Masoya ummu abiha - as

Masoya ummu abiha - as Wannan group din mun budeshine saboda masoya sayyada fatima (as)

A yau 13ga watan Rajab Ranar murnar haihuwar Imam Ali bn Abi Talib (AS) –mutumin da adalci ya samu mazauni a zuciyarsa,i...
02/01/2026

A yau 13ga watan Rajab Ranar murnar haihuwar Imam Ali bn Abi Talib (AS) –
mutumin da adalci ya samu mazauni a zuciyarsa,
ilimi ya kasance makamin rayuwarsa,
kuma tsoron Allah ya kasance garkuwarsa.
Ya Allah, Ka raya zuciyoyinmu da soyayyarsa da tafarkinsa.

01/01/2026

TARIHI

A RANA IRIN TA YAU: 12 Ga Watan Rajab

1.
وفاة عمّ النبي (ص) العباس بن عبد المطلب بن هاشم بن عبد مناف سنة 32هـ، ودُفن في البقيع إلى جنب الأئمة الأربعة (ع).

A irin wannan rana ne Kawun Manzon Allah (S.A.A.W), Sayyid Abbas bn Abdul-Muɗɗalib (A.S) ya rasu a shekara ta 32 bayan Hijira. Wannan na nufin ya rasu kimanin shekara 22 ko 23 bayan wafatin Annabi (S.A.A.W). An binne shi a Baƙi’a, ƙabarinsa yana kusa da ƙanurburan A’immatul Baqi’a (A.S).

2.
دخول أمير المؤمنين (ع) إلى الكوفة واتخاذها مقرّاً لخلافته، وذلك بعد حرب الجمل سنة 36هـ.

Har wayau a irin wannan rana a shekara ta 36 bayan Hijira, Imam Amirul-Mu’minina Ali (A.S) ya shiga Kufa, inda ya mayar da ita hedkwatar (cibiyar) halifancinsa. Wannan ya faru ne bayan Yaƙin Jamal, wanda aka yi da Ummul-Mu’minina A’isha da magoya bayanta.

3.
هلاك معاوية بن أبي سفيان في دمشق سنة 60هـ، ودُفن في الباب الصغير، وقد أورد ابن خلكان في ترجمة النسائي أنّه لما سُئل عن فضائل معاوية قال: ما أعرف له فضيلةً إلا قول النبي (ص): «لا أشبع الله بطنك».

A irin wannan rana ne a shekara ta 60 bayan Hijira, Mu’awiya bn Abi Sufyan, sarkin Sham mai tawaye, ya mutu a Damashƙa inda aka binne shi a wurin da ake kira Babus-Saghir (wanda a yau aka ce ya zama wurin zubar da shara).

Ibn Khalikan ya ruwaito a cikin tarjamar Nisa’i cewa, lokacin da aka tambaye shi game da falalar Mu’awiya, sai ya ce:
“Ban san wata falala da yake da ita ba, face addu’ar da Annabi (S.A.A.W) ya yi masa.”

Addu’ar ita ce:
لا أشبع الله بطنك
“Kada Allah ya ƙosar da shi.”

Dalilin wannan addu'ar kuwa shi ne: Wata rana Annabi (S.A.A.W) ya aika a kira Mu’awiya sai aka ce masa yana cin abinci,
Annabi ya sake aikawa kiransa a karo na biyu, har sau uku, amma Mu’awiya ya jinkirta saboda cin abinci sai Annabi (S.A.A.W) ya ce: Allah kada ya ƙosar da cikinsa. Wannan na nan a ruwayoyi daban-daban na Sunnah, musamman a Sahih na Muslim.

اللهم صلِّ على محمدٍ وآلِ محمد

23/12/2025

Hakikanin Duniya:

الإمـام علي الهـادي
عليه أفضل السَّلام:

"الدنيا سـوق ربــح فيها قوم وخســر آخــرون"

Ma'ana:

Imam Ali Hadi (S), ya ce: Duniya kasuwa ce, wasu ci riba ciki, wasu kuma sun yi hasara.

Madogara: Biharul Anwar Juz'i na 1, shafi na 366.

A rana irin ta yau 3 ga watan Rajab, shekara ta 254, bayan Hijra, Imam Hadi (SA) Ya yi Shahada sakamakon guba da khalifan Abbasawa mai suna Mu’utazz (L) ya shayar dashi.

أعظم الله أجورنا وأجوركم بذكرى شهادة الإمام الهادي عليه السلام

انا لله وانا اليه راجعون😭

@

muna taya dan uwa aliyu haidar  murna aurensa Allah  ya bada zaman lafiya   yabada zuria dayyiba
22/12/2025

muna taya dan uwa aliyu haidar murna aurensa Allah ya bada zaman lafiya yabada zuria dayyiba

TARIHIN IMAM MUHAMMAD AL-BAQIR (A.S)1) Cikakken suna:Imam Muhammad bin Ali bin al-Husain (A.S.)Ana kiransa al-Bāqir, ma’...
22/12/2025

TARIHIN IMAM MUHAMMAD AL-BAQIR (A.S)

1) Cikakken suna:

Imam Muhammad bin Ali bin al-Husain (A.S.)
Ana kiransa al-Bāqir, ma’ana “mai tsaga ilimi ya bayyana shi”.

2) Haihuwa

An haife shi a Madinah

Shekara: 57 A.H.

Mahaifi: Imam Ali Zaynul-Abidin (A.S.)

Mahaifiya: Sayyida Fatima bint Hasan bin Ali (A.S.)
Shi kaɗai ne Imamin da ya haɗa nasabar Imam Hasan da Imam Husain (A.S.)

3) Shahada

Ranar shahada: 7 Zul-Hijja, 114 A.H.

Wurin shahada: Madinah

Wanda ya sa aka kashe shi: Hisham bin Abdul-Malik (Umayyawa) ta hanyar guba

An binne shi a Makabartar Baqi’i tare da mahaifinsa da kakanninsa (A.S.) a Makka.

4) Imama

Ya zama Imam bayan shahadar mahaifinsa a 95 A.H.

Tsawon Imama: shekaru 19

Shi ne Imam na biyar daga Ahlul-Baiti (A.S.).

Matsayinsa a Ilimi

Imam al-Bāqir (A.S.) ya buɗe babbar makarantar ilimin Ahlul-Baiti

Ya yaɗa ilimin.:

1)Tafsirin Al-Kur’ani

2)Fiƙihu

3)Hadisi

4)Tauhidi da Aqida

Manyan malamai sun yi karatu a wajensa, ciki har da:

1) Jabir bin Yazid al-Ju‘fi

2) Zurara bin A‘yun

3) Muhammad bin Muslim

Ɗaya Daga cikin maganganunsa (A.S.) da yake cewa

“Cikar mutum tana cikin ilimi, haƙuri, da kyakkyawan hali.”

5) Falalarsa

Manzon Allah (S.A.W.W) ya ambace shi tun kafin haihuwarsa, ya ce wa Jabir bin Abdullah al-Ansari:
“Za ka haɗu da ɗana Muhammad al-Bāqir, ka isar masa da gaisuwa ta.”

Ubangiji Allah ya bamu albarkar imam bakir A'S 🙏

21/12/2025

IMAM ALI (a,s) : ya ce ban taɓa yi wa kowa wani alkhairi ba, kuma kowa bai taɓa cuta ta ba,
Wani a kusa da shi ya ce ya Amirul Muminin duk zaluncin nan da ake maka kuma duk kyautata mana da kake yi ?
Imam ya ce ba ku ji a Alqur'ani ba Allah ta'ala ya ce wanda ya cuci wani kanshi ya cuta, haka kuma wanda ya kyautata ma wani kan shi ya yi wa.!

10/12/2025

Ga taƙaitaccen *tarihin Sayyada Fadima (RA)* — ‘yar Manzon Allah (SAW) da Uwargida Khadija (RA):

---

*Suna*: Fatima bint Muhammad
*Lakabi*: Az-Zahra (mai kyalli), Sayyidatun Nisa’il Jannah (Shugabar matan Aljanna)
*Haihuwa*: Kimanin shekara ta 605 Miladiyya, a Makkah
*Iyaye*: Annabi Muhammad (SAW) da Khadija bint Khuwaylid
*Miji*: Sayyidina Ali bin Abi Talib (RA)
*’Ya’ya*:
- Hasan (RA)
- Husain (RA)
- Zainab
- Ummu Kulthum

---

*Rayuwarta da halayyarta:*

- Fadima (RA) ta kasance mai kamun kai, tsantseni, da kyakkyawar halayya.
- Tayi tsananin biyayya da ƙaunar Mahaifinta (SAW), kuma tana taimaka masa a wahalhalu.
- Tayi rayuwa mai tsanani da tsoron Allah, tana da sauƙin hali da tsafta.

---

*Aure da Rayuwa:*

- An aurar da ita ga Sayyidina Ali (RA) bayan hijira a Madina.
- Rayuwarsu ta kasance mai tsananin tsabta da sadaukarwa.
- Duk da ƙarancin dukiya, Fadima (RA) bata taɓa korafi ba.

---

*Rasuwarta:*

- Ta rasu watanni shida bayan wafatin Manzon Allah (SAW), a shekara ta 11 bayan hijira (632 Miladiyya).
- Ana ganin ita ce mace ta farko da ta rasu bayan Annabi (SAW) a Ahlul Baiti.

---

*Darajarta a Musulunci:*

- Annabi (SAW) ya ce: *“Fadima ita ce shugabar matan Aljanna.”*

07/12/2025

AYI HAKURI HAKA RABBI YA KADARTO FADIMA BA AKAIKU GIRMABA.

SHEIKH DAHIRU USMAN  BAUCHI  RAHIMAHULLA
27/11/2025

SHEIKH DAHIRU USMAN BAUCHI RAHIMAHULLA

Duk Wanda Baibi Tafarkin Ahlul-Baiti ba To Bai Fahimci Allah Da Annabi baCewar:- Fitaccan malamin addinin Muslinci SHARI...
24/11/2025

Duk Wanda Baibi Tafarkin Ahlul-Baiti ba To Bai Fahimci Allah Da Annabi ba

Cewar:- Fitaccan malamin addinin Muslinci SHARIFF Al-ALAWEEY

Me zaku ce

21/11/2025

DAGA GIRMIN AMINATU
AKA GIRMAMA ASIYATU ME MUSAN HAKA SAI YA MUTU

Address

Alibaba
Nasarawa

Telephone

+2349132038065

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Masoya ummu abiha - as posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share