
04/06/2025
Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar Kano
A lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023 al’ummar Kano sun fara ganin sauyi na gaske. Sauyin da ya tabbatar da aiki, tsare-tsare, da kula da lafiyar al’umma da tattalin arziki wannan ba mulki ba ne na alkawari kawai, wannan mulki ne mai cike da aiki da cika alkawari.
A cikin shekaru biyu kacal, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa mulki nagari ba a magana ba ne, aiki ne da kishin al'umma
A bangaren noma da ban ruwa, sama da hectare dubu an samar da su domin noman rani, tare da gine-ginen dam-dam a kananan hukumomi fiye da goma sha biyu.
A fannin lafiya, an cire dubban masu rijista na bogi, an dauki matakan inganta kulawa da marasa lafiya, tare da shigar da dubban talakawa cikin tsarin lafiya kyauta.
Gwamnatin Abba ta kawo karshen matsalar rashin magunguna a asibitoci, ta kafa cibiyoyi na musamman da samar da injinan iskar oxygene masu amfani da hasken rana.
An ba da kulawa ta musamman ga yara da mata masu fama da cututtuka ta hanyar shirin ABBACARE, tare da tallafawa masu sikila da marasa galihu.
Tsarin rajista da kididdiga na zamani (EMR) ya kara inganta tsarin lafiya da sarrafa bayanai a asibitoci fiye da goma.
Gaskiya ce, Gwamna Abba Kabir Yusuf yana aiki tukuru, yana gina jihar Kano bisa gaskiya, adalci da amana. Wannan gwamnatin ba ta yi alkawarin da ba ta cika ba cikin shekara biyu da fara mulkin jihar Kano!
ABAISWORKING
📅 29th May, 2025
Wanda ya shuka nagarta, shi zai girbi tagomashi