Potiskum Online News

Potiskum Online News Sashen Labarai.

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar NajeriyaƘungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi t...
25/11/2025

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar Najeriya

Ƙungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi taron ’yan jarida domin bayyana damuwa kan yadda Ministan FCT, Nyesom Wike, da kuma yadda INEC ke nuna rashin adalaci game da sakamakon gangamin PDP na Ibadan ke zama babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Najeriya.

NDYC ta zargi Wike da amfani da muƙaminsa wajen tsoma baki cikin jam’iyya, tayar da rikici, tsoratarwa da kokarin tilasta ra’ayinsa, abin da ke yi wa tsarin dimokuraɗiyya mummunar illa. Ta ce halayensa na nuna girman kai, raina doka da neman iko su na iya tarwatsa ƙasa.

Kungiyar ta roki Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi Wike, ya tunasar da shi cewa shi bawa ne na jama’a, ba sarki ba.

A bangaren INEC kuwa, NDYC ta nuna damuwa kan yadda take jan kafa wajen tabbatar da zababben shugaban PDP Kabiru Turaki, tana nuna fifiko ga Damagum. Ta ce wannan ya tauye adalci, ya kuma lalata amincewar jama’a da hukumar zabe.

NDYC ta jaddada cewa sakamakon taron Ibadan halastacce ne, kuma INEC dole ta tsaya kan doka ba tare da shiga hannun masu son murde sakamakon siyasa ba don biyan buƙatar Wike.

Ta kuma bayyana cewa halayen Wike ba sa wakiltar mutanen Niger Delta gaba ɗaya.

A ƙarshe, NDYC ta ce za ta ci gaba da kare dimokuraɗiyya da doka, domin Najeriya ta fi kowane mutum girma, kuma duk wanda ya yi barazana ga tsarin mulki dole a tsawatar masa.

Da hannun
Comr. Israel Uwejeyan, National Coordinator, NDYC

22/11/2025

INEC's Shameful Bias

It’s now clear that INEC under this new chairman has abandoned neutrality and is gradually turning into Wike’s personal agency. The same INEC that spoke with confidence on Arise News on November 11 is now contradicting itself just to please Wike.

This sudden turnaround shows dangerous bias, a deliberate attempt to weaken the PDP and serve selfish political interests. A national institution should not dance to the tune of one politician, yet this INEC chairman seems ready to destroy credibility at all cost.

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDPA babban taron da ja...
21/11/2025

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDP

A babban taron da jam’iyyar PDP ta gudanar a Ibadan ranar Asabar da ta gabata, an ga wani sabon salo na shugabanci da jajircewa wanda ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa PDP har yanzu tana da waɗanda za su tsaya tsayin daka domin kare darajarta.

A cikin waɗanda s**a fito fili wajen nuna wannan kwazo, akwai Kauran Bauchi, wanda ya jagoranci aikin gyara da tsaftace jam’iyya da tsantseni. Tsayuwarsa wajen korar masu tada zaune tsaye a ciki, musamman waɗanda ke aiki da boyayyun manufa don rusa jam’iyyar daga cikin gida, ya zama abin yabo da koyi. A gaskiya, Kauran Bauchi ya zama ginshiƙin da ya hana jam’iyyar durkushewa.

Baya ga haka, Gwamnan Zamfara Dr. Dauda Lawal ya nuna irin kishinsa ga dimokuraɗiyya. Goyon bayansa ga sahihin tsari da adalci a cikin jam’iyya ya karfafa gwiwar mambobi da magoya baya, ya tabbatar masu cewa PDP na da shugabanni da ba za su lamunci karya ko shisshigi ba.

A bangaren Seyi Makinde, Gwamnan jihar Oyo, ya ba da cikakken gudunmawa wajen tabbatar da cewa taron Ibadan ya kasance sahihi, kuma cikin tsarin da ya dace. Makinde ya tabbatar da cewa jam’iyya ta gudana bisa ka’ida, ba tare da batan batu ko rikice-rikice ba, aikin da ya kara tabbatar da cewa PDP jam’iyyar da take da ni’imar shugabanni masu hangen nesa.

A tare, waɗannan manyan shugabanni uku sun yi abin da ake kira ceto martabar PDP, tare da dawo da yarda da kwarin gwiwar jama’a. Sun nuna cewa jam’iyyar adawa ba ta mutu ba, kuma ba za ta mutu ba, muddin akwai shugabanni irin su Kauran Bauchi, Dr. Dauda Lawal da Seyi Makinde.

A Ibadan, PDP ta sake tsayawa kan kafafunta kuma hakan ya sake busawa dimokuraɗiyya a rai.

Zamu Maka Ka A Kotu Muddin Baka Janye Kalamanka Akan Ya'yan Jam'iyyar PDP Ba ~ Kiran Hon Rabi'u Sayyadi Ga Ahmed Yarima ...
20/11/2025

Zamu Maka Ka A Kotu Muddin Baka Janye Kalamanka Akan Ya'yan Jam'iyyar PDP Ba ~ Kiran Hon Rabi'u Sayyadi Ga Ahmed Yarima

Ni, Hon. Rabi’u Sayyadi Kabo, tsohon ɗan takarar Majalisar jiha a ƙaramar hukumar Kabo a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ina so inja hankalin Ahmad Yerima, wanda ya bar jam’iyyarmu ta PDP tare da Atiku zuwa ADC.

Yerima, kai da kanka ka fita daga jam’iyyar da ka ci moriyarta shekara da shekaru, yau ka zo kana yaɗa ƙarya da bata sunanmu kana cewa ‘yan PDP da s**a halarci taron gangamin Ibadan biyanu aka yi? Kana cewa taron jam’iyyar da ta haifeka a siyasa, ta koya maka siyasa, ta ba ka suna, taro ne na hayar jama’a?

Wallahi wannan magana taka ta wuce iyaka. Babu wanda ya biya mu kobo guda ɗaya, yan siyasa ne mu masu ƙima da mutunci. Mun je Ibadan ne da kuɗinmu, da girmamawa da kishin jam’iyya, kuma ba mu da bukatar wani ya koya mana yadda ake nuna biyayya ga PDP.

Idan har kai yanzu da ka koma ADC, ka zauna a can ka tsara matsalolin jam’iyyarku. Kada ka kuskura ka dawo ka yi wa PDP kalaman batanci. Jam’iyya mai tarihi ce, mai tsari ce, mai daraja ce ba irin wadda kuka koma ba, wadda bata da tsari b***e tasiri.

Muna kira gare ka nan take ka fito fili ka janye maganarka ka nemi afuwa ga mambobin PDP da ka ciwa mutunci. Idan ba haka ba, mu a matsayinmu na mambobi masu bin doka, ba za mu yi wata-wata ba za mu gurfanar da kai a kotu saboda bata suna da yada ƙarya.

PDP ba wurin cin mutunci bace. Kuma wallahi ko da ka bar jam’iyya, ka guji zancen da bai shafe ka ba. Ka bar PDP da mutuncinta, ka koma ku gyara ADC naku da kuka koma.

Mun isa, kuma ba za mu yi shiru ba.

– Hon. Rabi’u Sayyadi Kabo
Tsohon ɗan takarar Majalisar jiha,
Ƙaramar hukumar Kabo, 2023.

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar  PDP Daga Jimo...
19/11/2025

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar PDP

Daga Jimoh Isma'il Adetunji

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta tabbatar da cewa Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya na ƙasa Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ita ce hukuma ɗaya tilo da ta dace a doka.

INEC ta ƙi yarda da takardar bogi da wasu korarru Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu s**a aika suna kiran a dage zaben fidda gwani na gwamnan Jihar Ekiti, matakin da ya fallasa yunƙurinsu na rugujewa jam’iyyar adawa ta ƙasa ta hanyar karya doka da son zuciya.

INEC ta jaddada cewa wannan takardar da waɗannan haramtattun shugabanni s**a turo a ranar 6 ga Nuwamba, 2025, ba ta da wani inganci. Su kansu sun yi ikirarin shugabanci ne bisa ƙarya, inda s**a jingina dalilan karya na wai “matsalolin shirye-shirye” domin su kawo tangarda ga zaɓen ranar 8 ga Nuwamba.

Hukumar ta bayyana a fili cewa kawai sa hannun shugaban jam’iyya na ƙasa da sakataren ƙasa na halastattaccen NWC ne ake karɓa a hukumance.

Matakin INEC ya yi daidai da hukuncin da jam’iyyar PDP ta yanke tun farko na dakatar da Anyanwu, Abdulrahman da wasu abokan aikinsu a ranar 1 ga Nuwamba, 2025 saboda aikata laifukan karya tsarin jam’iyya, wanda ya sabawa sassan 57(3), 58(1)(a)(b)(c)(h), da 59(1) na kundin tsarin PDP (2017 da aka gyara).

Wadannan hukunci an tabbatar da su ne a babban taron jam’iyyar da aka yi a Ibadan a ranar 15 ga Nuwamba, 2025, inda aka zaɓi Barrister Tanimu Turaki a matsayin sabon shugaban jam’iyya na ƙasa, tare da tsige manyan masu tada fitina ciki har da Anyanwu, Abdulrahman, Nyesom Wike da Ayo Fayose saboda aikata manyan laifuka na tafka ayyukan adawa da jam’iyyar, ƙirƙiro bangarori, da amfani da kotu wajen rugujewa jam’iyya.

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EUƘungiyar Nigeria Unite ta aika wa ...
14/11/2025

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EU

Ƙungiyar Nigeria Unite ta aika wa ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) da wasika mai zafi, tana zargin Ministan Abuja, Nyesom Wike, da haifar da barazana ga dimokiraɗiyar Najeriya ta hanyar murkushe ‘yan adawa da goyon bayan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin tabbatar da wa’adi na biyu ba tare da hamayya ba.

Ƙungiyar ta ce bayan rugujewar dimokiraɗiya a Mali, Burkina Faso da Nijar, yanzu haka Najeriya ma na kan layin tangal-tangal, saboda irin matakan zaluntar ‘yan adawa da kuma amfani da cin hanci wajen tilasta sauya sheƙa.

Ta gargadi cewar idan ba a dauki mataki ba, lamarin zai iya jefa Najeriya cikin rikici, ya kawo bacewar tsaro a yankin Sahel, tare da tura miliyoyin ‘yan Najeriya zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘yan gudun hijira.

Nigeria Unite ta kuma bukaci EU, AU, Amurka da Birtaniya su sanya takunkumi kan Wike da dakatar da shi daga tafiye-tafiye, tare da daukar mataki kan wasu manyan alkalan ƙasar, kwamishinan ‘yan sanda Abuja da hukumar INEC, domin cewar suna sabawa dokokin siyasa da na aikinsu.

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi KanuKungiyar Gamayyar Kungi...
19/10/2025

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi Kanu

Kungiyar Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) ta bayyana adawa da s**a mai tsanani kan shirin gudanar da zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu.

CNG ta ce wannan yunkuri da wasu shugabannin siyasa da na al’ada na kabilar Igbo, da masu kiran kansu ‘yan gwagwarmaya kamar Omoyele Sowore, ke jagoranta tare da wasu ‘yan Arewa marasa kishin ƙasa wani makirci ne na yi wa ƙasa karan tsaye da barazana ga zaman lafiya da doka.

Kungiyar ta bayyana cewa Nnamdi Kanu da IPOB sun haifar da mutuwar fiye da mutane 1,200 ciki har da jami’an tsaro sama da 400, sun ƙone ofisoshin ‘yan sanda fiye da 100, kuma sun jawo asarar dukiya da ta haura ₦450 biliyan a Kudu maso Gabas.

CNG ta tunatar da cewa tun daga 2016 Kanu ya kasance mai yada ƙiyayya, tashin hankali da rarrabuwar kai ta hanyar IPOB da rundunarsa ta ESN, inda aka kashe ‘yan Arewa da dama, aka lalata kasuwanci, tare da hana zaman lafiya.

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da shari’ar Kanu ta tafi yadda doka ta tanada ba tare da matsin lamba na siyasa ba, tare da bukatar jami’an tsaro su hana duk wata zanga-zangar da zata kawo tashin hankali.

CNG ta gargadi ‘yan siyasa da masu daukar nauyin zanga-zangar da cewa za a bincike su, tare da kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya bari a yi masa barazana wajen yin doka bisa ra’ayi ko jin kai.

A ƙarshe, CNG ta jaddada cewa sakin Nnamdi Kanu ba zai kawo zaman lafiya ba, sai dai ya kara dagula ƙasa da karya tsarin shari’a. Ƙasar da ba ta mutunta doka ba, ba za ta samu zaman lafiya ba.

Sa hannu:
Comrade Jamilu Aliyu Charanchi
Koodineta Na Ƙasa, CNG
Abuja, Najeriya

DOKAR HARAJI: Sanatan da ya jagoranci ƙaddamar da dokar ƙara haraji ta 2023. Wacce ake kira da Cyber security Levy. Tun ...
09/10/2025

DOKAR HARAJI: Sanatan da ya jagoranci ƙaddamar da dokar ƙara haraji ta 2023. Wacce ake kira da Cyber security Levy. Tun 2015 ake taƙaddama akan wannan tsinanniyar dokar. An rasa sanatan da ze jagoranta Sanata Shehu Buba shine ya jagoranta.

Amma Shehu Buba da yake ba mutanen Najeriya bane a gaban sa yayi sponsoring. Sanadin wannan dokar gwamanti take cire wa mutane 0.5% na transactions da s**a yi. Shehu Buba ya dawo tauraruwa me wutsiya, duk yanda ya shiga mutane suna tir dashi.

Daga Elder Karofi

Honourable Jamilu Isa Felicitates with Nigerians on 65th Independence AnniversaryAs Nigeria marks her 65th Independence ...
01/10/2025

Honourable Jamilu Isa Felicitates with Nigerians on 65th Independence Anniversary

As Nigeria marks her 65th Independence Anniversary, Honourable Jamilu Isa, former Supervisory Councillor of Jos South Local Government Area, Plateau State, under the platform of the All Progressives Congress (APC), has joined millions of patriotic citizens in celebrating this historic milestone.

In a special independence message, Honourable Isa congratulated Nigerians for their resilience, strength, and unwavering hope despite the many socio-economic and political challenges that the nation has faced over the years. He noted that Nigeria’s journey since 1960 has been marked with both trials and triumphs, yet the courage and determination of its people remain the country’s greatest asset.

According to him, “At 65, Nigeria has every reason to thank Almighty God for sustaining our unity as one indivisible nation. We must continue to work together, irrespective of tribe, religion, or political affiliation, to build a prosperous country where justice, equity, and fairness reign supreme.”

Honourable Isa further commended the founding fathers who laid the foundation of independence through sacrifice and vision, urging present-day leaders to emulate their legacy by prioritising good governance, accountability, and service to the people.

He also encouraged Nigerians not to lose hope, stressing that with collective effort, the country has the potential to overcome its present difficulties and emerge stronger. He called for peaceful coexistence, tolerance, and renewed patriotism among citizens, while reminding them that the progress of Nigeria lies in the unity of its people.

In his concluding remarks, the former councillor expressed optimism that the years ahead will bring greater peace, economic recovery, and development to the nation. He prayed for continued divine guidance for Nigeria’s leaders at all levels and for the prosperity of the entire nation.

Announcer: Zakariya Muhammad Musa

Kun Gaza Samar Da Tsaro a Najeriya Amma Kuna Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro Na UN – Comr Haidar H Hasheem........
29/09/2025

Kun Gaza Samar Da Tsaro a Najeriya Amma Kuna Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro Na UN – Comr Haidar H Hasheem
......Permanent peace a gida kafin Permanent seat a UN!

Na tabbata al’ummar Najeriya musamman mu a Arewacin ƙasar nan mun gaji da ji da gani: tsaro ya gagara, rayuka da dukiyoyin al’umma suna salwanta kullum, amma gwamnati ta kasa kawo mafita ta dindindin.

Abin takaici shi ne, duk da wannan gazawa, har yanzu ana neman kujera ta dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (UN Security Council). Tambayata ita ce: ta yaya za a nemi kujerar dindindin a wajen duniya alhali kuwa an kasa samar da tsaro na dindindin a gida?

Idan har gwamnati na son ta gina karɓuwa a kasashen duniya, to wajibi ne ta fara tabbatar da zaman lafiya da tsaro a cikin ƙasar nan. Ba za mu ci gaba da zama cikin halin kashe-kashe, garkuwa da mutane, da hare-haren ta’addanci ba, a lokacin da shugabanni ke neman kujerar yabo a waje.

Daga farko ya kamata a samar da tsaro na hakika ga ‘yan ƙasa kafin a nemi tsayuwa kan babban kujerar duniya.

✍️ Comr Haidar H Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writers

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar  Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad ...
28/09/2025

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad Abubakar Isah Ana Zarginsu da Karɓar Naira Miliyan 23 a Badakalar Kwangila Da Aka Danganta Da Hon. Adamu Aliyu

Daga Tukur I. Tukur

Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, tare da Sa’ad Abubakar Isah, ana zargin sun karɓi Naira miliyan 23 daga hannun Mohammad Jidda, wanda ya shigar da ƙara kan batun badakalar kwangila a Jami’ar Jos ƙarar tana hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka (ICPC).

Wannan batu ya fito fili ne a wata hira da mai aikin, Mr. Lawal Abubakar, wanda yake cikin rashin lafiya a gidansa da ke Dutsin-Ma, Jihar Katsina. Ya ce Hon. Idrisa Jidda ɗan’uwan mai ƙarar ne, Mohammad Jidda.

Mr. Lawal Abubakar ya bayyana cewa Hon. Idrisa Jidda, wanda a halin yanzu yake matsayin Mashawarcin Gwamna kan Harkokin Gidaje ga Gwamna Babagana Umara Zulum na Jihar Borno, ya karɓi Naira miliyan 20 daga asusun Zenith Bank na kamfanin Imanal Concept Ltd, mallakar Sa’ad Abubakar Isah wannan kuɗi na daga cikin abin da ake tuhuma da shi da aka danganta da sunan Hon. Adamu Aliyu.

Mr. Abubakar ya ce shi dai kawai ya gabatar da Hon. Adamu Aliyu ga mai kasuwancin Mohammad Jidda, ya kuma umarce shi ya sanya kuɗi a asusunsa. Bayan kwangilar ta karye, “na faɗa wa Adamu ya mayar da duk abin da aka biya shi, kuma an shaida min cewa ya mayar.”

A cewar Mr. Lawal Abubakar, Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah sun tunkari Mohammad Jidda s**a karɓi kuɗaɗe daga kamfaninsa, Mohibba Investment Limited, s**a raba su tsakaninsu.

“Sun yaudari Mohammad Jidda suna cewa an biya Hon. Adamu Aliyu. Amma a ranar 29 ga Disamba, 2023, Alhaji Idrisa Jidda ya karɓi Naira miliyan 20 da aka shigar masa a asusun Zenith Bank daga Imanal Concept Ltd. Ina da rasit ɗin banki da zai tabbatar da hakan. Dukkanin asusun da aka yi ma’amala da su suna a Zenith Bank,” in ji Mr. Lawal Abubakar.

Ya ƙara cewa akwai ƙarin takardu da hujjoji da ke nuna wasu ma’amaloli da s**a shafi Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah.

“Sa’ad Abubakar Isah tare da Hon. Idrisa Jidda sun taɓa haɗuwa da mai ƙarar s**a ce suna wakiltar Mr. Lawal Abubakar. S**a karɓi Naira miliyan 23 s**a raba tsakanin su. Saboda haka ya kamata mai ƙarar ya mayar da ƙarar ne a kan Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah (mai kamfanin Imanal Concept Ltd), ba kan Hon. Adamu Aliyu ba,” ya yi nuni.

Gwamnatin Tinubu Ta Fi Duk Gwamnatocin Mulkin Soja Muni Da K**a Karya A Tarihin Nijeriya, Inji El-RufaiTsohon Gwamnan Ji...
22/09/2025

Gwamnatin Tinubu Ta Fi Duk Gwamnatocin Mulkin Soja Muni Da K**a Karya A Tarihin Nijeriya, Inji El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya jefa sabon kakkausan magana kan gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana cewa wannan gwamnati ta fi kowace gwamnatin soja da Najeriya ta taba fuskanta muni da zalunci, kamar yadda jaridar Channel Television s**a wallafa.

El-Rufai ya jaddada cewa talakawa na cikin mawuyacin hali, matsin tattalin arziki ya yi tsanani, farashin kaya ya haura sama, sannan rashin tsaro ya kara ta’azzara. Ya ce idan aka kwatanta halin da ake ciki yanzu da lokacin mulkin soja, rayuwar ‘yan Najeriya ta fi ta yanzu sauki.

Wannan furuci na El-Rufai ya janyo cece-kuce a tsakanin ‘yan kasa, inda wasu ke ganin ya dace a saurari wannan kira saboda gaskiyar abinda ke faruwa, yayin da wasu kuma ke kallon shi a matsayin kalaman tunzuri na siyasa.

Ko me zaku ce?

Daga Comr Haidar H Hasheem

Address

Potiskum State
Potiskum
YOBE

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Potiskum Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Potiskum Online News:

Share