04/12/2021
Zan jagoranci zanga-zangar adawa da karin kudin man fetur zuwa N340 da Buhari ke shirin yi , kai ba zanga-zanga kadai ba, harma da kashe-kashe sai an yi idan ta k**a~Inji Sheikh Bello Yabo
Babban malamin addinin musulunci a jihar Sokoto Sheikh Bello Yabo ya mayarda martani kan shirin gwamnatin Najeriya na karawa man fetur kudi a cikin sabuwar shekarar 2022.
Babban malamin ya ce babu dalilin da zai sa su zura ido ana gallazawa talakkawa a wannan gwamnati, don haka doli ne su fito su yi zanga-zangar wannan rashin imani da tausayin talakkawa da gwamnatin Buhari ke shirin yi na karawa man fetur kudi zuwa N340.
Malamin ya ce k**ar yadda Buhari ya fito ya yi zanga-zangar karawa man fetur kudi kafin ya hau mulki mu ma za mu fito mu yi zanga-zangar adawa wannan rashin tausayi.
Malamin ya ci gaba da cewa, ba zanga-zanga kadai ba, har ma da kashe-kashe sai an yi idan gwamnati ta ce za ta zartar da wannan kuduri na ta.
Shin meye ra'ayin ku ne akan wannan?
Sokoto Online