Ramadan

Babban Taron APC: Sanata Abdullahi Adamu na daf da zama shugaban jami'ya bayan da ƴan takara 6 su ka janye masaYan takar...
26/03/2022

Babban Taron APC: Sanata Abdullahi Adamu na daf da zama shugaban jami'ya bayan da ƴan takara 6 su ka janye masa

Yan takarar shugabancin Jam'iyyar APC sun janyewa tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Sanata Abdullahi Adamu.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da guda daga cikin Yan takarar Sanator George Akume ya Sanyawa hannu.

Wadanda s**a sanya hannu a wasikar sun hadar da:

1 Sanator Tanko Almakura
2George Akume
3 Sani Musa Muhammad
4 Abdulazeez Yari
5 Etsu Muhammad
6 Turaki Salifu Mustapha

Ƙarin bayani na nan tafe...

Daga YUSUF FINANCE

LABARI CIKIN HOTUNA: Gwamnan Jahar Nasarawa Abdullahi Sule da Ministan Yaɗa Labaru Lai Mohammed suna jawabi ga Shuwagaba...
26/03/2022

LABARI CIKIN HOTUNA:

Gwamnan Jahar Nasarawa Abdullahi Sule da Ministan Yaɗa Labaru Lai Mohammed suna jawabi ga Shuwagabannin Jami'an tsaro kan rikicin daya faru Ƙofar shiga Ɗakin taro na Eagle Square, inda ake gudanar da Babban Taron APC

Daga

Ku Fita Daga Batun Karin Girma Da Aka Yiwa Ministan Sadarwa Farfesa Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami, Ko Ku Fuskanci Shari...
19/02/2022

Ku Fita Daga Batun Karin Girma Da Aka Yiwa Ministan Sadarwa Farfesa Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami, Ko Ku Fuskanci Shari'a, Barista Iheanacho Agboti Dake Kudancin Najeriya Ya Gargadi Kungiyar ASUU

Ma’aikacin shari’a mai suna Barista Iheanacho Agboti ya yi barazanar daukan matakin shari’a a kan kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) bisa barazanar da ASUU ta yi na kakabawa jami’ar fasaha ta tarayya da ke Owerri (FUTO) takunkumi kan karin girma da jami'ar ta yiwa ministan sadarwa da tattalin arzikin dijital Farfesa Isa Ali (Pantami).

Mista Agboti ya ce ASUU ba ta da wani iko a karkashin dokar kungiyar kwadago ta 2005 ko wata doka, ta sanya wa hukumar gudanarwar kowace jami’a takunkumi kan ba da matsayin farfesa ga duk wani mutum da cibiyar ta ga ya dace a bashi.

Ya bayyana haka ne a Abakiliki ranar Alhamis yayin da yake zantawa da manema labarai.

Lauyan ya caccaki ASUU kan shishshigi da tayi na shiga hurumin da ba na taba, inda ya nanata cewa majalisar gudanarwar jami’o’i ce kawai aka baiwa irin wannan iko a karkashin tsarin "Universities Miscellaneous Provisions Act 2012" k**ar yadda aka tsara kuma majalisa ta amince.

Agboti ya ce: “Ni lauya ne kuma gaskiyar magana ita ce ASUU ba ta da ikon shiga wannan hurumin, kungiyar kwadago ta Najeriya ce za ta sanyawa mahukuntan Jami’ar Fasaha ta Tarayya (FUTO) takunkumi a kan duk abunda tayi da bai dace ba.

“ASUU ta jahilci gaskiya kuma wannan abin bakin cikine, wanda babu inda a karkashin dokar Kungiyar Kwadago ta 2005 (wacce ita ce dokar da ke jagorantar ayyukan duk kungiyoyin kwadago a Najeriya, ciki har da ASUU), da ta baiwa ASUU ikon hukunta shugabannin jami’o’i saboda wani abin da ake zaton ya saba wa doka.

“Kuma dokar da ke jagorantar al’amuran dukkan jami’o’in tarayya a Najeriya ita ce Dokar Jami’o’i (Miscellaneous Provisions) (Amendment) Act 2012.

"A karkashin wannan doka, hukumar gudanarwar jami'a ba za ta iya amincewa da kungiyar ta ASUU ba," in ji shi.

Agboti ya kuma yi kira ga shugabannin kungiyar ta ASUU

Daga karshe dai tsohuwar nan yar shekara 102 da ta fito takarar shugabancin Najeriya 2023 ta bugo Fosta a jam'iyyar APGA...
19/02/2022

Daga karshe dai tsohuwar nan yar shekara 102 da ta fito takarar shugabancin Najeriya 2023 ta bugo Fosta a jam'iyyar APGA mai alamar Zakara.

Shin matasa za ku zabi mama kuwa?

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UNAllah ya yiwa Mahaifiyar COMR. MUSA MUHAMMED MIKO rasuwa. Secretary Kungiyar Marubut...
09/12/2021

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN

Allah ya yiwa Mahaifiyar COMR. MUSA MUHAMMED MIKO rasuwa. Secretary Kungiyar Marubutan Arewa a kafofin sadarwar zamani "Arewa Media Writers" reshen karamar Hukumar Bursari dake Jahar Yobe.

A madadin dukkannin shugabanni da membobin kungiyar "Arewa Media Writers" muna miki sakon ta'aziyyarmu tare da yiwa Mahaifiyar tamu Addu'ar Allah yasa Aljannah Firdausi ta zamo makomarta Na karshe.

Sannan muna Addu'a ga yan uwa musulmai da s**a rigamu gidan gaskiya, Allah madaukakin Sarki ya jikan su da rahama.

Mu idan tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani. Amen Summa Amen
:
:
:
:
Sign.....
YUSUF FINANCE Chairman "Arewa Media Writer's" Rashen karamar hukumar Bursari a Jahar Yobe.

RUWAN KOGI NA YUNKURIN MAMAYE ILAHIRIN WANI YANKI A GARIN JUMBAM DAKE KARAMAR HUKAMR TARMUWA LG. A JAHAR YOBE ,Daga Kung...
05/09/2021

RUWAN KOGI NA YUNKURIN MAMAYE ILAHIRIN WANI YANKI A GARIN JUMBAM DAKE KARAMAR HUKAMR TARMUWA LG. A JAHAR YOBE ,

Daga Kungiyar Arewa Media Writer's Reshen Karamar Hukumar Bursari LG.

Ruwan kogi na yunkurin shiga gida jen mutane a garin Jambam daka jahar Yobe , Wanda ruwan a halin yanzu Yana yiwa al'umar garin Jambam barazana , Hakan yasa al'umar garin cikin tashi hankali da firgici.

Inda wani mazaunin garin ne yake Shedawa Wakilan mu da s**a ziyarci Garin,

Sannan kuma shi mazauni garin ya sheda mana cewa ruwan kogin bashi ne karo Na farko ba da yake musu barazanar shiga cikin garin nasu,

A shekarar 2019 ruwan yashiga garin Sannan yayiwa jam'ar garin barna sosai wanda hakan ya jawo asara sosai a harkar Noma da kuma sauran dukiyoyi Al'ummar garin.

al'umar garin Suna bukatar taimakon gwamnati Sabida yadda Ruwan kogin da yazo a wannan shekarar yafi na shekarar baya, Sabida suna gani yadda ruwan ya fusata, Da yinkurin mamaye ilahirin yakin da ruwan yake,

Al'ummar garin Jumbam suna Kara godiya da nuna Farin cikin ga Gwamnati Jahar Yobe Kar kashin jagoran cin Mai girma Gwamna Mai Mala Buni. Bisa Irin kokarin da yamusu a Karon Farko Na samar musu magudanar ruwa na Kolbati,

Amma har a halin Yanzu Al'ummar garin Jumbam suna bukatar tallafin gwamnati sosai Sabida ruwan Ba irin wanda zasu meke kafa su zauna bane dole sutashi su tsaya dan neman tallafin mai girma Gwamna jaha.

Muna Kira da babban murya da mai girma Gwamna jahar Yobe da ya karkato da hankalin wakilan sa masu bada tallafin gaggawa zuwa garin jumbam domin basu tallafin,

Sabida garin jumbam Yana daga cikin manyan Ward da Tarmuwa Local Govt take jida da shi, Duba da yadda s**a futo kwansu da korkotan s**a Zabe Mai girma Gwamna Jaha.

Rubutawa✍🏽✍🏽 YUSUF FINANCE Shugaban Kungiyar Arewa Media Writer's. Reshen Bursari LG Yobe Chapter

Muna Kira zuwa ga masu kera akwatin Lefe, Dasu Rage Zurfin sa..🙄Mun samu korafe korafe daga wajen Samari kan cewa Akwati...
29/08/2021

Muna Kira zuwa ga masu kera akwatin Lefe, Dasu Rage Zurfin sa..🙄

Mun samu korafe korafe daga wajen Samari kan cewa Akwatin da ake saka lefe yayi Zurfi sosai,

Sabili da haka, A matsayin mu Na masu kare hakkin matasa, Muna Kira DA babbar murya da kamfanin kera akwatin a Gaggauta Rage Zurfin sa,

Wannan lamari yajima Yana ciwa samari tuwo a kwarya, Nima kaina dama abin Yana dan min Kaikayi, Akwatin yayi Zurfi wlh😎

Wanna shine kashedi Karo Na farko, A Biyawa matasa bukatar su karsu fusata, Yauwa😡

---------------------------------------
Write...YUSUF FINANCE

Address

Maiduguri

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AL-Rayyan24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share


Other Media/News Companies in Maiduguri

Show All