GVC News

GVC News Online News Publishing and
Advertisement

Ƴansanda sun k**a ƴan bindiga su na kokarin sayen AK-47 a KanoRundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta k**a wasu mutane hudu da...
09/03/2025

Ƴansanda sun k**a ƴan bindiga su na kokarin sayen AK-47 a Kano

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta k**a wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan fashin daji waɗanda ake zargin suna kan hanyarsu ta sayen bindigar AK-47.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna, ya tabbatar da cafke waɗanda ake zargin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

A cewarsa, rundunar ta samu gagarumar nasara a kokarinta na dakile yaduwar ‘yan fashin daji da miyagun laifuka a jihar.

Ya ce, “A ranar 6 ga Maris, 2025, da misalin karfe 2:00 na rana, wata tawagar jami’an bincike na ‘yansanda ƙarƙashin jagorancin SP Ahmad Abdullahi, jami’in da ke kula da ofishin 'yansanda na Jar Kuka, sun cafke wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan bindiga a gidan man Chula dake Hotoro a Kano.

“Waɗanda aka k**a sun haɗa da Shukurana Salihu, mai shekara 25; Rabi’u Dahiru, mai shekara 35; da Ya’u Idris, mai shekara 30, duk daga Jihar Katsina, da kuma Muktar Sani, mai shekara 30, daga Yandodo Hotoro , Kano. An k**a su ne bisa sahihan bayanan sirri da s**a nuna cewa sun zo Kano da niyyar sayen bindigar AK-47.”

Kiyawa ya de an samu wannan nasara ne sak**akon biyayya ga umarnin Sufeto-Janar na Ƴansanda, Kayode Adeolu Egbetokun, ga dukkanin rundunonin ƴansanda kan wani sabon salo na yaƙi da ta'addanci da laifuka a fadin ƙasar.

Ya kara da cewa an samu mak**ai, da harsashi da guru da layu da ƴaƴan boris da kuma kudi kimanin Naira Miliyan 1 da dubu 28 a tare da waɗanda ake zargin.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa ya bar jam’iyyar PDP.Dan takarar shuga...
09/03/2025

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa ya bar jam’iyyar PDP.

Dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023 ya sake jaddada goyon bayansa ga hadakar jam’iyyun siyasa don kayar da jam’iyyar APC a 2027.

Daily Trust ta rawaito cewa, a baya-bayan nan, rahotanni daban-daban sun nuna cewa Atiku yana tunanin barin PDP don shirin takarar shugaban kasa a 2027.

Rahotannin sun ce yana shirin komawa jam’iyyar SDP.

Amma a cikin wata sanarwa da ofishin yada labaransa ya fitar a ranar Asabar, an bayyana cewa tsohon mataimakin shugaban kasar na nan a matsayin cikakken mamba na PDP.

Yayin da yake karyata rahotannin a matsayin “karya tsagwaronta”, ofishin yada labaran ya bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da su.

Ofishin yada labaran ya jaddada cewa Abubakar ya dade yana kira da a hada kawancen jam’iyyun adawa a Najeriya domin cire APC daga mulki a 2027.

Babu dalilin da Ƴan Najeriya za su sayi man fetur da tsada - Sanata NdumeƊan Majalisar Dattawan Najeriya daga Jihar Born...
07/03/2025

Babu dalilin da Ƴan Najeriya za su sayi man fetur da tsada - Sanata Ndume

Ɗan Majalisar Dattawan Najeriya daga Jihar Borno, Sanata Muhammed Ali Ndume ya ce babu dalilin da ƴan Najeriya za su dinga sayen man fetur da tsada, alhali a cikin ƙasar ake haƙo shi.

Ndume ya bayyana cewar tamkar yaudara ake yiwa jama'ar ƙasar da sunan tallafi, ko kuma sayar da man da ake samunsa a gida da tsada ga ƴan kasa.

Sanatan ya bayyana man k**ar ruwan da ake haƙowa ta hanyar rijiyar birtsatsai, wanda bayan tona shi, babu abin kashe kudin da ya wuce sayen man da za'a sanyawa inji domin deɓo shi.

Ɗan Majalisar ya ce shi ya kasa fahimtar dalilin da ƴan Najeriya za su biya kuɗi da tsada domin cin gajiyar arzikin man da ake samar da shi a gida, da kuma tace shi domin amfanin jama'a, yayin da ya yiwa watsi da batun biyan tallafin da ake ta mahawara akai.

Ndume ya kuma bayyana damuwa akan irin zagon ƙasar da ya ce ake yiwa attajiri Aliko Ɗangote da ya samar da matatar man da ake cin gajiyarta ayau.

📷 RFI Hausa

Magidanci ya rasu ana tsaka da Sallah a Abuja Wani magidanci mai suna Salihu Byezhe mai shekaru 52 ya rasu bayan ya yank...
07/03/2025

Magidanci ya rasu ana tsaka da Sallah a Abuja

Wani magidanci mai suna Salihu Byezhe mai shekaru 52 ya rasu bayan ya yanke jiki ya faɗi ana tsaka da sallar asuba a wani masallaci da ke kauyen Gudaba a karamar hukumar Kuje a babban birnin tarayya, Abuja.

Shedun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne a jiya Alhamis bayan da Byezhe ya gama yin Sahur, sai ya yi alwala, sannan ya shiga Masallacin ya bi jam'i.

“Ana ci gaba da Sallah,bkawai sai ya fadi ba zato ba tsammani, nan dai ƴan uwa a masallacin su ka yi gaggawar kai shi asibiti. Ya na ta numfashi a hanya, amma ana karasa wa asibitin likita ya ce ya rasu,” in ji Dantani.

Wani likita a asibitin da ke Kuje daga baya ya tabbatar da mutuwar Byezhe, yana mai alakanta cutar hawan jini.

Wakilinmu Leadership ya tattaro cewa marigayin ya kasance yana ciwon hawan jini.

An yi jana’izar sa da misalin karfe 10:12 na safiyar juya Alhamis k**ar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kaduna ta bayar da umarnin kwace wasu makudan kudade har biliyan N1.37bn...
06/03/2025

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kaduna ta bayar da umarnin kwace wasu makudan kudade har biliyan N1.37bn na wucin gadi, wadanda ake zargin an karkatar da su daga asusun gwamnatin jihar zuwa wani asusu na sirri a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Nasir El-Rufai.

INNA LILLAHI WA'INNA ILIAHI RAJI'UN: Fitaccen Malamin Izalah Sheikh Sa'eed Hassan Jingir Ya RâsuAllah Ya gafarta masa.
06/03/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILIAHI RAJI'UN: Fitaccen Malamin Izalah Sheikh Sa'eed Hassan Jingir Ya Râsu

Allah Ya gafarta masa.

HOTUNA: Yadda Yarima Salman Bin Sultan Ya Gabatar Da Muɗa Bakin Azumin Na 5 A Masallacin Al-Nabawi Dake Birnin Madina.” ...
05/03/2025

HOTUNA: Yadda Yarima Salman Bin Sultan Ya Gabatar Da Muɗa Bakin Azumin Na 5 A Masallacin Al-Nabawi Dake Birnin Madina.”

📸 Inside The Haramain

MATSALAR TSARO A arewacin Najeriya an k**a jami'in shige da fice da safarar manyan mak**ai ga yan ta'adda.Rundunar ‘yan ...
05/03/2025

MATSALAR TSARO A arewacin Najeriya an k**a jami'in shige da fice da safarar manyan mak**ai ga yan ta'adda.

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ta cafke wani tsohon jami’in shige da fice da ke yunkurin sayar da manyan bindigogi ga ‘yan bindiga da ke aiki a dazuzzukan Abuja-Kaduna.

Jami’in da aka kora, wanda ba a bayyana sunansa ba, an k**a shi ne bayan wani samame da hukumar ‘yan sanda ta kai.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja a ranar Larabar da ta gabata, jami’in da ke kula da sashin yaki da masu garkuwa da mutane, Mustafa Mohammed, ya ce farmakin ya hana mak**an kaiwa ga masu aikata laifuka,

Mohammed ya ce, “A bisa bayanan sirri, rundunar ta k**a wadannan bindigogi daga korarriyar jami’in shige-da-fice da ke yunkurin sayar da su ga ‘yan fashi da ke addabar dajin Abuja-Kaduna. An samu bayanan sirri cikin lokaci, kuma an k**a mak**ai a lokacin da yake kokarin kai kayan.

Mohammed ya ce daga cikin mak**an da aka kwato akwai Scorpion CZ EVO3, wani nagartaccen makami mai sarrafa kansa.

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta gabatar da ƙorafin a hukumance ga zauren majalisar dattawan Najeriya a yau Laraba, dai...
05/03/2025

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta gabatar da ƙorafin a hukumance ga zauren majalisar dattawan Najeriya a yau Laraba, dai dai lokacin da batun ke ci gaba da janyo cece-kuce a sassan ƙasar

📷 Dailytrust

Dandazon mutane na gudanar da zanga-zanga a harabar Majalisar Dattawan Najeriya da ke birnin Abuja, inda s**a buƙaci maj...
05/03/2025

Dandazon mutane na gudanar da zanga-zanga a harabar Majalisar Dattawan Najeriya da ke birnin Abuja, inda s**a buƙaci majalisar da ta sauke shugabanta Godswill Akpabio bisa zargin sa da yunƙurin lalata da sanata Natasha Akpoti-Uduaghan.

Ƙarin bayani: https://rfi.my/BT4y

INNALILLAHI WA INNAH ILAIHI RAJI'UN: Da shi aka sha ruwa jiya; bayan ya shiga tawagar da ta taro ɗan shugaban ƙasa Sheyi...
04/03/2025

INNALILLAHI WA INNAH ILAIHI RAJI'UN: Da shi aka sha ruwa jiya; bayan ya shiga tawagar da ta taro ɗan shugaban ƙasa Sheyi Bola Ahmed Tinubu, wajen Shan ruwa da aka yi da shi a daren jiya Litinin.

Allah Ya Jikan Yusuf Ashura da shi a a kayi komai inda akan hanyar su ne su kayi hatsari a State Road, Titin Gidan Gwmanatin Kano.

TIRƘAAHI: Kada Ka Yi Tunanin 'Yata Za Ta Yi Maka Girki Saboda Ba Dole Ba Ne, Idàn Ka Ga Ta Yi Maka Ģìŕki, To Ta Yi Ne Do...
04/03/2025

TIRƘAAHI: Kada Ka Yi Tunanin 'Yata Za Ta Yi Maka Girki Saboda Ba Dole Ba Ne, Idàn Ka Ga Ta Yi Maka Ģìŕki, To Ta Yi Ne Don Ta Samu Lada Ta Shiga Àljàñña, Sakon Wani Ubàñ Àmaŕya Ga Ango A Wajen Shagalin Bikinsu

Menene ra'ayinku?

Address

Behind Old Local Government Building Malumfashi
Malumfashi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GVC News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to GVC News:

Share