AREWA FRESH 11

AREWA FRESH 11 An bude wannan Gidan Jaridar na AREWA FRESH ne domin kawo abubuwan da ke faruwa a Arewacin Nijeriya da fadin kasar hadi da labaran kasashen ƙetare

21/09/2025

Gaskiyar Matana ta fito, Yaudarar Da Kansilar Abubakar Nuhu Doro yiwa uban gidan sa ta fito fili, wanda mugunta yasa s**a k**a dan jarida. PART 1

Daga Rariya Online

DA ƊUMI-ƊUMI: Biyo Bayan Sulhu, Ɗan Bindiga Isya Kwashen Garwa Ya Sako Mutum 40 a Faskari, Katsina Ɗan bindiga Isya Kwas...
19/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Biyo Bayan Sulhu, Ɗan Bindiga Isya Kwashen Garwa Ya Sako Mutum 40 a Faskari, Katsina

Ɗan bindiga Isya Kwashen Garwa ya sake sako mutum 40 dake hannunsa a ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina, bayan wani zaman sulhu da aka gudanar tsakaninsa da jami’an tsaro da shugabannin al’umma.

A ranar Laraba ma dai, waɗannan yan bindiga sun saki mutum 30, wanda idan aka haɗa da na yau, adadin ya kai mutum 70 da aka sallama daga hannunsu cikin kwanaki kaɗan.

Sai dai a wata sanarwa da Isya Kwashen Garwa ya fitar, ya nuna damuwa kan wani farmaki da ya zargi dakarun sojojin Najeriya da kai musu yau a kauyen Ruwangodiya a lokacin da ake gudanar da sallar Jumu’a.

Ya gargadi cewa, muddin hare-haren kan ’yan uwansu ya ci gaba, za su iya sake yin watsi da alƙawuran zaman lafiya da aka kulla da su.

Al’amuran sulhu da ’yan bindiga a yankin Katsina na ci gaba da jawo cece-kuce tsakanin al’umma, musamman kan tasirin su ga tsaron jama’a.

Karin bayanai na cigaba da bayyana kan badakalar kudin da dan jarida ya tona asirin wani kansila a jahar katsina.
18/09/2025

Karin bayanai na cigaba da bayyana kan badakalar kudin da dan jarida ya tona asirin wani kansila a jahar katsina.

Yadda Kotun Majistiri dake Katsina ta Aika da Dan Jarida Gidan Yari Saboda Zargin Fallasa Damfarar Kansilan Gundumar Dor...
18/09/2025

Yadda Kotun Majistiri dake Katsina ta Aika da Dan Jarida Gidan Yari Saboda Zargin Fallasa Damfarar Kansilan Gundumar Doro

A yau kotun majestire mai lamba biyu dake katsina ta aika da Editan jaridar Leadership Online Newspaper zuhair Ali Ibrahim gidan yari bisa bukatar yan sanda na ajiye shi har sai an gama binciken wani korafin da kansilan Doro dake karamar hukumar Bindawa Abubakar Nuhu ya shigar akan sa.

Kansilan ya shigar da korafin ne, akan wani labari da Jaridar leadership Hausa Online ta rubuta a ranar 7 ga watan satumba inda wani mai suna Alhaji Ibrahim sa'adu yayi korafi da ikirarin kansilan Doro Abubakar Nuhu ya canye masa wasu kudin sa har naira milyan talatin. (30M)

A labarin da Jaridar ta buga tace Alhaji Ibrahim sa'adu ya bayyana cewa shi Ubangidan kansilan ne,kuma ya sha taimakonshi ya kuma yarda dashi amma yayi amfani da wannan yardar wajen damfarar shi k**ar yadda yayi zargi.

Editan yayi kokarin jin ta bakin kansilan Abubakar Nuhu amma abin yaci tura don haka s**a buga labarinsu a bisa ana zargin kansilan Abubakar Nuhu .

Kansilan Abubakar Nuhu ya kai kara wajen yan sanda inda aka je har zaria aka kamo zuhair a ranar litinin din data gabata zuhair ya fada ma yan sanda duk yadda ya samu labarin shi da kokarin shi na jin ta bakin kansilan amma abin yaci tura.

Wasu mutane a katsina sunyi kokarin shiga maganar don dai daitawa amma kansilan ya rika Saba alkawalin da ya dauka na janye maganar da sasantawa.

Mutanen da s**a shiga maganar don sansantawa sune Mai ba Gwamnan Katsina Dr. Dikko Umaru Radda shawara akan harkokin jam'iyyu Alhaji shafi i Duwan, sai Dan majalisar tarayya mai wakiltar Mani da Bindawa, sai Alhaji yusufu Ibrahim jargaba sai kuma Malam Danjuma katsina .

Kansilan sai ya amsa za a dai daita amma kuma ya Saba alkawalin, Kansilan yana neman tozarta Editan na leadership online newspaper bisa wata bukatar kashin kanshi, ko kuma don ya tsorata marubuta su bar fallasa komai nashi.

Dr. Dikko Umaru Radda

TIRKASHI: Dubban jama’a sun ci gaba da arcewa daga Arewacin Gaza, sak**akon sabon gargadin Isra’ila na kai hare-haren ƙa...
15/09/2025

TIRKASHI: Dubban jama’a sun ci gaba da arcewa daga Arewacin Gaza, sak**akon sabon gargadin Isra’ila na kai hare-haren ƙasa da sama.

Rahotanni daga hukumar lafiya sun tabbatar da cewa sama da mutum miliyan ɗaya na fuskantar mummunar barazanar yunwa a yankin Gaza.

TIRKASHI: “Ina Tabbata Muku mu Fulani mun fi Hausawa Imani”, Dan Bindiga Malam Isiya Yayin Sasanci a Faskarin jihar Kats...
15/09/2025

TIRKASHI: “Ina Tabbata Muku mu Fulani mun fi Hausawa Imani”, Dan Bindiga Malam Isiya Yayin Sasanci a Faskarin jihar Katsina

A yayin zaman sasanci da aka gudanar a karamar hukumar Faskari ta jihar Katsina, wani jagoran ‘yan bindiga da aka fi sani da Malam Isiya ya bayyana cewa Fulani sun fi Hausawa imani.

Malam Isiya ya ce, “idan muka yi fada da Hausawa, in s**a k**a mutanenmu kashe su suke yi, amma mu Fulani idan muka k**a dan imaninmu sai mu sako su.”

Wannan kalamai na Malam Isiya sun biyo bayan tattaunawar zaman sulhu da aka gudanar tsakanin al’ummomi da shugabannin kungiyoyin da ke addabar yankin.

Rahotanni sun bayyana cewa sasancin na da nufin kawo karshen rikice-rikice da hare-haren da s**a dade suna addabar al’ummar yankin Faskari da kewaye.

14/09/2025

Ku zo mu kai gaisuwa ga shugaba Muhammadur Rasulullah SAWW

14/09/2025

ALBISHIRIN KU:AA Rano Gas Ingantaccen Gas Don Rayuwa Mai Sauƙi
Kamfanin AA Rano Gas ya zama ɗaya daga cikin manyan hanyoyin samar da iskar gas mai tsafta da inganci a Najeriya.

AA Rano Gas na bayar da sabis mai araha, mai sauri da kuma tabbacin tsaro ga gidaje da kasuwanci.
Masu amfani da kayayyakin kamfanin sun yaba da yadda gas ɗin yake da inganci, tare da samun sauƙin siye a duk inda aka samu rassa na kamfanin a fadin ƙasa.

AA Rano Gas na ci gaba da tabbatar da cewa abokan cinikin sa suna morewa:
✅ Gas mai tsafta
✅ Farashi mai sauƙi
✅ Tsaro da aminci

AA Rano Gas – Abokin amana, ingantaccen mafita ga girkin yau da kullum

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Rashin Kyawun Hanya Ya Yi Silar Mutuwar Iyalan Gidan Shehu Dauda Fass Har Su 19 , I...
14/09/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Rashin Kyawun Hanya Ya Yi Silar Mutuwar Iyalan Gidan Shehu Dauda Fass Har Su 19 , Inda Motar Su Ta Fada Cikin Rafi A Jihar Zamfara, Kusan Tsawon Shekara Biyar Kenan Ba A Gyara Gadar Ba

Allah Ya gafarta musu.

TIRKASHI: Mahaifin Jarudar TikTok Rahama Sa'idu ya ce ta fitar da mijin aure nan da kwana uku ko ya mata auren dole.
14/09/2025

TIRKASHI: Mahaifin Jarudar TikTok Rahama Sa'idu ya ce ta fitar da mijin aure nan da kwana uku ko ya mata auren dole.

KAJI KO: Kaf Masana'antar Kennywood babu wasu aminai da su ka kai Jarumi Sani Danja Da Yakubu Muhammad Amintaka tare da ...
14/09/2025

KAJI KO: Kaf Masana'antar Kennywood babu wasu aminai da su ka kai Jarumi Sani Danja Da Yakubu Muhammad Amintaka tare da hada kan ƴaƴan su waje daya.

In kuma akwai ku bayyana mana su.

ALLAHU AKBAR: Wannan shi ne Kabarin Annabi Yusuf (A.S) ɗa ga Annabi Yaƙub (A. S).Allah ya bamu Albarkacinsu
14/09/2025

ALLAHU AKBAR: Wannan shi ne Kabarin Annabi Yusuf (A.S) ɗa ga Annabi Yaƙub (A. S).

Allah ya bamu Albarkacinsu

Address

Malumfashi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA FRESH 11 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share