29/05/2025
Tabbas mu Ƴan Rano ne kuma muna alfahari da kasancewar mu Ƴan Rano,
Ɗaya daga cikin Hausa Bakwai a tarihin Hausa da Hausawa, Babbar daular Hausa gidan Autan Bawon Sarakunan Hausa.
Ta tabbata Rano tayi suna wajen zaman lafiya, kwanciyar hankali da yalwar arziƙi,
Kasancewar Rano mahaifar manyan Attajirai irin su Alhaji Dr. Auwalu Abdullahi Rano da Alhaji Saleh Baba wanda aka fi sani da SALBAS, da Alhaji Ɗanlami Ahmed Rano da sauran su.
A ɓangaren ilmi muna da manyan farfesoshi da manyan Ƙwararrun likitoci Injiniyoyi da Manyan Jami'an tsaro daga kowanne fanni.
Lallai samarin mu masu neman na kansu ne domin a duk faɗin Najeriya inda duk kaga gidajen man A A RANO, SALBAS Oil and Gas, Evergreen Oil, Rano Oil, Lausu Oil and Gas, Danlami Petroleum, Lifur Oil and Gas, Autan Bawo Oil and Gas da sauran su sai ka samu samarin mu na riƙe da madafun iko a wuraren.
Idan ka koma ɓangaren Sufuri jiragen sama Rano Air na nan, a ɓangaren samarwa da ƙasa abinci Rano Rice na nan, gami da kamfanin kayan aikin gona na Ranfield.
Muna sane da irin tausayawa da jajantawa da al'ummar Najeriya s**a yi mana a lokutan mabanbanta na rashin ɗan mu wanda shima babban jami'in Ƴan sanda ne wato DPO a jihar Katsina Marigayi Abdulkadir Abubakar Rano wanda Ƴan ta'adda s**a hallaka a shekarun baya. Sai kuma mafarauta ƴan asalin Masarautar Rano wanda mutanen Uromi ta jihar Edo s**a yiwa kisan gilla a cikin watan azumin da ya gabata a kan hanyar su ta dawowa gida domin yin shagulgulan Sallah cikin iyalai da ƴan'uwa.
Sai kuma gashi yau mun tsinci kanmu a wani yanayi maras daɗi inda wasu tsirarun yara baragurbi sun ɗauki doka a hannun su wajen yiwa CSP Muhammad Baba Ali kisan gilla bayan shafe shekaru da yayi na tabbatar da kariyar rayuka da dukiyoyin al'ummar Rano.
Lallai wannan abin Allah wadai ne, kuma a yayin da muke miƙa ta'aziyyar mu ga iyalai da abokan sa da kuma hukumar Ƴan sanda da sauran duk wanda wannan aikin ta'adanci ya shafa, muna roƙon Allah Ya jiƙansa da Rahma Yasa Aljanna ce makomarsa, Allah Ya dawo mana da zaman lafiya a wannan gari namu mai ɗimbin albarka, Allah Ya shiryi waɗannan yara Ya dawo mana da hankalin su, Allah Ya ƙarawa rayuwar mu albarka baki ɗaya.