Niger State Media News24

  • Home
  • Niger State Media News24

Niger State Media News24 Niger State Media News24 Jarida ce a harshen Turanci da Hausa. Don kawo Ingantattun Labarai Da Kuma Labaran Wasu Jiha Zuwa Ga Ƴan Neja.

A Ranar Lahadi 09/08/2015 , Aka Bude Shafin Gidan Jaridar Niger State Media News24 A Dandalin Sada Zumunta Na Facebook

An Kafa Jaridar Yanar Gizo Na NIGER STATE MEDIA NEWS24 Ne Domin Isar Da Sahihan Labaran Jiha Ga Al-umman Jihar Neja Da Harshen Hausa Dana Turanci. An Kafa Tane Badon Wani Yareba, Duk Abun Da Ya Sami Wani Yare A Faɗin Jihar Neja Ko Wani Jiha za'amu Isar Da Saƙo Ga Ƴan Jihar Neja Domin Susan Abun Dake Faruwa A Najeriya Da Duniya Baki Ɗaya.

Majalisar Dinkin Duniya ta nada Farfesa Rabi’a Sa’id daga Jami'ar Bayero ta Kano (BUK) a kwamitin bincike kan illar maka...
21/07/2025

Majalisar Dinkin Duniya ta nada Farfesa Rabi’a Sa’id daga Jami'ar Bayero ta Kano (BUK) a kwamitin bincike kan illar makaman nukiliya na duniya.

Masu Zanga-zangar Fensho Da Karin Albashin Ƴan Sanda Sun Mamaye Hedikwatar TsaroA safiyar yau, wasu ƴan sanda masu ritay...
21/07/2025

Masu Zanga-zangar Fensho Da Karin Albashin Ƴan Sanda Sun Mamaye Hedikwatar Tsaro

A safiyar yau, wasu ƴan sanda masu ritaya sun mamaye harabar hedikwatar tsaron Najeriya da ke Abuja, inda s**a fara zanga-zanga kan batun fansho da hakkokin su da ake zargin ba a biya su ba.

Ƴan sandan da s**a fito daga jihohi daban-daban na ƙasar sun bayyana cewa, "shekaru da dama ke nan suna jiran biyan fanshon su ba tare da wani ci gaba ba, duk da hidimar da s**a yi wa ƙasa".

Sun rike alluna masu dauke da rubuce-rubuce irin su, “Mun yi wa ƙasa hidima, muna bukatar hakkokinmu!"

“Ba za mu daina zanga-zanga ba har sai an biya mu!”

Wani daga cikin masu zanga-zangar ya ce, "Mun bar iyalanmu don kare rayukan mutane da dukiyoyin su. Yanzu munyi ritaya, gwamnati ta manta da mu. Wannan rashin adalci ne."

Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga rundunar ‘yan sanda ko hukumar fansho kan matakin da za a dauka, amma jami’an tsaro na ci gaba da lura da zanga-zangar cikin kwanciyar hankali.

Ana sa ran hakan zai ɗora matsin lamba kan gwamnati da hukumomin da abin ya shafa domin duba lamarin cikin gaggawa.

Hukumar raya Birane na Jihar Neja ta rushe Wasu Shaguna da akayi ba bisa kaida ba Da safiyar yau Litini Hukumar da Hon. ...
21/07/2025

Hukumar raya Birane na Jihar Neja ta rushe Wasu Shaguna da akayi ba bisa kaida ba

Da safiyar yau Litini Hukumar da Hon. Abdul Rahman JG chata ke jagoranta tayi dirar Mikiya a Unguwar Kapkungu da F layout da wasu Anguwan nin dake Cikin Babban birnin jihar, Minna Inda ta Rushe Wasu Shagunan Ƴan jari bola s**ayi Ba bisa ka'ida ba, bisa umurnin Gwamantin jihar Neja.

Tsananin tsadar taki ta sanya wasu manoman Nijeriya sun jingine noman shinkafa da na masara, in ji binciken jaridar Dail...
21/07/2025

Tsananin tsadar taki ta sanya wasu manoman Nijeriya sun jingine noman shinkafa da na masara, in ji binciken jaridar Daily Trust

Nawa ake sayar da buhun taki a yankin da kuka fito?

Daraktan Raya birane na jihar Neja Ya rikewa Wasu Jami'an tsaron Sakai Kuɗaɗen su Na tsawon wata ukuWasu daga cikin jami...
21/07/2025

Daraktan Raya birane na jihar Neja Ya rikewa Wasu Jami'an tsaron Sakai Kuɗaɗen su Na tsawon wata uku

Wasu daga cikin jami'an tsaron Sakai da s**ayi aiki da Daraktan hukumar Raya birane Hon. Abdul Rahman JG Chata sun kwarmatawa Jagoran Shirin Zarar Bunu da cewa Daraktan ya rike masu Albashi na tsawon wata uku.

Kamar yadda s**a shaida a cikin shirin Sunce sunyita binshi har yakai ko ɗaga wayarsu bayayi, muma mun nemeshi

Yadda magoya baya kuma mabiya shafin gidan Radio na rFI Hausa s**a yi wa sabon mai gabatarwa Chaaa!😂😂Duba cikakken labar...
21/07/2025

Yadda magoya baya kuma mabiya shafin gidan Radio na rFI Hausa s**a yi wa sabon mai gabatarwa Chaaa!😂😂

Duba cikakken labarin a qasa.⤵️

21/07/2025

GA ABUNDA YA FARU A ZIYARAR MAISOLA

Babban Editan mu Comrade-Zakari Y Adamu Kontagora ya binciko muna gaskiyar abun da ya faru kan ziyarar tawagar Maisola da ya haifar da harbin bindiga a garin Farardoka dake yankin Bangi na ƙaramar hukumar Mariga. Lamarin da ya yi nasadiyyar mutuwar yaro guda tare raunata yara hudu.

Ga halin da yaran ke ciki, da kuma matsayar iyayen waɗannan yara dangane da lamarin da kuma matakan da Maisolan ya ɗauka

Mai Gwarawa Dr Umaru Farouk bahago
21/07/2025

Mai Gwarawa Dr Umaru Farouk bahago

SANARWAR NADA SABBIN KWAMITOCIN JIBWIS A JIHAR NEJA TARE DA GAYYATAR TARON KADDAMAR DASU.Majalisar zartarwa na kungiyar ...
21/07/2025

SANARWAR NADA SABBIN KWAMITOCIN JIBWIS A JIHAR NEJA TARE DA GAYYATAR TARON KADDAMAR DASU.

Majalisar zartarwa na kungiyar JIBWIS a Jihar Neja karkashin jagorancin Alh.Hassan Nuhu Mayanan Minna.

Na sanar da yayan kungiyar Musamman Yan Majalisar koli na Jihar tare da shugaban nin kananan Hukumomi 25 Dake fadin Jihar Neja da s**a hada da shugabanin Agaji cewa Akwai Taron kaddamar da sabbin kwamitocin da aka nada domin gudanar da aikin kungiyar a matakai daban daban domin cibgaban Addinn Musulunci.

Za,a gudanar da Taron ne a ranar Asabar Mai zuwa 26/7/2025 a Hedikwatar kungiyar JIBWIS ta Jihar Neja Dake kan titin Bosso a Birnin Minna da Misalin Karfe 11 na safe idan Allah ya kaimu,

Haka zalika ana bukatar halartar duk Wanda yaga sunanshi a daya daga cikin kwamitocin da aka nada,An saki sunayen ta kafofin sadarwa daban daban da ake anfani dasu domin isar da sakonni kamar yadda kungiyar ta Saba.

Domin neman Karin bayani ana iya tuntubar Sakataren kungiya na Jihar Malam Muhammadu Sanusi Erana,
Ko Sakataren labarai na Jiha Malam Abubakar Gidado,
Ko Kuma Mustapha Nasiru Batsari Maitaimakin Sakataren Labarai.
Allah ya bada iKon zuwa Amin.

SANARWAR daga Sakataren kungiya na Jihar Neja Malam Sanusi Erana,
Ta Hannun Ofishin yada Labaru.

21/07/2025

TIRKASHI: Gwamnan jihar Imo yayi kuskuren mika ta'aziyyar Tinubu maimakon ta marigayi Muhammadu Buhari.

Ashe hatsarin yayi muni har Gwamnan Katsina ya samu buguwa da kuma karaya a kafarsa ..Bai karye ba kuma bai ji rauni sos...
21/07/2025

Ashe hatsarin yayi muni har Gwamnan Katsina ya samu buguwa da kuma karaya a kafarsa
..Bai karye ba kuma bai ji rauni sosai ba! -inji Gwamnatin Jihar Katsina

Rahotanni sun nuna Gwamnan jihar Katsina Malam Umaru Dikko Raɗɗa ya samu hatsari a kan hanyarsa ta komawa Katsina daga Daura, inda rahotanni su ka ce ya samu karaya a ƙafarsa. A yanzu haka ya na samun kulawa a asibitin FMC Daura.

Ayau News ta ruwaito bayanai sun ce mutanen da yake tare da su a motar suma sun ji jiki. "Taho mugama motar Gwamnan tayi da wata motar fasinja kirar Golf wacce har sai da injinta ya fita" inji wata majiya wacce ta ce fitar sirri Gwamnan yayi babu tawagar motoci a tare dashi

Sai dai kawo yanzu ana dakon sanarwa a hukumance kan hakikanin yadda abun ya faru da kuma halin da ake ciki "domin yanzu wata majiya na cewa Gwamnan yana cikin koshin lafiya wani jami'i ne dai ya bugu shima ba sosai ba" inji majiyar

SABON LABARI: Daga bisani Gwamnatin Jihar Katsina ta bakin mai magana da yawun Gwamnan ta ce hadarin ya zo da sauki kuma babu karaya. A cewar sanarwar tuni an kebe Gwamnan tare da kwararrun likitoci domin duba lafiyarsa "amma dai bai wani jin jiki kamar yadda ake fada ba"

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƴan Najeriya Sun Fara Kiraye-Kiraye Ga Shugaban Tinubu Da Ya Saki Abba Kyari Da Gwamnatin Marigayi Muhamma...
20/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Ƴan Najeriya Sun Fara Kiraye-Kiraye Ga Shugaban Tinubu Da Ya Saki Abba Kyari Da Gwamnatin Marigayi Muhammadu Buhari Ta Tsãre A Gidaɲ Yari

Shin Kana Ɗaya Daga Cikin Ƴan Najeriya Masu Goyon Bayan Tinubu Ya Sãki Abba Kyari Da Gwamnatin Buhari Ta Tsãre ?

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Niger State Media News24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Niger State Media News24:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share