28/04/2026
Assalamu alaikum warahmatullah.
Ina muku fatan alkhairi baki ɗaya. Gaskiya na ji daɗin yadda na ga al’umma suna nuna so da ƙauna ga ɗan takararmu na House of Representatives na Nàngere/Potiskum, wato Hon. Yahaya Bello Garba (YG). Yadda mutane suke tururuwa wajen bayar da gudummawa domin sayen fom ɗin takara, abin a yaba ne sosai, in shaa Allah.
Wannan yana nuna irin kyakkyawan halaye da kyautatawar da Hon. YG yake yi wa al’umma—ta fuskar tallafawa matasa da jari, taimakon marayu, da kuma kula da marasa lafiya, da sauransu. Haƙiƙa wannan matashi abin koyi ne; idan za a lissafa ayyukansa, ba za a gama ba. Ni na san shi sosai—ganau ne, ba jiyau ba kuma ina tabbatar da ƙoƙarinsa.
Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce a cikin
Alƙur’ani:
“Lallai Allah yana umurni da adalci da ihsani (kyautatawa)…”
“هل جزاء الإحسان إلا الإحسان” (a cikin Qur'an, Suratul Rahman
“Shin akwai wani sakamakon kyautatawa face kyautatawa
Don haka, ina kira ga al’ummar Nàngere/Potiskum da mu fito mu zaɓi gwarzo, Hon Yahaya Garba Bello