Muryar Rano

Muryar Rano Muryar Rano shafi ne da zai dinga kawo abubuwa da su ka shafi ƙaramar hukumar Rano, musamman matasa

03/07/2025

Babban Asibitin Rano: A Ina Matsalar Ta Ke?

Da farko dai ban so na ce komai ba, amma wannan saƙo ya ƙara min ƙwarin gwiwa na cewa wani abu a kan matsalolin babban asibitinmu na Rano.

Na samu Rahotanni kan yadda marasa kishi suke illata mana wannan asibiti ta hanyar sace kayayyakin aiki na miliyoyin nairori da gwamnatin Ganduje ta saka a bangarori dabam-dabam na asibiti tun bayan ɗaga likkafarsa zuwa babban mataki.

Kusan dukkanin kayan aikin da aka zuba a wannan asibiti na zamani a kan idona aka saka su, wasu kuma daga baya na kan kai ziyara domin gani da ido. Na san cewa an kashe maƙudan kuɗaɗe millions of naira wajen inganta mana wannan asibiti da waɗannan kayayyakin aiki, wadda ko Asibitin Murtala ma ba shi da irin wasu kayayyakin da aka zuba mana.

Amma fa a yanzu an mayar da mu baya, bayan-baya ma, domin an sace da yawa daga cikin waɗannan kayayyaki, kai hatta batiran Solar na samu rahoton cewa ana zuwa ana sace su ɗaya bayan ɗaya. Saboda rashin sanin kai sakacin namu ya kai hatta karafunan windows ɓallesu ake yi ta ƙarfin tsiya ana sacewa. Haba jama'a? Kuma a haka sunan muna da shugabanni kenan? Sunan muna da Dattijan yanki da a baya s**a dage cewa sai Jami'an lafiyarmu sun sadaukar da kai domin bawa yankin gudunmawa?

Ina shugaban ƙaramar hukuma, ina ɗan majalisar Jiha, ina ɗan majalisar tarayya? Ina Sanatan yankinmu? Ina girma da tasirin masarautarmu? Duk kishin yankin namu a baki yake kenan?

Shin girman wannan matsala bata kai a ce zuwa yanzu dukka masu faɗa a ji sun zo sun haɗa kai domin ɗaukar matakin gyara ba?

Ina zargin dole da ɗan gari a kan ci gari, domin ƙwarya-ƙwaryan bincike da na fara yi, ya tabbatar min da cewa wannan mummunar sata da ɓarna ta kayayyakin asibitinmu, da ma sakaci wajen gudanar da wasu ayyukan, akwai sa hannun wasu manyan asibitin da ba kishin yankin ne a gabansu ba. Muna roƙon kwamitin dattijai da cigaban yankinmu su gaggauta bincika lamarin nan tare da ɗaukar mataki domin hukunta duk waɗanda suke da hannu a cikin wannan lamari komai girmansu, kuma a ɗauki matakin kiyaye afkuwar hakan a gaba.

Wannan kira, matakin farko ne na ɗaga muryarmu game da wannan mummunan al'amari da ya shafi al'ummarmu. Allah Ya sa ya zama silar samun gyara.

Fatan Alheri ga kowa🙏🏼

©️ Ibrahim Ɗan'uwa Rano

30/05/2025

Mu yiwa juna adalci

Da farko ina jajantawa iyalan wadanda wannan iftila'i na rikin Rano ya rutsa da su. Ina taya shugabanni da mutanen Karamar Hukumar Rano dama Jihar Kano jaje. Ina kuma addu'a Allah ya jikan wadanda s**a rasa rayukan su a wannan rikici. Mu mutanen Rano mun cikin bakin ciki sosai game da wannan abu domin ba'a cika samun mu a sabgogi na rashin da'a ba. Da yawan mu mun kasa magana ne saboda jikin babu karfi sak**akon girgiza da kaduwa da muka yi.

Amma na lura wasu mutane marasa fahimta sun samu ga6a ta zagi da cin mutunci da tsangwamar mutanen Rano; kai kace wadancan yara sun yi wannan barna ne bisa umarnin mutanen gari. Jahilci yasa mutane na sakar baki suyi ta surutu marasa kan gado.

Akwai wani ma da na karanta sakon sa yana cewa da ace shine Kwamishina da sai ya sanya mutanen Rano duka sun yi gudun hijira. Irin wadannan marasa hankali basu da bambanci da wadancan tantiran yara da jahilci da rashin tarbiyya ya sanya s**a aikata wannan ta'adddancin. Kuma suma suna bayyanar da rashin tarbiyya su ne a fili wajen burin muzgunawa bayin Allah da basu ji ba basu gani ba.

Irin wadancan mutane marasa da'a sun jahilci rayuwa. Yak**ata su sani uwar data haifi Abubakar Shekau ma tana nan a raye babu wanda ya tsangwame ta domin bada yawun ta danta yayi abin da yayi ba. Kuma ko a dokar kasa babu yadda za'a yi a hukunta wani da laifin wani. Kenan sai muce 'yan daba dake kashe mutane kusan kullum a Kano da yawun mutanen gari suke wannan ta'adddanci.

Ku sani mu mutanen Rano mun fi kowa bakin cikin faruwar wannan lamari kuma muna Allah wadai da wadannan matasa tare da kira akan lallai ayi bincike na gaskiya a kuma tabbata an hukunta duk wanda aka samu da laifi daidai da abinda ya aikata. Bama ganin laifin masu yin Allah wadai da wannan dabi'a da yaran nan s**a nuna ta rashin imani, amma duk wanda ya zagi mutanen Rano saboda abinda wawayen cikin mu s**a aikata to shima wawan cikin mu ne.

Wannan muna kallon sa a matsayin jarrabawa kuma tuni mun fara daukar matakan ganin irin wannan abin bakin ciki bai sake faruwa damu ba. Da cewa irin kokarin da manyan Rano keyi wajen shiga rayuwar matasa bana jin ana samun haka a sauran garuruwa.

A Rano da kuke aibatawa akwai daidaikun mutane dake daukar nauyin karatun dubunnan matasa, ciki harda marayu masu yawan gaske, wadda yake da wahala ka samu irin haka a sauran gurare. Na san mutum daya dan wannan gari na Rano da a makaranta daya ma ya dauki nauyin karatun yara dubu.

Saboda haka jahilai kadai zasu kalli wannan ta'adddancin a matsayin aikin mutanen Rano duka. Akwai bayin Allah da yawa da s**a yi kokari wajen hana yaran nan amma ba suyi nasara ba saboda yawan su. Sai dai ina tsammanin masu yiwa mutanen Rano kudin goro zasu fahimci abinda nake fada ne kawai ranar da s**a ci karo da tasu jarrabawar.

Ina kira ga iyaye da su kara sanya idanu akan tarbiyyar 'ya'yan su. Kuma dole ne mutane a mataki na unguwa dama gari su hada kai wajen ganin an dora yara akan tarbiyya tare da yakar rashin da'a a tsakanin matasa. Dole ne mu hada kai da jami'an tsaro mu zakulo mutanen dake safara da cinikayyar kayan maye don ganin mun dakile matsalar shaye-shaye. Aiki ne mai wahala amma dole mune zamu yi ba wani ne zai zo daga wata duniya ya mana ba.

Ina yabawa hukumar 'yan-sanda kan yadda take gudanar da aikin zakulo wadannan masu laifi cikin kwarewa tare da fatan zata yi adalci wajen ganin ba'a cutar da wadanda basu da hannu cikin wannan lamari ba.

Dr. Kawu Sule Rano
30052025

Tabbas mu Ƴan Rano ne kuma muna alfahari da kasancewar mu Ƴan Rano,Ɗaya daga cikin Hausa Bakwai a tarihin Hausa da Hausa...
29/05/2025

Tabbas mu Ƴan Rano ne kuma muna alfahari da kasancewar mu Ƴan Rano,
Ɗaya daga cikin Hausa Bakwai a tarihin Hausa da Hausawa, Babbar daular Hausa gidan Autan Bawon Sarakunan Hausa.
Ta tabbata Rano tayi suna wajen zaman lafiya, kwanciyar hankali da yalwar arziƙi,
Kasancewar Rano mahaifar manyan Attajirai irin su Alhaji Dr. Auwalu Abdullahi Rano da Alhaji Saleh Baba wanda aka fi sani da SALBAS, da Alhaji Ɗanlami Ahmed Rano da sauran su.
A ɓangaren ilmi muna da manyan farfesoshi da manyan Ƙwararrun likitoci Injiniyoyi da Manyan Jami'an tsaro daga kowanne fanni.
Lallai samarin mu masu neman na kansu ne domin a duk faɗin Najeriya inda duk kaga gidajen man A A RANO, SALBAS Oil and Gas, Evergreen Oil, Rano Oil, Lausu Oil and Gas, Danlami Petroleum, Lifur Oil and Gas, Autan Bawo Oil and Gas da sauran su sai ka samu samarin mu na riƙe da madafun iko a wuraren.
Idan ka koma ɓangaren Sufuri jiragen sama Rano Air na nan, a ɓangaren samarwa da ƙasa abinci Rano Rice na nan, gami da kamfanin kayan aikin gona na Ranfield.
Muna sane da irin tausayawa da jajantawa da al'ummar Najeriya s**a yi mana a lokutan mabanbanta na rashin ɗan mu wanda shima babban jami'in Ƴan sanda ne wato DPO a jihar Katsina Marigayi Abdulkadir Abubakar Rano wanda Ƴan ta'adda s**a hallaka a shekarun baya. Sai kuma mafarauta ƴan asalin Masarautar Rano wanda mutanen Uromi ta jihar Edo s**a yiwa kisan gilla a cikin watan azumin da ya gabata a kan hanyar su ta dawowa gida domin yin shagulgulan Sallah cikin iyalai da ƴan'uwa.
Sai kuma gashi yau mun tsinci kanmu a wani yanayi maras daɗi inda wasu tsirarun yara baragurbi sun ɗauki doka a hannun su wajen yiwa CSP Muhammad Baba Ali kisan gilla bayan shafe shekaru da yayi na tabbatar da kariyar rayuka da dukiyoyin al'ummar Rano.
Lallai wannan abin Allah wadai ne, kuma a yayin da muke miƙa ta'aziyyar mu ga iyalai da abokan sa da kuma hukumar Ƴan sanda da sauran duk wanda wannan aikin ta'adanci ya shafa, muna roƙon Allah Ya jiƙansa da Rahma Yasa Aljanna ce makomarsa, Allah Ya dawo mana da zaman lafiya a wannan gari namu mai ɗimbin albarka, Allah Ya shiryi waɗannan yara Ya dawo mana da hankalin su, Allah Ya ƙarawa rayuwar mu albarka baki ɗaya.

Jami'ar Al-Istiqama da ke ƙaramar hukumar Sumaila a jihar Kano ta karrama ɗaya daga cikin ɗaliban Rano da su ka kammala ...
29/04/2025

Jami'ar Al-Istiqama da ke ƙaramar hukumar Sumaila a jihar Kano ta karrama ɗaya daga cikin ɗaliban Rano da su ka kammala karatu a jami'ar wato Muhammad Lawal Rano da lambar yabo ta ɗalibi mafi hazaƙa a sashen koyar da tattalin arziki da sana'o'in dogaro da kai wato Department of Economics (Entrepreneurship).

Muna taya shi murna.

Dear MTN Nigeria  ,We express deep dissatisfaction with the ongoing call and internet connectivity issues in Rano Local ...
04/04/2025

Dear MTN Nigeria ,

We express deep dissatisfaction with the ongoing call and internet connectivity issues in Rano Local Government Area, Kano State. Despite the area being a significant business hub with a large population, we have faced persistent difficulties in making calls and accessing the internet for over a month. This has significantly impacted both personal and professional activities.

It is unacceptable that such a large community continues to experience poor service, and we urge MTN Customer Services to address this issue promptly to restore reliable communication services.

MTN Nigeria: Shafin Hausa

06/03/2025

Saurari Cikakken Sharhi Tare Da Bayani Kan Batun Daular Usmaniyya

15/02/2025
07/08/2024

An ƙara Naira Dubu Ashirin (₦20,000) Akan Kowanne Buhun Fulawa Guda. A baya ana sayar da shi ₦63,500 amma yanzu ya koma ₦82,000.

Kamar yadda Rahma TV su ka rawaito

07/08/2024

Dole sai mun sa azzaluman ƴan kasuwa a addu'oinmu na musamman. Wallahi a halin da muke ciki sun fi kowa gana mana azaba fiye da shugabanni. Matsiyata kawai masu talaucin zuci. Allah ya mana maganinsu. Ya karya jarinsu. Ya ɗebe musu albarkar kasuwancin da su ke yi, ameen.

Da izinin Allah hakan zai tabbata. Zamu samu ci gaba.Za a samar da guraben aiki ga matasan mu.Zamu samu manyan ayyuka.
10/07/2024

Da izinin Allah hakan zai tabbata.

Zamu samu ci gaba.

Za a samar da guraben aiki ga matasan mu.

Zamu samu manyan ayyuka.

Ƙaramar hukumar Rano ta karɓi Naira miliyan 45 daga mai girma gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf domin gyaran ma...
26/06/2024

Ƙaramar hukumar Rano ta karɓi Naira miliyan 45 daga mai girma gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf domin gyaran makarantu a fadin karamar hukumar.

Waɗanne makarantu ne su ka fi buƙatar gyara? Ku ajiye mana sunayen makarantun a comment section

Ibrahim Ishaq Danuwa Rano: Jan Gwarzo Abin MisaliTabbas Fitaccen Dan jaridar nan wato Ibrahim Ishaq Danuwa Rano ya zama ...
12/06/2024

Ibrahim Ishaq Danuwa Rano: Jan Gwarzo Abin Misali

Tabbas Fitaccen Dan jaridar nan wato Ibrahim Ishaq Danuwa Rano ya zama Jan Gwarzo kuma abin misali a cikin dukkanin al'ummar da ilimi da kuma hankali ya zame mata tafarki.

A lokacin da Ibrahim Danuwa ya ke aiki da gidan rediyon Freedom ya kasance Dan Jarida fitacce wanda ya shahara a fagen aikin jarida musamman Rediyo, kuma ya kasance marar kwaɗayi wanda ba shi da tsoron faɗar gaskiya komai ɗacinta a lokacin da ya k**ata a faɗeta.

Ga duk mai bibiyar abubuwan da su ke faruwa ya san Ƴanci ne ya sanya Danuwa ya ajiye aiki da Freedom Radio bisa Raɗin Kan sa. Kuma ga duk wanda ya san tarihin abin da ake nufi da ƊAUKAKA ko SHAHARA to tabbas Ɗanuwa Rano ya k**a hanyar samun GAGARUMAR ƊAUKAKA A DUNIYA!

Tabbas Al’ummar Rano muna alfahari da kai tare yi maka fatan alkhairi a duk inda ka saka ƙafarka.

Address

Rano
710101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Rano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category