GVC News

GVC News Online News Publishing and
Advertisement

Sarkin Zuru ya kai ziyarar jaje ga yan' kasuwar Zuru ya bayar da tallafin Naira ₦250,000 ga kowane Mutum Daya wadanda Go...
16/09/2025

Sarkin Zuru ya kai ziyarar jaje ga yan' kasuwar Zuru ya bayar da tallafin Naira ₦250,000 ga kowane Mutum Daya wadanda Gobarar kasuwar ta rutsa da su.

Mai martaba sarkin Zuru Alh Sanusi Mikailu Sami Sami Gomo III a yayin ziyararsa ya bayyana matukar jimaminsa game da wannan masifa da ta afkawa dimbin yan kasuwar tare da kone dukiyoyi masu tarin yawa.

Mai martaba Sarkin Zuru ya bayyana tausayinsa ga wadanda abin ya shafa Allah ya mayar musu da sabon arziki.

Sarkin ya baiwa kowane mai shago da Gobarar ta rutsa da shi Naira dubu ₦250,000 don rage musu radadin wannan babban al'amarin.

Sarkin Zuru ya samu rakiyar mataimakin shugaban karamar hukumar Mulkin Zuru Hon Samaila Abdullah da APC Chairman Zuru Alh Aliyu Abubakar Abiola da jami'an tsaro domin yin jaje ga yan' kasuwar da abin ya shafa.

📸 Abbakar Aleeyu Anache

Gwamnan Jihar Kebbi ya bada tabbacin kawo karshen matsalar rashin tsaron Jihar inda ya baiwa al'ummar Tadurga Kyabu da h...
22/06/2025

Gwamnan Jihar Kebbi ya bada tabbacin kawo karshen matsalar rashin tsaron Jihar inda ya baiwa al'ummar Tadurga Kyabu da hare-haren yan bindiga ya shafa Naira Miliyan 50,000,000

Mataimakin gwamnan jihar Kebbi ya bayyana jimaminsa a madadin gwamnan Kebbi Dr, Nasir Idris Kauran Gwandu kan hare-haren yan Bindigar da s**a afkawa al'ummar Zuru Danko-Wasagu wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum talatin 30.

Mataimakin gwamnan ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kebbi na daukar matakan da s**a dace wajen shawo kan matsalolin tsaron da s**a addabi al'ummar jihar Kebbi.

Bayan gudummuwar gwamnan Kebbi Sanata mai wakiltar Kebbi ta kudu ya bayar da Naira Miliyan 2,000,000 da buhuhuwa abinci 100 da tamfofi Dan majalisar wakilai mai wakiltar masarautar Zuru Hon Kabir Ibrahim Tukura wanda ya bayar da Naira Miliyan 20,000,000 da buhuhuwan 200 na kayan abinci da a tamfofi kakakin majalisar dokokin Kebbi Hon Usman Ankwe ya bayar da gudummuwar Naira Miliyan 2,000,000.

Wannan tallafin ya biyo bayan wani hare-haren yan Bindigar da s**a kaddamar wa al'ummar Tadurga Kyabu dake Zuru Danko-Wasagu da ke jihar Kebbi a makon da ya gabata.

📸 Abbakar Aleeyu Anache

Shugaba Trump ya ce Amurka ta kai wasu manyan hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, ya kuma ce hare-haren "na...
22/06/2025

Shugaba Trump ya ce Amurka ta kai wasu manyan hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, ya kuma ce hare-haren "nasarar soja ce mai ban mamaki."

Shugaban ya kara da cewa, an lalata muhimman cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran gaba daya.

Yan bindiga sun kaddamar da sabbin hare-hare a Jihar Kebbi sun mamaye kauyukan karamar hukumar Zuru.Rahotanni daga jihar...
17/06/2025

Yan bindiga sun kaddamar da sabbin hare-hare a Jihar Kebbi sun mamaye kauyukan karamar hukumar Zuru.

Rahotanni daga jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana cewa yan ta'adda sun kai hari a kauyen Tadurga a karamar hukumar Zuru.

Mazauna kauyen sun shaida wa Abbakar Aleeyu Anache cewa yan bindigar sun kai harin ne a kan babura sama da 100 tare da bude wa wuta ga al'ummar kauyen da misalin karfe 7 na daren ranar Litinin.

Wasu mazauna yankin sun ce sak**akon tsananin tashin hankali wasu sun tsere cikin daji wasu kuma yan bindigar sun tafi da su.

Kebbi na daya daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalolin rashin tsaro da hare-haren yan bindiga.

📸 Abbakar Aleeyu Anache

YANZU-YANZU: An sami hargitsi bayan da Ganduje ya bayyana goyon bayan tazarcen Tinibu ba tare da Kashim baAn samu rikici...
15/06/2025

YANZU-YANZU: An sami hargitsi bayan da Ganduje ya bayyana goyon bayan tazarcen Tinibu ba tare da Kashim ba

An samu rikici a taron shugabannin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na Arewa maso Gabas da aka gudanar a ranar Lahadi, bayan da Comrade Mustapha Salihu, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na Kasa a yankin, ya gaza ambaton sunan Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima yayin da yake goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya sake tsayawa takara karo na biyu.

Taron, wanda aka gudanar a jihar Gombe, ya samu halartar ministoci, 'yan majalisa, da gwamnoni kusan duka daga yankin.

Abdullahi Ganduje, Shugaban Jam’iyyar na Kasa, shima ya jagoranci wasu manyan mutane zuwa taron.

Lokacin da aka bawa Salihu damar yin jawabi, ya bayyana goyon bayansa ga Tinubu domin ya tsayawa takara a matsayin dan takarar jam’iyyar ba tare da hamayya ba — amma bai ambaci Shettima ba kwata-kwata.

Da zarar ya gama jawabin sa, wakilan taron s**a fara zagin sa da fadin kalmomi masu zafi, wasu ma suna barazanar kai masa hari. Dole jami’an tsaro s**a rako shi s**a fitar da shi daga wurin taron.

Domin kwantar da tarzoma, Bukar Dalori, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na Kasa, ya fito ya bayyana goyon bayan sa ga Tinubu da Shettima duka domin su ci gaba da mulki.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Shettima dan jihar Borno ne, daya daga cikin jihohin Arewa maso Gabas.

Ganduje ma bai ambaci Shettima ba

Taron ya rabu da wuri bayan da Shugaban Jam’iyyar na Kasa, Abdullahi Ganduje, shima ya bayyana goyon bayan sa ga Tinubu kadai, ba tare da ambaton Shettima ba.

Wakilinmu ya bayyana cewa Ganduje bai ambaci sunan Shettima ko sau daya ba a cikin jawabin sa da ya dauki kusan minti 10.

Dole shima jami’an tsaro s**a fitar da shi daga wurin bayan taron

2027: Abin Da Obi Zai Iya Samu Mafi Girma Shi Ne Ya Zama Mataimakin Atiku – Cewar Deji AdeyanjuFitaccen dan gwagwarmaya ...
11/06/2025

2027: Abin Da Obi Zai Iya Samu Mafi Girma Shi Ne Ya Zama Mataimakin Atiku – Cewar Deji Adeyanju

Fitaccen dan gwagwarmaya Kuma mai sharhi kan al’amuran siyasa, Deji Adeyanju, ya yi hasashen cewa a zaben 2027 da ke tafe, mafi abin da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, zai iya samu shi ne ya zama mataimakin Atiku Abubakar.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Adeyanju ya bayyana cewa ’yan siyasar Arewa ne kadai a halin yanzu da ke da karfin da za su iya kalubalantar shugaba mai ci, Bola Ahmed Tinubu, a babban zaben da ke tafe.

“Abin da Obi zai iya samu mafi yawa a 2027 shi ne ya zama mataimakin Atiku,” in ji Adeyanju. “Atiku da sauran ’yan siyasar Arewa yanzu su ke da dukkan katunan nasara. ’Yan Obidient suna cikin ruɗani; har yanzu ba za su gane halin da ake ciki ba, duk da rubutun da ke bango.”

Wannan furuci ya janyo cece-kuce daga masu sharhi da magoya bayan jam’iyyu, wasu na ganin hakan wata alama ce ta kira ga hadin gwiwa tsakanin Atiku da Obi, yayin da wasu kuma ke kallon hakan a matsayin rage girman tasirin Obi a siyasar kasar.

Peter Obi, wanda ya zo na uku a zaben 2023, bai bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara ba tukuna, amma magoya bayansa da ake kira “Obidients” na ci gaba da nuna kwarin guiwa da goyon baya.

Sai dai a cewar Adeyanju, lissafin siyasa da karfin gwiwar jam’iyyu ya fi karkata ga Arewa da manyan ‘yan siyasa irin su Atiku da Tinubu.

Yayin da siyasar 2027 ke kara daukar salo, tattaunawa kan hadin kai, tasirin kabilanci da matsayi a siyasarmu na ci gaba da daukar hankali a kasar.

Ambaliyar Mokwa: Bago ya bukaci mazauna kogi da su kaura, ya ba da gudummawar Naira Biliyan daya da filaye don sake tsug...
09/06/2025

Ambaliyar Mokwa: Bago ya bukaci mazauna kogi da su kaura, ya ba da gudummawar Naira Biliyan daya da filaye don sake tsugunar da wadanda abin ya shafa.

Daga Abbakar Aleeyu Anache

Gwamna Muhammad Umaru Bago na Jihar Neja ya yi kira ga mazauna yankunan koguna da ke fadin jihar da su gaggauta ficewa daga wadannan wurare masu rauni domin kare afkuwar asarar rayuka da dukiyoyi, sak**akon mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a Mokwa.

Gwamna Bago ya dawo daga Saudiyya a ranar Lahadin da ta gabata ya ziyarci garin da ambaliyar ruwa ta shafa, ya kuma yi Allah wadai da wannan bala’in, yana mai bayyana lamarin a matsayin wani bala’i da jihar Neja ta fuskanta a wannan shekarar.

A wani nuna hadin kai, Gwamnan ya bayar da tallafin Naira biliyan daya domin tallafawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.

Ya kuma umurci ma’aikatar filaye ta Jiha da ta ware filaye mai yawa tare da bayar da takaddun shaidar zama ga Gwamnatin Tarayya don shirin sake tsugunar da mutanen da bala’in ya raba da muhallansu.

Ƴansanda sun k**a ƴan bindiga su na kokarin sayen AK-47 a KanoRundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta k**a wasu mutane hudu da...
09/03/2025

Ƴansanda sun k**a ƴan bindiga su na kokarin sayen AK-47 a Kano

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta k**a wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan fashin daji waɗanda ake zargin suna kan hanyarsu ta sayen bindigar AK-47.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna, ya tabbatar da cafke waɗanda ake zargin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

A cewarsa, rundunar ta samu gagarumar nasara a kokarinta na dakile yaduwar ‘yan fashin daji da miyagun laifuka a jihar.

Ya ce, “A ranar 6 ga Maris, 2025, da misalin karfe 2:00 na rana, wata tawagar jami’an bincike na ‘yansanda ƙarƙashin jagorancin SP Ahmad Abdullahi, jami’in da ke kula da ofishin 'yansanda na Jar Kuka, sun cafke wasu mutane hudu da ake zargi da zama ‘yan bindiga a gidan man Chula dake Hotoro a Kano.

“Waɗanda aka k**a sun haɗa da Shukurana Salihu, mai shekara 25; Rabi’u Dahiru, mai shekara 35; da Ya’u Idris, mai shekara 30, duk daga Jihar Katsina, da kuma Muktar Sani, mai shekara 30, daga Yandodo Hotoro , Kano. An k**a su ne bisa sahihan bayanan sirri da s**a nuna cewa sun zo Kano da niyyar sayen bindigar AK-47.”

Kiyawa ya de an samu wannan nasara ne sak**akon biyayya ga umarnin Sufeto-Janar na Ƴansanda, Kayode Adeolu Egbetokun, ga dukkanin rundunonin ƴansanda kan wani sabon salo na yaƙi da ta'addanci da laifuka a fadin ƙasar.

Ya kara da cewa an samu mak**ai, da harsashi da guru da layu da ƴaƴan boris da kuma kudi kimanin Naira Miliyan 1 da dubu 28 a tare da waɗanda ake zargin.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa ya bar jam’iyyar PDP.Dan takarar shuga...
09/03/2025

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin da ke cewa ya bar jam’iyyar PDP.

Dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023 ya sake jaddada goyon bayansa ga hadakar jam’iyyun siyasa don kayar da jam’iyyar APC a 2027.

Daily Trust ta rawaito cewa, a baya-bayan nan, rahotanni daban-daban sun nuna cewa Atiku yana tunanin barin PDP don shirin takarar shugaban kasa a 2027.

Rahotannin sun ce yana shirin komawa jam’iyyar SDP.

Amma a cikin wata sanarwa da ofishin yada labaransa ya fitar a ranar Asabar, an bayyana cewa tsohon mataimakin shugaban kasar na nan a matsayin cikakken mamba na PDP.

Yayin da yake karyata rahotannin a matsayin “karya tsagwaronta”, ofishin yada labaran ya bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da su.

Ofishin yada labaran ya jaddada cewa Abubakar ya dade yana kira da a hada kawancen jam’iyyun adawa a Najeriya domin cire APC daga mulki a 2027.

Babu dalilin da Ƴan Najeriya za su sayi man fetur da tsada - Sanata NdumeƊan Majalisar Dattawan Najeriya daga Jihar Born...
07/03/2025

Babu dalilin da Ƴan Najeriya za su sayi man fetur da tsada - Sanata Ndume

Ɗan Majalisar Dattawan Najeriya daga Jihar Borno, Sanata Muhammed Ali Ndume ya ce babu dalilin da ƴan Najeriya za su dinga sayen man fetur da tsada, alhali a cikin ƙasar ake haƙo shi.

Ndume ya bayyana cewar tamkar yaudara ake yiwa jama'ar ƙasar da sunan tallafi, ko kuma sayar da man da ake samunsa a gida da tsada ga ƴan kasa.

Sanatan ya bayyana man k**ar ruwan da ake haƙowa ta hanyar rijiyar birtsatsai, wanda bayan tona shi, babu abin kashe kudin da ya wuce sayen man da za'a sanyawa inji domin deɓo shi.

Ɗan Majalisar ya ce shi ya kasa fahimtar dalilin da ƴan Najeriya za su biya kuɗi da tsada domin cin gajiyar arzikin man da ake samar da shi a gida, da kuma tace shi domin amfanin jama'a, yayin da ya yiwa watsi da batun biyan tallafin da ake ta mahawara akai.

Ndume ya kuma bayyana damuwa akan irin zagon ƙasar da ya ce ake yiwa attajiri Aliko Ɗangote da ya samar da matatar man da ake cin gajiyarta ayau.

📷 RFI Hausa

Magidanci ya rasu ana tsaka da Sallah a Abuja Wani magidanci mai suna Salihu Byezhe mai shekaru 52 ya rasu bayan ya yank...
07/03/2025

Magidanci ya rasu ana tsaka da Sallah a Abuja

Wani magidanci mai suna Salihu Byezhe mai shekaru 52 ya rasu bayan ya yanke jiki ya faɗi ana tsaka da sallar asuba a wani masallaci da ke kauyen Gudaba a karamar hukumar Kuje a babban birnin tarayya, Abuja.

Shedun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne a jiya Alhamis bayan da Byezhe ya gama yin Sahur, sai ya yi alwala, sannan ya shiga Masallacin ya bi jam'i.

“Ana ci gaba da Sallah,bkawai sai ya fadi ba zato ba tsammani, nan dai ƴan uwa a masallacin su ka yi gaggawar kai shi asibiti. Ya na ta numfashi a hanya, amma ana karasa wa asibitin likita ya ce ya rasu,” in ji Dantani.

Wani likita a asibitin da ke Kuje daga baya ya tabbatar da mutuwar Byezhe, yana mai alakanta cutar hawan jini.

Wakilinmu Leadership ya tattaro cewa marigayin ya kasance yana ciwon hawan jini.

An yi jana’izar sa da misalin karfe 10:12 na safiyar juya Alhamis k**ar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kaduna ta bayar da umarnin kwace wasu makudan kudade har biliyan N1.37bn...
06/03/2025

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kaduna ta bayar da umarnin kwace wasu makudan kudade har biliyan N1.37bn na wucin gadi, wadanda ake zargin an karkatar da su daga asusun gwamnatin jihar zuwa wani asusu na sirri a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Nasir El-Rufai.

Address

Behind Old Local Government Building Malumfashi
Malumfashi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GVC News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to GVC News:

Share