Masoya ummu abiha - as

Masoya ummu abiha - as Wannan group din mun budeshine saboda masoya sayyada fatima (as)

15/11/2025

Wacece Matar da Manzon Allah (SAW) Ya Cire Rigar Jikinsa Domin ai mata likkafani dashi?

Wacece wannan mace da Manzon Allah ﷺ ya cire rigan jikinsa ya ce a yi mata likkafani da ita? Kuma me ya sa lokacin da aka shigar da ita kabari, sai Annabi ya shiga ya shimfiɗa ƙasa da hannunsa, yana ƙara faɗaɗa kabarin da kansa, har ma ya kwanta a cikinta kafin a rufe ta?

Wacece wannan mace da Manzon Allah ﷺ ya roƙi Allah da a tashe ta a ranar ƙiyama tana sanye da tufafi, saboda ana so a yi mata likkafani da rigan sa? Kuma me ya sa bayan an rufe kabarin sai wasu sahabbai s**a ce, "Ya Rasulullah, mun ga wani abu da ba mu taɓa ganinka ka yi wa wani ba?"

Sai Annabi ﷺ ya ce:

"Na sa mata rigata domin ta sanya daga tufafin Aljanna, kuma na kwanta cikin kabarinta domin a taji dadin kwanciya cikin kabarinta. Saboda ita ce wadda ta fi kowa kyautata mini daga cikin halittar Allah, bayan Abū Ṭālib."

Wacece wannan mata?

Ita ce Fāṭima bint Asad bint Hāshim bint ʿAbd Manāf, 'yar ƙabilar Quraysh, daga gidauniyar Banu Hāshim. Ita ce matar Abū Ṭālib (ƙanen mahaifin Annabi), kuma uwa ga Sayyidina ʿAlī bn Abī Ṭālib (RA).

Manzon Allah ﷺ ya rayu a ƙarƙashin kulawar kakansa, ʿAbdul-Muṭṭalib, har ya kai shekara 8. Bayan rasuwar kakansa, aka ɗauke shi zuwa gidan Abū Ṭālib. A nan ne Fāṭima bint Asad ta ɗauke shi tamkar ɗanta a wasu riwayoyi ma ana cewa ta fi ƙaunar Annabi fiye da 'ya'yanta.

Kalaman Abū Ṭālib ga matarsa:

"Wannan ɗan yayana ne, kuma ya fi mahimmanci a gare ni fiye da dukiyata da raina. Ina roƙonki da kada ki bari wani ya hana shi abin da ya ke so."

Ta amsa da murmushi, tana cewa:

"Kana mini wasiyya a kan ɗana Muhammadu? Wallahi, ina son shi fiye da raina da ’ya’yana!"

Kulawar Fāṭima bint Asad:

Ta rika yi masa hidima kamar uwa.

Ta kan ba shi abinci da tufafi fiye da na ‘ya’yanta.

Ta kan wanke masa jiki, ta shafa masa mai, ta gyara gashinsa, ta ƙanshafa shi.

Har sai ya ɗauke ta da sunan "UWA TA".

Ko da lokacin da Manzon Allah ya auri Sayyida Khadīja (RA), Fāṭima bint Asad

AMINCIN ALLAH YA TABBATA AGAREKI RANAR HAIHUWARKI I ZUWA  RANAR KOMA WARKI GA MAHALLICINKI   YA TSOKAR JIKIN MANZON  ALL...
06/11/2025

AMINCIN ALLAH YA TABBATA AGAREKI RANAR HAIHUWARKI I ZUWA RANAR KOMA WARKI GA MAHALLICINKI YA TSOKAR JIKIN MANZON ALLAH S A W W♥️

"Tabbas farashin soyayyar Imam Ali (A.S) da riƙo da shi yana da tsada sosai , idan aka kasheka kisan gilla wannan shine ...
04/11/2025

"Tabbas farashin soyayyar Imam Ali (A.S) da riƙo da shi yana da tsada sosai , idan aka kasheka kisan gilla wannan shine mafi ƙarancin abinda za ka fuskanta a tafarkin "

Muna Taya Al-ummar Musulmi Murna Da Zagayowar Ranar Da Aka Haifi Sayyidah Zainabul Kubra (SA), Ɗiyar Imam Ali (AS), Ƴa G...
27/10/2025

Muna Taya Al-ummar Musulmi Murna Da Zagayowar Ranar Da Aka Haifi Sayyidah Zainabul Kubra (SA), Ɗiyar Imam Ali (AS), Ƴa Ga Sayyidah Faɗimatuz Zahra (AS), Jikar Manzon Allah (Saww)💐🌹.

حين ولدت سيدة زينب الكبرى، فطلبها رسول الله (ص)، وقبلها، وقال ﴿أوصي الحاضرين والغاءبين أن يحفظوا هذه البنت من أجلي٬ فهي شبيهة خديجة الكبرى (ص)}.

A Irin Wannan Rana Ce 5 Ga Watan Jimada Ula Shekara Ta 5 Ko Ta 6 Bayan Hijira, Aka Haifi Aqilatu Bani Hashim Wato Sayyidah Zainabul Kubra (SA).

Mahaifinta Shine Imam Ali Bn Abiɗalib (AS), Mahaifiyarta Itace Sayyidah Faɗimatuz Zahra (AS), Sayyidah Zainabul Kubra (SA) Itace Jikar Manzon Allah (Saww) Ta Farko a Mata, Mijinta Shine Ɗan Amminta Abdullahi Bn Jafar Bn Abiɗalib (AS), Tana Da Ƴaƴa 5 a Duniya 4 Maza 1 Mace, Sune; Ali, Aun, Abbas, Muhammad Da Ummul Kulthum, Ana Yimata Alkunya Da (UMMUL MASA'IB), Laƙubbanta Ana Kiranta Da; Aqilatu Bani Hashim, Aqilatuɗ Ɗalibina, Assiqatus Sugra, Waliyyatullah Da Sauransu.

Sayyidah Zainabul Kubra (SA) Taga Jarabawoyi a Rayuwa Domin Gabanta Manzon Allah (Saww) Yayi Wafati, Kuma Gabanta Mahaifiyarta Sayyidah Faɗimatuz Zahra (AS) Tayi Shahada, Kuma Gabanta Mahaifinta Imam Ali Bn Abiɗalib (AS) Yayi Shahada, Kuma Gabanta Yayanta Imam Hassan Almujtaba (AS) Yayi Shahada, Kuma Tareda Ita Akaje Karbala A Gabanta Yayanta Imam Hussain (AS) Yayi Shahada Shiyasa Ake Ce Mata (UMMUL MASA'IB) Kuma Itace Ta Zama Garkuwa Ga Imam Hussain (AS) Da Ahlul-bayt a Karbala, Daga Ƙarshe Tayi Shekara 57 a Duniya.

Muna Roƙon Allah (SWT), Ya Ƙara Ɗaukaka Matsayinta, Mu Kuma Allah (SWT) Ya Ƙara Mana Sonsu, Kuma Ya Bamu Ikon Koyi Da Irin Aikinsu Wato Ahlul-bayt 🤲🏻.

26/10/2025
Mafificiyar Sallah inji Annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم itace sallar asuba ranar Jumu'a acikin jam'iALLAH ya datar da...
23/10/2025

Mafificiyar Sallah inji Annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم itace sallar asuba ranar Jumu'a acikin jam'i
ALLAH ya datar damu baki daya 🤲
Juma'a Mubarak 🥰 to all Muslims umma 🤝

21/10/2025

SOYAYYAR KACE TANADINA
ANNABI S A W TUN INA JINJIRI.

16/10/2025

duniya kiyama ni agareki na
sallama maulaty♥️♥️♥️

13/10/2025

AYI HAKURI HAKA RABBI
YA KADARTO FADIMA [AS]
BA AKAIKU GIRMA BA @

Tambaya Nake Da Ita Ga Malamai, Meyasa Masu Ruwaito Hadisai Basa Ruwaito Hadisan Jikokin Annabi Da Ahlinsa? Wanda Suna H...
09/10/2025

Tambaya Nake Da Ita Ga Malamai, Meyasa Masu Ruwaito Hadisai Basa Ruwaito Hadisan Jikokin Annabi Da Ahlinsa? Wanda Suna Hadisan su Yakamata Yafi Na Kowanne Yawa.

Sayyadina Hassan Da Hussaini Jikokin Annabi Ne, Nana Fatima Diyar Annabi Ce, Ga Sayyadina Ali Sirikin Annabi Ne, Kuma A Hannun Manzon Allah Ya Girma - Chizo 1 Germany

Me Za ku ce?

muna taya daukacin ma abota imani juyayin wafatin sayyada zainab khubra kanwar imam hassan da hussain  yar nana fadima d...
02/10/2025

muna taya daukacin ma abota imani juyayin wafatin sayyada zainab khubra kanwar imam hassan da hussain yar nana fadima da imam ali jikar manzo allah s a w w ♥️ tabbas babu wasu kalmomi da baki zai fada su daidai da jarumtarki sai dai kawai baki ya fada da kwatantawa jarumtarki da tausayi da jinkai da mika lamuranki ga mahalinciki duk kasan da cewarki mace amma kin dau bala i da maza baza su iya daukaba kai hatta duwatsu aka doramusu atake zasu zama kura ya ummu musaib amincin Allah ya tabbata agareki ranar da aka haifeki zuwa ranar daki koma ga mahalliciki

nan na tsaya  ban kaucewa
30/09/2025

nan na tsaya ban kaucewa

Address

Alibaba
Nasarawa

Telephone

+2349132038065

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Masoya ummu abiha - as posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share