AREWA FRESH 11

AREWA FRESH 11 An bude wannan Gidan Jaridar na AREWA FRESH ne domin kawo abubuwan da ke faruwa a Arewacin Nijeriya da fadin kasar hadi da labaran kasashen ƙetare

YANZU-YANZU: Jarumar Kannywood Fiddausi Yahaya ta saki sabbin hotunan ta masu daukar hankali domin faranta ran masoyanta...
15/11/2025

YANZU-YANZU: Jarumar Kannywood Fiddausi Yahaya ta saki sabbin hotunan ta masu daukar hankali domin faranta ran masoyanta

Wace fata zaku mata?

YANZU-YANZU: Wani Matashi Dan Kwankwasiya Ya Yaba Kan Tausayi Da Jin Kai Ga Talakawa Da Fahad Dankabo Ke Nunawa Al'ummar...
02/11/2025

YANZU-YANZU: Wani Matashi Dan Kwankwasiya Ya Yaba Kan Tausayi Da Jin Kai Ga Talakawa Da Fahad Dankabo Ke Nunawa Al'ummar sa Ta Gwarzo Da Kabo Dake Jahar Kano

Wani masoyin matashin ɗan siyasa, Fahad Dankabo, ya bayyana cewa kyawawan halayen Fahad Dankabo da ayyukan alherinsa sun yi dai-dai da irin salon da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-gida) ke nunawa ga al’umma.

Bayanin Hakan Ya Biyo Bayan wani taimakon gaggawa da Dan siyasar ya kaiwa wani masoyinsa Sadiq a asibiti bayan jarrabawar Hatsari ta sameshi.

Masoyin ya ce Fahad Dankabo mutum ne mai kishin jama’a, mai saukaka wa mutane da kuma taimakawa jama’a ba tare da nuna bambanci ba.

Ya ƙara da cewa irin wannan hali na tausayi da taimako shi ne yake ƙara janyo ƙauna daga matasa da jama’a baki ɗaya, wadanda suke ganin zai taka rawar gani a harkokin siyasa a nan gaba.

Masoyin ya kuma yi addu’ar Allah ya ƙara masa juriya, basira da ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri domin ci gaban Kano da Najeriya baki ɗaya.

YANZU-YANZU: Ƙungiyar RHAYEI ta naɗa Kwamishinan Muhalli na Katsina, Hon. Suleiman Hamza, a matsayin Grand Patron na Kam...
01/11/2025

YANZU-YANZU: Ƙungiyar RHAYEI ta naɗa Kwamishinan Muhalli na Katsina, Hon. Suleiman Hamza, a matsayin Grand Patron na Kamfen ɗin “10 Million PVC Enrolment Campaign”

Ƙungiyar Renewed Hope Arewa Youth Engagement Initiative (RHAYEI) ta sanar da naɗin Hon. Suleiman Hamza (Wamban Faskari), Kwamishinan Muhalli na Jihar Katsina, a matsayin Grand Patron na shirin “10 Million PVC Enrolment Campaign for President Bola Ahmed Tinubu and Governor Dikko Umar Radda.”

An gudanar da bikin naɗin ne jiya a birnin Katsina, inda manyan jami’an gwamnati, shugabannin matasa, da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa s**a halarta. Taron ya kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin kai da wayar da kan matasa kan muhimmancin mallakar katin zabe (PVC) a shirye-shiryen zabubbuka masu zuwa.

A yayin taron, Barr. Usman Rosi, Esq., Kodineta na Arewa maso Gabas na ƙungiyar RHAYEI, ya bayyana cewa naɗin Hon. Suleiman Hamza ya zo a kan lokaci kuma yana da muhimmanci wajen nuna irin rawar da yake takawa wajen ƙarfafa matasa, kare muhalli, da gina dimokuraɗiyya mai ɗorewa a Najeriya.

Ya ce manufar wannan kamfen ita ce wayar da kai da haɗa matasa miliyan goma (10 million) daga jihohin Arewa 19 domin su mallaki PVC kafin zabubbukan da ke tafe.

Barr. Rosi ya jaddada cewa jajircewa, hangen nesa da kishin al’umma da Hon. Hamza ke da shi za su ƙara ƙaimi ga ƙungiyar wajen isar da saƙon ta da kuma ƙarfafa shiga siyasa, musamman a tsakanin matasa.

A nasa jawabin bayan karɓar takardar naɗin, Hon. Suleiman Hamza ya nuna godiya bisa wannan girmamawa, inda ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya domin ganin an cimma nasarar kamfen ɗin 10 Million PVC Enrolment Campaign.

Ya kuma jaddada muhimmancin wayar da kan masu zabe, fahimtar siyasa, da haɗin kai tsakanin matasa, domin ci gaba da tabbatar da manufar Renewed Hope ta gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Takardar naɗin ta fito daga Kodineta na Arewa maso Gabas, Barr. Usman Rosi, Esq., kuma an sanya hannu a hukumance daga Barr. Aisha Garba, Esq., a madadin jagorancin ƙasa na ƙungiyar Renewed Hope Arewa Youth Engagement Initiative (RHAYEI).

Ƙungiyar RHAYEI na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen haɗa matasan Arewacin Najeriya domin shiga harkokin siyasa, haɓaka jagoranci, da gina dimokuraɗiyya mai ɗorewa bisa tsarin Renewed Hope Agenda.

Kwararren ɗan siyasa, Engr. Nuraini Adamu, na neman kujerar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Karu, Keffi da Kokona a ƙ...
29/10/2025

Kwararren ɗan siyasa, Engr. Nuraini Adamu, na neman kujerar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Karu, Keffi da Kokona a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Al’ummar yankin Karu sun nuna cikakken goyon baya da amincewarsu ga Engr. Nuraini Adamu bisa jajircewarsa, hazakarsa, da jajircewar da yake nunawa wajen kawo cigaba ga matasa da al’umma baki ɗaya.

Engr. Nuraini Adamu wanda aka sani da kishin al’umma da nuna gaskiya a aikinsa, ya bayyana cewa idan Allah Ya bashi nasara a zaben 2027, zai mayar da hankali wajen:

Ƙirƙirar guraben ayyukan yi ga matasa, ta hanyar bunƙasa sana’o’in hannu da fasahar zamani. Tare da tallafa wa mata da kananan ‘yan kasuwa domin su samu damar bunƙasa harkokinsu.

Engr ya kara da cewa zai Inganta harkar ilimi ta hanyar samar da tallafin karatu da gina cibiyoyin ilimi na zamani. Kawo ci gaba a fannin lafiya da ruwa, musamman a ƙauyuka da yankunan da ke buƙatar taimako.

Bugu da kari zai sanar da Haɗa kai da sauran ‘yan majalisa domin tabbatar da cewa yankin Karu, Keffi da Kokona ya samu wakilci na gaskiya da ci gaba mai ɗorewa.

A cewar wasu daga cikin magoya bayansa, Engr. Nuraini Adamu mutum ne mai hangen nesa, jajircewa, da ƙaunar al’umma, wanda idan ya samu dama zai kawo canji mai ma’ana ga yankin.

“Ba mu da wata shakka, Engr. Nuraini Adamu ne zabin da ya dace domin cigaban mu da makomar matasan mu,” in ji wani ɗan asalin Karu da ke cikin masu goyon bayansa.

ZAƁE;- Kungiyar Matasan Kasuwan Chancaga Sun Shiryawa Dr. Mustapha Alheri, Gagarumin Yaƙin Neman Zaɓe.A ranar Alhamis da...
29/10/2025

ZAƁE;- Kungiyar Matasan Kasuwan Chancaga Sun Shiryawa Dr. Mustapha Alheri, Gagarumin Yaƙin Neman Zaɓe.

A ranar Alhamis da ta gabata ne kungiyar matasan kasuwa ta ƙaramar hukumar Chancaga (Youth Marketers Movement Association) ƙarƙashin jagorancin mataimakin Shugaban ta, Malam. Ahmed Mashiru, sun shirya gagarumin taron yaƙin neman zaɓe ga ɗan takarar kujerar ƙaramar hukumar Chancaga a jam'iyyar APC.

Ahmed Mashiru, ya shirya gagarumin taron ne a ɗakin taro na Maryam Babangida Children Center dake Minna, Matashin yayi kira ga 'yan kasuwar Chancaga da su zaɓi Dr. Alheri, a zaɓen dake tafe ranar Asabar 01/011/2025 domin yanada kyawawan manufa ga 'yan kasuwa.

Ahmad Adamu Bagas 🖊️

TIRKASHI: Yadda wani fusataccen dattijo, ya dauke allon bankin ’Acces’ da aka rubuta ba a tsayuwa, ya yi hakane saboda c...
27/10/2025

TIRKASHI: Yadda wani fusataccen dattijo, ya dauke allon bankin ’Acces’ da aka rubuta ba a tsayuwa, ya yi hakane saboda cire masa 'yan kwabbai da bankin ke yi daga asusun ajiyarsa ba gaira babu dalili.

TIRKASHI:An Gano Ɗaya daga cikin manyan Jaruman Masana'antar Kennywood masu koyar da Tarbiyya, Maryam Yahaya a Dakin Wan...
26/10/2025

TIRKASHI:An Gano Ɗaya daga cikin manyan Jaruman Masana'antar Kennywood masu koyar da Tarbiyya, Maryam Yahaya a Dakin Wani Hotel a Kano.

Zargi na ta bayyana a kanta kan mummunan rashin lafiyar da tayi kwanakin baya.

SHU'AIBU LAWAN KUMURCI: Shi Ne Jarumin Da Bai Taba Shiga Rigima A Masana'antar Fim Ba1. Shi ne jarumin da ba ya faɗa kum...
24/10/2025

SHU'AIBU LAWAN KUMURCI: Shi Ne Jarumin Da Bai Taba Shiga Rigima A Masana'antar Fim Ba

1. Shi ne jarumin da ba ya faɗa kuma ba a faɗa da shi.

2. Shi ne jarumin da ba shi da account ko ɗaya a soshiyal midiya.

3. Jarumin da ya auri ƴar Kannywood marigayiya Balaraba

4. Kowa nasa ne a Kannywood.

5. Shekarunsa 25 a cikin masana'antar.

6. Mutumin kirki ne yana da mu'amala mai kyau, kuma ba ya wasa da sallah, da an kira sallah zai bar abin da yake yi ya je ya yi sallah

Wane fata za ku yi masa?

ALLAHU AKBAR: Sheikh Dahiru Usman Bauchi Ya Zama Malami Mafi Yawan Dalibai a Fadin Afirka — In Ji Binciken MasanaWani ra...
22/10/2025

ALLAHU AKBAR: Sheikh Dahiru Usman Bauchi Ya Zama Malami Mafi Yawan Dalibai a Fadin Afirka — In Ji Binciken Masana

Wani rahoton bincike daga masana addini da ilimi a nahiyar Afirka ya tabbatar da cewa Sheikh Dahiru Usman Bauchi ne malami guda da ke da yawan dalibai da mahaddatan Al-Kur’ani fiye da kowane malami a yankin.

Masana sun bayyana cewa, wannan nasara ta Sheikh Dahiru Bauchi ta samo asali ne daga tsawon shekaru na hidima ga ilimin addini, karatun Al-Kur’ani, da kuma wa’azin da ya shimfiɗa ko’ina cikin Afirka.

Sheikh Dahiru Bauchi ya kasance jigo a harkar ilimi da karantarwa, kuma ya kafa makarantu masu tarin yawa da s**a samar da dubban hafizai da malamai da ke yada ilimi a sassa daban-daban na duniya.

A yayin da rahoton ya ke yawo a kafafen sada zumunta, mutane da dama sun rika bayyana fatan alheri da addu’o’in samun karin lafiya, tsawon rai da ƙarfafa masa gwiwa wajen ci gaba da hidima ga addini.

“Allah Ya ƙara masa lafiya, Ya tsawaita rayuwarsa cikin albarka, Ya ba shi ikon ci gaba da jagorantar al’umma bisa tafarkin Al-Kur’ani da Sunnah.”

YANZU-YANZU: Masana'antar Kennywood ta yi sabuwar Jaruma, sai dai har zuwa yanzu bamu san sunan ta ba.Ko zaku iya bayyan...
22/10/2025

YANZU-YANZU: Masana'antar Kennywood ta yi sabuwar Jaruma, sai dai har zuwa yanzu bamu san sunan ta ba.

Ko zaku iya bayyana mana sunan ta?

MU TATTAUNA: Me yasa mafi yawan Matan Kannywood suke Saurin Yin Kudi akan Mazan?
20/10/2025

MU TATTAUNA: Me yasa mafi yawan Matan Kannywood suke Saurin Yin Kudi akan Mazan?

TIRKASHI: Duk wanda ya ce wai ƴan Kannywood fadakarwa suke yi a finafinansu to ya ɗauki ƴarsa ya kai wa Ali Nuhu, Cewar ...
20/10/2025

TIRKASHI: Duk wanda ya ce wai ƴan Kannywood fadakarwa suke yi a finafinansu to ya ɗauki ƴarsa ya kai wa Ali Nuhu, Cewar Jikan Malam

Me za ku ce?

Address

Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA FRESH 11 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share