Malumfashi Reporters

Malumfashi Reporters Domin samun sahihai kuma ingantattun labarai, na yau da kullum.

RAI BAKON DUNIYAAllah Madaukakin Sarki Ya karbi rayuwar Babban Malamin Darikar Sufaye Sheikh Usman Kusfah Rigi-Rigi Mala...
02/02/2026

RAI BAKON DUNIYA

Allah Madaukakin Sarki Ya karbi rayuwar Babban Malamin Darikar Sufaye Sheikh Usman Kusfah Rigi-Rigi

Malamin da yayi fice wajen karanto sunayen Sahabban Shehu

Hakika Malam ya debe mana kewa, Malami mai yawan fara'a

Muna roko masa rahama da gafaran Allah

Ubangiji Allah Ya jikansa tare da dukkan Musulmi, Allah Ya kyautata namu karshen

reporters

Najeriya Ta Amince Da Kafa Ƙasar Palastinu Mai Cin Gashin KantaGwamnatin Najeriya ta bayyana goyon bayanta ga kafa ƙasar...
23/09/2025

Najeriya Ta Amince Da Kafa Ƙasar Palastinu Mai Cin Gashin Kanta

Gwamnatin Najeriya ta bayyana goyon bayanta ga kafa ƙasar Palastinu mai cikakken 'yanci da ikon tafiyar da kanta.

Wannan mataki ya zo ne a daidai lokacin da kasashen duniya da dama ke ƙara matsa lamba kan batun 'yancin Palastinu, musamman a yankin Gabas ta Tsakiya.

Najeriya ta kasance cikin jerin kasashen da ke kira da a samar da mafita mai dorewa, ta hanyar zaman lafiya da fahimta tsakanin Palastinu da Isra'ila.

Source - ATP Middle East.

23/09/2025

Malumfashi Ta Lallasa Funtua daci 2-1 a Karkanda Stadium Katsina

24/07/2024

Kun shirya Fita Zanga-Zanga Kuwa?

24/07/2024

Fully Activated Now!

'YAN DAMFARA SUN SHIGO DA SALO IRI IRI Yanzu Yanzu wani dan damfara yazo shagon dake kallon gidana  dake unguwar kofar H...
23/12/2023

'YAN DAMFARA SUN SHIGO DA SALO IRI IRI

Yanzu Yanzu wani dan damfara yazo shagon dake kallon gidana dake unguwar kofar Halliru Gashua, da niyya sayan kaya. Bayan sun kammala ciniki da mai shagon sai ya nemi a bashi number Account, bayan an bashi number Account sai yace ya tura kuɗin mai shago yace kuɗi bai shigo ba fa.

Dan damfarar yazo da wadannan kwalaye da kuke gani guda biyar makare da kaya harda bacco bacco sabbi a cike da kaya. Sai yace wa mai shagon ga kayan sa zai koma kasuwa ya dawo Amma mai shagon ya bashi kuɗi #30,000 kafin ya dawo ga kayan sa nan.

Mai shago dai yaki bada kuɗi, sai Dan damfara yace to yana zuwa a jire masa kayan sa. Haryanzu dai bai dawo ba tin da safe, mai shago yace bari muga menene a ciki kar ya dawo yayi mana sharri.

Ya kira mu mukazo a matsayin shedu muna budewa sai mukaga kwalaye cike da yayi da duwatsu, kasa da sauran tarkace.

Ya jama'a mu kara kula sosai da irin wannan damfara da yan damfara ke yi a cikin Al'umma.

Allah ya raba mu da dukkan sharrin masu sharri.
Shehu A.A Gashua

Innanillahi wa'inna'ilaihi raji'un!Wannan duniyar ina zata kaimu, yau naga abinda tunda nake a duniya ban taba gani ba s...
22/12/2023

Innanillahi wa'inna'ilaihi raji'un!

Wannan duniyar ina zata kaimu, yau naga abinda tunda nake a duniya ban taba gani ba sai dai a bani labari ko na gani a film ko a mafarki

Wannan bawan Allah Faisal Ahmad Abubakar abokin mu ne dan Jos mazaunin Anguwan Rogo, yana university of Jos, Law Department inda yanzu haka ya karasa final exam dakyar da rokon ubangiji

An raba faisal da abokan shi, an gusar masa da tunanin shi, tun 2018 faysal yake shan wahala sai yau Allah ya kawo karshen sihirin da azzalumai s**a masa

Haka kawai faysal zaije wajen abokan shi ya karbi kudi ko wayar su daka lokacin ba zasu kara ganin shi ba, babu kudin ko wayar babu labarin su. Irin kudin da faysal ya karba a wajen mutane Allah yayi yawa dasu wanda saboda haka mutane s**a dane alaka dashi saboda suna kallon shi a matsayin dan damfara ko macuci

Wannan kayan tsafin da kuke gani dasu aka hada aka yiwa faisal asiri a cikin harda hoton shi, da kudi naira dari, da wasu ganye da rubutun Arabic aka hada aka daure aka tura a cikin kwalba k**ar yanda kuke gani a jikin wannan hoton

Dalilin gano wannan asiri shine, tsahon wahalar da faisal yayi yana sha wata bai baiwar Allah ta umarce mu da muje tsohon shagon da faysal ya k**a tun 2018 akan zai fara sna'ar POS a shiga cikin silin din shagon za'aga wani abu a ciki

Bayan an dauko wannan kayan tsafin, ana fara kona su faisal ya fara ihu yana salati daka karshe muka dauke shi zuwa gida. Dan girman Allah duk wanda yaga wannan post din ya taimaka yayi sharing saboda duniya tasan azzaluman da s**a hada faisal gaba da mutane s**a saka abokan shi s**a kaurace masa s**a lalata masa rayuwa. Innanillahi wa'inna'ilaihi raji'un

Wannan labarin a ido na ya faru ba labari ba, a ido na aka fara komai aka gama, nine na dauki wannan hotunan da videon yanda aka kulla wannan zalinci. Ubangiji Allah ya nesanta mu da azzalumai makiya son cigaban mu

Aliyu Naziru Officer 󱢏

Aunty Fauziyya D. Sulaiman; Gatar Marasa Gata. Burbushin Matan Sahabbai.Haqiqa ita gata ce, garkuwa ce, kuma uwa ce ga w...
26/10/2023

Aunty Fauziyya D. Sulaiman; Gatar Marasa Gata. Burbushin Matan Sahabbai.

Haqiqa ita gata ce, garkuwa ce, kuma uwa ce ga wadanda s**a rasa gata, mace ce irin wacce tayi fintinkau a cikin tsararrakin ta mata da maza, samun tamkarta sai an tona kwarai, ta sanya walwala a fuskokin mutanen da bata san adadin su ba, tayi sanadiyar canzawar rayuwar mutane marasa adadi, ita abar yarda ce dari bisa dari ga masu buqatar sarrafa dukiyar su ta hanyar taimakawa mabuqata, ina mai basu tabaccin dukiyar su zata kai ga ire-iren mabuqatar da suke cikin yanayi na buqatar taimako kwarai.

Kuyi amfani da dukkan wani nau'in suna na Girmamawa da kuka sani, a yayin da kuka tashi ambatar sunan wannan baiwar Allah, dukkan sunan girmama da kuka ambace ta da shi, ba alfarma kuka yi mata ba, ina yi muku rantsuwa da Allah ta cancanci hakan daga garemu, alkairan ta ba zasu lissafu ba, babu abinda zamu ce da Aunty Fauziyya D. Sulaiman saidai muce Allah ya saka mata da alkhairy, zuciyar (FAUZIYYA) ba bu hassada ko ƙyashi a ciki, bata da ƙyamar mutane, ta na da tsarkin zuciya, kullum hannun ta mai bayarwa ne ga talakawa, ba ta da kwaɗayi, ta na girmama kai, amma sam - sam ba ta da girman kai, ta na da tausayi, mai son karatu da makaranta ce, mai son nishaɗi ce da raha, akwai ta da ƙoƙarin dogaro da kai, ta na son rayuwa ta girmama juna da mutunta juna.

HAJIYA FAUZIYYA D. SULAIMAN YAR ALJANNA CE IN SHA LLAHU DAMU BAKI DAYA.

Gwagwarmaya itace da gewa da jajircewa domin kawowa al'umma mafita a cikin cigaban rayuwarsu ko addininsu, Hajiya Fauziya D sulaiman duniya ta shaida da tarin alkhairin dake yi a cikin gwagwarmayarta, Macece mai fikirar rubutun labari, ko na film ko kuma na littatfi masu ma'ana da suke koyar da darasi ga rayuwar al'umma, kullum cikin fafutuka take da gwagwarmaya domin nemawa al'umma talakawa marasa qarfi taimako, tayi sanadin ceton rayuwar jama'ar annabi marasa adadi wanda s**a kamu da matsanantan rashin lafiya wajen nema musu tallafin kudin magani karkashin qungiyarta mutanen data ciyar bazasu lissafu sannan tayi sanadin da marayu da talakawa da yawa s**a samu matsuguni ko da yaushe dare da rana aikin tallafawa mabuqata shine a gabanta samun mutanen arziki irinsu hajiya fauziyya babbar rahama ce, duniya ta shaida da ayyukan alkhairinta bugu da kari macece mai kare mutuncin addininta a duk inda take bata wasa da addininta da al'adarta.

A shekarun baya lokacin ina yawan karance karance litattafin hausa ina yawan karanta litattafanta. To amma daga baya da na daina karatun litattafai sai na daina jin d'uriyarta. Kwatsam yanzu kuma sai nake yawan cin karo da postings dinta a media duk da dai bata cikin friends nawa.

Fauziyya D. Suleman marubuciya ce. Kuma macece jajirtacciya mai tsayawa akan lamarin talakawa wadanda basu da gata Ta zama tamkar uwa ko uba a garesu.Yawan kai kawo da take yi akan abin da ya shafi tallafi da nemawa bayin Allah taimako har ya mantar da ita aikinta. Kuma da alama Allah ya hadata da miji mai goya mata baya da bata had'in kai kan wannan aikin da ta d'orawa kanta.

Malama Fauziyya ba wai da aljihunta take taimakawa mabuqata ba a'a Tana dai amfani da baiwar da Allah ya bata ne ta rubutu tana taimakawa wajen rubuta halin da wani ko wata ke ciki game da rashin lafiya da kuma yawan kudin da ake buqata a wajen sayen magani Bayan rubutu kuma tana bin mutane masu hali wadanda suke da zuciyar tausayi tana kai musu koken talakawa Cikin ikon Allah sai ka ga duk yawan kudin da ake buqata an dace Babban kuma abin da ke birgeni da tsarin aikinta shine duk wani tallafi da ta samo ko adadin kudin da aka samu tana yin posting tare da sunayen wadanda s**a bayar din dan cire shakka ko zargi A takaice dai komai dai ana yinshi a bisa tsari da kuma dacewa.

Da irin wannan zamu fahimci cewa taimakon mabuqata ba sai mai kudi ba Ni da kai duka zamu iya yinsa ta hanyar yin amfani da irin baiwar da Allah ya bamu Kuma irin wannan aikin shine za kayi ko bayan ranka mutane ba zasu manta da alkhairyn da kayi musu ba Kuma uwa uba ka tarar da tarin ladan ka a cen lahira yana jiranka.

Muna rokon Allah (SWT) ya saka mata da mafificin alkhairinsa ya cigaba da daga kima da mutuncinta, Allah (SWT) ya kara mata Imani, lafiya, arziki da daukaka alfarmar Annabi Muhammad (SAW) Allah (SWT) ya yi mata tsari daga kowane irin sharri na duniya, Allah (SWT) ya yi ma gabanta da bayanta albarka saboda Alfarmar Annabi Muhammad (SAW).

YA ALLAH KA TALLAFAWA DUK MAI TALLAFAWA AL'UMMAH 🙏🙏🙏

Rubutawa ✍️ Abubakar S Malumfashi

Ko ka san cewa ƙasar FALASƊIN ita ce ƙasar da aka kira ta da ƙasar ANNABAWA!??👇01: Falasɗin ta kasance ƙasar Annabawan A...
21/10/2023

Ko ka san cewa ƙasar FALASƊIN ita ce ƙasar da aka kira ta da ƙasar ANNABAWA!??👇

01: Falasɗin ta kasance ƙasar Annabawan Allah, amincin Allah ya tabbata a garesu baki ɗaya.

02: Annabi Ibrahim (a.s) shine ya fara yin hijira zuwa ƙasar Falasɗin.

03: Allah Ta’ala ya tseratar da Annabi Lut (a.s) daga azabar da ta afkawa Mutanensa a ƙasar Falasɗin.

04: Annabi Dawud (a.s) ya rayu a wannan ƙasar, kuma ya gina masallaci a nan.

05: Annabi Sulaiman (AS) ya kasance yana zaune a ƙasar nan, kuma yana mulkin duniya baki ɗaya.

06: Annabi Musa (A.S) ya gaya wa sahabbansa game da wannan ƙasa da kuma shiga wannan gari mai tsarki (Falasɗin). Ya kira wannan gari da mai tsarki saboda kasancewarsa ya barranta daga shirka da kuma kasancewarsa ƙasar Annabawa.

07: Mu'ujizozi da dama sun faru a wannan gari, ciki har da haihuwar Annabi Isah ɗan Maryam amincin Allah su tabbata a garesu.

08: A lokacin da Mutanen Annabi Isa (AS) s**a so su kashe shi sai Allah Ta’ala ya dauke shi zuwa sama daga Qudus (watau Jerusalem).

09: Ɗaya daga cikin alamomin tashin ƙiyama shine dawowar Annabi Isa (AS) duniya a wannan ƙasar.

10: Annabi Isa (AS) zai kashe Dajjal a wani waje da ake kira (Bab Lud) a wannan ƙasar.

11: Falasɗin ita ce ƙasar da za a tashe kowa, Allah ya yi masa hisabi.

12: Daga wannan birnin ne Yajuju da Majuju za su fito su yaƙi Mutanen duniya da hargitsa duniyar.

13: Bayan haka ƙasar Falasɗin tana da darajar kasancewarta ALQIBLA ta farko ta Musulmi bayan an wajabta salloli biyar. Daga baya aka umurci Annabi Muhammad (ﷺ) da ya juya fuskarsa daga Masallacin Aqsa na (Jerusalem) zuwa Ka’aba na (Makkah) yayin Sallah. Masallacin da wannan lamari ya faru har yanzu ana kiransa da sunan Masallacin (Al-Qibla).

14: Bayan haka kuma anzo da Manzon Allah (ﷺ) daga Makka zuwa BAITUL-MAQDIS (Jerusalem) kafin a dauke shi zuwa sama a daren Mi'iraji.

15: Dukan Annabawa sun yi sallah anan, bayan da Annabi Muhammad ﷺ ya jagorance su sallah. Shine dalilin da yasa Falasɗin ta zama ƙasar dukkan Annabawan Allah.

HADISI👇
16: Sayyidina Abu Zarr yana cewa: "Na tambayi Manzon Allah ﷺ, wane Masallaci ne aka fara ginawa a doron ƙasa? Sai ya ce: Masjidul Haram (wato Ka'aba). Yace sai wanne kuma sai Mazon Allah ﷺ ya ce: Sai Masallacin Al-Aqsa (wato BAITUL-MAQDIS). Sai nace shekara nawa tsakanin su biyun? Sai Annabi (ﷺ) ya ce: Shekaru Arba'in ne, (40yrs) kuma duk lokacin da ku ka samu dama, ku yi salla a can"

17: A zamanin mulki na Musulunci, Sayyidina Umar na matsayin Khalifa, ya bar duk sauran yaƙuƙuwan da Musulmi suke yi a faɗin duniya, don ƙwato Falasɗin, da kansa ya fita daga Madina yaje ya yi sallah a a wurin, yana mai bayyana mahimmanci da girman wannan ƙasar.

18: Sake ƙwato wannan ƙasar da (SULTAN) SALAHUDDEEN AL-AYYUBI ya yi a ranar Juma’a 27 ga watan Rajab 583 Hijira, shi ma alama ce ta izzar Allah.

19: Sunan Jerusalem shi ne (Baitul Maqdis) saboda tsarkin wannan birni wanda shine ya bambanta shi da sauran garuruwa, sama da Sahabban Manzon Allah (ﷺ) 5000 ne s**a sadaukar da rayuwarsu wajen mallakar wannan gari da kuma ceto shi daga zaluncin Romawa Kirista.

20: Musulmi su sani cewa: ba a rufe babin shahada ba wajen dawo da martabar wannan wuri (Qudus) daga hannun YAHUDAWA maƙiya Allah da Manzonsa ba. Kuma wannan birni na Qudus ana kiransa da suna birnin (SHAHIDAI)

Allah ya taimaki Addinin Musulunci da Musulmi Allahumma Ameen!! 🇵🇰🕌🕋☪️🤲

Nazir Umar (naxeer_kaoje)

Engr. Muntari Sagir Yaba  mahaddatan makarantar sheik Dahiru Usman Bauchi, dubu biyar biyar su 42 tare da Alkawarin zaga...
21/10/2023

Engr. Muntari Sagir Yaba mahaddatan makarantar sheik Dahiru Usman Bauchi, dubu biyar biyar su 42 tare da Alkawarin zagaye makarantar da kuma gyara ajujuwa 4.

Allah ya saka masa da alkhairi Aameen.

HOTO:Lokacin da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da Gwamna Abba Kabir Yusuf suke raba dollar Amurka $200 kwatankaacin ku'din...
21/10/2023

HOTO:

Lokacin da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da Gwamna Abba Kabir Yusuf suke raba dollar Amurka $200 kwatankaacin ku'din naira N200,000 ga ko wanne dalibi cikin daliban da Gwamnatin Jihar Kano ta dauki nauyin turasu Zuwa kasar India domin karo karatu.

An rabawa daliban ku'din ne amatsayin ku'din Shan ruwa a hanya koda zasu ga Wani Abu a hanya suyi sha'awa.

MÚHAWARA: A Cìkìn Manyan Ƴan Síyasar Nájeriya, Wanéné Kuké Túnanìn Céwa Zai Iya Tara Irín Waɗannan Mútanen Haka, Ba Tare...
21/10/2023

MÚHAWARA: A Cìkìn Manyan Ƴan Síyasar Nájeriya, Wanéné Kuké Túnanìn Céwa Zai Iya Tara Irín Waɗannan Mútanen Haka, Ba Tare Da Ya Basu Kó Sisin Kwabó Ba, Saí Dan Sabóda Ƙaunar Da Súké Masa ?

Address

Malumfashi

Telephone

+2348137180558

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Malumfashi Reporters:

Share