Arewa A Yau

Arewa A Yau Mun Kirkiri Wannan Shafin Badan Komai Ba Sai Dan Nemowa Talakan Arewa Mafita Da Zaman Lumana. Arewa Tamuce

Tun ƙarfe 5 na asubahin yau ake jin ƙarar bqma-bqmai gami da ɓarin wutq mai zafi na tashi har yanzu a cikin dajin dake y...
04/09/2026

Tun ƙarfe 5 na asubahin yau ake jin ƙarar bqma-bqmai gami da ɓarin wutq mai zafi na tashi har yanzu a cikin dajin dake yammacin Yantumaki ta ƙaramar hukumar Ɗanmusa a jihar Katsina, muna Addu'ar Allah yasa muji alkhairi ya taimaki dakarun mu yasa ayi nasarar sheƙe duk wani ɗan t*adda dake cikin dajin amen

04/09/2026

ALHAMDULILLAH!!
jama'a akwai labari tafe an saki boma bomai anyi masu ruwan wvta ta sama da kasa a safiyar yau jumma'a !
💥💪

03/09/2026

Ku saka garin FUNTUA a addu'a, yanzu haka ƴan ta'addā suna cikin garin suna harbe harbe, Allah yayi musu mafita 😭

26/07/2026

ALLAH YAYI MUKU MAFITA 😭😭

WANI SABON AL'AMARI YA KUNNO KAI A AREWA 😭hattara dai mutanen mu dake karkara Daga rahotan da muke samu daga maban-banta...
30/05/2026

WANI SABON AL'AMARI YA KUNNO KAI A AREWA 😭

hattara dai mutanen mu dake karkara
Daga rahotan da muke samu daga maban-banta gurare , musamman arewa maso gabas
bakin mutane na shigowa da kudi masu yawa , suna bin kauye suna siyan bishiyar kuka , babu abinda zasuyi da ita , suna kashe tane ta mutu har jijiyar ta

HIKIMAR YIN HAKA -
Zargi ya nuna cewa akwai shiryayen wani lamari da yãhūdawa ke shirin yi , domin sunce babu kalar mak!rcinda basu ƙullawa mutanen arewa amma abin yana rushewa ,cewa ita kukar tana da mahimmanci a jikin dan Adam , akwai sunadaran dake kare Garkuwa jiki da kaucewa duk wata guba da akaci ko akasha
Don haka muna sanar da mutane mu na kauye su kula
Talauci kada yasa ka kassara albarka da Allah ya ajiye
Wanda baka shuka ba kaima haka ka ganta a gonar ka

22/03/2026

Iran Ta Yaudari Duniya

Akwai wani mataki da yaƙi yake kaiwa ta yadda harsashi zai zama ba shi ne babban makami ba. Rudarwa (Deception) ita ce zata zama takobi, ruda tunanin makiyi.

Har yanzu kana kallon labarai Amma idan kana gaskata duk abin da ka gani, to lallai baka fara nazarin yadda duniyar 2026 take juya tunani ba.

Maganar mutuwar Ayatollah da sauran shugabannin Iran ba batu ne na inason nasan asalin gaskiyar ba ne; magana ce ta zamba da dabarar yaƙin da aka shirya wa tsawon shekaru 40.

Ta yaya ƙasar da take da biranen makamai a ƙarƙashin ƙasa (Underground Missile Cities), waɗanda satellite mafi ƙarfi ma ya gaza gano su, za ta kasa kare mutum ɗaya? Iran ba iya ƙasa ce kawai ba; tsari ne (System) da aka gina akan rukunai uku; Addini (Martyrdom), Sojoji (Revolutionary Guard), da kuma Ilimin Injiniyanci (Technology).

Babban abin da ya kamata ka tambayi kanka shi ne: Me ya sa har yanzu ba a binne Ayatollah ba? A al’adar Musulunci, mutum baya wuce sa’o’i 24 zuwa 72 ba a binne shi ba, amma ga shi yau mun kusa kwashe wata guda ana tura ranar jana’iza. Idan har shugabannin soji irin su Ali Larijani za su iya yawo a kan t**i ranar Juma’a suna nuna wa duniya cewa ba sa tsoro, me zai hana su binne jagoransu?

A nan ne dabarar Strategic Disappearance ta shigo ciki. Ta hanyar barin duniya ta yi amanna cewa ya mutu, Iran ta cire babban Target ɗin da Isra'ila take nema. Sun ɓoye shi a cikin rami mai zurfi (Bunker) inda babu na'urar da za ta iya gano numfashinsa, don ya ci gaba da juya yaƙin cikin kwanciyar hankali yayin da maƙiyi yake murnar nasarar ƙarya.

Wani sirrin kuma yana ga yadda Iran take amfani da Martyrdom (Shahada). Kamar yadda tarihin Annabi Isa (A.S) ya nuna, jinin jagora baya zama asara; yana zama makamashi ne da yake ninka ƙarfin mabiya.

Amma lissafin ya ruguje a nan. Idan har Ayatollah ya zaɓi ya mutu a ofishinsa kamar yadda ake faɗa, me ya sa zai tafi da jikoki da matasa? A ilimin yaƙin kwakwalwa, ba a kashe matasa don Symbolism; A cikin tafiyar da ta ginu akan akida, babban burin tsoho (jagora) shi ne ya tabbatar da cewa ya gina matasa waɗanda za su ci gaba da jan ragamar tafiyar. Yin shahada ko mutuwa ga tsoho ba rashi ba ne; hanya ce ta ba wa matasa dama su fito fili su nuna ƙwazonsu, yayin da suke amfani da hasken (ilimi da akida) da tsohon ya bari.

Wannan yana nuna cewa dukkan labarin an tsara shi ne don a yaudari na'urorin leƙen asiri na Yamma. Kalli abin da ya faru da Ahmadinejad da janar-janar ɗin da aka ce an kashe a yaƙin kwanaki 12; kashi 75% na waɗanda aka ce sun mutu sun dawo a raye suna dariya. Wannan ba yaƙin makami ba ne; yaƙi ne na Ghosting, zama fatalwa a idon maƙiyi.

Iran ta nuna cewa ta fi son ta bugi tattalin arziƙin Amurka da kawayenta (Financial Leverage) maimakon nutsar da jiragen ruwansu, don gudun kada talakawan Amurka su fusata su shigo yaƙin. Wannan hikima ce ta Asymmetric Warfare (wato Yaƙi ne na rashin daidaiton ƙarfi).

Sun san cewa idan s**a nutsar da jirgin Abraham Lincoln, za su janyo wa kansu harin nukiliya. Don haka s**a zaɓi su bugi aljihun duniya (Oil refineries & Hormuz Strait). Suna da makaman da za su iya harba wa tsawon watanni shida ba kakkautawa, kuma suna jiran maƙiyi ya shigo gidansu ne don su nuna masa asalin Hypersonic Trap.

Idan baka zama babban mai nazari (Analyst) ba, to za ka zama abincin farfaganda. Kada ka nemi Victory a cikin labaran TV; nemi gaskiya a cikin abubuwan da ba a cika faɗa ba. Gaskiya tana ɓoye a cikin wannan shirun, kuma Iran ta gwanance wajen tayi wannan shiru mai sautin ruguji.

Bayan wannan hawan jinin ya lafa, duniya za ta ga Rayayyun Matattu waɗanda aka ce sun mutu sun fito daga ƙarƙashin ƙasa suna mulkar sabuwar duniya. Domin a yaƙi, wani lokacin mutuwa ita ce hanya ɗaya tilo ta ci gaba da rayuwa.

Shin kana ganin lallai Iran tana da ikon yaudarar duniya na tsawon wannan lokacin, ko kuwa dai muna witnessing ɗin ƙarshen wani zamani ne?

22/03/2026

MUN RANTSE DA GIRMAN ALLAH....

Hedikwatar sojojin Iran sunyi rantsuwa tare da gargadi mai karfi, idan aka kai hari akan kayayyakin makamashinta, zata mayar da martani ta hanyar kai hari kan dukkan kayayyakin makamashi, fasahar bayanai (IT), da cibiyoyin tace ruwan teku (desalination) na Amurka da kawayenta dake yankin gabas ta tsakiya...

Desalination (tace ruwan teku zuwa ruwan sha).

Kasashen yankin Tekun Fasha (Gulf) suna samun mafi yawan ruwan shansu ne daga cibiyoyin tace ruwan teku Desalination Centres..

Wani rahoto ya kiyasta idan da cibiyar Jubail ta Saudiyya zata tsaya aiki na sati daya kacal, hakan zai tilasta wa mazauna birnin Riyadh miliyan 8.5 yin ƙaura cikin gaggawa domin kaso 90 na ruwan da ake amfani dashi a birnin ana samunsa ne daga Desalination...

Haka nan shima Birnin Dubai duk ruwan da ake amfani dashi yana zuwa ne daga irin waɗannan cibiyoyin da suke aikin tace ruwan teku zuwa ruwan sha, tsayawar aikinsu na nufin ya zama dole ayi kaura da birnin Dubai saboda matsalar ruwan sha da zaa fuskanta...

Donald Trump ya ba Iran wa’adin awa 48 ta bude mashigar Hormuz, in ba haka ba zai fara lalata cibiyoyin samar da wutar lantarki.

Iran ta mayar da martani da sanya alama kan abu guda da kasashen Gulf ba za su iya rayuwa ba tare da shi ba: ruwan sha mai tsafta.

Idan har kuka bari Amurka tayi amfani da kasashen ku wajen kai harin da zai lalata cibiyoyin samar da lantarki da kadarorin Iran na Gas hakan na nufin kuma zaku fuskanci matsala sama da wacce Iran zata fuskanta....

Kuna da kyakkyawar alaka da Trump ku hanashi kai mana hari idan kuna son cibiyoyin Desalination dinku su zauna lafiya...

SASSAKEN KUKA DA MADARA Asamo sassaken kuka a tafasa shi kamar shayi asaka madara ake sha yana da amfani a jikin mata ha...
22/03/2026

SASSAKEN KUKA DA MADARA
Asamo sassaken kuka a tafasa shi kamar shayi asaka madara ake sha yana da amfani a jikin mata harma da maza.
Yana ciko da gaban yaya mata.
Yana kara kwayoyin halitta na maza da maza
Yana maganin amosanin mara.
Yana maganin warin gaba.

Ayi shearing group biyar.

AREWAWA MASU ABIN MAMAKIAkwai damuwa mai sosa zuciya ganin yadda al’ummar Arewa suke rayuwa, rayuwar yan Arewa cike take...
27/02/2026

AREWAWA MASU ABIN MAMAKI

Akwai damuwa mai sosa zuciya ganin yadda al’ummar Arewa suke rayuwa, rayuwar yan Arewa cike take da son rai da kuma makauniyar soyayya ta wasu mutane wadanda kullum suke amfani da jahilcin da ya dabaibaye Arewa domin amfanar da siyasar su.

Acikin mutanen duniya irin su Barr. AUDU BULAMA BUKARTI basu da yawa, Bulama mutum ne da yake fadar ra’ayin sa na gaskiya baya damuwa ya fadi abinda mutane suke so suji, ko kuma yabi ra’ayoyi mafi rinjaye (majority) domin jama’a su yaba masa saboda yana tsoro kar a zage sa. Ba ruwan sa, ko ka zage sa ko ka yabe sa, shi dai zai fadi abinda ya gamsu na gaskiya ne.

A wata daya da ya gabata, kowa yaga yadda aka kulla makirci a duniya akan Arewa da Musulmai, aka rubutawa Amurka korafi cewa Musulmai nayiwa Kiristoci kisan kare dangi acikin Najeriya, mutumin da yafi kowa jajircewa akan yakar wannan makircin shine AUDU BULAMA BUKARTI, ya shiga cikin manyan jaridu na duniya irin su ALJAZEERA ya karyata wannan labarin na kashe kiristoci a Najeriya, ya kare Arewa da Musulunci, yafito ya fadawa duniya asalin halin kunci da yan ta’addan s**a jefa musulmai aciki a yankunan Arewa.

Kowa yaga irin gudunmawar da Barr Bulama Bukarti ya bayar, an jinjina masa, an yaba masa bisa irin wannan namijin kokarin, babu wanda ya biya shi, babu wanda ya taimaka masa, amma kullum burin sa yaga ankawo karshen zaluncin da akeyiwa yan Arewa, ya sadaukar da rayuwar sa wajan fadin gaskiya da yakin yan ta’adda.

A wannan sati Barr Bulama Bukarti yayi cikakken bayani akan Mallam Nasiru Elrufai, yadda Elrufai ke yada karya da propaganda akan abokan hamayyar sa na siyasa, da kuma irin yadda yayi bayani a babban gidan talabijin na kasa Arise cewa sunyi kutse cikin wayar mai bawa shugaban kasa shawara akan sha’anin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu kuma suna sauraron duk wasu bayanai da yake fada, Barr Bulama Bukarti ya nuna yadda Nasiru Elrufai ya daure kan sa da yayi wannan jawabi, domin wannan kadai ya isa yaja a daure sa abisa dokar PRIVACY ta Najeriya.

Akwai takaici da damuwa yadda wasu ke ainata ko zagin Barr Bulama Bukarti domin su kare Nasiru Elrufai, wallahi kaf yan siyasar Arewa a yanzu babu wanda yake bayar da gudunmawar da Barr Bulama Bukarti yake bayarwa domin Arewa, yadda Bulama ya sadaukar da rayuwar sa domin nemawa Arewawa yanci da wayar musu da kai akan irin mulkin zaluncin da akeyi a yankunan mu. Allah yakara maka jagora. Mungode Barr Bulama Bukarti.

~ Allah yasa mu gane masu sonmu na Gaskiya ya bamu ikon ganewa.!!!!

Me ake kullawa Nigeria; Dan Majalisar Amurka Ya Miƙa Rahoto Mai Zafi ga Fadar White House dake nuna Lokaci Ya Yi da Za a...
24/02/2026

Me ake kullawa Nigeria; Dan Majalisar Amurka Ya Miƙa Rahoto Mai Zafi ga Fadar White House dake nuna Lokaci Ya Yi da Za a Dakatar da Tsananta wa Kiristoci a Najeriya

A wani mataki mai ƙarfi da ya jawo hankula a Yammacin Afirka da ma duniya baki ɗaya, ɗan Majalisar Wakilan Amurka, Riley Moore, ya bayyana a gaban White House a ranar 23 ga Fabrairu 2026, yana riƙe da cikakken rahoton majalisa da aka tsara domin dakile ci gaba da tashin hankalin da ake zargin ana yi wa Kiristoci a Najeriya.

Rahoton ya biyo bayan bincike na ɓangarorin siyasa biyu (bipartisan), ciki har da wata ziyara ta gano gaskiya da Moore ya kai zuwa yankin Middle Belt na Najeriya, inda aka ce rikice-rikice sun daɗe suna addabar al’umma. Daga bisani, Moore ya miƙa rahoton ga gwamnatin Donald Trump. Wannan na zuwa ne watanni bayan da Shugaban Ƙasar ya sake ayyana Najeriya a matsayin Country of Particular Concern (CPC) a ranar 31 ga Oktoba 2025, bisa zargin take ‘yancin addini — matakin da ya soke cire sunan da aka yi a baya.

Moore, mabiya ɗariƙar Roman Catholic mai wakiltar West Virginia, ya yi magana kai tsaye ba tare da ɓoye ra’ayi ba. Ya ce, “’Yan’uwanmu Kiristoci sun daɗe suna shan wahala cikin shiru. Yanzu duniya na kallo.”

Binciken ya tattaro bayanai masu tayar da hankali, inda aka ce ‘yan bindiga da ake dangantawa da Fulani da wasu ƙungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi sun aikata kisan gilla, ƙona ƙauyuka, da tilasta wa jama’a barin muhallansu, musamman a kan al’ummomin manoma Kiristoci. Wasu da s**a tsira sun ba da labaran asarar rayuka da dukiya, da kuma mawuyacin halin da suke ciki a sansanonin ‘yan gudun hijira na cikin gida (IDP), waɗanda a wasu lokuta ake kai wa hare-hare.

Rahoton ya ƙunshi shawarwari masu tsauri da s**a haɗa da:

• Ƙulla sabuwar yarjejeniyar tsaro tsakanin Amurka da Najeriya domin kare al’umma masu rauni da rusa hanyoyin ‘yan ta’adda

• Dakatar da wasu tallafin Amurka muddin gwamnatin Najeriya ba ta nuna ƙwazo a kare Kiristoci ba

• Ɗora takunkumi da hana biza ga waɗanda ake zargi da hannu a rikice-rikicen, ciki har da jami’an da aka ce sun yi sakaci

• Ba da tallafin fasaha domin rage barazanar ƙungiyoyin ‘yan bindiga

• Kira da a sake duba dokokin Shari’a da na batanci da ake zargin suna haifar da wariya

• Haɗa kai da ƙasashe abokan hulɗa kamar France, Hungary, da United Kingdom

Moore ya jaddada muhimmancin haɗin kai maimakon gaba, yana mai kira ga gwamnatin Najeriya da ta yi amfani da wannan dama wajen ƙarfafa dangantaka da Amurka tare da tabbatar da tsaron dukkan ‘yan ƙasa.

Saƙon ya haifar da muhawara mai zafi a kafafen sada zumunta. Wasu Kiristoci ‘yan Najeriya da ‘yan diaspora sun nuna godiya kan yadda aka jawo hankalin duniya, yayin da wasu kuma s**a nemi a ɗauki matakai masu ƙarfi. A gefe guda, masu s**ar rahoton sun yi zargin cewa mayar da hankali kan bangare guda na iya yin watsi da faɗaɗɗen matsalar tsaro da ke shafar kowa.

Sai dai babban saƙon rahoton ya fito fili: bayan shekaru na tashin hankali da asarar dubban rayuka, ana neman a ɗauki matakan da za su tabbatar da adalci da sauyi.

Rahoton ya isa White House. Tambayar yanzu ita ce: shin za a ga mataki mai ma’ana? Kuma yaushe ne waɗanda s**a daɗe suna jira za su samu sauƙi?

Address

Sokoto
Rabah

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa A Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share