Malumfashi Media Center

Malumfashi Media Center Exclusive News

🚨 Gwamna Radda Ya Jagoranci Zaman Gaggawa Kan Matsalar Tsaro a Jihar Katsina 🚨A yau, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, , ...
06/04/2026

🚨 Gwamna Radda Ya Jagoranci Zaman Gaggawa Kan Matsalar Tsaro a Jihar Katsina 🚨

A yau, Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, , ya jagoranci wani muhimmin zaman gaggawa na masu ruwa da tsaki a bangaren tsaro, domin tattauna hanyoyin shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassan jihar.

Zaman ya samu halartar manyan jami’an tsaro daga hukumomin gwamnati daban-daban, shugabannin ƙananan hukumomin da matsalar tsaro ta fi shafa, da kuma sauran masu ruwa da tsaki a bangaren tsaro. Taron ya mayar da hankali ne kan nazarin halin da ake ciki a halin yanzu tare da samar da sabbin dabaru da hanyoyin inganta tsaro a fadin jihar.

A yayin zaman, Gwamna Radda ya jaddada kudirin gwamnatinsa na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da hada kai da dukkan hukumomin tsaro domin kawo karshen matsalolin da s**a addabi yankunan da abin ya shafa.

Haka kuma, mahalarta taron sun gabatar da shawarwari masu muhimmanci kan yadda za a kara inganta hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, shugabannin al’umma, da kuma hukumomin ƙananan hukumomi domin dakile ayyukan masu tayar da hankali.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakan da s**a dace domin dawo da zaman lafiya mai dorewa a dukkan sassan jihar Katsina.

🛡️ Al’umma na ci gaba da fatan irin wadannan matakai za su taimaka wajen kara karfafa tsaro da zaman lafiya a jihar baki daya.




🚨 Gwamnan Jihar Katsina ya kai ziyara kauyen Sayaya bayan harin ‘yan bindigaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Rad...
05/04/2026

🚨 Gwamnan Jihar Katsina ya kai ziyara kauyen Sayaya bayan harin ‘yan bindiga

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kai ziyara kauyen Sayaya da ke Karamar Hukumar Matazu biyo bayan harin da ‘yan bindiga s**a kai wa al’ummar yankin.

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun kai farmaki garin, inda s**a kai hari ofishin ‘yan sanda, lamarin da ya yi sanadiyyar rasuwar jami’in dan sanda guda. Haka kuma sun lalata Cibiyar Kula da Lafiya ta Farko (PHC) tare da kwashe kayayyaki daga shaguna da dama a garin. 🏥💔

Da isarsa Sayaya, Gwamna Radda ya zagaya wuraren da harin ya shafa domin tantance irin barnar da aka yi. Ya kuma gana da al’ummar yankin tare da jajanta musu kan wannan mummunan lamari. 🤝

A yayin ziyarar, Gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga jami’an ‘yan sanda, musamman DPO da sauran jami’ai, bisa rasuwar dan sandan da ya rasa ransa, tare da jajantawa iyalansa da daukacin al’ummar yankin.

Sannan Gwamnan ya bayar da umarnin kara tura jami’an tsaro domin karfafa tsaro a garin Sayaya da kewaye, tare da tabbatar da daukar matakan da s**a dace don kare rayuka da dukiyoyin al’umma. 🛡️

Allah Ya jikan wanda ya rasu, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai dorewa a jihar Katsina da kasa baki daya. 🤲

🚨 SANARWA GA AL’UMMAR JIHAR KATSINAGwamnatin Jihar Katsina ta yi Allah-wadai da kisan da ya faru a ƙauyen Kokami, ta tab...
05/04/2026

🚨 SANARWA GA AL’UMMAR JIHAR KATSINA

Gwamnatin Jihar Katsina ta yi Allah-wadai da kisan da ya faru a ƙauyen Kokami, ta tabbatar da cewa zaman lafiya ya dawo.

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana takaicinta kan rikicin da ya faru a ƙauyen Kokami na Ƙaramar Hukumar Danja a ranar 4 ga Afrilu, 2026, wanda ya samo asali daga saɓani tsakanin mutane biyu kan sayen garri da ruwan leda.

Rikicin ya kai ga rasuwar Ibrahim Khalil Auwal bayan an soka masa wuka. Daga bisani kuma wasu fusatattun matasa sun kashe wanda ake zargi da aikata laifin tare da ƙona gawarsa.

Gwamnati ta jaddada cewa wannan rikici ba rikicin addini ko ƙabila ba ne, illa rikicin kashin kai. Ta kuma tabbatar da cewa za a hukunta duk masu hannu a lamarin.

An tura jami’an tsaro yankin, kuma zaman lafiya ya dawo. Gwamnati ta buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da gujewa yaɗa jita-jita.

Mai Girma Gwamna Malam Dikko Umaru Radda ya miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan tare da kira ga shugabannin al’umma da su taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a jihar 🤲.

✍️ Dr. Nasir Mu’azu
Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida
Jihar Katsina

CI GABA DA SAMAWA MATASA AIKI A MATAKIN GWAMNATIN TARAYYA. Distinguished Senator Muntari Dandutse (Chairman, Senate Comm...
04/04/2026

CI GABA DA SAMAWA MATASA AIKI A MATAKIN GWAMNATIN TARAYYA.

Distinguished Senator Muntari Dandutse (Chairman, Senate Committee on TETFUND) ya kara samar wa matasa guda shida (6) daga yankin Funtua Zone guraben aikin yi a Jami’ar Tarayya ta Bayero University Kano (BUK).

Wannan na daga cikin irin kokarin da yake ci gaba da yi wajen samo damar aiki ga matasa daga mazabarsa a matakin Gwamnatin Tarayya.

Haka kuma, wannan karin guraben aikin yi guda shida kari ne a kan sama da mutum dari (100) da s**a riga s**a amfana da irin wannan tsari na tallafawa matasa domin gina rayuwarsu da kuma karfafa ci gaban al’umma.

Muna fatan Allah Ya ci gaba da taimaka masa wajen samar da karin damammaki ga matasa domin amfanin al’umma baki daya.

Wane kira gareku ga Sen. Muntari Dandutse?

Da sunan ALLAH mai rahama, mai jin kai.
01/04/2026

Da sunan ALLAH mai rahama, mai jin kai.

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Kameel L Ayuba, Abdulyasar Isah, Salim Mustapha Sani, Sen...
01/04/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Kameel L Ayuba, Abdulyasar Isah, Salim Mustapha Sani, Senior Man, Ummulkairi Abdullahi, Zaenab Rabiu, Ibrahim Aminu Mlf, Ibrahim Amina

SHUGABAN TINUBU YA BA DA UMARNIN ƘARFAFA TSARO A JIHAR KATSINA BAYAN ZUWAN TAWAGAR GWAMNA RADDA FADAR A*O ROCK. Shugaban...
02/09/2025

SHUGABAN TINUBU YA BA DA UMARNIN ƘARFAFA TSARO A JIHAR KATSINA BAYAN ZUWAN TAWAGAR GWAMNA RADDA FADAR A*O ROCK.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin gaggawa na ƙarfafa tsaro a Jihar Katsina bayan ganawar da ya yi da Gwamna Malam Dikko Umaru Radda tare da wata babbar tawaga da ta nemi agajin gwamnatin tarayya kan ƙarin tabarbarewar tsaro a jihar.

Shugaban ya umarci duka hukumomin tsaro da su sake duba dabarun yakar ‘yan ta’adda tare da ƙara tura jiragen leƙen asiri na sama (air drones), sannan ya amince da sake shirin tura dakarun ƙasa tsakanin Katsina da iyakokin jihohi domin fatattakar ‘yan ta’adda.

> “Yau na umarci hukumomin tsaro su sake karfafa dabarun da suke amfani da su. A ƙara tura jiragen leƙen asiri, sannan idan akwai buƙatar motsa dakarun tsaro tsakanin Katsina da sauran iyakokin, a yi hakan. Kuma za su ba ni rahoto nan da gobe,” in ji Shugaba Tinubu yayin taron.

Shugaban ya bayyana cewa kalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta na da matuƙar girma, inda ya ce:

> “Matsalolin tsaro da muke fuskanta a ƙasar nan sun yi yawa. Mun gaji matsalolin iyakoki marasa ƙarfi, abin da ya k**ata tun da farko a gyara. Amma wannan ƙalubale ne da dole mu fuskanta kuma muna fuskantarsa.”

Ya ƙara da cewa dakarun ƙasa za su ƙara matsa kaimi wajen kawar da miyagun ƙungiyoyi daga cikin al’umma:

> “Dakarun ƙasa suna nan, kuma za mu ci gaba da fatattakar su.”

Shugaba Tinubu ya kuma bayyana aniyar gwamnatin sa na kafa ‘yan sandan jihohi a matsayin ɗaya daga cikin dabarun magance matsalolin tsaro.

> “Dole mu kare ‘ya’yanmu, mutanenmu, abincinmu, wuraren ibada da wuraren hutu. Ba za mu bari su tsoratar da mu ba,” in ji shi.

A nasa jawabin, Gwamna Radda ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa bisa manufar bude ƙofa da tallafin da yake bai wa Katsina a kowane lokaci:

> “Shugaba ya nuna kansa ɗan Katsina ne. Mun gode matuƙa bisa kulawar sa kan matsalolin tsaro a jiharmu,” in ji gwamnan.

A farkon taron, mai martaba Sarkin Katsina wanda Waziri na Katsina, Sanata Ibrahim Ida, ya wakilta, ya roƙi Shugaban Ƙasa da ya tabbatar da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro tare da kafa bataliyar soja da kuma rundunar ‘yan sandan MOPOL a kudancin jihar.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta kashe fiye da Naira biliyan 40 wajen tallafawa tsaro duk da ƙarancin kuɗaɗenta, inda ya roƙi gwamnatin tarayya ta maido mata da wani ɓangare tare da tallafa wa al’umman da s**a shiga cikin bala’in.

Tawagar da ta raka Gwamna Radda ta haɗa da mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruq Lawal Jobe; Kakakin majalisar dokoki ta jiha, Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura; tsohon gwamna Aminu Bello Masari; dukkan Sanatocin Katsina da wakilan majalisar tarayya.

Haka kuma akwai Ministan Ayyuka da Gidaje, Injiniya Ahmed Musa Dangiwa; Ministan Al’adu, Harshe da Tattalin Arzikin Kirkira, Barrista Hannatu Musa Musawa; Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsara Manufofi, Hajiya Hadiza Bala Usman; da Jagoran AUDA-NEPAD a Najeriya, Jabiru Salisu Tsauri.

Sauran su ne: wasu mambobin majalisar zartarwa ta jihar, Mai martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Faruq Umar, Malam Yakubu Musa (Sautus Sunnah), tsohon mataimakin gwamnan Katsina Alhaji Tukur Jikamshi, Malam Gambo (Babban Limamin Masallacin Juma’a na Katsina), da attajirin kasuwanci Alhaji Dahiru Barau Mangal.

Wannan taro na A*o Rock ya kasance wani mataki na dabarun karshe wajen kawo ƙarshen matsalar ‘yan bindiga da ta addabi jihar Katsina da sauran yankunan Arewa maso Yamma.

SABON POSTING NA PRINCIPALS A FADIN KATSINA. Gwamnatin Jihar Katsina karkashin Ma’aikatar Ilimi ta sanar da sabon sauye-...
02/09/2025

SABON POSTING NA PRINCIPALS A FADIN KATSINA.

Gwamnatin Jihar Katsina karkashin Ma’aikatar Ilimi ta sanar da sabon sauye-sauyen shugabannin makarantu (principals) a manyan makarantu na sakandare a fadin jihar.

Wannan mataki, a cewar ma’aikatar, na daga cikin shirin gwamnati na inganta harkar ilimi, da kuma tabbatar da cewa an samar da shugabanni masu kwarewa da jajircewa wajen tafiyar da makarantun sakandare.

Hukumar ta ce, an yi la’akari da ƙwarewa, cancanta da kuma nagartar shugabannin makarantu wajen wannan sabon posting, domin tabbatar da cewa ɗalibai da malamai sun samu jagoranci nagari.

An bayyana cewa wannan sauyin zai taimaka wajen kawo sabbin dabaru, kuzari da kuma ingantacciyar tafiyar da harkokin makarantu a fadin Katsina.

A karshe, Ma’aikatar Ilimi ta yi kira ga dukkan sabbin shugabannin makarantun da su ɗauki wannan amanar da muhimmanci tare da yin aiki tukuru domin ci gaban ilimi a Jihar Katsina.

NASARA DAGA ALLAH: ‘Yan Sanda Sun K**a Matasan Da Ke Safarar Manyan Mak**ai Zuwa ‘Yan Ta’addaDaga Ingawa, Jihar Katsina‘...
02/09/2025

NASARA DAGA ALLAH: ‘Yan Sanda Sun K**a Matasan Da Ke Safarar Manyan Mak**ai Zuwa ‘Yan Ta’adda

Daga Ingawa, Jihar Katsina

‘Yan sanda a Jihar Katsina sun samu gagarumar nasara a fafutukarsu na yaki da ta’addanci bayan da s**a k**a wasu matasa biyu da ke safarar manyan mak**ai zuwa ga ‘yan ta’adda a daji.

An k**a matasan ne da sanyin safiya, misalin karfe 4:35 na asuba, a karamar hukumar Ingawa, yayin da suke kan hanyar jigilar mak**an zuwa karamar hukumar Safana, kafin a kai su cikin daji ga ‘yan ta’addan.

Matasan da aka k**a sun hada da:

Abdulsalam Muhammad, mai shekaru 25

Aminu Mamman, mai shekaru 23

Rahoton ya tabbatar da cewa an k**a su ne dauke da bindiga mai sarrafa kanta wacce ake iya harbo jirgin sama da ita, tare da harsashi sama da dubu daya (1,000). An gano cewa mak**an sun taho ne a cikin mota kirar Volkswagen Golf mai launin shudi (blue) tare da lambar rajista RSH 528 BY ABJ.

Wannan na daga cikin ci gaban da hukumomin tsaro ke samu a kokarinsu na dakile ayyukan ta’addanci a yankin arewa maso yamma, musamman a jihar Katsina da kewaye.

Wata majiya daga rundunar ‘yan sandan jihar ta bayyana cewa, bincike na ci gaba domin gano sauran mutanen da ke da alaka da safarar mak**an.

Al’umma da dama sun bayyana wannan a matsayin babbar nasara, inda s**a yi addu’ar Allah ya cigaba da tona asirin masu taimaka wa ‘yan ta’adda, tare da tabbatar da zaman lafiya a kasar nan.

Address

Malumfashi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Media Center posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Malumfashi Media Center:

Share