Malumfashi Post

Malumfashi Post Exclusive News

SHUGABAN TINUBU YA BA DA UMARNIN ƘARFAFA TSARO A JIHAR KATSINA BAYAN ZUWAN TAWAGAR GWAMNA RADDA FADAR A*O ROCK. Shugaban...
02/09/2025

SHUGABAN TINUBU YA BA DA UMARNIN ƘARFAFA TSARO A JIHAR KATSINA BAYAN ZUWAN TAWAGAR GWAMNA RADDA FADAR A*O ROCK.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin gaggawa na ƙarfafa tsaro a Jihar Katsina bayan ganawar da ya yi da Gwamna Malam Dikko Umaru Radda tare da wata babbar tawaga da ta nemi agajin gwamnatin tarayya kan ƙarin tabarbarewar tsaro a jihar.

Shugaban ya umarci duka hukumomin tsaro da su sake duba dabarun yakar ‘yan ta’adda tare da ƙara tura jiragen leƙen asiri na sama (air drones), sannan ya amince da sake shirin tura dakarun ƙasa tsakanin Katsina da iyakokin jihohi domin fatattakar ‘yan ta’adda.

> “Yau na umarci hukumomin tsaro su sake karfafa dabarun da suke amfani da su. A ƙara tura jiragen leƙen asiri, sannan idan akwai buƙatar motsa dakarun tsaro tsakanin Katsina da sauran iyakokin, a yi hakan. Kuma za su ba ni rahoto nan da gobe,” in ji Shugaba Tinubu yayin taron.

Shugaban ya bayyana cewa kalubalen tsaro da ƙasar ke fuskanta na da matuƙar girma, inda ya ce:

> “Matsalolin tsaro da muke fuskanta a ƙasar nan sun yi yawa. Mun gaji matsalolin iyakoki marasa ƙarfi, abin da ya k**ata tun da farko a gyara. Amma wannan ƙalubale ne da dole mu fuskanta kuma muna fuskantarsa.”

Ya ƙara da cewa dakarun ƙasa za su ƙara matsa kaimi wajen kawar da miyagun ƙungiyoyi daga cikin al’umma:

> “Dakarun ƙasa suna nan, kuma za mu ci gaba da fatattakar su.”

Shugaba Tinubu ya kuma bayyana aniyar gwamnatin sa na kafa ‘yan sandan jihohi a matsayin ɗaya daga cikin dabarun magance matsalolin tsaro.

> “Dole mu kare ‘ya’yanmu, mutanenmu, abincinmu, wuraren ibada da wuraren hutu. Ba za mu bari su tsoratar da mu ba,” in ji shi.

A nasa jawabin, Gwamna Radda ya nuna godiya ga Shugaban Ƙasa bisa manufar bude ƙofa da tallafin da yake bai wa Katsina a kowane lokaci:

> “Shugaba ya nuna kansa ɗan Katsina ne. Mun gode matuƙa bisa kulawar sa kan matsalolin tsaro a jiharmu,” in ji gwamnan.

A farkon taron, mai martaba Sarkin Katsina wanda Waziri na Katsina, Sanata Ibrahim Ida, ya wakilta, ya roƙi Shugaban Ƙasa da ya tabbatar da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro tare da kafa bataliyar soja da kuma rundunar ‘yan sandan MOPOL a kudancin jihar.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta kashe fiye da Naira biliyan 40 wajen tallafawa tsaro duk da ƙarancin kuɗaɗenta, inda ya roƙi gwamnatin tarayya ta maido mata da wani ɓangare tare da tallafa wa al’umman da s**a shiga cikin bala’in.

Tawagar da ta raka Gwamna Radda ta haɗa da mataimakin gwamnan jihar, Malam Faruq Lawal Jobe; Kakakin majalisar dokoki ta jiha, Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura; tsohon gwamna Aminu Bello Masari; dukkan Sanatocin Katsina da wakilan majalisar tarayya.

Haka kuma akwai Ministan Ayyuka da Gidaje, Injiniya Ahmed Musa Dangiwa; Ministan Al’adu, Harshe da Tattalin Arzikin Kirkira, Barrista Hannatu Musa Musawa; Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsara Manufofi, Hajiya Hadiza Bala Usman; da Jagoran AUDA-NEPAD a Najeriya, Jabiru Salisu Tsauri.

Sauran su ne: wasu mambobin majalisar zartarwa ta jihar, Mai martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Faruq Umar, Malam Yakubu Musa (Sautus Sunnah), tsohon mataimakin gwamnan Katsina Alhaji Tukur Jikamshi, Malam Gambo (Babban Limamin Masallacin Juma’a na Katsina), da attajirin kasuwanci Alhaji Dahiru Barau Mangal.

Wannan taro na A*o Rock ya kasance wani mataki na dabarun karshe wajen kawo ƙarshen matsalar ‘yan bindiga da ta addabi jihar Katsina da sauran yankunan Arewa maso Yamma.

SABON POSTING NA PRINCIPALS A FADIN KATSINA. Gwamnatin Jihar Katsina karkashin Ma’aikatar Ilimi ta sanar da sabon sauye-...
02/09/2025

SABON POSTING NA PRINCIPALS A FADIN KATSINA.

Gwamnatin Jihar Katsina karkashin Ma’aikatar Ilimi ta sanar da sabon sauye-sauyen shugabannin makarantu (principals) a manyan makarantu na sakandare a fadin jihar.

Wannan mataki, a cewar ma’aikatar, na daga cikin shirin gwamnati na inganta harkar ilimi, da kuma tabbatar da cewa an samar da shugabanni masu kwarewa da jajircewa wajen tafiyar da makarantun sakandare.

Hukumar ta ce, an yi la’akari da ƙwarewa, cancanta da kuma nagartar shugabannin makarantu wajen wannan sabon posting, domin tabbatar da cewa ɗalibai da malamai sun samu jagoranci nagari.

An bayyana cewa wannan sauyin zai taimaka wajen kawo sabbin dabaru, kuzari da kuma ingantacciyar tafiyar da harkokin makarantu a fadin Katsina.

A karshe, Ma’aikatar Ilimi ta yi kira ga dukkan sabbin shugabannin makarantun da su ɗauki wannan amanar da muhimmanci tare da yin aiki tukuru domin ci gaban ilimi a Jihar Katsina.

NASARA DAGA ALLAH: ‘Yan Sanda Sun K**a Matasan Da Ke Safarar Manyan Mak**ai Zuwa ‘Yan Ta’addaDaga Ingawa, Jihar Katsina‘...
02/09/2025

NASARA DAGA ALLAH: ‘Yan Sanda Sun K**a Matasan Da Ke Safarar Manyan Mak**ai Zuwa ‘Yan Ta’adda

Daga Ingawa, Jihar Katsina

‘Yan sanda a Jihar Katsina sun samu gagarumar nasara a fafutukarsu na yaki da ta’addanci bayan da s**a k**a wasu matasa biyu da ke safarar manyan mak**ai zuwa ga ‘yan ta’adda a daji.

An k**a matasan ne da sanyin safiya, misalin karfe 4:35 na asuba, a karamar hukumar Ingawa, yayin da suke kan hanyar jigilar mak**an zuwa karamar hukumar Safana, kafin a kai su cikin daji ga ‘yan ta’addan.

Matasan da aka k**a sun hada da:

Abdulsalam Muhammad, mai shekaru 25

Aminu Mamman, mai shekaru 23

Rahoton ya tabbatar da cewa an k**a su ne dauke da bindiga mai sarrafa kanta wacce ake iya harbo jirgin sama da ita, tare da harsashi sama da dubu daya (1,000). An gano cewa mak**an sun taho ne a cikin mota kirar Volkswagen Golf mai launin shudi (blue) tare da lambar rajista RSH 528 BY ABJ.

Wannan na daga cikin ci gaban da hukumomin tsaro ke samu a kokarinsu na dakile ayyukan ta’addanci a yankin arewa maso yamma, musamman a jihar Katsina da kewaye.

Wata majiya daga rundunar ‘yan sandan jihar ta bayyana cewa, bincike na ci gaba domin gano sauran mutanen da ke da alaka da safarar mak**an.

Al’umma da dama sun bayyana wannan a matsayin babbar nasara, inda s**a yi addu’ar Allah ya cigaba da tona asirin masu taimaka wa ‘yan ta’adda, tare da tabbatar da zaman lafiya a kasar nan.

GWAMNATIN KATSINA TA BAIWA WANI MATASHI TALLAFIN NAIRA MILIYAN 35 Gwamnatin jihar Katsina ta bayar da tallafin naira mil...
30/08/2025

GWAMNATIN KATSINA TA BAIWA WANI MATASHI TALLAFIN NAIRA MILIYAN 35

Gwamnatin jihar Katsina ta bayar da tallafin naira miliyan 35 ga wani matashi mai suna Usman Musa, wanda ya rasa rabin hannunsa yayin da yake tsare a gidan gyaran hali da akida ta ƙananan yara, watau Babbar Ruga Reformatory Center Katsina.

An mika tallafin ne ta hannun Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Barrister Abdullahi Garba Faskari, a madadin Gwamnan jihar, Malam Dikko Umar Radda, PhD, a yayin wani taro da aka gudanar tare da mambobin kwamitin da gwamnati ta kafa domin binciken lamarin.

Barrister Faskari ya bayyana cewa wannan tallafi alama ce ta jajircewar gwamnatin Malam Dikko Radda wajen sauraren ƙorafe-ƙorafen jama’a tare da kyautata musu. Ya bukaci matashin da ya yi amfani da tallafin yadda ya k**ata tare da kasancewa mai kyakkyawar ɗabi’a. Haka kuma ya shawarce shi da ya ɗauki abin da ya same shi a matsayin ƙaddarar Allah.

YADDA ZA A KASANCE DA TALLAFIN

Daga cikin wannan tallafi na miliyan 35:

Naira miliyan 8 za a yi amfani da ita wajen samar masa da hannu na zamani (bionic arm).

Naira miliyan 10 za a gina masa gida.

Naira miliyan 4 za a bude masa shago da kayayyakin kasuwanci irin su shadda, atamfa, takalma, sarƙoƙi da leshi.

Naira miliyan 10 kuma za a saka a kayayyakin kasuwancin shagon.

Sai kuma Naira miliyan 3 da za a ajiye masa a matsayin kudade na ko-ta-kwana.

INGANTA BABBAR RUGA REFORMATORY CENTER

Sakataren gwamnatin ya kara da cewa gwamnati na da niyyar inganta cibiyar gyaran hali ta Babbar Ruga domin ta dace da zamani, ta hanyar samar da kayan koyon sana’o’i da sauran muhimman kayayyaki da ake bukata.

RAHOTON KWAMITIN

A nasa jawabin, mai baiwa gwamna shawara a bangaren kiwon lafiya mai zurfi, Alhaji Umar Mammadau, ya ce kwamitin da aka kafa domin binciken lamarin ya yi aiki tukuru tare da gabatar da rahoto ga gwamnati. Ya bayyana cewa gwamna Radda ya amince da shawarwarin kwamitin da kuma rokon da aka gabatar a madadin matashin.

GODIYAR IYALAI

A madadin iyalan matashin, Abubakar Musa ya gode wa gwamnatin jiha da kwamitin bisa wannan tallafi tare da bayar da tabbacin cewa za su yi kyakkyawan amfani da shi.

Gwamnatin Katsina Ta Amince da Tura Babura 700 da Motocin Hilux 20 da Kuma Buffalo zuwa Yankunan Da Babu zaman lafiya. G...
29/08/2025

Gwamnatin Katsina Ta Amince da Tura Babura 700 da Motocin Hilux 20 da Kuma Buffalo zuwa Yankunan Da Babu zaman lafiya.

Gwamnatin Jihar Katsina ta amince da tura babura 700, motocin Hilux 20 da kuma motocin Buffalo zuwa wasu yankuna masu wahalar isa da kuma wuraren da ake samun tashin hankali, ciki har da kauyen Mantau na ƙaramar hukumar Malumfashi da sauran wurare.

Wannan mataki na dabarun tsaro zai baiwa jami’an tsaro damar shiga cikin duwatsu da dazuzzukan da ‘yan bindiga ke fakewa, tare da sauƙaƙa motsi da ƙarfafa ayyukan tabbatar da zaman lafiya a faɗin jihar.

A cewar gwamnatin jihar, wannan shiri na daga cikin manyan matakan da ake ɗauka domin magance matsalar tsaro da tabbatar da dorewar zaman lafiya ga al’ummar Katsina.

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa za a gudanar da jarabawar tantance daliban da za su fara karatu a sabbin makaran...
29/08/2025

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa za a gudanar da jarabawar tantance daliban da za su fara karatu a sabbin makarantun gwamnati na musamman da ake ginawa a Radda, Jikamshi da Dumurkul.

Rahotanni sun nuna cewa dalibai 2,172 daga cikin ’ya’yan talakawa ne za su zauna jarabawar, inda kuma za a zabi dalibai 996 da s**a fi hazaka domin karatu a makarantun.

An bayyana manyan cibiyoyin da za a gudanar da jarabawar sun hada da:

1. Katsina College Katsina
2. Government Girls Secondary School Funtua
3. Government Day Secondary School Daura
4. Government Pilot Secondary School Dutsinma
5. Government Unity Secondary School Malumfashi
6. Government Day Secondary School Kankia
7. Government Day Secondary School Mani

Gwamnati ta ce dukkan daliban da za a karɓa za su ci moriyar ilimi kyauta tun daga kayan makaranta (uniform), kwamfutoci, wuraren zama, da kuma malamai na musamman da aka tanadar domin tabbatar da ingantaccen ilimi.

Mai girma Gwamna ya jaddada muhimmancin tabbatar da adalci a yayin gudanar da jarabawar, tare da jan hankalin duk masu ruwa da tsaki da su tabbatar an fitar da dalibai masu hazaka domin cigaban jihar Katsina a nan gaba.

INA JIN RADADIN KU A ZUCIYATA” – GWAMNA RADDA YA FADA WA AL'UMMAR MANTAU DA BALA’IN ’YAN BINDIGA YA SHAFA — Ya yi alkawa...
27/08/2025

INA JIN RADADIN KU A ZUCIYATA” – GWAMNA RADDA YA FADA WA AL'UMMAR MANTAU DA BALA’IN ’YAN BINDIGA YA SHAFA

— Ya yi alkawarin gina makaranta, asibiti, gyaran masallaci da tallafin kudi ga iyalan da abin ya shafa

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kai ziyarar ta’aziyya zuwa kauyen Mantau a karamar hukumar Malumfashi, inda ya jajanta wa iyalan wadanda s**a rasa rayuka sak**akon harin ’yan bindiga a lokacin sallar asubahi.

Gwamnan, wanda ya dakatar da jinyar da yake yi a ƙasashen waje domin ya halarci wajen, ya bayyana cewa gwamnatin jiharsa za ta baiwa kowace gida da abin ya shafa tallafin naira dubu dari biyar (₦500,000) nan take, tare da aiwatar da muhimman ayyukan raya al’umma a kauyen.

> “Rayuwar dan Adam abu ne mai tsarki, ba wasa ba ce. Mun zo ne domin mu yi jaje tare da ku, mu raba damuwa da ku,” in ji Gwamna Radda.

Ya kara da cewa:

> “Abin da kuke ji a zuciya, shi nake ji a raina. Ni ma na rasa dan uwa a dalilin matsalar tsaro. Wannan shi ne dalilin da ya sa na kuduri aniyar ci gaba da daukar matakai na karfi domin dawo da zaman lafiya a jihar nan.”

Gwamna Radda ya umurci shugaban karamar hukumar Malumfashi da ya yi aiki tare da masu sarauta wajen shirya matasa domin horar da su a fannin kare al’ummarsu. Haka kuma ya tabbatar wa jama’a cewa ana shirin tura bataliyar soja a yankin Malumfashi domin tabbatar da tsaro.

Daga cikin muhimman ayyuka da ya yi alkawarin aiwatarwa akwai: gina makaranta zamani, gina asibiti, gyaran masallacin kauyen gaba ɗaya, da kuma samar da hanyoyin mota don sauƙaƙa isowar jami’an tsaro cikin gaggawa.

> “Gwamnati za ta sake gina duk gidajen da aka lalata a harin nan,” in ji shi.

Haka kuma, gwamnan ya yi gargadi ga wadanda suke neman amfani da matsalar tsaro domin buga siyasa:

> “Batun tsaro batun ceton rayukan mutane ne, ba siyasa ba. Duk wanda ya tsaya a kan hanyar zaman lafiya, za mu fuskance shi, kuma In Sha Allah, za mu yi nasara.”

A jawabinsa yayin ziyarar, Galadiman Katsina, Mai Shari’a Sadiq Abdullahi Mahuta, ya yaba da jajircewar gwamnan wajen yaki da matsalar tsaro. Haka nan, Magajin Garin Karfi, Malam Wa’alamu Garba, ya nuna godiya ga Gwamnan bisa kin ci gaba da jinya a waje, ya dawo domin ya kwantar da hankalin al’ummarsa.

Tawagar da ta raka gwamnan sun hada da:

Sanata Muntari Dandutse (Funtua Zone)

Dan Majalisar Tarayya Hon. Aminu Ibrahim (Malumfashi/Kafur)

Mai Bai wa Shawara kan Community Watch Corps, Alhaji Yusuf Ibrahim Safana

Galadiman Katsina kuma Hakimin Malumfashi

Wasu Kwamishinonin Jiha

Shugaban ’Yan sanda na Jihar Katsina da Darakta Janar na DSS

Shugabannin tsaro ciki har da DPO na Malumfashi

Sarakunan gargajiya, shugabannin kananan hukumomi daga Funtua Zone

Jiga-jigan jam’iyyar siyasa daga matakin jiha da karamar hukuma.

MD KATSINA MD KATSINA STATE WATER BOARD YA MIKA MOTA MAI SULKE GA AL'UMMAR KARFI A yau Lahadi, Babban Daraktan Hukumar R...
24/08/2025

MD KATSINA MD KATSINA STATE WATER BOARD YA MIKA MOTA MAI SULKE GA AL'UMMAR KARFI

A yau Lahadi, Babban Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Dr. Tukur Tingilin ya mika mota mai sulke ga al’ummar garin Karfi da ke karamar hukumar Malumfashi, domin taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da ta’addanci.

Mika wannan mota an gudanar da shi ne ta hannun Magajin Garin Karfi, Alhaji Wa’alamu Garba, tare da rakiyar DPO na Malumfashi da kuma jami’an ’yan sanda MOPOL.

Yayin bikin mika motar, Dr. Tingilin ya tabbatar wa al’ummar garin Karfi cewa, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, yana ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen magance matsalar tsaro da ta addabi jama’a. Ya ce gwamnati ta dauki duk matakan da s**a dace don dakile ayyukan ’yan ta’adda tare da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

A nasa jawabin, Magajin Garin Karfi, Alhaji Wa’alamu Garba, ya mika godiya ga MD bisa wannan namijin kokari na kawo sauyi a sha’anin tsaro. Haka kuma ya yaba da irin gudummawar da yake bayarwa a fannoni daban-daban na rayuwa, ciki har da ilimi da lafiya, tare da yi masa fatan alheri.

A wajen bikin, an samu halartar manyan baki ciki har da Shugaban Jihar na Dikko Radda House-to-House Campaign Organization, Alhaji Saifiddeen Yakubu Karfi, da kuma Sakataren Tsara Ayyuka, Zaharaddeen Sule.
State Water Board Ya Mika Mota Mai Sulke Ga Al’ummar Karfi

A yau Lahadi, Babban Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina, Dr. Tukur Tingilin, ya mika mota mai sulke ga al’ummar garin Karfi da ke karamar hukumar Malumfashi, domin taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da ta’addanci.

Mika wannan mota an gudanar da shi ne ta hannun Magajin Garin Karfi, Alhaji Wa’alamu Garba, tare da rakiyar DPO na Malumfashi da kuma jami’an ’yan sanda MOPOL.

Yayin taron mika motar, Dr. Tingilin ya tabbatar wa al’ummar garin Karfi cewa, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, yana ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen magance matsalar tsaro da ta addabi jama’a. Ya ce gwamnati ta dauki duk matakan da s**a dace don dakile ayyukan ’yan ta’adda tare da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

A nasa jawabin, Magajin Garin Karfi, Alhaji Wa’alamu Garba, ya mika godiya ga MD bisa wannan namijin kokari na kawo sauyi a sha’anin tsaro. Haka kuma ya yaba da irin gudummawar da yake bayarwa a fannoni daban-daban na rayuwa, ciki har da ilimi da lafiya, tare da yi masa fatan alheri.

A wajen taron, an samu halartar manyan baki ciki har da Shugaban Jihar na Dikko Radda House-to-House Campaign Organization, Alhaji Saifiddeen Yakubu Karfi, da kuma Sakataren Tsara Ayyuka, Zaharaddeen Sule.

Gwamnatin Katsina Ta Ce Ta Kashe Biliyan 36 a Fannin TsaroGwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa ta kashe kimanin Naira...
24/08/2025

Gwamnatin Katsina Ta Ce Ta Kashe Biliyan 36 a Fannin Tsaro

Gwamnatin Jihar Katsina ta bayyana cewa ta kashe kimanin Naira biliyan 36 domin inganta tsaro a jihar.

Kwamishinan tsaro na cikin gida, Dr. Nasir Danmusa, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a gidan gwamnati, jim kaɗan bayan kammala taron masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro.

A cewar kwamishinan, gwamnatin jihar ta sayi motocin sulke na APC guda 42 tare da wasu muhimman kayayyakin yaki domin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar daga hare-haren ‘yan bindiga.

“Ko a safiyar Asabar dinnan mun samu nasarar ceto mutane 76 da aka yi garkuwa da su a dajin Fauwa,” in ji Dr. Danmusa.

Ya ce kokarin gwamnati ya fara kawo sauki, inda rahotanni ke nuna cewa hare-haren ‘yan bindiga a wasu sassan jihar sun ragu.

Sai dai duk da wannan cigaba, jihar Katsina na daga cikin jihohin Arewa da ke fama da matsalar tsaro. A makon da ya gabata ne aka kashe mutane fiye da 27 a kauyen Gidan Mantau, karamar hukumar Malumfashi, sak**akon wani mummunan hari da ‘yan bindiga s**a kai.

ZA A FARA BIYAN KUƊIN RRR CCT A MALUMFASHI – HUKUMAR TA FITAR DA JADAWALIN YANDA AIKIN ZAI GUDANA. Malumfashi, Katsina S...
23/08/2025

ZA A FARA BIYAN KUƊIN RRR CCT A MALUMFASHI – HUKUMAR TA FITAR DA JADAWALIN YANDA AIKIN ZAI GUDANA.

Malumfashi, Katsina State – Hukumar bayar da tallafin CCT ta sanar da fara biyan kuɗaɗen shirin RRR CCT ga al’ummar Karamar Hukumar Malumfashi. An tsara jadawalin biyan kuɗin cikin tsari na kwanaki biyar domin sauƙaƙa wa jama’a da kuma kauce wa cunkoso a wuraren karɓa.

A cewar sanarwar, biyan kuɗin zai gudana k**ar haka:

Rana ta 1 – Malumfashi A
Unguwanni sun haɗa da: Arewa 1 & 2, Dan Fili, Dan Rimi, Dan Tafi, Gangarawa, Gwamatsawa, Halilu B, Hayin Gada, Hayin Majema, Hayin Maji Dadi, Kan Tsauni, Kofar Fada, Tsohuwar Kasuwa, Tudun Kura Danbilago, Unguwar Dan Dagazau, Unguwar Dawo, Unguwar Garba, Unguwar Makera, Unguwar Sambo da Unguwar Sodangi.

Rana ta 2 – Malumfashi B
Za a gudanar da biyan kuɗi ga jama’ar Tudun Wada A1 da Tudun Wada B.

Rana ta 3 – Malumfashi B
Wannan rana ta ƙunshi Tudun Wada B2 da Unguwar Aliyu A.

Rana ta 4 – Malumfashi B
Unguwannin da za su karɓi kuɗi sun haɗa da Unguwar Aliyu B, Unguwar Aliyu B2, Unguwar Dan Kuro da Unguwar Dutse.

Rana ta 5 – Malumfashi B da sauran yankuna
Unguwannin da s**a haɗa da Unguwar Nagandi A, Unguwar Nagandi B, Unguwar Sale, Unguwar Tsamiya da Unguwar Tura Koshe za su karɓi kuɗinsu.
Bugu da ƙari, mazabu k**ar su Borin-dawa, Dayi, Gorar-Dansaka, Karfi, Makaurachi, Na Alma, Rawan-sanyi, Ruwan-sanyi da Yaba, duk za su karɓi kuɗaɗensu a wannan rana ta ƙarshe gaba ɗaya.

Hukumar ta yi kira ga jama’a da su tabbatar da halartar wurin karɓar kuɗin a ranar da aka ware wa unguwarsu, domin gujewa tsaiko ko rasa damar karɓa.

An kuma jaddada cewa duk wanda bai samu damar zuwa a ranar da aka ware wa unguwarsa ba, zai jira wani lokaci na gaba kafin sake samun dama.

Domin amfanin tsarin, jama’a za su buƙaci gabatar da NIN da BVN a wajen karɓar kuɗin. Hukumar ta ce za a sanar da tak**aiman ranar da biyan kuɗin zai fara a nan gaba.

Gwamnatin Katsina Ta Kara Sayen Sabbin Motocin Yaki Masu Sulke Don Karfafa Fada Da Ta’addanciA wani mataki na karfafa ja...
23/08/2025

Gwamnatin Katsina Ta Kara Sayen Sabbin Motocin Yaki Masu Sulke Don Karfafa Fada Da Ta’addanci

A wani mataki na karfafa jajircewarta wajen yaki da matsalar tsaro a jihar, gwamnatin Katsina ta sake sayen sabbin motoci masu sulke guda takwas (8) domin taimakawa jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukansu na fatattakar ‘yan ta’adda a sassa daban-daban na jihar.

Wannan sabon ci gaban ya biyo bayan irin damuwar da al’ummar jihar ke fuskanta sak**akon hare-haren ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifuka da ke addabar yankunan karkara. Motocin masu sulken za su baiwa dakarun tsaro damar shiga wuraren da ke da cike da hadari cikin kwarin gwiwa tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.

Al’umma da dama sun yaba da wannan mataki, inda s**a bayyana shi a matsayin sabuwar alamar jajircewa daga gwamnatin jihar wajen tunkarar matsalar tsaro da ta dade tana addabar jama’a.

LABARI MAI DADISOJOJIN SAMA SUN RUSA MABOYAR BABARO A KANKARA, SUN CETO MUTANE 76An samu gagarumar nasara a jihar Katsin...
23/08/2025

LABARI MAI DADI

SOJOJIN SAMA SUN RUSA MABOYAR BABARO A KANKARA, SUN CETO MUTANE 76

An samu gagarumar nasara a jihar Katsina bayan da sojojin sama na Najeriya s**a kai luguden wuta a kan maboyar fitaccen dan ta’adda Babaro da yaransa a tsaunin Pauwa, karamar hukumar Kankara.

A wannan hari, an ceto mutane 76 da s**a hada da mata da yara, wadanda aka yi garkuwa da su a lokacin mummunan harin da ‘yan ta’addan s**a kai Unguwan Mantau a Malumfashi.

Harin, wanda aka gudanar da yamma tsakanin 6:00 zuwa 7:00, ya hallaka sansanin Babaro, wanda aka dade ana cewa shi ne wurin da suke fito suna addabar jama’a. Sai dai a cikin wannan al’amari, an ce an rasa yaro guda daya.

Majiyar gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da wannan ci gaba, inda ta bayyana cewa aikin ya nuna yadda tsaro ke kara samun karfi a jihar. Gwamnatin ta kuma yaba da jarumtar sojojin sama da na kasa, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da tallafawa ayyukan tsaro ta fuskar kayan aiki, bayanan sirri da kuma hada kai da jama’a.

Wannan nasara ta sa jama’a ke cike da murna da farin ciki, musamman ganin yadda aka kubutar da daruruwan mata da yara daga hannun masu garkuwa.

A yanzu haka ana ci gaba da gudanar da bincike da kuma aikin zakulo sauran maboyar ‘yan ta’adda, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai cikin lokaci domin taimakawa jami’an tsaro.

Al’umma dai na fatan wannan nasara za ta zama tubalin kawo karshen garkuwa da mutane da kisan gilla a jihar Katsina da ma kasa baki daya.

Malumfashi Post

Address

Malumfashi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Malumfashi Post:

Share