02/05/2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 4 a Katsina, Sun Kwato Mak**ai da Kayan Aiki
Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da wani gagarumin nasara da rundunar sojoji ta samu a yaƙin da take yi da ’yan ta’adda a jihar.
Rahotanni sun nuna cewa rundunar sojoji ta Brigade ta 17 ta kashe ’yan ta’adda guda huɗu a yayin wani sintiri na yaƙi da s**a gudanar a hanyar Turare zuwa Yantumaki.
An ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:40 na safe, lokacin da ’yan ta’addan s**a kai hari ga sojojin, inda nan take sojojin s**a mayar da martani tare da bin su, har s**a kashe su baki ɗaya ba tare da asarar rai a ɓangaren sojojin ba.
A yayin aikin, an kwato mak**ai da kayayyaki da s**a haɗa da bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya da harsasai, babura guda biyu, wayoyin hannu da dama, ciki har da na zamani (Android), da kuma kuɗi kimanin naira dubu ɗari da hamsin da uku da ɗari huɗu.
Binciken farko ya nuna cewa daga cikin waɗanda aka kashe akwai manyan jagororin ’yan ta’adda da s**a haɗa da Bishir Holami, Jamilu Baki, Ibrahim Doro da Abdurraman Maje. Ana zargin su da jagorantar hare-hare a yankunan Gobirawa, Raddawa, Kuki da sauran sassan ƙananan hukumomin Dutsinma da Matazu.
Rahoton ya kuma nuna cewa kashe waɗannan mutane na daga cikin manyan nasarorin da za su raunana ƙungiyar wani fitaccen shugaban ’yan ta’adda da ke addabar wasu yankuna a jihar.