15/11/2025
Sulhun da ake yi da ƴanbindiga a Katsina ne ke haifar da hare-haren Kano
Jagoran jam'iyyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce sulhu da ƴanbindiga da wasu al'umomin jihar Katsina ke yi ne ya janyo samun hare-hare a wasu yankunan jihar Kano.
Yayin da yake jawabi a wurin taron yaye ɗalibai na jami'ar skyline da ke Kano, Sanata Kwankwaso ya ce gwamnatin tarayya ce ya kamata ta yi sulhu ba ƙaramar hukuma ba.
Tsohon gwamnan jihar Kanon ya ce ƴan bindiga na shiga Kano daga Katsina su kashe mutane bayan sulhu a wasu ƙananan hukumomi.
''Babu laifin sulhu amma dole gwamnatin tarayya ta sa baki, babu ma'ana ƙaramar hukuma ɗaya ta ɗauki matakin ita kaɗai, dole gwamnatin tarayya ta sa baki'', in ji shi.
Kwankwaso ya kuma yi kira ga shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ƙara mayar da hankali kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar.
Dole shugaban ƙasa ya nuna jajircewa a matsayin babban kwamandan hafoshin tsaro.