Malumfashi Media Concept

Malumfashi Media Concept Malumfashi Media Concept

02/01/2026

💥 YANZU-YANZU: Abba Kabir Yusuf Ya Koma APC — Sanarwa Na Dab Da fita.

Tirƙashi: Yadda wasu Fulani makiyaya su ka yi ta wasa da makami mai linzami da Amurka ta jefo dajin jihar Sokoto bai yi ...
02/01/2026

Tirƙashi: Yadda wasu Fulani makiyaya su ka yi ta wasa da makami mai linzami da Amurka ta jefo dajin jihar Sokoto bai yi aiki ba, inda su ka yi ta mirginawa tare da yunƙurin ɗadaga sama amma su ka kasa sakamakon nauyin da ya ke da shi.

An ce “yaro bai san wuta ba sai ya taka”.

Ku na ganin waɗannan sun san abin da su ke wasa da shi kuwa?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari a Kano, Soja Ɗaya da Farar Hula Sun Rasa Rayukansu..‘Yan bindiga sun sake kai mummunan ha...
02/01/2026

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari a Kano, Soja Ɗaya da Farar Hula Sun Rasa Rayukansu..

‘Yan bindiga sun sake kai mummunan hari a ƙauyen Faruruwa da ke ƙaramar hukumar Shanono, a jihar Kano, inda rahotanni daga mazauna yankin ke nuna cewa soja ɗaya na Najeriya da farar hula ɗaya sun rasa rayukansu.

Harin ya fara ne tun daren jiya, inda ya ci gaba har zuwa wayewar gari kusan ƙarfe 5:00 na safe, lamarin da ke nuna tsawon lokacin da ‘yan bindigar s**a kwashe suna cin karensu babu babbaka.

Baya ga asarar rayuka, an kuma kwashe dabbobi da dama kamar yadda Shafin Bakatsine ya rawaito.

Lamarin ya ƙara jefa al’ummar yankin cikin fargaba, jimami da rashin tabbas.

‎wata sabuwa.“Zamu tabbatar mun je Afrika Musamman Najeriya don Ƴaki da Ta'addanci” Musamman kisan Kiristoci da ake yi, ...
02/01/2026

‎wata sabuwa.
“Zamu tabbatar mun je Afrika Musamman Najeriya don Ƴaki da Ta'addanci” Musamman kisan Kiristoci da ake yi, inji Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.

‎Acikin Wani Jawabinsa a Faifan Video, Natenyahu ya bayyana cewa Isra’ila za ta faɗaɗa ayyukanta na yaki da Ta'addanci, A Afrika Musamman a Najeriya 🇳🇬, Afirka, da Turai. — In ji Firayim Ministan Isra’ila, “ Benjamin Netanyahu.
Meza kuce tattare wannan tsarin na Benjamin?

Ku Doke Najeriya, Ku Karɓi Naira Miliyan 11.3 Kowannenku — Shugaban Mozambique Ga 'Yan WasansaShugaban ƙasar Mozambique ...
02/01/2026

Ku Doke Najeriya, Ku Karɓi Naira Miliyan 11.3 Kowannenku — Shugaban Mozambique Ga 'Yan Wasansa

Shugaban ƙasar Mozambique ya yi wa ‘yan wasan ƙasarsa alkawarin ba su ladan kuɗi har Naira miliyan 11.3 kowanne, idan har s**a doke tawagar Najeriya a wasan da ke gabatowa.

Shugaban ya bayyana hakan ne domin ƙara musu ƙwarin gwiwa da ƙaimi, yana mai cewa nasara a kan Najeriya za ta zama babbar nasara ga ƙasar Mozambique.

Wannan alkawari ya ƙara zafafa fafatawar, yayin da ake sa ran wasa mai cike da taka-tsantsan da ƙwazo daga ɓangarorin biyu.

DA DUMI-DUMI: 'Yan Majalisun Tarayya guda biyu masu ci a jihar Legas sun shiga jam'iyyar hadaka ta ADC. 'Yan majalisar d...
02/01/2026

DA DUMI-DUMI: 'Yan Majalisun Tarayya guda biyu masu ci a jihar Legas sun shiga jam'iyyar hadaka ta ADC.

'Yan majalisar da s**a shiga jam'iyyar ta ADC a jihar Lagos sune Hon George Adegeye Olawande da Hon Seyi Sowunmi kuma sunyi hakan ne bisa umarnin Peter Obi.

Me za ku ce?

Gwamnan Bauchi Ya Zargi Ministan Abuja Wike da Ta’addanci da Ɓarnar FilayeGwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir M...
02/01/2026

Gwamnan Bauchi Ya Zargi Ministan Abuja Wike da Ta’addanci da Ɓarnar Filaye

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Muhammad, ya zargi Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, da aikata abin da ya kira ta’addanci da kuma wawure filayen a Abuja.

Gwamnan ya yi wannan zargi ne yayin da yake magana da gidan talabijin na Channel, yayin mayar da martani kan zargin alakanta shi da akayi da ɗaukar nauyin Ta'addanci.

Menene Ra'ayinku kan wannan kai ruwa rana da ake yi tsakanin Kaura da Gwamnati ?

A wane rukuni kuke?
02/01/2026

A wane rukuni kuke?

Wannan mata akwai tsoron cin haram, ta tsinci N330m a account dinta na banki, ta mayar ma banki su a nemi mai suWannan i...
02/01/2026

Wannan mata akwai tsoron cin haram, ta tsinci N330m a account dinta na banki, ta mayar ma banki su a nemi mai su

Wannan ita ce Aisha Isah Yelwa, ‘yar asalin Jihar Neja daga Ƙaramar Hukumar Lapai, wadda ta nuna gagarumar gaskiya da amana bayan da ta mayar wa wani banki Naira miliyan 330 da aka yi kuskuren turawa zuwa asusun ajiyarta.

Rahotanni sun bayyana cewa, bayan Aisha ta samu saƙon shigowar kuɗin, ba ta sanar da kowa ba, sai dai nan take ta tashi zuwa reshen First Bank da ke garin Lapai domin sanar da su kuskuren da aka yi.

Bayan tabbatar da lamarin, bankin ya karɓi kuɗin gaba ɗaya daga hannunta.

Matakin da Aisha Isah Yelwa ta ɗauka ya ja hankalin jama’a, inda da dama ke yabawa da jinjina mata bisa gaskiya, rikon amana da tsoron Allah da ta nuna.

HOTO: Sen Rabi'u kwankwaso ya sauka jihar kano bayan kwashe kwanaki  jihar Lagos.
01/01/2026

HOTO: Sen Rabi'u kwankwaso ya sauka jihar kano bayan kwashe kwanaki jihar Lagos.

Hon Lado Suleja Ya Mika Katafaren Masallacin Juma'a Da Ya Gina Mai Daukar Mutane 400 Ga Shugaban Izala, Sheikh Bala Lau ...
01/01/2026

Hon Lado Suleja Ya Mika Katafaren Masallacin Juma'a Da Ya Gina Mai Daukar Mutane 400 Ga Shugaban Izala, Sheikh Bala Lau

A yau ne tsohon dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Suleja, Tafa da Gurara dake jihar Neja, wato Hon Lado Suleja, Fmr ya mika masallacin Juma'a mai daukar mutane 400 ga shugaban Izala na kasa, Sheikh Bala Lau.

Masallacin, wanda Hon Lado Suleja ya gina, zai taimaka wa al'ummar Musulmin yankin Suleja.

Daga Ali Wego
Ciyaman Lado Media

A Jihar Katsina, mazauna Unguwar Jan Bango Rahamawa na fama da matsalar ruwan sha.
01/01/2026

A Jihar Katsina, mazauna Unguwar Jan Bango Rahamawa na fama da matsalar ruwan sha.

Address

Malumfashi
Malumfashi
25880

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Media Concept posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share