Nijalite Hausa Tv

Nijalite Hausa Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Nijalite Hausa Tv, Media/News Company, Cikin Garina Babban Birnin Jihar Neja, Minna.

Naijalite Hausa TV Jarida Ce Na Jihar Neja An kafata Ne Domin Kawu Labarai, Na Cikin Jihar Neja Dama Sauran Jahohi Nijeriya Harma Duniya Baki Daya 08063398775

WhatsApp 08084664424

MANOMI GWAMNA UMARU BAGO YA HALARCI RANAR KARSHE TA GASAR POLO TA KASA TA MINNA 2026Gwamnan Jihar Neja, Manomi Gwamna Mo...
02/08/2026

MANOMI GWAMNA UMARU BAGO YA HALARCI RANAR KARSHE TA GASAR POLO TA KASA TA MINNA 2026

Gwamnan Jihar Neja, Manomi Gwamna Mohammed Umaru Bago, ya kasance cikin manyan baƙi da s**a halarci wasan ƙarshe na Gasar Polo ta Ƙasa ta Minna ta shekarar 2026, wadda aka gudanar a filin wasan Polo na Minna.

Manomi Gwamnan ya kalli wasan cikin farin ciki yayin da ƙungiyar Profile ta doke ƙungiyar Malcomines tare da lashe babbar kofin IBB Cup.

Ƙungiyar Bago Farms Polo Team, ƙarƙashin jagorancin Marwan Mohammed Bago, ɗan Manomi Gwamnan, ita ma ta yi nasarar lashe Emir's Cup da kuma Governor's Cup, yayin da Profile Polo Club ta lashe General Hassan Cup.

Da yake jawabi bayan kammala gasar, Manomi Gwamnan ya taya dukkan ƙungiyoyin da s**a fafata a kofuna daban-daban murnar nuna kyakkyawan ɗabi'ar wasanni da haɗin kai tun daga farkon gasar har zuwa ƙarshe.

Manomi Gwamnan, wanda kuma shi ne Shugaban Minna Polo Club, ya sake nuna godiyarsa ga Mataimakin Shugaban Ƙungiyar na Farko, Mohammed Babangida, bisa jagoranci da ƙoƙarinsa wajen tabbatar da dorewar wasan Polo a Jihar Neja.

Haka kuma, Manomi Bago ya sake jaddada aniyarsa ta ci gaba da bai wa wasan Polo dukkan goyon bayan da ya dace domin cigabansa.

Daga cikin abubuwan da s**a kayatar a wajen taron akwai rabon kofuna da lambobin yabo ga ƙungiyoyin da s**a yi nasara, tare da karrama fitattun 'yan wasa da s**a yi bajinta a yayin gasar.

Taron ya samu halartar manyan baƙi da s**a haɗa da Mai Martaba Sarkin Minna, Alhaji Umar Faruk Bahago, da Wakilin Birnin Adamawa, Dr. Umar Usman Bazza, tare da sauran manyan baƙi.

Bologi Ibrahim
Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan Jihar Neja
02/08/2026

02/08/2026

Halin da hanyar kauyen Goro ke ciki ta gundumar kwarau a karamar hukumar Igabi jihar Kaduna ga bayanan da Ranar Wanka ta hada

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHI RAJI'UN: Shahararren Mawaƙin Siyasa, Buhari Wanda Aka Fi Sani Da Ƙosan Waƙa Ya Rasu, Yau Lah...
02/08/2026

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHI RAJI'UN: Shahararren Mawaƙin Siyasa, Buhari Wanda Aka Fi Sani Da Ƙosan Waƙa Ya Rasu, Yau Lahadi A Wani Asibiti Dake Kano

Allah Ya Jiƙan Sa Da Rahama!

HOTUNA: Matasan Kiristoci na Majami'ar ECWA 2 da ke unguwar Railway Quarters, Ƙofar Dumi a garin Bauchi, sun gudanar da ...
01/08/2026

HOTUNA: Matasan Kiristoci na Majami'ar ECWA 2 da ke unguwar Railway Quarters, Ƙofar Dumi a garin Bauchi, sun gudanar da aikin gayya domin gyaran magudanan ruwan yankin.

Wannan aiki na daga cikin matakan da ake ɗauka domin taimakawa wajen rage matsalar ambaliyar ruwa a kan titin Ƙofar Dumi zuwa mashigar unguwar Karofin Madaki a cikin garin Bauchi.

Wannan shi ne karo na biyu da matasan ke gudanar da irin wannan aikin gayya, a matsayin wani ɓangare na shirye-shiryen bikin Makon Matasa na Majami'ar ECWA, wanda ake gudanarwa a faɗin Najeriya.

WATA SABUWA: Anyi Nasarar Kamo Mutumin Da Yabar Yan Uwansa Ya Koma Kudu Bayan Shekaru 8 da Bacewa, An Gano Mutumin da Ak...
01/08/2026

WATA SABUWA: Anyi Nasarar Kamo Mutumin Da Yabar Yan Uwansa Ya Koma Kudu Bayan Shekaru 8 da Bacewa, An Gano Mutumin da Aka Yi Zaton Ya Mutu

Wani mutum da ya shafe shekaru takwas ba tare da iyalansa sun ji duriyarsa ba, kuma aka dade ana zaton ya rasu, ya bayyana da rai a wani yanki na kudancin Najeriya.

Rahotanni sun ce wasu matasa daga ƙauyensu da s**a je neman aiki a kudu ne s**a yi karo da shi kwatsam. Bayan sun tabbatar da shi ne, sai s**a k**a shi tare da shirya mayar da shi gida domin ya sake haɗuwa da iyalansa bayan dogon lokaci.

Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce da mamaki, yayin da ake jiran jin dalilin da ya sa ya bar gida tsawon shekaru takwas ba tare da ya tuntubi iyalansa ba.

NASRUMILLAH: 'Yan Sakai din mu dake Kanoma Birni masu aikin gadin gari daga saman tsaunukkan Kanoma a jihar Zamfara, sun...
01/08/2026

NASRUMILLAH: 'Yan Sakai din mu dake Kanoma Birni masu aikin gadin gari daga saman tsaunukkan Kanoma a jihar Zamfara, sun samu nasarar kawar da barayi ukku yanzu nan akan hanyar Rayau ta Yammacin Kanoma.

Ubangiji Allah Ya kara taimakon su

NASRUMILLAH: Mataimakin shugaban ƙasurgumin ɗan bindiga Muhammad Gwaska, mai suna Abubakar Dattiya, na daga cikin 'yan b...
01/08/2026

NASRUMILLAH: Mataimakin shugaban ƙasurgumin ɗan bindiga Muhammad Gwaska, mai suna Abubakar Dattiya, na daga cikin 'yan bindiga shida da s**a mutu sak**akon ɓarkewar cutar kwalara a sansanin Gwaska da ke ƙaramar hukumar Anka ta jihar Zamfara. Rahotanni sun ce cutar ta bazu cikin sansanin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar waɗannan 'yan bindiga cikin ɗan ƙanƙanin lokaci.

INNALILLAHI SUBHANALLAH. /DAN ACABA YA RASA RANSA A MUMMUNAN HATSARIN MOTA A HANYAR COCA-COLA–MOKWA A BIDA, JIHAR NIGER3...
31/07/2026

INNALILLAHI SUBHANALLAH. /DAN ACABA YA RASA RANSA A MUMMUNAN HATSARIN MOTA A HANYAR COCA-COLA–MOKWA A BIDA, JIHAR NIGER
31 GA YULI, 2026

Wani direban babur ya rasa ransa sak**akon wani mummunan hatsarin mota da ya faru da safiyar Juma'a, 31 ga Yuli, 2026, a kan hanyar Coca-Cola–Mokwa da ke garin Bida, Jihar Neja.

Rahotanni sun bayyana cewa mamacin ya yi arangama kai-tsaye da wata babbar mota (trailer). Ya samu munanan raunuka a kansa, kuma an tabbatar da rasuwarsa nan take a wurin da hatsarin ya faru.

Wannan lamari ya sake tayar da hankalin jama'a kan yadda hatsurran ababen hawa ke ƙaruwa a garin Bida. Mazauna yankin na kira ga hukumomin da abin ya shafa da su ɗauki matakan gaggawa domin inganta tsaron hanyoyi, tabbatar da bin dokokin zirga-zirga, da kuma kare rayukan masu amfani da hanyoyin. Nijalite Hausa Tv

Ya zuwa yanzu babu tabbatacciyar shaida game da raɗe-raɗin da ke yawo a kafafen sadarwa kan mutuwar auren jarumi Adam A ...
31/07/2026

Ya zuwa yanzu babu tabbatacciyar shaida game da raɗe-raɗin da ke yawo a kafafen sadarwa kan mutuwar auren jarumi Adam A Zango da Amaryarsa Maimuna.

Rahotannin farko da ba a tabbatar da sahihancin su ba dai sun nuna cewar auren ya mutu kuma tuni aka fara yaɗa wasu hotunan da ke nuni da cewar kayan ɗakin Maimuna ne ake kwashewa daga gidan Zango.

Shin me kuka sani kan wannan jita-jitar?

Alakanta Mutum Da Shan Ƙwaya, Shan Giya Ko Hauka, Ba Adawar Siyasa Ba Ce, Keta Mutunci Ne Da Cin Zarafi Ƙarara Kuma Lall...
31/07/2026

Alakanta Mutum Da Shan Ƙwaya, Shan Giya Ko Hauka, Ba Adawar Siyasa Ba Ce, Keta Mutunci Ne Da Cin Zarafi Ƙarara Kuma Lallai Ya Kamata Sheikh Pantami Ya Ɗauki Mataki Akan Sa, Saboda Siyasa Ba Hauka Ba Ce, Cewar Masanin Shari'a, Barista Abba Hikima

Address

Cikin Garina Babban Birnin Jihar Neja
Minna
MINN

Telephone

+2348084664424

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nijalite Hausa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nijalite Hausa Tv:

Shortcuts

Share