23/09/2025
Najeriya Ta Amince Da Kafa Ƙasar Palastinu Mai Cin Gashin Kanta
Gwamnatin Najeriya ta bayyana goyon bayanta ga kafa ƙasar Palastinu mai cikakken 'yanci da ikon tafiyar da kanta.
Wannan mataki ya zo ne a daidai lokacin da kasashen duniya da dama ke ƙara matsa lamba kan batun 'yancin Palastinu, musamman a yankin Gabas ta Tsakiya.
Najeriya ta kasance cikin jerin kasashen da ke kira da a samar da mafita mai dorewa, ta hanyar zaman lafiya da fahimta tsakanin Palastinu da Isra'ila.
Source - ATP Middle East.