Potiskum Online News

Potiskum Online News Sashen Labarai.

Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar  KanoA lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a r...
04/06/2025

Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar Kano

A lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023 al’ummar Kano sun fara ganin sauyi na gaske. Sauyin da ya tabbatar da aiki, tsare-tsare, da kula da lafiyar al’umma da tattalin arziki wannan ba mulki ba ne na alkawari kawai, wannan mulki ne mai cike da aiki da cika alkawari.

A cikin shekaru biyu kacal, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa mulki nagari ba a magana ba ne, aiki ne da kishin al'umma

A bangaren noma da ban ruwa, sama da hectare dubu an samar da su domin noman rani, tare da gine-ginen dam-dam a kananan hukumomi fiye da goma sha biyu.

A fannin lafiya, an cire dubban masu rijista na bogi, an dauki matakan inganta kulawa da marasa lafiya, tare da shigar da dubban talakawa cikin tsarin lafiya kyauta.

Gwamnatin Abba ta kawo karshen matsalar rashin magunguna a asibitoci, ta kafa cibiyoyi na musamman da samar da injinan iskar oxygene masu amfani da hasken rana.

An ba da kulawa ta musamman ga yara da mata masu fama da cututtuka ta hanyar shirin ABBACARE, tare da tallafawa masu sikila da marasa galihu.

Tsarin rajista da kididdiga na zamani (EMR) ya kara inganta tsarin lafiya da sarrafa bayanai a asibitoci fiye da goma.

Gaskiya ce, Gwamna Abba Kabir Yusuf yana aiki tukuru, yana gina jihar Kano bisa gaskiya, adalci da amana. Wannan gwamnatin ba ta yi alkawarin da ba ta cika ba cikin shekara biyu da fara mulkin jihar Kano!

ABAISWORKING
📅 29th May, 2025
Wanda ya shuka nagarta, shi zai girbi tagomashi

AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimma Wajen Dawo da Zaman Lafiya a ArewaGamayyar Kungiyar Ayyukan ...
01/06/2025

AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimma Wajen Dawo da Zaman Lafiya a Arewa

Gamayyar Kungiyar Ayyukan Arewa (AJAM) ta jinjina wa Gwamnatin Tarayya bisa manyan nasarori da ta samu wajen dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin Arewa, wanda da can ya kasance cike da matsalolin ta’addanci da miyagun laifuka.

Kungiyar ta bayyana musamman rawar da Ma'aikatar Tsaro ke takawa wajen aiwatar da manyan ayyukan tsaro masu amfani da fasahar zamani a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Tsakiya.

A cikin wata sanarwa da mai jagorantar kungiyar, Lauretta Bako ta fitar a ranar Alhamis, AJAM ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a fannin tsaro a yankin, wanda hakan ya biyo bayan dabarun rundunonin tsaro da gwamnatin ke aiwatarwa.

"A yau muna rayuwa a wani sabon yanayi na tsaro fiye da da, inda aka kore Boko Haram zuwa matsugunan duhu, yayin da shugabannin masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga s**a hallaka ko s**a tsere."

"Nasarorin da aka samu wajen kawar da ‘yan bindiga, ‘yan ta’adda da kuma sarkakiyar hanyoyin aikata laifi, tare da farfado da tattalin arzikin yankuna, ya nuna ingancin wannan tsari."

A cewar AJAM, daya daga cikin ginshikan wannan nasara shine Operation FANSAR YAMMA, wanda ya samu nasarori da dama, ciki har da hallaka sanannen shugaban ‘yan bindiga, Kachalla Dogo Isah, tare da wasu ‘yan ta’adda 44 a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kashe fitattun masu aikata laifi ciki har da masu sayar da mak**ai da shugabannin ‘yan bindiga ya tarwatsa manyan hanyoyin aikata laifi, tare da isar da sako ga sauran masu laifi cewa gwamnati ba za ta yarda da rashin tsaro ba.”

Tasirin wadannan matakan tsaro ya wuce kidayar alkaluma kawai; yana da tasiri kai tsaye ga rayuwar yau da kullum ta ‘yan kasa. Hanyoyi k**ar hanyar Kaduna-Abuja, wanda da can aka fi jin tsoro, yanzu sun fi aminci ga matafiya, hakan kuma yana taimakawa wajen kasuwanci da zirga-zirga.

Kasuwanni a wurare irin su Giwa, Birnin Gwari da Jibia suna samun sabuwar rayuwa, inda shugabannin al’umma da jama’a ke tabbatar da ingancin tsaro. Farfadowar harkokin kasuwanci na da nasaba kai tsaye da nasarorin da sojoji s**a samu tare da samar da yanayi mai kyau ga kasuwanci.

Gina Brigade na National Mission Force a Samaru Kataf shima ya taka rawa wajen warware matsalolin tsaro a Kudu ta Kudancin Kaduna, wanda ya haifar da ingantattun yanayin zamantakewa da tattalin arziki. A cikin watanni ukun farko na shekarar 2025 kadai, an hallaka ‘yan ta’adda 122 kuma an k**a fiye da 1,000 daga cikin masu laifi.

A matsayinmu na Arewa Joint Action Movement, muna tare da kokarin da Ma’aikatar Tsaro ke yi wajen kare al’ummominmu da dawo da fata a zukatan jama’a. Muna fahimtar cewa har yanzu akwai kalubale, amma nasarorin da aka samu sun haskaka mana hanya. Zamu ci gaba da goyon bayan manufofi da matakan da za su kawo zaman lafiya, tsaro da cigaba mai dorewa a Arewarmu.

Peter Obi Ya Karyata Jita-Jitar Zama Mataimakin Atiku A Zaben 2027 – Inji Obidient MovementDaga Comr Haidar H Hasheem Ob...
19/05/2025

Peter Obi Ya Karyata Jita-Jitar Zama Mataimakin Atiku A Zaben 2027 – Inji Obidient Movement

Daga Comr Haidar H Hasheem

Obidient Movement ta bayyana cewa rahoton da ke yawo a kafafen yada labarai na cewa tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP a zaben 2023 Mr. Peter Obi ya amince ya zama mataimakin Alhaji Atiku Abubakar a wani sabon hadin gwiwar siyasa da ake kokarin kafa wa gabanin zaben 2027, karya ne kuma babu gaskiya a cikin rahotan.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Nana Kazaure, Daraktar Sadarwa da Tsare-Tsare ta kungiyar, ta fitar a ranar 19 ga Mayu, 2025, inda ta bayyana cewa rahoton ya kasance kirkirar wasu marubuta ne kawai, kuma hakan yana iya janyo rudani da kuskuren fahimta a tsakanin jama'a.

Ta ce ko da yake ana ci gaba da gudanar da tattaunawa cikin lumana da wasu manyan ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki don samar da hadakar da za ta ceto Najeriya, babu wata tantama cewa Mr. Obi bai amince da mukamin mataimaki ba, kuma babu wata yarjejeniya da ta shafi hakan.

Sanarwar ta bayyana cewa manufar Mr. Obi da Obidient Movement ita ce samar da cikakken hadin kai don yaki da mulkin rashin nagarta, cin hanci da rashawa, yunwa, talauci, matsalar kiwon lafiya, da karancin ilimi ga yara ba siyasar karbar mukami kawai ba.

Kungiyar ta sake jaddada cewa Mr. Obi har yanzu na cikin jam’iyyar Labour Party, kuma idan zai sauya sheka ko jam’iyya a nan gaba, zai bayyana hakan da kansa.

Daga karshe, Obidient Movement ta bukaci 'yan Najeriya da kafafen yada labarai da su kauce wa yada jita-jita da rahotannin da ka iya tada tarzoma saboda rashin tushe, su maida hankali wajen taimakawa tare da gina Najeriya mai inganci da adalci.

Ranar: 19/05/2025
Sa hannu: Nana Kazaure, Daraktar Sadarwa da Tsare-Tsare, Obidient Movement

Invitation!! Invitation!! Invitation!!!Matriculation ceremony.Zenith College of Health Science and Technology Jos is off...
14/05/2025

Invitation!! Invitation!! Invitation!!!
Matriculation ceremony.
Zenith College of Health Science and Technology Jos is officially inviting you to her first matriculation ceremony slated to take place as follows:

Saturday 17 May 2025.

Time: 10:00 prompt

Venue: M&S international School Bukuru Jos south.

Hope to see your present as you serve as a special guest of honour!!

An samu wasu maciya amana masu anfani da sunan kungiyar kwankwasiyya a jihar kebbi suna karban kudi da sunan cewa su yan...
07/05/2025

An samu wasu maciya amana masu anfani da sunan kungiyar kwankwasiyya a jihar kebbi suna karban kudi da sunan cewa su yan kwankwasiyya ne kuma sun bar kungiyar kwankwasiyya i zuwa APC domin su bata tafiyar kwankwasiyya a jihar kebbi.

05/05/2025

Ashe haka Kauran Bauchi ya gina katafaren gida dama na maƙudan biliyoyin kudi jama'a 🤔

30/04/2025

Me yasa wasu mutane suke cewa 500k ba zata isa jari ba?😒

Kuyi Watsi Da Duk Wata Jita-Jita Da Makiyan Cigaban Jihar Kebbi Da Jam'iyyarmu Ta APC Cewa Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwan...
30/04/2025

Kuyi Watsi Da Duk Wata Jita-Jita Da Makiyan Cigaban Jihar Kebbi Da Jam'iyyarmu Ta APC Cewa Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwandu") Yana Shirin Komawa PDP.

Hon. Dr, Hussaini Suleiman Kangiwa ("Sarkin Arawan Kabi") Yayi Allah Wadai Da Waɗanda S**a Ƙirkiri Wannan Labari Na Karya, Sunyi Hakane Domin Kawo Hargitsi Cikin Wannan Jaha Tamu.

Ɗan Takarar Sanatan Kebbi Ta Arewa Hon. Dr, Hussaini Suleiman Kangiwa Yace Mai Girma Gwamna Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwandu") Yana Nan Cikin Jam'iyyar APC Kuma Yana Tareda Shugaban Ƙasa Asiwajo Bola Ahmed Tinubu Ɗari Bisa Ɗari.

Mu Al'ummar Jihar Kebbi Muna Nan Cikin Jam'iyyar APC Ƙarkashin Jagorancin Mai Girma Gwamna Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwandu") Da Shugaban Ƙasa Asiwajo Bola Ahmed Tinubu Kuma Insha Allahu Zasu Yi Nasara 2027.

Makiyan Mai Girma Gwamna Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwandu") Da Shugaban Ƙasa Asiwajo Bola Ahmed Tinubu Sun Karbi Ƙwangilar Kawo Rikici A Wannan Jahar Tamu Mai Albarka Jihar Kebbi.

Bakin Cikinsu Shine Mai Girma Gwamna Yayi Abunda Bazasu iyaba Na Kawo Cigaba Cikin Ƙanƙanin Lokaci A Ƙasa Da Shekara Biyu. Tunda Aka Kirkiri Jihar Kebbi A 1991 Munyi Gwamnoni Daban-Daban Amma Babu Kamar Kauran-Gwandu Wannan Shine Baƙin Cikinsu.

Kusani Hakarku Bazata Cimma Ruwa Cewar Hon. Dr, Hussaini Suleiman Kangiwa, Kuma Insha Allahu Zamu Ɗauki Mataki Akan Wannan Abu. Bazamu Lamuncin irin Wannan Cin Mutuncin Da Kazafi Da Akeyima Mai Girma Gwamnaba.

Zamu Duƙufa Wajen Gano Waɗannan Mutanen Das**a Ɗauki Aniyar Kawo Hargitsi Cikin Jihar Kebbi Da Jam'iyyar APC, Zamu Dauki Ƙwaƙƙwaran Matakin Daya Dace Akansu.

Jihar Kebbi Ta APC Ce Kuma Mai Girma Gwamna Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwandu") Na Asiwajo Bola Ahmed Tinubu Ne. Kauran-Gwandu Da Asiwajo Bola Ahmed Tinubu Zaɓin Allah Ne.

Duk Abunda Akeyi Na Cigaba Mai Girma Gwamna Da Shugaban Ƙasa Sunyi Munashi.

Daga Ƙarshe Ƴan-Tagwayen Kangiwa Yayi Addu'ar Allah Ya Ƙaraba Mai Girma Gwamna Dr. Nasir Idris ("Kauran-Gwandu") Da Shugaban Ƙasa Asiwajo Bola Ahmed Tinubu Nasara Suci Gabada Kawo Cigaba Cikin Jiharmu Ta Kebbi Da Najeriya Baki Ɗaya.

Ministan Tsaron Nigeria, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai...
30/04/2025

Ministan Tsaron Nigeria, Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai

A ranar Talata, 29 ga Afrilu 2025, mai girma Ministan Tsaro na Ƙasa, H.E. Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya karɓi baƙuncin Mr. Mohamed Malick Fall, wanda shi ne Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya a Najeriya kuma mai kula da harkokin jinƙai.

Tattaunawar wanda aka gudanar a ofishin Ministan dake Ship House, Abuja, ta mayar da hankali ne kan yadda Najeriya za ta ƙara tallafawa ayyukan jinƙai da Majalisar Ɗinkin Duniya ke gudanarwa a ƙasar.

Address

Potiskum State
Potiskum
YOBE

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Potiskum Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Potiskum Online News:

Share