Arewa A Yau

Arewa A Yau Mun Kirkiri Wannan Shafin Badan Komai Ba Sai Dan Nemowa Talakan Arewa Mafita Da Zaman Lumana. Arewa Tamuce

AREWAWA MASU ABIN MAMAKIAkwai damuwa mai sosa zuciya ganin yadda al’ummar Arewa suke rayuwa, rayuwar yan Arewa cike take...
27/02/2026

AREWAWA MASU ABIN MAMAKI

Akwai damuwa mai sosa zuciya ganin yadda al’ummar Arewa suke rayuwa, rayuwar yan Arewa cike take da son rai da kuma makauniyar soyayya ta wasu mutane wadanda kullum suke amfani da jahilcin da ya dabaibaye Arewa domin amfanar da siyasar su.

Acikin mutanen duniya irin su Barr. AUDU BULAMA BUKARTI basu da yawa, Bulama mutum ne da yake fadar ra’ayin sa na gaskiya baya damuwa ya fadi abinda mutane suke so suji, ko kuma yabi ra’ayoyi mafi rinjaye (majority) domin jama’a su yaba masa saboda yana tsoro kar a zage sa. Ba ruwan sa, ko ka zage sa ko ka yabe sa, shi dai zai fadi abinda ya gamsu na gaskiya ne.

A wata daya da ya gabata, kowa yaga yadda aka kulla makirci a duniya akan Arewa da Musulmai, aka rubutawa Amurka korafi cewa Musulmai nayiwa Kiristoci kisan kare dangi acikin Najeriya, mutumin da yafi kowa jajircewa akan yakar wannan makircin shine AUDU BULAMA BUKARTI, ya shiga cikin manyan jaridu na duniya irin su ALJAZEERA ya karyata wannan labarin na kashe kiristoci a Najeriya, ya kare Arewa da Musulunci, yafito ya fadawa duniya asalin halin kunci da yan ta’addan s**a jefa musulmai aciki a yankunan Arewa.

Kowa yaga irin gudunmawar da Barr Bulama Bukarti ya bayar, an jinjina masa, an yaba masa bisa irin wannan namijin kokarin, babu wanda ya biya shi, babu wanda ya taimaka masa, amma kullum burin sa yaga ankawo karshen zaluncin da akeyiwa yan Arewa, ya sadaukar da rayuwar sa wajan fadin gaskiya da yakin yan ta’adda.

A wannan sati Barr Bulama Bukarti yayi cikakken bayani akan Mallam Nasiru Elrufai, yadda Elrufai ke yada karya da propaganda akan abokan hamayyar sa na siyasa, da kuma irin yadda yayi bayani a babban gidan talabijin na kasa Arise cewa sunyi kutse cikin wayar mai bawa shugaban kasa shawara akan sha’anin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu kuma suna sauraron duk wasu bayanai da yake fada, Barr Bulama Bukarti ya nuna yadda Nasiru Elrufai ya daure kan sa da yayi wannan jawabi, domin wannan kadai ya isa yaja a daure sa abisa dokar PRIVACY ta Najeriya.

Akwai takaici da damuwa yadda wasu ke ainata ko zagin Barr Bulama Bukarti domin su kare Nasiru Elrufai, wallahi kaf yan siyasar Arewa a yanzu babu wanda yake bayar da gudunmawar da Barr Bulama Bukarti yake bayarwa domin Arewa, yadda Bulama ya sadaukar da rayuwar sa domin nemawa Arewawa yanci da wayar musu da kai akan irin mulkin zaluncin da akeyi a yankunan mu. Allah yakara maka jagora. Mungode Barr Bulama Bukarti.

~ Allah yasa mu gane masu sonmu na Gaskiya ya bamu ikon ganewa.!!!!

Me ake kullawa Nigeria; Dan Majalisar Amurka Ya Miƙa Rahoto Mai Zafi ga Fadar White House dake nuna Lokaci Ya Yi da Za a...
24/02/2026

Me ake kullawa Nigeria; Dan Majalisar Amurka Ya Miƙa Rahoto Mai Zafi ga Fadar White House dake nuna Lokaci Ya Yi da Za a Dakatar da Tsananta wa Kiristoci a Najeriya

A wani mataki mai ƙarfi da ya jawo hankula a Yammacin Afirka da ma duniya baki ɗaya, ɗan Majalisar Wakilan Amurka, Riley Moore, ya bayyana a gaban White House a ranar 23 ga Fabrairu 2026, yana riƙe da cikakken rahoton majalisa da aka tsara domin dakile ci gaba da tashin hankalin da ake zargin ana yi wa Kiristoci a Najeriya.

Rahoton ya biyo bayan bincike na ɓangarorin siyasa biyu (bipartisan), ciki har da wata ziyara ta gano gaskiya da Moore ya kai zuwa yankin Middle Belt na Najeriya, inda aka ce rikice-rikice sun daɗe suna addabar al’umma. Daga bisani, Moore ya miƙa rahoton ga gwamnatin Donald Trump. Wannan na zuwa ne watanni bayan da Shugaban Ƙasar ya sake ayyana Najeriya a matsayin Country of Particular Concern (CPC) a ranar 31 ga Oktoba 2025, bisa zargin take ‘yancin addini — matakin da ya soke cire sunan da aka yi a baya.

Moore, mabiya ɗariƙar Roman Catholic mai wakiltar West Virginia, ya yi magana kai tsaye ba tare da ɓoye ra’ayi ba. Ya ce, “’Yan’uwanmu Kiristoci sun daɗe suna shan wahala cikin shiru. Yanzu duniya na kallo.”

Binciken ya tattaro bayanai masu tayar da hankali, inda aka ce ‘yan bindiga da ake dangantawa da Fulani da wasu ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi sun aikata kisan gilla, ƙona ƙauyuka, da tilasta wa jama’a barin muhallansu, musamman a kan al’ummomin manoma Kiristoci. Wasu da s**a tsira sun ba da labaran asarar rayuka da dukiya, da kuma mawuyacin halin da suke ciki a sansanonin ‘yan gudun hijira na cikin gida (IDP), waɗanda a wasu lokuta ake kai wa hare-hare.

Rahoton ya ƙunshi shawarwari masu tsauri da s**a haɗa da:

• Ƙulla sabuwar yarjejeniyar tsaro tsakanin Amurka da Najeriya domin kare al’umma masu rauni da rusa hanyoyin ‘yan ta’adda

• Dakatar da wasu tallafin Amurka muddin gwamnatin Najeriya ba ta nuna ƙwazo a kare Kiristoci ba

• Ɗora takunkumi da hana biza ga waɗanda ake zargi da hannu a rikice-rikicen, ciki har da jami’an da aka ce sun yi sakaci

• Ba da tallafin fasaha domin rage barazanar ƙungiyoyin ‘yan bindiga

• Kira da a sake duba dokokin Shari’a da na batanci da ake zargin suna haifar da wariya

• Haɗa kai da ƙasashe abokan hulɗa k**ar France, Hungary, da United Kingdom

Moore ya jaddada muhimmancin haɗin kai maimakon gaba, yana mai kira ga gwamnatin Najeriya da ta yi amfani da wannan dama wajen ƙarfafa dangantaka da Amurka tare da tabbatar da tsaron dukkan ‘yan ƙasa.

Saƙon ya haifar da muhawara mai zafi a kafafen sada zumunta. Wasu Kiristoci ‘yan Najeriya da ‘yan diaspora sun nuna godiya kan yadda aka jawo hankalin duniya, yayin da wasu kuma s**a nemi a ɗauki matakai masu ƙarfi. A gefe guda, masu s**ar rahoton sun yi zargin cewa mayar da hankali kan bangare guda na iya yin watsi da faɗaɗɗen matsalar tsaro da ke shafar kowa.

Sai dai babban saƙon rahoton ya fito fili: bayan shekaru na tashin hankali da asarar dubban rayuka, ana neman a ɗauki matakan da za su tabbatar da adalci da sauyi.

Rahoton ya isa White House. Tambayar yanzu ita ce: shin za a ga mataki mai ma’ana? Kuma yaushe ne waɗanda s**a daɗe suna jira za su samu sauƙi?

WALLAHI TALLAHI BANTAƁA GANIN ƘABILAR DA BÃTA KISH!N ƘABILARTA BA KAMAR HAUSA WALLAHI Duba yadda ake k!san hausawan ƙasa...
06/02/2026

WALLAHI TALLAHI BANTAƁA GANIN ƘABILAR DA BÃTA KISH!N ƘABILARTA BA KAMAR HAUSA WALLAHI

Duba yadda ake k!san hausawan ƙasar nan, k!san da ko dabbobi ba'ayiwa shi

A isko bahaūshe a gonar sa a hãrbē shi ko a k**a shi a tafi dashi daji a ɗaurē shi ana bashi mūgūn duka kuma daga baya dõle sai ƴan uwan sa sun haɗa miliyoyin kuɗaɗe domin amso sa

Wani sai anyi bara ake samun abinda aka amso sa, wani kuma sai ƴan uwa sunyi karo karo, wani kuma sai an saida duka kadarorinsa har gidan da yake a ciki sannan a amso sa, wani ma sai an kai musu kuɗi kuma su haɗa da wanda yakai kuɗi da wanda yake hannun su duk su kãshē su

Zumunta tayi ƙaranci saboda mutum yana tsoron yaje garin da ƴan uwan sa suke a sãce shi

Kana saman hanyarka ta neman abinda zakaci baka tsira ba, kana gida ma baka tsira ba

Azo ak**a Yaranku mata kunaji kuna gani aje dasu ayi masu fyãɗē

Arewa an ƙonē mutanē da ransu a sokoto hanyar isa, an ƙõna mutane da ransu a zamfara, an yãnka mutane da ransu a kebbi mutum 17 an yãnka wasu a Niger mutum 40

An maida mata da yawa zãwarawa wasu kuma an mai dasu marãyu an kuma maida masu arziƙi da yawa mabaratæ

Arewa ba'a baiwa yarãn mu ilim! ba wasu makarantin nen ma a rufe suke

Arewa babu tit!n mai kyau wanda direbobin mu zasuji daɗin sa

Arewa anbar assibitayye sun lãlace anƙi gyarawa saboda talakawa ne ke zuwa neman magani ba ku ba

Arewa babu wutar nefa wasu ƙauyukan babu ruwan sha masu kyãu

Yanzu abin har yakai a k**a mutanē da ransu ayi masu yañkan rãgõ har sai an cire kan mutūn a aza a saman ƙirj!nsa wasu kuma a ƙonã su da ransū 😭

Amma malaman arewa sunyi shiru, babu abinda Sukeyi sai kaf!rta junansu

Ƴan social media namu babu abinda sukeyi sai shi!rme da yaɗa munãnan abubuwa domin su samu Followers ko monietization

Mutanen arewa su kuma babu abinda suke sharing sai sh!rme da hauka amma duk abinda ya shafi harkar tsãrõ kowa yayi halin ko in kula ba ruwansa

Abinma bãkin cikin yanzu sai lokaci zãɓē yazo azo ana baiwa ƴar arewa taliya ko tirmin ƴar leda ko mudun masara ko 10k kuma su sake zãɓelēn waɗan nan azzãlūmãn mutãnēn marasa !mani

Indai kana kishin AREWA kuma na baƙin cik!n da abinda yake faruwa a ãrewa to kayi Sharing na wannan saƙon koda a cikin group 2 har sai yakai ga ãzzãlūman mūtanen

Kuma kaje ka faɗakar da al'umar garinku kona shiyarku cewa bana sabuwar tafiya za'ãyi kar su yarda su ƙara zãɓēn mutanen da basa ƙaūnãrsu basa son rãyūwársu

Daga Ɗan Gwagwarmayar Nan Ne Naku, Sadiqu Sani Gandi. Hasbunallahu wani'imal wakil 😭

Saboda ƙin Allah Yanzu Nasan Idan Zaka Sharing Na Wannan Post Facebook Zasu Cema Wannan Ba Labarin Gaskiya Ba Ne Don Suna Maƙ!yãn Allah

ALLAH KA ISÃR WA MUTANEN AREWAAllah Sarki Arewa😭😭 wannan shine abinda muke gani yana faruwa a kusan kullun da 'yan uwan ...
06/02/2026

ALLAH KA ISÃR WA MUTANEN AREWA

Allah Sarki Arewa😭😭 wannan shine abinda muke gani yana faruwa a kusan kullun da 'yan uwan mu, ana kash£ mana 'yan uwa k**ar dabbobi

A cikin sati biyu kadai, 'yan ta'adda sun kash£ mutanen Arewa mutum 43 a jihar Katsina, mutum 17 a jihar Zamfara, mutum 19 a jihar Niger, kebbi 17 mutum 170 a jihar Kwara, adadin da aka kashe 256. Kuma waɗan nan basu kaɗai bane akwai na gabascin Sokoto da aka kashewa kullum

Wani dan siyasa ne daga Arewa ya fito yayi magana?
Wani Babban Basarake ne daga Arewa ya fito yayi magana?
Wani Babban Malami ne ya fito yayi magana?

Ina ga babu, idan akwai watakila hankalina bai kai gurin ba, akwai bukatar hadin kan manyan Arewa cikin gaggawa domin su yi magana da murya daya

Ba kuma batun a fito ayi magana ba kadai, tsawatarwa ya k**ata su yi, idan wadanda suke da alhakkin daukar mataki sun ki dauka sai manyan Arewa su ja layi k**ar yadda manyan Kudanci suke yi

Abin takaici, kana fadin gaskiya akan zaluncin da aka yiwa Arewa wanda ya saba da ra'ayin masu iko da Gwamnati zasu tura a k**aka a duk inda ka buya, amma ga can 'yan ta'adda suna kashe al'umma an gagara kawar da su

Akwai ranar kin dillanci, kowani azzalumi zai hadu da sak**akonsa tun anan duniya kafin mu isa lahira

Yaa Allah Ka isar wa Arewa da mutanenta

02/02/2026
ALLAHU AKBAR.ALLAH subhanahu wata'ala ya karbi rayuwar Sheikh Usman Kusfah Rigi-Rigi Muna rokon Allah ya jikansa da raha...
02/02/2026

ALLAHU AKBAR.

ALLAH subhanahu wata'ala ya karbi rayuwar Sheikh Usman Kusfah Rigi-Rigi

Muna rokon Allah ya jikansa da rahama ya gafartamasa.

Allah ya jikan musulami da s**a rigamu gidan gaskiya yayi mana afuwar gamawa da duniya lafiya Ameen.🤲🏾

25/11/2025

We Don’t Even Know Who’s Next… We’re Tired of Losing Soldiers to Ambushes” — Nigerian Soldier Cries Out, Prays for God’s Protection Over Every Military Personnel

ALHAMDULILLAH Yanzun nan Kotu ta yanke wa t$ag£eri Nnamdi Kano jag0ran 'yan tá'add@n Bi¥afara daurin rai da rai a gidan ...
20/11/2025

ALHAMDULILLAH

Yanzun nan Kotu ta yanke wa t$ag£eri Nnamdi Kano jag0ran 'yan tá'add@n Bi¥afara daurin rai da rai a gidan yarin Kuje dake Abuja

Alkalin Kotun ya tausaya masa ya rage masa hukunci daga hukuncin ki$a zuwa daurin rai da rai bayan k**ashi da laifin aikata ta'add@nci da cin amanar Kasa har guda bakwai

Shikenan an shafe tarihin Nnamdi Kanu a doron duniya, Nigeria ikon Allah ne ba na mutum ba, Nigeria zata zauna lafiya da ikon Allah

Allah Ka tabbatar mana da zaman lafiya a Kasarmu Nigeria

20/11/2025

Arewacin Nigeria 🇳🇬 Da Niger 🇳🇪. 😭

Don Allah Kusaka Arewa Da Niger A Addu'a

20/11/2025
Ko kunsan cewa mafiyawan shanun da fulanin daji ke kiwo banasu bane?Shanun wasu attajiran yan siyasa ne, sarakunan garga...
20/11/2025

Ko kunsan cewa mafiyawan shanun da fulanin daji ke kiwo banasu bane?

Shanun wasu attajiran yan siyasa ne, sarakunan gargajiya da masu mulki

Shiyasa idan shanu s**a cinye amfanin gonarku, babu wani mataki da ake ɗauka a hukumance

- Idan ka kai ƙara gurin yan sanda, sai a kira DPO daga sama ace ya janye wannan case.

Address

Sokoto
Rabah

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa A Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share