Arewa A Yau

Arewa A Yau Mun Kirkiri Wannan Shafin Badan Komai Ba Sai Dan Nemowa Talakan Arewa Mafita Da Zaman Lumana. Arewa Tamuce

Rikicin ƴan bindiga ya sake ƙazanta a ƙaramar hukumar Shagari ta jihar Sakkwato, inda aka kashe aƙalla mutum biyar tare ...
01/09/2025

Rikicin ƴan bindiga ya sake ƙazanta a ƙaramar hukumar Shagari ta jihar Sakkwato, inda aka kashe aƙalla mutum biyar tare da yin garkuwa da limamai da hakimin garin Rinaye.

Shaidu daga yankin sun ce hare-haren sun ci gaba tsawon kwanaki uku a jere, inda ƴan bindigar ke kai farmaki ƙauyuka daban-daban, suna kashe mutane tare da sace wasu, ko a garin Rinaye, an tabbatar da cewa sun yi garkuwa da mai garin da limaman garin, bayan sun kashe mutum uku.

Rahotanni sun nuna cewa sama da ƙauyuka goma sun watse sak**akon tsanantar hare-haren, lamarin da ya tilastawa daruruwan mazauna yankin yin zanga-zanga a babbar hanyar da ta haɗa Sokoto, Kebbi da Neja domin nuna fushi da rashin kulawar gwamnati agare su.

Wasu daga cikin mutanen da abin ya shafa sun ce ba su da wani tallafi daga gwamnati ko jami’an tsaro, inda s**a yi kira da a kawo musu ɗauki cikin gaggawa.

Hukumomin bayar da agajin gaggawa na ƙasa dana jihar NEMA da SEMA sun tabbatar da samun rahoton ƴan gudun hijira daga yankin, inda s**a ce sun kai ziyara wasu rukunin gidaje da s**a karɓi waɗanda s**a tsere daga hare-haren.

Wannan itace Masallacin da ke jihar Katsina A garin Malumfashi wanda 'yan ta'adda s**a yi dirar mikiya cikinta har s**ai...
22/08/2025

Wannan itace Masallacin da ke jihar Katsina A garin Malumfashi wanda 'yan ta'adda s**a yi dirar mikiya cikinta har s**ai sanadiyyar mutuwar mutane Aƙalla 30 😭 ubangiji Allah muke Roƙo da yayi musu rahama su kuma 'yan ta'addan ubangiji Allah ya yi mana maganinsu tare da iyayen gidan nasu bijahi sayyidina Rasulullah s.a.w 😘🥰

ALLAH ya kawo mana mafuta'''Idan jahilci ne yasanya Fulani s**a karbi ta'addanci sukuma ɗaiɗaikun hausawa da sukeyimusu ...
12/08/2025

ALLAH ya kawo mana mafuta'''

Idan jahilci ne yasanya Fulani s**a karbi ta'addanci sukuma ɗaiɗaikun hausawa da sukeyimusu informers menene yajanyo hakan?

Ansha k**a informers acikinmu hausawa, wani ɗanuwanka ne wani kuma abokinka ne, wani makwabcinka ne amma za'a haɗa kai dashi akasheka ko ayi garkuwa dakai, dukwani motsinka yana kallo dayaganka dawasu yan canji zaigayawa Fulani kuma ya sanar dasu sanda zasu iskeka

Harwasu ma naganin cewa illar informer tafi ta ɗan ta'adda sbd informer muna fukine kuma yanatare dakai

Shiyasa zaiyi wahala a iya maganin wannan matsalar saboda kunsan meyasa?

Akwai sa hannun kowa da kowa aciki.

1-Gwamnati
2-Fulani
3-Jami'an tsaro
4-ɗaiɗaikun hausawa
5-Dawasu ƙabilu waɗanda ma ba yan arewa bane.
6-Sarakuna
7-Malaman zamani
8-Saikuma uwa uba turawa da yahudawa dake tsara komai

Dukkan wadannan dana lissafo sunada hannu awannan taaddanci saidai baduka ba duk lalacewa akwai nagari.

Kowace irin matsala aduniya sai anfara gano hakikanin masu haddasata kafin a maganceta

Mekuke ganin yajefa ɗaiɗaikun hausawanmu suke zama informers?

Sulhu da B£||0 T¥rj¡ ko wasu ƙungiyoyin ’yan T★a’adda ba alheri ba ne a Najeriya.A zahiri, irin wannan sulhu yakan ƙara ...
12/08/2025

Sulhu da B£||0 T¥rj¡ ko wasu ƙungiyoyin ’yan T★a’adda ba alheri ba ne a Najeriya.

A zahiri, irin wannan sulhu yakan ƙara musu ƙarfin guiwa, ya sa su ɗauka cewa kullun ana jin tsoronsu ne, kuma hakan na iya sa su sake komawa aikata laifukansu na T★æddãnci da kæ$he-kã$hen mutane.

A ƙa’ida, zalunci ba a sasanta shi siddan sai da hukunci na adalci.

Idan aka yi sulhu da wanda yake kashe mutane, ya yiwa Mata fyade, ya kona ƙauyuka, kuma aka yi masa rangwame ba tare da hukunci ba, zai zama ƙalubale ga tsaron kasa.

Domin nan gaba ma wata ƙungiya zata iya ɗaukan makami ta yi T★æddãnci ganin cewa su ma za a yafe musu ayi sulhu da su ayi musu afuwa.

A Musulunci, sulhu hanya ce ta samun zaman lafiya da kawar da barna, amma sulhu yana da sharudda, ba a kowanne hali ake yin sulhu ba, musamman idan za a ƙarawa masu aikata zalunci ƙarfi.

A cikin Al-ƙur'ani Allah yana cewa:👇

إِنَّمَا جَزَٰٓؤُا۟ ٱلَّذِينَ يُحَارِبُونَ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَيَسْعَوْنَ فِى ٱلْأَرْضِ فَسَادًا أَن يُقَتَّلُوٓا۟ أَوْ يُصَلَّبُوٓا۟ أَوْ تُقَطَّعَ أَيْدِيهِمْ وَأَرْجُلُهُم مِّنْ خِلَـٰفٍ أَوْ يُنفَوْا۟ مِنَ ٱلْأَرْضِ ۚ ذَٰلِكَ لَهُمْ خِزْىٌۭ فِى ٱلدُّنْيَا ۖ وَلَهُمْ فِى ٱلْـَٔاخِرَةِ عَذَابٌ عَظِيمٌ

"Lalle sak**akon waɗanda s**a yi yaƙi da Allah da Manzonsa, s**a yi ta yin fasaɗi a ƙasa, shi ne a kashe su, ko a gicciye su, ko a sare musu hannaye da ƙafafu daga ɓangarori daban-daban, ko a kore su daga ƙasa. Wannan shi ne hukuncin wulakanci a gare su a duniya, kuma a lahira suna da azaba mai girma"

Wannan na nuna mana cewa kæshe mutane da aikata fasadi a kasa laifi ne mai girma, kuma hukuncinsa ba tattaunawa ba ce, kaɗai hukunci ne na adalci.

Manzon Allah ﷺ ya yi sulhu da makiya a wasu lokuta, amma duk lokacin da aka yi sulhu da su, ba a bar su sun ci gaba da aikata zalunci ba.

Amma idan wani yana ci gaba da kashe bayin Allah, ya na fashi da fyaɗe, yana kona ƙauyuka, ya sace mutane ya karɓi kuɗin fansa, toh sulhu da shi na nufin ba shi izini da kariya don gobe ma waɗansu yan T★ddã su ci gaba

25/07/2025

SHIN KA IYA SALLAH GAWA ?

To bari in bayyana mataki-mataki yadda ake gudanar da Sallar Gawa (Salatul Janazah) a Musulunci. Wannan salla tana da sauki amma tana bukatar fahimta da tsabta da niyya.



***YADDA AKE SALLAR GAWA (SALATUL JANAZAH)

✅ Sharuɗɗan Sallar Janaza:

1. Gawa ta zama Musulmi.

2. A wanke ta, a nade da likkafani.

3. A shimfiɗa gawa a gaban masu salla.

4. Jama’a su tsaya cikin layi (ba ruku’u, ba sujada).

5. A yi niyya.

**** Matakan Sallar Gawa:

1. Niyya (a zuciya):
“Zan yi sallar janaza ga wannan mamaci domin Allah.”
(Ba a furta niyya da baki).

2. Takbira na Farko:

Ka ce “Allahu Akbar”

Ka karanta Fatiha (Bismillah har zuwa Walad-daallin. Ameen ba dole ba)

3. Takbira na Biyu:

Ka ce “Allahu Akbar”

Ka karanta Salati ga Annabi (SAW):
“Allahumma salli ala Muhammadin wa ala aali Muhammadin...”

4. Takbira na Uku:

Ka ce “Allahu Akbar”

Ka yi addu’a ga mamaci, k**ar:
“Allahummaghfir lahu warhamhu wa ‘aafihi wa’fu anhu...”
(In mamaci mace ne: laha maimakon lahu)

5. Takbira na Hudu:

Ka ce “Allahu Akbar”

Ka yi addu’ar karshe, k**ar:
“Allahumma la tahrimna ajrahu wa la taftinna ba’dahu...”

6. Sallama:

Ka ce “Assalamu Alaikum wa Rahmatullah” (sau ɗaya, a dama kawai ko dama da hagu).

📝 Lura:

Ba a yin ruku’u ko sujada.

Ana yin sallar ne da tsaye idan mutum na da lafiya.

Za a iya yin sallar mutum ɗaya ko da jama’a ba su da yawa.

Kuyi F0ll0wing din Wannan shafin 👉 Tsoratarda Musulmi Daga Jinkirta Salla Domin Samun Fadakarwa Tunatarwa da sauran karatun Addini

25/07/2025

Aɗa'u ɗan yasar ya ce " shi ( wailun ) wani kwari ne a cikin jahannama, ita kanta jahannama tana neman tsarin Allah daga bala'in zafin wailun, kuma shi ne mazaunin masu jinkirta sallah daga LOKACINTA

An tambayi Hassan al_busari game da ayar da Allah ke cewa bone ya tabbata ga masallatan da suke marabkana daga barin sallolinsu" sai yace Ana nufin wanda yake barin sai lokacin sallah ya shige sannan ya yi".wasu kuma daga cikin masu tafsir s**ace "wanda idan yayi sallar a cikin LOKACINTA bayayin farinciki, kuma in ya jinkirtata bayajin ɓaƙinciki, kuma baya ganin cewa gabatar da ita a cikin lokacinta shi ne alheri, kuma jinkirta ta babban laifi ne, don wannan yana daga mutuwar zuciya

Shi kuma wahab ɗan munabbahi yace yana mamakin yadda mutane ke yiwa wanda ya mutu kuka alhali kuwa mai makon suyiwa wanda zuciyarsa ta mutu kuka, domin kuwa mutuwar zuciya yafi rabuwa da duniya musifa

Ku tarbemu a gaba kaɗan, ku kuma yi follow na wannan page mai albarka wato Tsoratarda Musulmi Daga Jinkirta Salla

25/07/2025

Kai CHONKA ya kai mai barin sallah. Kana raye a cikin duniya kana ta wahala kuma kana ta gajiya domin neman jin daɗin rayuwa. Kuma kana kwaɗayin yardar mutum ɗan'uwanka. Allah maɗaukaki ya umurce ka da yin sallah, ya kuma sanya ta tsira a gareka daga wuta, amma kai sai ga ka kana wofintar da ita, kana yin kasalar yinta kuma kana wulaƙanta ta.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su ƙara dawwama a gare shi yace, Duk wanda yabar sallar La'asr haƙiƙa dukkanin ayukkansa sun ɓaci" A cikin wata riyawar kuma aka ce "Duk wanda yabar sallar La'asr ta wuce shi k**ar an kwashe masa iyalinsa da dukiyarsa ne baki ɗaya

Allah yasa mu gyara, kuyi follow na wannan page mai albarka wato Tsoratarda Musulmi Daga Jinkirta Salla

25/07/2025

Manzon Allah tsira da amincin Allah su dawwama a gare shi yace,, '' Duk wanda ya haɗa salloli biyu batare da wani uzuri ƙwarara ba, to kuwa yajewa wata kofa daga kofofi manya na zunubi".

Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su dawwama a gare shi yace "Duk wanda yabar sallah da gangan to Allah ya rubutu sunansa a kofar wuta daga jimlar wanda zaya shigeta" A wata faɗar kuwa akace wanda yabar sallah da gangan haƙiƙa aikinsa ya ɓaci".

Allah yasa mudace, ayi follow na wannan page mai albarka watoTsoratarda Musulmi Daga Jinkirta Salla

INNALILAHI WA INNA ILAHI RAJI'UUN!!Wannan wace irin kasa ce mu ke cikin ta😥😥😥😥Yadda 'yan bindiga su ka hallaka wasu mata...
25/05/2025

INNALILAHI WA INNA ILAHI RAJI'UUN!!

Wannan wace irin kasa ce mu ke cikin ta😥😥😥😥

Yadda 'yan bindiga su ka hallaka wasu mata da qananan yara a karamar hukumar Kauran Namoda da ke cikin jihar Zamfara.

Ya Rabbi mun kawo kukanmu a gare ka, muna rokonka da ka hallaka wadannan miyagun bayunka masu cutar da bayun ka.😥😥😥

Address

Sokoto
Rabah

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa A Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share