09/09/2026
Yau Shekaru 5 da Rasuwa: Tarihin Marigayi Sarkin Sudan na Kontagora, Sa’idu Namaska
Yau, 9 ga Satumba, 2026, shekaru biyar ke nan da rasuwar Marigayi Sarkin Sudan na Kontagora, Alhaji Sa’idu Umaru Namaska (CON), wanda ya rasu a ranar 9 ga Satumba, 2021, yana da shekaru 84.
Marigayi Sa’idu Namaska ya hau karagar Sarkin Sudan na Kontagora a shekarar 1974, inda ya shafe kusan shekaru 47 yana jagorantar masarautar har zuwa rasuwarsa. Wannan ya sanya shi cikin sarakunan da s**a dade suna kan karagar mulki a tarihin Masarautar Kontagora.
A tsawon mulkinsa, an san shi da hakuri, mutunci da kokarin hada kan al’umma, tare da taka rawa wajen zaman lafiya da ci gaban masarautar. A lokacin rasuwarsa, an bayyana shi a matsayin basaraken da ya yi tasiri wajen hada kan al’umma da kuma kula da al’adun masarautar.
Rasuwarsa ta kasance babban gibi ga Masarautar Kontagora, bayan kusan rabin karni da ya shafe a kan karagar sarauta. Shekaru biyar bayan rasuwarsa, har yanzu ana ci gaba da tunawa da shi da kyawawan halayensa da tarihin mulkinsa.
Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa, Ya sa Aljannatul Firdausi ce makomarsa. Amin.
Dame kuke tunada marigayi Maimartaba Sarkin Sudan?
Hasmag TV.