Dauratush Shu'ara'i Maje

Dauratush Shu'ara'i Maje Haqiqa An Azurce ni da Qaunar Sayyidil Kauni Na gode maka rabbani da ka Sanya ni Masoyinsa ne Mawakan fiyayyen halitta Annabi Muh'd s.a.w. Na gari Daguru da Maje

I'm in the top 22% of Saifullahi Abdulkareem Masoyi fans. I earned 87 points on their weekly engagement list last week.
07/01/2026

I'm in the top 22% of Saifullahi Abdulkareem Masoyi fans. I earned 87 points on their weekly engagement list last week.

Duk mai kishin Iyayensa shima yace:- Ameen Ya Rabbal Alameen ๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™
07/01/2026

Duk mai kishin Iyayensa shima yace:- Ameen Ya Rabbal Alameen ๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™

Komai na Manzan ALLAH yayi daidaiImanin na Manzan ALLAH yafi na kowaTausayin Manzan ALLAH SAW yafi na kowa Shi yasa mala...
07/01/2026

Komai na Manzan ALLAH yayi daidai
Imanin na Manzan ALLAH yafi na kowa
Tausayin Manzan ALLAH SAW yafi na kowa
Shi yasa malamai s**a ce Allah yabawa Manzan Allah suna AlAzeemu SAW

Idan an dubeka akace hoton Manzon Allah ne ajikinka sai akace kayi ibada domin tabbatarwa kanka a inda kafito SAWAW

Shehu Allah ฦ™ara maku lpya alfarmar Kakanka Sayyiduna Rasulullahi SAWAW

Daga Sheikh Muhammadul Kabir RTA
Mai Nasutu Muradi

wani Balarabe a zamanin jahiliyya, lokacin da aka kawo masa amaryarsa a kan doki, sai ya tashi ya kashe dokin nan take.M...
07/01/2026

wani Balarabe a zamanin jahiliyya, lokacin da aka kawo masa amaryarsa a kan doki, sai ya tashi ya kashe dokin nan take.
Mutanen da ke kewaye da shi s**a yi mamaki ฦ™warai, s**a tambaye shi dalilin wannan aiki mai ban alโ€™ajabi.

Sai ya ce musu:
โ€œNa ji tsoron kada mehawa dokin ya zauna a wurin da matata ta zauna, alhali har yanzu wurin yana ษ—auke da ษ—uminta.โ€

Daga cikin abubuwan da s**a fi ban mamaki, kuma suke nuna irin tsananin kishi, da ake da shi a wancan lokaci, akwai wannan labari:

Wata mata ta je gaban alฦ™ali Musa bin Ishaq a birnin Rayy a shekara ta 286 bayan hijira, sai wakilinta ya yi ฦ™ara cewa mijinta yana binsa dinari 500 (sadakinta).
Mijin ya musanta wannan zargi.

Sai alฦ™ali ya ce wa wakilin matar:
โ€œIna shaidunka?โ€

Ya ce: โ€œNa zo da su.โ€
Sai wani daga cikin shaidun ya nemi ya kalli matar, domin ya iya nuna ta da kyau a cikin shaidarsa.

Sai shaidar ya ce wa matar:
โ€œKi tashi tsaye.โ€

Nan take sai mijin ya ce da ฦ™arfi:
โ€œMe kuke shirin yi haka?โ€

Wakilin ya ce:
โ€œSuna so ne su kalli matarka domin su gane ta.โ€

Sai mijin ya ce:
โ€œIna shaida wa alฦ™ali cewa hakika sadakin nan yana kaina kamar yadda take ikirari , amma ba za a buษ—e fuskarta ba.โ€

Da matar ta ji haka, sai ta ce:
โ€œNi kuma ina shaida wa alฦ™ali cewa na yafe masa wannan sadakin, kuma na wanke shi daga wannan bashi duniya da lahira.โ€

Sai alฦ™ali ya yi murmushi, ya nuna matuฦ™ar jin daษ—i da kishin da mutuncin da s**a nuna, sannan ya ce:
โ€œA rubuta wannan lamari a cikin littafin Makarmar ษ—abiโ€™a (kyawawan halaye).โ€

A yau, alโ€™umma idan mutum yana da kishi, sai a ce masa:
โ€œTsohon tunani neโ€ฆ mai tsaurin raโ€™ayi neโ€ฆ mai rikitarwa neโ€ฆ mai tsanani ne.โ€

Ibnul Qayyim (ุฑุญู…ู‡ ุงู„ู„ู‡) ya ce:

โ€œIdan kishi ya tashi daga zuciya, to ฦ™auna ma ta tashi daga zuciyar. Eh, hatta addini ma yana barinta gaba ษ—aya.โ€

Kaโ€™ida ba ta rabuwa gida biyu:
Mutumin da yake da mutunci da jarumtaka shi ne wanda yake iya kare gidansa da mutanensa.

Hakika:
Wanda ba shi da kishi , ba shi da addini.
Kuma idan kana son sanin hakikanin darajar nam

Rayuwa bazata koya wa mutum komai a rana ษ—aya ba. Wasu darussa suna zuwa ne ta hanyar jinkiri, wasu kuma ta hanyar rashi...
06/01/2026

Rayuwa bazata koya wa mutum komai a rana ษ—aya ba. Wasu darussa suna zuwa ne ta hanyar jinkiri, wasu kuma ta hanyar rashin nasara. Amma duk darasin da baka guje masa ba, wata rana zai zama hikima a rayuwarka.
Kada ka daina ฦ™oฦ™ari saboda sau ษ—aya ka faษ—i. Wanda ya dage, shi ne wanda daga ฦ™arshe yake gane dalilin da yasa Allah ya tsaida shi a wani matsayi.
โ€”

ุงู„ู„ูŽู‘ู‡ูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ูŽู‘ ุตูŽู„ูู‘ ุนูŽู„ูŽู‰ ุณูŠูู‘ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุฏูู†ูŽุง ู…ุญู…ุฏู ุงู„ูุงุชูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุญู ู„ูู…ูŽุง ุฃูุบู’ู„ูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู‚ูŽ ูˆุงู„ุฎูŽู€ุงุชูู€ู€ู€...
06/01/2026

ุงู„ู„ูŽู‘ู‡ูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ูŽู‘ ุตูŽู„ูู‘ ุนูŽู„ูŽู‰ ุณูŠูู‘ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุฏูู†ูŽุง ู…ุญู…ุฏู ุงู„ูุงุชูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุญู ู„ูู…ูŽุง ุฃูุบู’ู„ูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู‚ูŽ ูˆุงู„ุฎูŽู€ุงุชูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ู ู„ูู…ูŽุง ุณูŽุจูŽู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู‚ูŽุŒ ู†ูŽุงุตูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุฑู ุงู„ุญูŽู‚ูู‘ ุจุงู„ุญู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู‚ูู‘ุŒ ูˆุงู„ู‡ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุงุฏููŠ ุฅู„ู‰ ุตูุฑูŽุงุทูู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ูƒูŽ ุงู„ู’ู…ูุณู’ุชูŽู‚ููŠู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ูุŒ ูˆูŽุนูŽู„ูŽู‰ ุขู„ูู‡ู ุญู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู‚ูŽู‘ ู‚ูŽุฏู’ุฑูู‡ู ูˆู…ูู‚ู’ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ุฏูŽุงุฑูู‡ู ุงู„ุนูŽุธููŠู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู€ู…ูโœจ

06/01/2026

Idan an ษ“ata a gyara,
Burina mu shine Rayuwar kowa ta ษ—auki saiti. ๐Ÿ˜Š

Khalifa Dr Aliyu Sheikh Ahmad Abulfath ya ce kar mu manta da dan uwan mu a cikin addu,o,in mu mu roki Allah yaye ma sa h...
06/01/2026

Khalifa Dr Aliyu Sheikh Ahmad Abulfath ya ce kar mu manta da dan uwan mu a cikin addu,o,in mu mu roki Allah yaye ma sa halin da ya ke ciki.

DA DUMI DUMI: Muna Kira Ga Gwamnatin Tarayya Ta Sake Mana Babban Shehin Musulunci, Domin Hakan Tozarci Ne Ga Musulmai. -...
06/01/2026

DA DUMI DUMI: Muna Kira Ga Gwamnatin Tarayya Ta Sake Mana Babban Shehin Musulunci, Domin Hakan Tozarci Ne Ga Musulmai. -Hon. Aminu Sani Minister Sardauna Sharifai.

06/01/2026

Daga Murmushin Ma'aiki Haske yake fita๐Ÿ‘‡

RANAR SHA UKU (13) GA WATAN RAJAB ITA CE RANAR HAIHUWAR IMAM ALI (AS)An haifi Imam Ali (AS) a ranar Jumaโ€™a, 13 ga watan ...
02/01/2026

RANAR SHA UKU (13) GA WATAN RAJAB ITA CE RANAR HAIHUWAR IMAM ALI (AS)

An haifi Imam Ali (AS) a ranar Jumaโ€™a, 13 ga watan Rajab, shekara 23 kafin hijira. An haife shi ne a birnin Makka, a cikin ษ—akin Kaโ€™aba mai girma. Wannan wani lamari ne na musamman a tarihin bilโ€™adama, domin ba a taษ“a jin labarin haihuwar wani mutum a cikin Kaโ€™aba ba sai Imam Ali (AS). Wannan alโ€™amari yana nuna irin matsayi da darajar da Allah (SWT) ya ba Imam Ali (AS) a idon duniya baki ษ—aya.

Mahaifinsa shi ne Abu ฦŠalibi ษ—an Abdul Muษ—allib, kawun Manzon Allah (SAW). Abu ฦŠalibi da Abdullahi, mahaifin Annabi Muhammad (SAW), uwa ษ—aya uba ษ—aya ne. Don haka Imam Ali (AS) ฦ™ani ne ga Manzon Allah (SAW) ta fuskar zumunci.

Imam Ali (AS) ya taso ne a gidan Manzon Allah (SAW), inda ya samu cikakkiyar tarbiyya da ilimi a hannunsa tun yana ฦ™arami har zuwa girma.

Imam Ali (AS) ya yi aure yana da shekara 25, lokacin da Manzon Allah (SAW) ya aurar masa da ฦดarsa Sayyida Fatimatuz-Zahra (AS). Wannan aure ya kasance bisa umarnin Allah (SWT), domin an rawaito cewa Malaโ€™ika Jibril (AS) ne ya sauko da saฦ™on auren daga wajen Allah.

Imam Ali (AS) yana da matsayi mai girma a wajen Allah da Manzonsa (SAW). Shi ne Aliyu Ibn Abi Talib (AS):

โ–ช๏ธShi ne wanda Kaโ€™aba ta buษ—e aka haife shi a cikinta.

โ–ช๏ธShi ne wanda Manzon Allah (SAW) ya ce: โ€œNi ne birnin ilimi, Ali kuwa shi ne ฦ™ofarsa.โ€

โ–ช๏ธShi ne wanda duk wata matsala da aka kasa warwarewa a zamanin Abubakar, Umar da Usman, sai a turo a nemo shi ya zo ya warwareta.

โ–ช๏ธShi ne wanda Manzon Allah (SAW) ya ce masa: โ€œMatsayinka a wurina kamar matsayin Haruna ne a wurin Annabi Musa (AS), sai dai babu Annabi bayana.โ€

Hakika, haihuwar Imam Ali (AS) a cikin Kaโ€™aba alama ce bayyananniya da ke nuna falala, daraja da matsayinsa na musamman a cikin addinin Musulunci.

Daga Taskar: Mahadee Musa Aliyu

ยฉZaria Media Forum
02/01/2026

Address

Unguwar Daji Minna
Minna

Telephone

+2347037874788

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dauratush Shu'ara'i Maje posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dauratush Shu'ara'i Maje:

Share