01/08/2025
MUNA TAYA YAN UWA JUYAYIN SHAHADAR IMAM HASSAN BIN ALI (AS)
A rana mai kamar ta yau, wato 7 ga watan Safar, Imam Hasan al-Mujtaba (As), Imami na biyu yayi shahada sakamakon gubar da aka shayar da shi.
Bayan shahadarsa dai, dan'uwansa Imam Husaini (As) da sauran Ahlulbaiti da mabiyansu sun dauko gawarsa mai tsarki da nufin bisne ta a kusa da makwancin Ma'aiki (S) to amma wasu 'manyan gari' karkashin jagorancin 'Uwar Muminai' Aisha sun hana haka din da kuma barazanar amfani da 'karfin soji' wajen hana faruwar hakan.
Ganin haka sai Imam Husaini (As) ya ba da umurnin da a tafi da gawar don bisne ta a Makabartar Baqi'a don tabbatar da maslahar al'ummar musulmi da kuma guje wa zubar da jinin musulmi. Hakan kuwa yana koyi ne da mahaifinsa Imam Amirul Muminin Ali (As) wanda yayi watsi da hakkinsa don tabbatar da maslaha ta al'umma da kuma guje wa duk wani abin da zai kawo rarrabuwan kan musulmi.
An ruwaito cewa bayan shahadar Imam Hassan (As), baki daya garin Madina sun karade da yin kuka. An kuma ruwaito cewa a lokacin binne shi, makabartar Baqi’ah ta cika da mutane sannan an kulle kasuwanni na tsawon mako guda.
Imam Hassan (As) ya bar wa dan uwan sa Imam Hussain (As) wasiyyar cewa a binne shi kusa da kakan sa Manzon ALLAH (S), sannan idan aka hana hakan, to a binne shi kusa da kakar Fatima Bint Assad (Mahaifiyar Imam Ali (As).
Bayan yayi shahadar, dan uwan sa Imam Hussain (As) ya so cika masa wannan wasiyyar amma sai Banu Umayya da yan Barandan s**a hana, s**a dauki makami har da harba kibiyoyi 70 a jikin gangan jikin sa mai tsarki, ganin za’a zubar da jini ne, Imam Hussain (A.S) ya ce a kai gawar mai tsarki makabartar Baki’ah.
Imam Hassan (As) yayi shahada ne a ranar 28 ga watan Safar, shekaru 50 bayan Hijira. Amma akwai ruwayoyi daban daban da s**a sha bamban da wannan, amma dai wannan ita ce tafi inganci.
Ina amfani da wannan damar wajen jajantawa Manzon Rahma (S), Ahlulbayt (As), masoyan su da ma daukacin al’ummar musulmi kan shahadar Imam Hassan (As).
Aminc