22/04/2024
SABON ALLAH BAYAN RAMADAN.
Assalamualaikum warahmatullah wabarakatuh. Dafatan Mallam yana cikin koshin lafiya? Allah ya ƙara ma Mallam Imani da daraja.
Mallam tambayar mu itace, shin wanda azumci watan Ramadan gaba ɗaya sannan ya koma aikata mugayen ayyuka bayan Ramadan kamar su Shaye Shaye, Zina da makamantansu amma banda Shirka.
Shin Mallam Dagaske ne Azumin watan Ramadan da yayi ba karɓaɓɓiya bace a banza yayi ta tunda hakan bai hana shi aikata alfahasha ba?
Wa alaikumus salamu warahmatullah wabarakatuh Amin.
Shi Allah ya shar'anta Azumin Ramadan ne domin a samu tsoron Allah kawai, domin ba'a shiga Aljana sai da tsoron Allah, kuma Neman shiga Aljana dole ne, shine ka'ida tace:
DUK ABINDA WAJIBI BAYA CIKA SAI DA SHI TO SHIMA WAJIBIN NE.
Aya ta 183 a suratul Bakarah Allah yace:
(YA KU WADANDA S**A BADA GASKIYA, AN FARLANTA MAKU AZUMIN KAMAR YADDA AKA FARLANTA WA WA DANDA SUKE A GABANIN KU, DOMIN KUJI TSORON ALLAH).
👉 Tsoron Allah ana samun shine da abu biyu:
1. Aiwatar da umurce umurcen Allah,
2. da barin hane hanen sa.
👉 Wannan itace hikimar shar'anta Azumin Ramadan.
Idan aka rasa ta, do Azumin Ramadan din baiyi fa'ida ba.
TACEWA:
1. Hikimar ko Anfanin Azumin Ramada, aci gaba da kiyaye dokokin Allah wajen yin Duk Abinda akayi Umurni da shi, kamar Sallah akan lokacin ta, da zakka da Hajj ga mai Hali, da zumunci da dai sauransu.
2. Nisantar hane hanen Allah, kamar shaye shaye Zina sata Karya gulma, da makamantan su.
3. Acikin Azumin Ramadan ankoya mana dangogin ibada, kamar Sallah farillar ta da Nafilar ta, Azumin shi karan Kansa, saboda haka sitta shauwal ba zai tada maka da hankali ba, Haka kyauta da Sadaka, karatun Kur'anin da zikirori da addu'o'in. Dadai sauransu.
4. Ankoya mana barin sabon Allah, duk Wanda bai bar karya ba ko aiki da ita da sabon Allah a Ramadan ba, Allah baya da bukatar barin cin Abincin sa da shan abin Shan sa, domin baya da lada, Amma idan yaci ko yasha ya takalo wata tsuliyar dodon.
5. Haka ma Koda ya bari a cikin Ramadan din, sai