Nijalite Hausa Tv

Nijalite Hausa Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Nijalite Hausa Tv, Media/News Company, Cikin Garina Babban Birnin Jihar Neja, Minna.
(1)

Naijalite Hausa TV Jarida Ce Na Jihar Neja An kafata Ne Domin Kawu Labarai, Na Cikin Jihar Neja Dama Sauran Jahohi Nijeriya Harma Duniya Baki Daya 08063398775

WhatsApp 08084664424

06/05/2026

Shirin WAKILCI tare da Alh Yahaya Designer, SUTURAN MINNA.

Firan namu na yau ya maida hankali ne akan gudun mawar Wakilai dama muhimmancin zayyanama shuwagabanni gaskiya komai dacin ta.

Designer ya bayyana mana cewa akan hakkin Alummah a shirye yake ya fuskanci koma waye!

Daga karshe yayi kira ga Alummah dasu dauki Alhakin kulawa da kayayyakin da ake ikirari na gwamnati ne, inda yace sam hakan ba gaskiya bane, domin kuwa da dukiyoyin mu ne ake mana duk wani abu da gwamnati keyi, don haka mu kula da dukiyoyin mu.

ROMON ƊIMOKARADIYYA: Wasu Matasa na yankin Suleja, Tafa da Gurara sun samu sabbin babura, mota da kuɗaɗe a hannun ATL a ...
06/05/2026

ROMON ƊIMOKARADIYYA: Wasu Matasa na yankin Suleja, Tafa da Gurara sun samu sabbin babura, mota da kuɗaɗe a hannun ATL a yau Litinin.

A yau ne Ɗan Majalissar Wakilai na yankin ya raba Mashina kirar roba-roba guda ashrin da mota kirar Peugeot da kudade.

YANZU-YANZU: Hukumar ICPC ta sake gurfanar da El-rufa'i a Kotun Kaduna.Hukumar Independent Corrupt Practices and Other R...
06/05/2026

YANZU-YANZU: Hukumar ICPC ta sake gurfanar da El-rufa'i a Kotun Kaduna.

Hukumar Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission (ICPC) ta sake gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmed El-rufa'i a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Kaduna.

Hukumar ta gurfanar da shi ne a yau Laraba 6 ga watan Mayu 2026, domin sauraren sabbin tuhume-tuhumen da ake masa.

Kalli bidiyon zuwansa 👇
https://www.facebook.com/reel/2263422790855799/?app=fbl

MALAM AHMAD VAHIDI YACE...Mashigir ruwan Hormuz ba za ta bude  ba kawai saboda Shugaban Amurka yayi Tweets, kula da sarr...
05/05/2026

MALAM AHMAD VAHIDI YACE...

Mashigir ruwan Hormuz ba za ta bude ba kawai saboda Shugaban Amurka yayi Tweets, kula da sarrafa wannan hanyar ruwan yana karkashin ikon Iran, babu wani da yake da ikon shiga ba tare da izini ba, idan aka karya wannan doka za a dauki hakan a matsayin halal ne dakarun juyin juya hali na Iran s**ai farmaki akan ko waye...

Sojojin juyin juya halin na Iran sune suke rike da makullin wannan hanyar, idan sunga dama su bude ko idan sun ga dama su rufe..

Ba wani mutum da ya isa ya zare mana idanu, ba wata burga da zaa yi mana, mun riga mun san nauyin kowa yanzu, duk wanda ya takale mu dole ne ya jimu...

05/05/2026

Labarin dake shigomana yanzu yanzu daga majiya metushe ayau da yammacin talata Haɗaɗɗiyar Daular larabawa tana shan wuta yamzu haka kubiyomu danjin halin da ake ciki a gabas ta tsakiya.

05/05/2026

Ruhoton yadda Ɗan Majalissar Wakilai na yankin Suleja, Tafa da Gurara Hon. Adamu Tanko Lakwaja ya Gwangwaje Al'ummar Mazabar sa da Romon Dimokaraɗiyya a safiyar yau.

04/05/2026

Yanzu yanzu; Iran ta harba makami mai linzami kan wani jirgin ruwan Amurka da yai yunƙurin keta mashigar Hormuz k**ar yanda majiyarmu ta tabbatar.

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 4 a Katsina, Sun Kwato Mak**ai da Kayan AikiGwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da wani ga...
02/05/2026

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 4 a Katsina, Sun Kwato Mak**ai da Kayan Aiki

Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da wani gagarumin nasara da rundunar sojoji ta samu a yaƙin da take yi da ’yan ta’adda a jihar.

Rahotanni sun nuna cewa rundunar sojoji ta Brigade ta 17 ta kashe ’yan ta’adda guda huɗu a yayin wani sintiri na yaƙi da s**a gudanar a hanyar Turare zuwa Yantumaki.

An ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:40 na safe, lokacin da ’yan ta’addan s**a kai hari ga sojojin, inda nan take sojojin s**a mayar da martani tare da bin su, har s**a kashe su baki ɗaya ba tare da asarar rai a ɓangaren sojojin ba.

A yayin aikin, an kwato mak**ai da kayayyaki da s**a haɗa da bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya da harsasai, babura guda biyu, wayoyin hannu da dama, ciki har da na zamani (Android), da kuma kuɗi kimanin naira dubu ɗari da hamsin da uku da ɗari huɗu.

Binciken farko ya nuna cewa daga cikin waɗanda aka kashe akwai manyan jagororin ’yan ta’adda da s**a haɗa da Bishir Holami, Jamilu Baki, Ibrahim Doro da Abdurraman Maje. Ana zargin su da jagorantar hare-hare a yankunan Gobirawa, Raddawa, Kuki da sauran sassan ƙananan hukumomin Dutsinma da Matazu.

Rahoton ya kuma nuna cewa kashe waɗannan mutane na daga cikin manyan nasarorin da za su raunana ƙungiyar wani fitaccen shugaban ’yan ta’adda da ke addabar wasu yankuna a jihar.

Allah Sarki:Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Kori Sojan Nan, Umar Jamilu Wanda Ya Yi Korafi Kan Rashin Wadataccen Abinci Ga ...
02/05/2026

Allah Sarki:Rundunar Sojojin Nijeriya Ta Kori Sojan Nan, Umar Jamilu Wanda Ya Yi Korafi Kan Rashin Wadataccen Abinci Ga Sojojin Da Suke Yakàr Ýan Ta'aďda

Ayi masa addu’a 😭“Mama, na yi imani zan dawo da rai saboda ina jin ƙarfin addu’o’inki yana bani ƙarfi a jikina.” 🇳🇬‘Yan ...
02/05/2026

Ayi masa addu’a 😭
“Mama, na yi imani zan dawo da rai saboda ina jin ƙarfin addu’o’inki yana bani ƙarfi a jikina.” 🇳🇬
‘Yan uwana ‘yan Najeriya, ku taimaka ku yi mana addu’a ga sojojinmu. 🙏🙏🙏
Ya Allah Ubangiji Ka zama garkuwa a gare su, Ka kare su daga duk wani haɗari, Ka ba su lafiya da dawowa gida lafiya wajen iyalansu.
Allah ya ƙara musu ƙarfi da nasara. 🇳🇬🙏

DAKARUN SOJI SUN CI GABA DA SAMAME, SUN KASHE ‘YAN TA’ADDA, SUN K**A MASU TAIMAKA MUSU, AN KUMA SAMU MIKA WUYA A AREWA M...
01/05/2026

DAKARUN SOJI SUN CI GABA DA SAMAME, SUN KASHE ‘YAN TA’ADDA, SUN K**A MASU TAIMAKA MUSU, AN KUMA SAMU MIKA WUYA A AREWA MASO GABAS

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Joint Task Force (North East), wato Operation HADIN KAI (OPHK), sun ci gaba da gudanar da hare-haren samame a faɗin yankin aikin Operation DESERT SANITY V, inda s**a samu nasarori masu yawa a yaƙin da suke yi da ta’addanci, ciki har da kashe ‘yan ta’adda, k**a wasu da ake zargi da taimaka musu, da kuma samun mika wuya daga wani ɗan Boko Haram/ISWAP.
A wani samame da aka gudanar tare da haɗin gwiwar ‘yan Civilian Joint Task Force (CJTF), dakarun OPHK sun fafata da wasu ‘yan ta’adda da ke motsi daga Yale zuwa yankin dajin Sambisa. A yayin artabun, an kashe ‘yan ta’adda huɗu, sannan an ƙwato bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya tare da harsasai da kuma kayan abinci da ake zargin kayan tallafin ‘yan ta’adda ne. Dakarun sun koma sansaninsu lafiya ba tare da samun asara ba.

Matasa Sun Cinna Wa Gidan Nafiu Bala Wuta A Unguwarsu Da Ke Gombe Jim Kaɗan Bayan Yanke Hukuncin Kotun Koli Inda Bangare...
30/04/2026

Matasa Sun Cinna Wa Gidan Nafiu Bala Wuta A Unguwarsu Da Ke Gombe Jim Kaɗan Bayan Yanke Hukuncin Kotun Koli Inda Bangaren David Mark Ya Yi Nasara.
Ba A Samu Rashin Rai Ba Sai Dai Dukiya Ta Salwanta.
Har Yanzun Jami'an Tsaro Ba Su K**a Wadanda S**a Yi Wannan Aika-aika Ba

Address

Cikin Garina Babban Birnin Jihar Neja
Minna
MINN

Telephone

+2348084664424

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nijalite Hausa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nijalite Hausa Tv:

Share