15/11/2025
Wacece Matar da Manzon Allah (SAW) Ya Cire Rigar Jikinsa Domin ai mata likkafani dashi?
Wacece wannan mace da Manzon Allah ﷺ ya cire rigan jikinsa ya ce a yi mata likkafani da ita? Kuma me ya sa lokacin da aka shigar da ita kabari, sai Annabi ya shiga ya shimfiɗa ƙasa da hannunsa, yana ƙara faɗaɗa kabarin da kansa, har ma ya kwanta a cikinta kafin a rufe ta?
Wacece wannan mace da Manzon Allah ﷺ ya roƙi Allah da a tashe ta a ranar ƙiyama tana sanye da tufafi, saboda ana so a yi mata likkafani da rigan sa? Kuma me ya sa bayan an rufe kabarin sai wasu sahabbai s**a ce, "Ya Rasulullah, mun ga wani abu da ba mu taɓa ganinka ka yi wa wani ba?"
Sai Annabi ﷺ ya ce:
"Na sa mata rigata domin ta sanya daga tufafin Aljanna, kuma na kwanta cikin kabarinta domin a taji dadin kwanciya cikin kabarinta. Saboda ita ce wadda ta fi kowa kyautata mini daga cikin halittar Allah, bayan Abū Ṭālib."
Wacece wannan mata?
Ita ce Fāṭima bint Asad bint Hāshim bint ʿAbd Manāf, 'yar ƙabilar Quraysh, daga gidauniyar Banu Hāshim. Ita ce matar Abū Ṭālib (ƙanen mahaifin Annabi), kuma uwa ga Sayyidina ʿAlī bn Abī Ṭālib (RA).
Manzon Allah ﷺ ya rayu a ƙarƙashin kulawar kakansa, ʿAbdul-Muṭṭalib, har ya kai shekara 8. Bayan rasuwar kakansa, aka ɗauke shi zuwa gidan Abū Ṭālib. A nan ne Fāṭima bint Asad ta ɗauke shi tamkar ɗanta a wasu riwayoyi ma ana cewa ta fi ƙaunar Annabi fiye da 'ya'yanta.
Kalaman Abū Ṭālib ga matarsa:
"Wannan ɗan yayana ne, kuma ya fi mahimmanci a gare ni fiye da dukiyata da raina. Ina roƙonki da kada ki bari wani ya hana shi abin da ya ke so."
Ta amsa da murmushi, tana cewa:
"Kana mini wasiyya a kan ɗana Muhammadu? Wallahi, ina son shi fiye da raina da ’ya’yana!"
Kulawar Fāṭima bint Asad:
Ta rika yi masa hidima kamar uwa.
Ta kan ba shi abinci da tufafi fiye da na ‘ya’yanta.
Ta kan wanke masa jiki, ta shafa masa mai, ta gyara gashinsa, ta ƙanshafa shi.
Har sai ya ɗauke ta da sunan "UWA TA".
Ko da lokacin da Manzon Allah ya auri Sayyida Khadīja (RA), Fāṭima bint Asad