Dan umma enterprises

Dan umma enterprises Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Dan umma enterprises, News & Media Website, OFF LIMPOPO STREET, Mpape.

An yi takwara wa mahaifin Annabi Muhammadu (SAW) a jihar Bauchi..--------------Daya daga cikin matasan malamai a jihar B...
05/05/2024

An yi takwara wa mahaifin Annabi Muhammadu (SAW) a jihar Bauchi..
--------------

Daya daga cikin matasan malamai a jihar Bauchi AMB Sheik Nasir Sheik Ado Musa Tafawa-Balewa Bauchi ne ya sanya sunan mahaifin Annabi Muhammadu SAW a matsayin takwara gare shi.

Shehin malamin ya ce koda a baya iyayen mu suna sanya wannan suna ne don faranta rai da samun Albarkan mahaifin Annabi Muhammadu Sayyidina Abdullahi.

Kuma a yanzu ina shawartan dukkan masoyan Annabi Muhammadu SAW su ci gaba da dabbaga wannan aiki na sanya sunan mahaifan sa Sayyiduna Abdullahi da Sayyid Amina don faranta ran ɗan su Annabin Rahama (saw).

04/05/2024

WANDA BAZAI GA ANNABI (ﷺ) BA RAN KIYAMA .

Daga Nana Aisha (ra) tace: “Na kasance a cikin ɗakina ina ɗinke wani tufafi nawa sai fitila ta mutu kuma ɗakin ya yi duhu lokacin da alluran ta faɗi kasa, ina cikin wannan hali ina laluben alluran sai ga Manzon Allah (ﷺ) ya ɓullo da fuskarsa daga kofar ɗaki “Ya ɗaga labulen kofar sannan ya shigo da fuskarsa”
Nana A’isha tace “Na rantse da Allah wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi hakika sassan ɗakin ya haskaka daga hasken fuskarsa.
Sai na waigo zuwa gare shi nace Mahaifina fansa ne a gareka ya RASULULLAHI BABU ABIN DA YAKAI FUSKARKA HASKE!
Sai Annabi (ﷺ) ya ce ya A’isha, kwarin Azaba ya tabbata ga wanda ba zai gan ni ba ranar Alkiyama!”

Sai Nana A’isha (RA) tace: “ranar Alkiyama Wanene Wanda bazaya ganka ba, YA RASULULLAHI (ﷺ) ?
Ta maimaita sau biyu.
Sai Annabi (ﷺ) ya ce: “wanda aka ambace ni a gurinsa bai yi salati a gare ni ba”

SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAM.
TIRMIDHI Da IMAM AHMAD

Allah Ubangiji ya sadamu da Manzon S A W gobe kiyama

Mai sana'ar ƙanƙarar ruwa ya zama hamshakin attajirin Afrika na biyu - Shine Alhaji Auwal Abdullahi Rano daga jihar Kano...
04/05/2024

Mai sana'ar ƙanƙarar ruwa ya zama hamshakin attajirin Afrika na biyu - Shine Alhaji Auwal Abdullahi Rano daga jihar Kano.

Mafi ƙarancin kiyasi ya nuna ya mallaki gidajen mai 120 a shekarun baya a fadin Najeriya, ya mallaki motoci jigila 600 ya mallaki wajen ajiye mai na kimanin Naira miliyan 60 ya samar da kamfanin Jiragen sama mafi girma a Najeriya.

ƊA ƊUMI-ƊUMI: Jarumin Finafinan Hausa na Kannywood Sani Danja, zai aurar da ƴarsa mai suna Rizqat. Wane fata zaku yi mas...
04/05/2024

ƊA ƊUMI-ƊUMI: Jarumin Finafinan Hausa na Kannywood Sani Danja, zai aurar da ƴarsa mai suna Rizqat. Wane fata zaku yi masu?

03/05/2024
Cikin maki 100% maki nawa zaku bawa alkalan shari'ar Kano?
12/01/2024

Cikin maki 100% maki nawa zaku bawa alkalan shari'ar Kano?

YANZU-YANZU: Kotun koli ta tabbatatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf, a matsayin halastaccen zababban Gwamna jihar Kano.
12/01/2024

YANZU-YANZU: Kotun koli ta tabbatatar da Gwamna Abba Kabir Yusuf, a matsayin halastaccen zababban Gwamna jihar Kano.

HANNUNKA MAI SANDA (17)******************************Ka kyale mai hassada da sharrinsa. Domin chutar dake zuciyarsa ma k...
08/01/2024

HANNUNKA MAI SANDA (17)
******************************
Ka kyale mai hassada da sharrinsa. Domin chutar dake zuciyarsa ma ka'dai ta isheshi bala'i..

Kada ka rama mugunta da mugunta.. Wannan halin Qaskanci ne. Amma rama mugunta da alkhairi shine halin Annabawa (as) kuma sune ababen koyinmu.

Kyautata zato ga mutane koda sharrinsu ya bayyana gareka Qarara.. Kada ka kalli kanka amatsayin fiyayye a bainar jama'a domin Allah shine masanin asiran bayinsa kuma shiriya ahannunsa take..

Kai da ka shiryu ba wayonka ne ya shiryar dakai ba.. Ba kuma iliminka ne ka'dai ba. A'a za'bin Ubangiji ne da kuma falalarsa gareka.

Hakanan arziki ko rufin asirin da Allah yayi maka ba wai yana nufin cewa Allah yafi sonka ne fiye da kowa ba. Sai dai ya baka ne domin ya jarrabeka ya bayyanar da halayenka.

Haka shima talauci jinya idan aka dora maka ba wai yana nufin cewa Allah ba ya sonka bane. A'a soyayyar tasa ce ma ta janyo haka.. Kuma ya zabeka ne domin ya jarrabi halayenka.

Wanda yafi kowa daraja awajen Allah shine wanda yafi tsoron Allah tare da kyawawan dabi'u.

Allah yasa mu dace, ameen thumma ameen.

Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanal Janar Taoreed Lagbaja, ya je ta'aziya kan harin bam da Rundunar Sojin Ƙas...
05/12/2023

Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanal Janar Taoreed Lagbaja, ya je ta'aziya kan harin bam da Rundunar Sojin Ƙasar ta ce ta kai bisa 'kuskure' a jihar Kaduna.

📸 - Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya

Address

OFF LIMPOPO STREET
Mpape

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dan umma enterprises posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share