
19/09/2025
Karamcin ANNABI Muhammadu S.A.W Qissa Qayatacce Qisssan Imamul Busairy Wanda Ya rubuta Littafin Alburda da Littafin Hamziyya Bari kaji Karamcin Da ANNABI Yayi masa
Watarana Imamul Busairy yafito yaje wani gari da niyya zai wa'azi Sai dare yayi masa kuma gashi bako ne shi a garin kuma bai San kowa ba
Sai ya shiga wani masallaci don yayi
barci kafin safe!
Ana cikin wannan hali sai wani Barawo yayi sata aka biyoshi da gudu gashi garin yayi duhu dare yayi !
Sai ba aga barawon ba a kace a duba masallacin nan ko ya buya aciki!
Ana dubawa sai akaga mutum akwance imamu busairy aka k**a dukanshi sun sha shine barawon yace bashi bane s**a ki yarda har aka yanke masa hannu sai yabar garin!
Sai ya tafi wani garin ya nata bada ilimai sarkin garin ya bashi masauki har ya zama babban malami a garin har sarki ya aura masa yansa!
Ranan Shigan daki sai amarya taga bashi da hannu an yanke Safe nayi ta tafi gidansu ta fadama babanta Sarki.
Shi kuma sarkin yana jin kunyan Malamin sai yayi hikima: yasa rana ta musamman wai kowa yazo fada zai gaisa da Sarki.
Imam Busairi yana jin haka yasan
dashi akeyi!
Ana gobe Ranan da daddare busairi ya kwana Yana Karanta Littafin Alburda Littafin da ya rubuta Na yabon ANNABI Muhammadu S.A.W Yana ta karanta Alburda yana Neman dauki wajen ANNABI Muhammadu S.A.W har barci ya kwashe shi
Acikin Barcinsa Sai Yaga Fuskannan
mai Albarka wato : ANNABI Muhammadu S.A.W ANNABI yace masa naga damuwanka kuma Nazo ne domin
in yaye maka Gobe Idan sarki ya baka hannu kaima ka bashi Kuma kunsan shi hannunsa ayanke take; da safe tayi fadan cika a nata gaisawa da Sarki har akazo kansa k**an yadda ANNABI ya umurcesa hakan yayi
Sarki yana bashi hannu shima ya bashi yana mika hannu sai gashi Allah ya fitar masa da hannu ya tsiro kuma ya gaisa da sarkin Ana ta kabbara
Allahu Akbar
Anan yabada labarin Irin wannan karamcin da ANNABI yayi masa Sabida haka Muma Mu dage da yawaita Salati da yabo Na ANNABI Muhammadu S.A.W
Happy Maulid of Nabiyi S.A.W