Niger State Media News24

Niger State Media News24 Niger State Media News24 Jarida ce a harshen Turanci da Hausa. Don kawo Ingantattun Labarai Da Kuma Labaran Wasu Jiha Zuwa Ga Ƴan Neja.

A Ranar Lahadi 09/08/2015 , Aka Bude Shafin Gidan Jaridar Niger State Media News24 A Dandalin Sada Zumunta Na Facebook

An Kafa Jaridar Yanar Gizo Na NIGER STATE MEDIA NEWS24 Ne Domin Isar Da Sahihan Labaran Jiha Ga Al-umman Jihar Neja Da Harshen Hausa Dana Turanci. An Kafa Tane Badon Wani Yareba, Duk Abun Da Ya Sami Wani Yare A Faɗin Jihar Neja Ko Wani Jiha za'amu Isar Da Saƙo Ga Ƴan Jihar Neja Domin Susan Abun Dake Faruwa A Najeriya Da Duniya Baki Ɗaya.

1. Niger State will establish 10 specialized Universities by 2027.2. Niger is set to plant 1 billion trees.3. We have cl...
16/08/2025

1. Niger State will establish 10 specialized Universities by 2027.

2. Niger is set to plant 1 billion trees.

3. We have cleared 1 million hectares of farmlands for cultivation.

4. We generated N600Bn in 2024 from agriculture.

5. We will rear 1M Cows and establish a Yoghurt factory.

6. We will sponsor 1000 students on foreign scholarships.

Add your own line of lies by the Governor to complete the list.😎

By Mohammed Munagi

16/08/2025

Jam'iyyar APC ta koka kan yadda ake tafka mata magudi, a zaben cike gurbi na jihar Kano.

DA DUMI-DUMI: Ko kuri’a daya jam'iyyar ADC ta su Atiku bata samu ba a wani akwati dake karamar hukumar Ganye jihar Adama...
16/08/2025

DA DUMI-DUMI: Ko kuri’a daya jam'iyyar ADC ta su Atiku bata samu ba a wani akwati dake karamar hukumar Ganye jihar Adamawa

APC = 64
PDP = 95
ADC = 0

Anya wannan hadaka ta ADC za ta kai labari kuwa?

Hotuna: Ziyarar dubiya da Shugaban Izala Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau da tawagarsa s**a kai ga Daraktan agaji na Izala ...
16/08/2025

Hotuna: Ziyarar dubiya da Shugaban Izala Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau da tawagarsa s**a kai ga Daraktan agaji na Izala mai helkwata a Jos, Alh Isa Waziri Gombe, domin rashin lafiya da yake fama da shi a gidansa dake birnin Gombe.

Cikin Tawagar shugaban akwai shugaban majalisar Malamai na ƙasa, Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo, babban sakataren ƙungiyar, Sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe, daraktan agaji na ƙasa, Sheikh Engr Mustapha Imam Sitti, Alaramma Ahmad Suleiman, Alaramma Nasiru Salihu Gwandu da shugaban JIBWIS na Jahar Gombe Engr Salisu Muhammad Gombe da sauran jama'a s**a raka Shugaban.

Allah ya bashi lafiya da sauran musulmai muminai masu lalura. Amin

Jibwis Nigeria

Hukumomin Tsaro Ta Najeriya Sun K**a Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ta’addanci Ta AnsaruHukumomin tsaro na Najeriya sun tab...
16/08/2025

Hukumomin Tsaro Ta Najeriya Sun K**a Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ta’addanci Ta Ansaru

Hukumomin tsaro na Najeriya sun tabbatar da cafke wasu manyan shugabannin ƙungiyar ta’addanci ta Ansaru, wacce ke da alaƙa da ƙungiyar Al-Qaida. Mai ba wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ne ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai da shugabannin tsaro na ƙasa s**a gudanar a Abuja.

Ribadu ya ce wannan nasara ta samu ne sak**akon bincike da dabarun hadin gwiwar jami’an tsaro, domin kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci a ƙasar.

Daga cikin wadanda aka k**a akwai Mahmud Muhammad Usman wanda aka fi sani da Abu Barra, da kuma Abubakar Abba wanda ake kira da Mahmud Al-Nigeri ko Malam Mamuda.

Ribadu ya ce cafke wadannan shugabannin na daga cikin manyan nasarorin da gwamnati ke samu wajen ragargazar ƙungiyoyin ta’addanci, tare da tabbatar da zaman lafiya da tsaro ga al’umma.

Angama Da Gundumomi Takwas (8 Wards) Daga Cikin Gundumomi 11 Dake Ƙaramar Hukuman Munya.Har Yanzu Ana Ci-gaba Da Ƙidaya....
16/08/2025

Angama Da Gundumomi Takwas (8 Wards) Daga Cikin Gundumomi 11 Dake Ƙaramar Hukuman Munya.

Har Yanzu Ana Ci-gaba Da Ƙidaya.

1. Daza Ward
APC: 1194
PDP:374
2. Kazai Ward
APC: 627
PDP: 283
3. DAN DAUDU Ward
APC: 1,476
PDP: 249
Voting ongoing at Central Pri.
4. Kuchi Ward
APC:1, 009
PDP: 670
5. Sarkin Pawa Ward

APC: 1308
PDP: 1248
6. Fuka Ward
APC 1,117
PDP 251
7. Dangunu Ward
APC total:1,298
PDP total:1,167
8. Gini Ward
APC: 1,712
PDP: 256

Sak**akon zaben gundumomi 5 cikin 10 da Ake dasu a karamar hukumar munya Jihar NejaZaben ciki gurbi na Dan majalisan Dok...
16/08/2025

Sak**akon zaben gundumomi 5 cikin 10 da Ake dasu a karamar hukumar munya Jihar Neja

Zaben ciki gurbi na Dan majalisan Dokokin Jihar Neja na Karamar Hukumar Munya

1. Gundumar Daza
APC: 1194
PDP:374
2. Gundumar Kazai
APC: 627
PDP: 283
3. Gundumar DAN DAUDU
APC: 1270
PDP: 249
4. Gundumar Kuchi
APC:1, 009
PDP: 670
5. Gundumar Sarkin Pawa
APC: 1308
PDP: 1248

Niger North APC Youth Forum Meets APC Zonal Chairman, Reaffirms Support for Governor Bago’s 2027 Re-ElectionThe Niger No...
16/08/2025

Niger North APC Youth Forum Meets APC Zonal Chairman, Reaffirms Support for Governor Bago’s 2027 Re-Election

The Niger North APC Youth Forum has paid a courtesy visit to the All Progressives Congress (APC) Zonal Chairman of Niger North, Alhaji Yahaya Borgu, at the party headquarters in Kontagora.

The delegation, led by the Forum’s Chairman, Comrade Umar Isah Karabonde, comprised executives and members of the group across eight local government of Zone C. During the meeting, they outlined their mission and objectives, which focus on youth development, political inclusion, and strengthening the APC in Niger State particularly Niger North.

Speaking at the meeting, the Chairman of the Forum, Comrade Karabonde commended Governor Mohammed Umar Bago for his people-oriented projects across Zone C and the entire state. He noted that the Governor’s initiatives in infrastructure, education, agriculture, and youth empowerment have brought remarkable progress to Niger State.

“We are fully committed to supporting Governor Bago,” he stated. “The Niger North APC Youth Forum will work tirelessly to ensure his re-election in 2027 so that he can continue his transformational agenda for the state.”

In his response, the APC Zonal Chairman of Niger North, Alhaji Yahaya Borgu, praised the Forum for their unity and dedication to the progress of youths and the party. He assured them of the party’s total support at the zonal, state, and government levels.

“The APC is proud of this Forum,” he said. “Your commitment to the growth of Niger North and the empowerment of our youths is commendable. Be assured that the party will stand firmly with you.”

The Forum also expressed deep appreciation to Alhaji Yahaya Borgu for the warm reception accorded to them. In recognition of his leadership and encouragement, the Niger North APC Youth Forum conferred on him the honorary position of Patron of the Forum.

Signed
Secretary

Babban Titin 'Trans-Sahara' Zai Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da Ƙarin Damar Tattalin Arziki – Minista IdrisMinistan Yaɗa Labarai ...
16/08/2025

Babban Titin 'Trans-Sahara' Zai Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da Ƙarin Damar Tattalin Arziki – Minista Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce an tsara babban titin 'Trans-Sahara' ne domin ƙarfafa haɗin gwiwar yankuna da buɗe damarmakin tattalin arziki.

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya wajen duba aikin wanda ake ci gaba da yi mai tsawon kilomita 118 da ya tashi daga Kalaba zuwa Ibonyi.

Ya bayyana babban titin a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnati da ake aiwatarwa a ƙarƙashin shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ministan ya bayyana cewa gina gada mai tsawon mita 700 da faɗin 12 a kan titin zai magance matsalar ambaliyar da ta daɗe tana addabar yankin Bakin Ruwa na N’dibe tare da dawo da damar zirga-zirga ga al’ummomin da abin ya shafa.

A cewar sa, yanzu ne karon farko da Jihar Ibonyi take samun manyan ayyuka masu yawa na Gwamnatin Tarayya a lokaci guda, wanda hakan alama ce ta jajircewar gwamnati wajen tabbatar da cigaba daidaitacce.

Haka kuma ya shawarci masu kwangilar aikin da su kiyaye inganci tare da hanzarta kammala aikin, yana tabbatar wa da jama'ar Nijeriya cewa gwamnati ta mayar da hankali kan ayyukan raya ƙasa da za su inganta rayuwa da hanyoyin samun abin dogaro a duk faɗin ƙasar nan.

Ana gina babban titin 'Trans-Sahara' ɗin ne ta hannun kamfanin Infouest Nigeria Limited a kan kuɗin da ya kai naira biliyan 445, kuma yana da shimfiɗar kankare mai ƙarfi, sannan ya haɗa Kalaba, Ibonyi, Binuwai, Nasarawa da Abuja.

Tinubu ya amince da ɓukatar ministan yaɗa labarai na gyara gadar MokwaShugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin gy...
16/08/2025

Tinubu ya amince da ɓukatar ministan yaɗa labarai na gyara gadar Mokwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin gyaran babbar gadar garin Mokwa da ke jihar Neja, k**ar yadda Ministan Yada Labarai Mohammed Idris ya buƙata.

Ministan ayyuka Mista David Umahi, wanda ya bayyana haka da yake jawabi ga ƴan jarida yau Asabar a garin Abakaliki na jiharsa ta Ebonyi, ya ce ayyukan na daga cikin ƙarin ayyuka da shugaba Tinubu ya bada umarnin gudanarwa a baya-bayan nan.

Minista Umahi ya ce aikin sake gina gadar zai lashe kuɗi har naira Biliyan 16.7.

Gadar ita ce babbar hanyar da take haɗa jihar Nrja da jihar Kwara da kuma yankunan Kudancin Najeriya.

Gadar ta Mokwa ta karye ne sak**akom ambaliyar ruwan da ya faru a watannin baya.

Bayan faɗuwar ambaliyar ruwan Ministan Yada Labarai ya kai ziyarar jaje tare da bada gudunmawar ƙashin kansa ta Naira miliyan 25.

Haka kuma mataimakin Shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima ya jagoranci babbar tawaggar gwamnatin tarayya zuwa garin na Mokwa tare da bada gudunmawar naira Biliyan ɗaya da kayan tallafi l.

A baya-bayan nan mai ɗakin shugaban ƙasa Misis Remi Tinubu ita ma ta kai ziyarar jaje jihar tare da bada tallafin Naira Biliyan ɗaya gaw waɗanda abun ya shafa.

YANZU-YANZU: Dan jarida Sani Zangina ya shaki iskar Yanci daga hannun Yan bindiga. Bayan shafe kwanaki 1 a hannun Masu g...
16/08/2025

YANZU-YANZU: Dan jarida Sani Zangina ya shaki iskar Yanci daga hannun Yan bindiga. Bayan shafe kwanaki 1 a hannun Masu garkuwa da Mutane.

Zaben cike gurbi na Dan majalisan Dokokin Jihar Neja a karamar hukumar munya na tafiya k**ar yanda aka Sara lami lafiya
16/08/2025

Zaben cike gurbi na Dan majalisan Dokokin Jihar Neja a karamar hukumar munya na tafiya k**ar yanda aka Sara lami lafiya

Address

Maitumbi New GRA
Minna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Niger State Media News24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Niger State Media News24:

Share