Malumfashi Media Concept

Malumfashi Media Concept Malumfashi Media Concept

ƘURUN ƘUS: Abdulmumin Kofa Ya Ce Ya Karɓi Korar Da NNPP Ta Yi Masa Hannu BibbiyuA sanarwar da ya fitar a daren nan, ya y...
06/09/2025

ƘURUN ƘUS: Abdulmumin Kofa Ya Ce Ya Karɓi Korar Da NNPP Ta Yi Masa Hannu Bibbiyu

A sanarwar da ya fitar a daren nan, ya yi wa jam'iyyar fatan alheri tare da bai wa magoya bayansa zaɓi ko su cigaba da zama a jam'iyyar ko su biyo shi inda zai tsallaka.

Menene ra'ayinku?

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ba Da Naira Biliyan 1.85 Domin Tallafawa Ilimi Da Rayuwar Matan ChibokShugaba ...
06/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaba Tinubu Ya Amince Da Ba Da Naira Biliyan 1.85 Domin Tallafawa Ilimi Da Rayuwar Matan Chibok

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da bada tallafi na Naira biliyan 1.85 domin tallafawa ilimi da gyaran rayuwa ga Yan Matan Chibok da aka kubutar tun daga sace su a shekarar 2014, har zuwa shekarar 2027.

Bisa bayanin Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, daga cikin ‘yan Chibok da aka kubutar, 108 na ƙarƙashin kulawar gwamnati, inda 68 ke karatu a Jami’ar Amurka ta Najeriya (AUN), dake Yola. Gwamnatin tarayya na ci gaba da biyan kudin makaranta, masauki da sauran hakkokin su.

An bayyana cewa shirin tallafin ya haɗa da, Kudin makaranta da masauki, Horar da Su sana’o’i da kayan fara aiwatarwa, Tallafin lafiyar kwakwalwa da ta jiki, Tallafin iyaye da yara, Kula da ci gaban karatu. Jimillar dukkan waɗannan tsare-tsare ya kai N1,854,277,768.

Ma’aikatar ta ce shirin ba wai tallafi na kudi kawai ba ne, yana nuna ƙudurin Najeriya na mayar da wannan munanan lamari cikin labarin jarumta, mutunci da kyakyawan fata. Haka zalika, ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ya nuna shugabanci nagari ta hanyar tabbatar da ci gaba da karatun ‘yan Matan Chibok a AUN duk da ya sami s**a daga wasu ‘yan siyasa.

Tuni shekaru fiye da goma s**a wuce tun lokacin da Boko Haram s**a sace dalibai 276 daga Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Chibok, Borno, yayin da suke shirin kammala jarabawar karshe. Ya zuwa yanzu, fiye da 178 sun samu kubuta ko sun tsere, amma fiye da 90 har yanzu ba a san inda suke ba.

"Dan Allah, ku nuna kauna, ku yi ma Nijeriya addu'a " - Remi Tinubu ta roki yan Nijeriya a sakon ta na barka da Maulidi
05/09/2025

"Dan Allah, ku nuna kauna, ku yi ma Nijeriya addu'a " - Remi Tinubu ta roki yan Nijeriya a sakon ta na barka da Maulidi

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji Gwamnatin Tar...
05/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji

Gwamnatin Tarayya ta miƙa ta’aziyyar ta ga iyalan waɗanda s**a rasa ran su a haɗarin jirgin ruwa da ya faru kwanan nan a yankin Borgu na Jihar Neja, wanda ya yi sanadin mutuwar kimanin mutum 32.

A wata sanarwa da ya fitar a yau, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wannan lamari a matsayin abin da “ya tayar da hankali.”

Ya ce: “Wannan ibtila’i ya yi matuƙar tayar da hankali, kasancewar ya faru ne cikin ƙasa da watanni huɗu bayan ambaliyar ruwa mai muni da ta afku a Mokwa, shi ma a Jihar Neja.

“Muna miƙa ta’aziyyar mu ta musamman ga iyalan waɗanda abin ya shafa, gwamnatin jihar da kuma al’ummar Neja. Jimamin mu da addu’o’in mu suna tare da duk wanda wannan ibtila’i ya shafa.”

Ministan ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta samar da dukkan tallafi da ake buƙata ga iyalan waɗanda s**a mutu da waɗanda s**a tsira, tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin Jihar Neja domin tabbatar da gaggawar tallafi da taimako.

Haka kuma, gwamnatin ta umurci Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) da ta gudanar da babban kamfen na wayar da kai a faɗin ƙasar nan domin ƙara faɗakar da jama’a kan matakan tsaro yayin amfani da hanyoyin ruwa.

Idris ya yaba wa gwamnatin Jihar Neja, ta hannun Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha, bisa gaggawar gudanar da aikin ceto da ya tabbatar an tantance dukkan fasinjojin da ke cikin jirgin da ya yi hatsarin.

Ya ce: “Zan yi amfani da wannan dama in sake tunatar da jama’a da su riƙa bai wa batun tsaro muhimmanci yayin tafiya ta hanyoyin ruwa.

“Musamman, babu wanda ya kamata ya shiga tafiyar jirgin ruwa ba tare da sanya rigar kariya ta musamman ba. Matakan tsaro na iya ceton rayuka.”

Ya yi addu’ar samun rahamar Allah ga rayukan waɗanda s**a salwanta tare da yi wa waɗanda s**a tsira fatar samun lafiya cikin gaggawa.

YANZU-YANZU: Za Mu Bayyana Suɲãyēɲ Masu Aláƙá Da 'Yãɲ Bíɲḍíĝá Da Masu Amfani Da Tá'aḍḍáɲcí Wajēɲ Cimma Manufar Su Ta Siy...
05/09/2025

YANZU-YANZU: Za Mu Bayyana Suɲãyēɲ Masu Aláƙá Da 'Yãɲ Bíɲḍíĝá Da Masu Amfani Da Tá'aḍḍáɲcí Wajēɲ Cimma Manufar Su Ta Siyasa, Inji Dan Bello

Kuna goyon baya ?

Yadda Al'ummar Musulmai s**a halarci Taron Mauludi a Bauchi karkashin jagorancin Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
05/09/2025

Yadda Al'ummar Musulmai s**a halarci Taron Mauludi a Bauchi karkashin jagorancin Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Rundunar "yan sandan Najeriya reshen jihar Kaduna, na neman Nasiru El-rufa'i ruwa a jallo.Me zaku ce???
05/09/2025

Rundunar "yan sandan Najeriya reshen jihar Kaduna, na neman Nasiru El-rufa'i ruwa a jallo.

Me zaku ce???

ANNABI:  Yadda miliyoyin al'ummar Musulmin s**a gudanar da taron murnar tunawa da watan da aka haifi fiyayyen halitta (M...
04/09/2025

ANNABI: Yadda miliyoyin al'ummar Musulmin s**a gudanar da taron murnar tunawa da watan da aka haifi fiyayyen halitta (Mauludi) Annabi Muhammad (SAW) a Kasar Yemen.

Allah Ya karawa Annabi Muhammad SAW!

"Daga yanzu karku sake jiran Umarni daga sama, duk inda aka kaiku aiki kuka ga ba daidai ba, ku saki Wùta kawai"_-Inji- ...
04/09/2025

"Daga yanzu karku sake jiran Umarni daga sama, duk inda aka kaiku aiki kuka ga ba daidai ba, ku saki Wùta kawai"_-Inji- Christopher Musa

Shugaban sojojin Najeriya Christopher Musa yace bai son wani soja ya kara bashi uzurin cewa wai an yi abinda bai dace ba a kusa dashi ko kuma an kai hari a kusa dashi bai dauki mataki ba yace masa wai saboda ba’a bashi umarni bane, yace kada sojojin su sake jiran umarni.

Sannan ya gargadi kwamandojin sojojin da cewa duk wanda aka samu barakar aikata ba daidai ba a rundunarsa zai dandana kudarsa.

DA DUMI-DUMI:  ’Yan sanda sun gayyaci shugabar ALGON ta Kano bisa zargin umartar ɗan sanda ya harbi ma’aikataRundunar ’Y...
04/09/2025

DA DUMI-DUMI: ’Yan sanda sun gayyaci shugabar ALGON ta Kano bisa zargin umartar ɗan sanda ya harbi ma’aikata

Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kano ta tabbatar da gayyatar shugabar ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi ta jihar (ALGON), Hajiya Binta Bayero, domin gudanar da bincike kan wani rikici da ya ɓarke a wani kamfani da ya jawo zargin tashin hankali.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wani sabani tsakaninta da ma’aikata a masana’antar, inda ake zargin ta umarci ɗan sandan dake gadinta da ya yi amfani da bindiga kan wasu daga cikin ma’aikatan. Wannan zargi ya tayar da hankula, inda aka ruwaito cewa wasu sun jikkata sakamakon harbin.

Kakakin rundunar ’yan sanda a jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da cewa an gayyaci shugabar ALGON domin amsa tambayoyi. Ya ce:
“Babu wanda ya fi doka girma. Rundunar ta himmatu wajen gudanar da bincike bisa gaskiya da adalci, tare da tabbatar da cewa an dauki mataki da ya dace bisa ga sakamakon binciken.”

A nata martanin, Hajiya Binta Bayero ta karyata zargin, tana mai cewa ana ƙoƙarin bata mata suna ta siyasa. Ta ce ba ta taba bayar da irin wannan umarni ba, sannan ta nemi a gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da gaskiya.
“Ina matuƙar mamakin irin wannan zargi. Ni a matsayina na shugaba, ba zan taɓa goyon bayan amfani da karfi wajen warware matsala ba. Wannan shiri ne kawai na siyasa domin a tozarta ni.” in ji ta.

Ƙungiyar ALGON ta jihar Kano ta fito da sanarwa, inda ta goyi bayan gudanar da bincike na gaskiya, tare da kira da a guji daukar lamarin da hannu da siyasa.

Lamarin dai ya ci gaba da jawo muhawara a Kano, inda jama’a ke rarrabuwa tsakanin masu ganin cewa dole ne a dauki matakin shari’a mai tsauri, da kuma masu cewa ana yi ne kawai don ƙoƙarin kaskantar da shugabar ƙungiyar.

~KTG Hausa News

DA ƊUMI-ƊUMI: Hukumar Kwastam ta samu Naira Tiriliyan 3.7 a Cikin Rabin Farko na Shekara Hukumar Kwastam ta Najeriya (NC...
04/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Hukumar Kwastam ta samu Naira Tiriliyan 3.7 a Cikin Rabin Farko na Shekara

Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS) ta sanar da cewa ta samu kudin shiga na Naira Tiriliyan 3.7 a rabin farko na shekarar 2025, wanda ya zarce yadda aka zata da Naira Biliyan 390.2, wanda ya kai kashi 11.85 cikin dari.

Wannan bayanin ya fito ne daga kakakin hukumar, Abdullahi Maiwada, a ranar Talata a Abuja bayan taron hukumar na 63 a karkashin jagorancin Ministan Kudi da Ministan Tattalin Arziki, Wale Edun.

Hukumar ta danganta wannan nasara da ingantattun gyare-gyare, ingantaccen bin ka’ida daga masu ruwa da tsaki, da kuma karfafa fasahar aiki a cikin ayyukan kwastam.

A cewar Maiwada, wannan adadin ya nuna cewa a cikin watanni shida, NCS ta cimma kashi 55.93 cikin dari na burin kudaden shiga na shekara.

~Rariya Online

BABBAN MAGANA: 'Yan sanda sun gargadi mata cewa karɓar kuɗin mota a hannun maza da nufin kai masu ziyara amma kuma mace ...
04/09/2025

BABBAN MAGANA: 'Yan sanda sun gargadi mata cewa karɓar kuɗin mota a hannun maza da nufin kai masu ziyara amma kuma mace ta ƙi zuwa babban laifi ne a Najeriya

Ayau News ta ruwaito wata babbar jam'iar yar sanda SP Grace Koko ta fitar da jawabi don wayar da kan mata dokoki inda ta ce hakan yana cikin “419” (wato zamba cikin aminci), kuma ana iya gurfanar da duk mai aikata hakan a kotu.

Rahoton Ayau News
Follow us => Ayau News

Me zaku ce?

Address

Malumfashi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Malumfashi Media Concept posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share