21/12/2025
DA DUMI-DUMI: Asirin EFCC da Malami Ya Fallasa Ya Haifar da Rikicin Ramuwar Gayya A Kansa
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC) na fuskantar zargi da gudanar da ramuwar gayya ta kashin kai kan tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a na Ƙasa, Abubakar Malami, SAN, biyo bayan fitar da wata sanarwa da ya yi dangane da Babi na 9 na Rahoton Kwamitin Binciken Shari’a karkashin jagorancin Mai Shari’a Ayo Salami.
Rahoton, wanda aka ce an rufe shii tsawon lokaci, na zargin Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, da aikata laifuffukan almundahana ta kuɗi da cin zarafin ofis. Ofishin Malami ya bayyana cewa samamen da EFCC ta kai kwanan nan kan ofisoshinsa da gidajensa na sirri da ke Abuja da Jihar Kebbi, martani ne kai-tsaye ga kiran da Malami ya yi na Olukoyede ya janye daga shugabancin EFCC saboda zargin son kai da nuna bangaranci.
Samamen, waɗanda aka ce ba tare da sanarwa ba, sun fi karkata ne wajen neman takardu da s**a shafi Babi na 9 na rahoton, lamarin da ya haifar da damuwa game da tsoratarwa, ramuwar gayya, da barazanar tsaro ga Malami da ma’aikatansa. Ofishin Malami ya bayyana matakin EFCC a matsayin “tsoratarwa da aka tsara tun da fari”, da kuma yunƙurin tozarta gaskiya da hana ta fitowa fili.
Majiyoyi sun ce Babi na 9 na Rahoton Kwamitin Ayo Salami na ƙunshe da manyan zarge-zarge masu nauyi kan Olukoyede, ciki har da cin hanci, amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba, da hana adalci gudana.
Rahoton ya kuma zargi Olukoyede da shiga yarjejeniyoyi masu duhu, ciki har da ba da manyan kwangiloli ga abokansa da ’yan uwansa.
Ofishin Malami ya ce matakan EFCC wani yunƙuri ne na rufe baki da hana shi fitar da cikakken rahoton. “Matakan EFCC hujja ce a sarari cewa suna da abin ɓoyewa,” in ji Mohammed Bello Doka, Mataimakin Malami kan Harkokin Yaɗa Labarai.
“Ba za mu yarda a tsoratar da mu ko a rufe bakinmu ba. Za mu ci gaba da gwagwarmayar gaskiya da rikon amana.”
EFCC ta musanta dukkan zarge-zargen, tana mai cewa samamen wani ɓangare ne na binciken da take gudanarwa kan Malami. Sai dai ofishin Malami ya nuna shakku sosai, yana mai cewa lokacin da aka kai samamen yana da matuƙar alamar tambaya.
“Muna tambayar lokaci da izinin da aka yi amfani da su wajen wadannan binciken,” in ji Doka.
“Me ya sa aka jira sai bayan mun fitar da sanarwarmu kan Babi na 9? Me suke ƙoƙarin ɓoyewa?”
Lamarin ya jawo ƙorafe-ƙorafe daga kungiyoyin farar hula da masu kare haƙƙin ɗan Adam, inda s**a nemi a gudanar da bincike mai zaman kansa kan ayyukan EFCC.
“Wannan bayyanannen cin zarafin iko da tsoratarwa ne,” in ji kakakin Human Rights Writers Association of Nigeria (HURIWA).
“Muna neman Shugaban EFCC ya sauka daga mukaminsa domin a yi bincike cikin adalci.”
Yayin da rikicin ke ƙara kamari, Malami ya jaddada cewa yana shirye ya fuskanci ingantaccen tsarin doka mai zaman kansa, yana mai cewa tsoratarwa da shari’ar kafafen yaɗa labarai ba za su maye gurbin adalci ba.
Hakan ya kuma haifar da tambayoyi game da ’yancin cin gashin kan EFCC da kuma iya gudanar da bincike cikin adalci.
“Idan aka bar EFCC ta ci gaba da wannan hanya, hakan zai lalata tsarin mulki da amincewar jama’a,” in ji wani babban lauya.
Haka kuma an nuna damuwa kan lafiyar Malami da ma’aikatansa, inda ofishinsa ya ce EFCC za ta ɗauki alhakin duk wani abu da ya same su.
Yayin da rikicin ke ci gaba, ’yan Najeriya na ci gaba da tambaya, “Wane sirri ne EFCC ke ƙoƙarin ɓoyewa a Babi na 9?”
An kuma ƙara kiran Olukoyede ya ajiye mukaminsa, domin bai wa bincike damar gudana cikin adalci.
“Idan babu abin ɓoyewa, ya kamata ya sauka gefe,” in ji wani fitaccen ɗan siyasa.
Kungiyar Lauyoyin Najeriya (NBA) ma ta soki EFCC, tana zargin ta da cin zarafin iko da take hakkin doka.
A ƙarshe, an bukaci gwamnati ta shiga tsakani domin tabbatar da cewa EFCC ba ta zama kayan tsangwama na siyasa ba.