Masoya ummu abiha - as

Masoya ummu abiha - as Wannan group din mun budeshine saboda masoya sayyada fatima (as(

24/09/2025

"Idan kana so ka ga wanda ya fi kamala a cikin halayya, to ka kalli Manzon Allah ﷺ."

—Imam Ali

🎹Haƙiƙa Watan Haihuwar Haske Ya Kusanto💃💃 Duk Me Farin Ciki da Hakan Allah Ya Faranta Masa🎤📸🌹🌹💐💦
03/09/2025

🎹Haƙiƙa Watan Haihuwar Haske Ya Kusanto💃💃 Duk Me Farin Ciki da Hakan Allah Ya Faranta Masa🎤📸🌹
🌹💐💦

INA TAYA DAUKACIN ALUMMAR MUSULMI ZAGAYOWAR RANAR DA AKA HAIFI FIYAYYEN HALLITTA                S.  ♥️  A.    ♦️ W. ♦️
03/09/2025

INA TAYA DAUKACIN ALUMMAR MUSULMI ZAGAYOWAR RANAR DA AKA HAIFI FIYAYYEN HALLITTA
S. ♥️ A. ♦️ W. ♦️

25/08/2025

MUNA TAYA DAUKACIN MASOYA
FATIMA AS MURNAR ZAGAYOWAR WATAN DA AKA HAIFI FIYAYYEN HALITTA S A W W ♥️ 💖 ❤️

Mai Yabon Ahlul Bait Fatima ta Batul ta ziyarci Haramin Imam Ali bn Abi Ɗalib dake Kasar Iraq.
16/08/2025

Mai Yabon Ahlul Bait Fatima ta Batul ta ziyarci Haramin Imam Ali bn Abi Ɗalib dake Kasar Iraq.

Sai Na Tina Wasiyyar Imam Ja'afar (A.s) Ga Ƴan Shi'ar Sa......!Da naga waɗannan bayin Allah su na Hidima ga Maziyarta Im...
10/08/2025

Sai Na Tina Wasiyyar Imam Ja'afar (A.s) Ga Ƴan Shi'ar Sa......!

Da naga waɗannan bayin Allah su na Hidima ga Maziyarta Imam Husaini (A.s)‚ sai na tuna wasiyyar Imam Ja'afar (A.s) ga ƴan Shi'ar sa. In da wasikar take cewa;

“Ina gargaɗinku da girman kai‚ da nuna ɗagawa ga Allah. Ku sani cewa babu wani mutum da za a jarrabe shi da ɗagawa ga Allah face sai ya yi ɗagawa ga addinin Allah.”

“Don haka ku tsaya ƙyam a tafarkin Allah kada ku juya da baya sai ku wayi gari cikin masu asara. Ina roƙon Allah da ya tsare mu da ku daga ɗagawa ga Allah. Mu da ku ba mu da wani ƙarfi sai ta hanyar dogaro da Allah.”

-10/08/2025

TABBAS KAYI ABUDA YA DACE
03/08/2025

TABBAS KAYI ABUDA YA DACE

MUNA TAYA YAN UWA JUYAYIN SHAHADAR IMAM HASSAN BIN ALI (AS)A rana mai kamar ta yau, wato 7 ga watan Safar, Imam Hasan al...
01/08/2025

MUNA TAYA YAN UWA JUYAYIN SHAHADAR IMAM HASSAN BIN ALI (AS)

A rana mai kamar ta yau, wato 7 ga watan Safar, Imam Hasan al-Mujtaba (As), Imami na biyu yayi shahada sakamakon gubar da aka shayar da shi.

Bayan shahadarsa dai, dan'uwansa Imam Husaini (As) da sauran Ahlulbaiti da mabiyansu sun dauko gawarsa mai tsarki da nufin bisne ta a kusa da makwancin Ma'aiki (S) to amma wasu 'manyan gari' karkashin jagorancin 'Uwar Muminai' Aisha sun hana haka din da kuma barazanar amfani da 'karfin soji' wajen hana faruwar hakan.

Ganin haka sai Imam Husaini (As) ya ba da umurnin da a tafi da gawar don bisne ta a Makabartar Baqi'a don tabbatar da maslahar al'ummar musulmi da kuma guje wa zubar da jinin musulmi. Hakan kuwa yana koyi ne da mahaifinsa Imam Amirul Muminin Ali (As) wanda yayi watsi da hakkinsa don tabbatar da maslaha ta al'umma da kuma guje wa duk wani abin da zai kawo rarrabuwan kan musulmi.

An ruwaito cewa bayan shahadar Imam Hassan (As), baki daya garin Madina sun karade da yin kuka. An kuma ruwaito cewa a lokacin binne shi, makabartar Baqi’ah ta cika da mutane sannan an kulle kasuwanni na tsawon mako guda.

Imam Hassan (As) ya bar wa dan uwan sa Imam Hussain (As) wasiyyar cewa a binne shi kusa da kakan sa Manzon ALLAH (S), sannan idan aka hana hakan, to a binne shi kusa da kakar Fatima Bint Assad (Mahaifiyar Imam Ali (As).

Bayan yayi shahadar, dan uwan sa Imam Hussain (As) ya so cika masa wannan wasiyyar amma sai Banu Umayya da yan Barandan s**a hana, s**a dauki makami har da harba kibiyoyi 70 a jikin gangan jikin sa mai tsarki, ganin za’a zubar da jini ne, Imam Hussain (A.S) ya ce a kai gawar mai tsarki makabartar Baki’ah.

Imam Hassan (As) yayi shahada ne a ranar 28 ga watan Safar, shekaru 50 bayan Hijira. Amma akwai ruwayoyi daban daban da s**a sha bamban da wannan, amma dai wannan ita ce tafi inganci.

Ina amfani da wannan damar wajen jajantawa Manzon Rahma (S), Ahlulbayt (As), masoyan su da ma daukacin al’ummar musulmi kan shahadar Imam Hassan (As).

Aminc

26/07/2025

Karka Bari Zargin Wawaye Da zantukan su ya Hanaka Bayyana Soyayyar Yayan Gidan Annabi SAW Ahlul baitin Nubuwa ✊✌️

17/07/2025

SALAMU ALAIKI MADINAYA

MUNA TAYA MUMINAI MURNAR WANNAN RANAR MAI ALBARKA.A irin wannan ranar ta 17 ga Watan Ramadan na Shekara ta 2 bayan Hijir...
17/03/2025

MUNA TAYA MUMINAI MURNAR WANNAN RANAR MAI ALBARKA.

A irin wannan ranar ta 17 ga Watan Ramadan na Shekara ta 2 bayan Hijira aka Gwabza Yakin nan da Ya Shahara a Duniyar Tarihi Wato Yakin Badar. Yakin da Allah ya bawa Muminai Nasara ta Zahiri da ta Badini, Kuma Allah ya Kunyata Mushrikan Quraishawa da Sauran Masu mara Musu baya wajan ganin Bayan Kiran Ma'aiki (S) . Yakin Badar Yaki ne da a duk Ma'aunan Duniya bata yanda za ayi Muminai suyi Galaba, domin kuwa basuda Karfin yawa bare Kuma na Makamai, Kuma ba ma sun fito ne da Nufin yin Yaki ba. Sun Fito ne da nufin tsare Ayarin kayan Mushrikan Makka da s**a samu labarin Abu Sufyan ya biyo ta Madina da Kayan. Amma kwatsam sai abin Ya Juya ya zama Yaki ,ga shi Kuma a cikin Watan Ramadan ne Kuma ga Matsanancin Zafin Rana.

Su kuwa Mushirikan Makka sun Fito ne da fushi da kuma muggan makamai, ga kuma Yawan Mayaka da sun nunka na Muminai Yawa sau wajan Uku, domin adadin Muminai 313 ne, Mushrikan Kuraishawa kuwa sun Kusa Mayaka Dubu.

Ranar BADAR ,rana CE ta farin ciki abisa nasarar Rundunar Allah akan ta shedan !

Ranar Badar !Rana CE da rundunoni biyu s**a hadu ! Rana ce dauwamammiya a tarihin musulunci da makomar Dan Adam .

"ولقد نصر كم الله ببدر وانتم اذلة فاتقوا الله لعلكم تشكرون" (١٢٣)

سورة ال عمران

Kuma Hakika Allah Ya baku Nasara a Badar Alhali Kuna raunana, Saboda haka Kuji Tsoron Allah ko zaku Zama Masu Godiya.

Tarihin Badar na tunatar damu gwagwarmaya tsakanin gaskiya da bata ! Tsakanin adalci da zalunci !

Samun nasarar da Manzon Allah (s) ya yi bayan hijirarsa daga Makka zuwa Madina, da kuma irin karɓar da mutanen Madina s**a yi masa ya sanya kafiran Makkan cikin halin damuwa da kuma kara gaba da shi. Don haka s**a fara tunanin hanyar da za su bi wajen kawo ƙarshen wannan addini na Musulunci da kuma wanda ya kawo shi (Annabi). Don cimma wannan manufa, kafiran Makkan da 'yan koransu s**a fara kawo hare-hare ga yankunan da suke kusa da garin Madinan da kuma lalata kayayyakin gonakin musulmi da kuma ɗiban

SARKIN HAKURI DA  GUDUN DUNIYAASSALAMU ALAIKA YA HASSAN ALMUJTAFHA JININ SAYYADA JIKIN ANNABI (S A W W). BARKA DA SAUKA ...
15/03/2025

SARKIN HAKURI DA GUDUN DUNIYA
ASSALAMU ALAIKA YA HASSAN
ALMUJTAFHA JININ SAYYADA JIKIN ANNABI (S A W W). BARKA DA
SAUKA SARKIN HAKURI

Address

Alibaba
Nasarawa

Telephone

+2349132038065

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Masoya ummu abiha - as posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share