Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia Ayzan Multimedia – Bringing news, Islamic education, and history. Under Ayzan Group, connected with مجالس النوابغ لتكوين العلماء & Tamkeen Qur'anic Channel.

17/11/2025
Cikin wata sanarwa da jam'iyyar ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce ta ɗauki matakin ne domin kawo haɗin kai da lad...
15/11/2025

Cikin wata sanarwa da jam'iyyar ta wallafa a shafinta na Facebook, ta ce ta ɗauki matakin ne domin kawo haɗin kai da ladabtarwa a jam'iyyar da kuma mayar da hankali ga zaɓukan 2027 masu zuwa.

Kotun Turkiyya ta bada belin mutumin da ya wallafa hotunan barkwanci ta hanyar batanci ga Annabi Muhammad (SAW) a jarida...
15/11/2025

Kotun Turkiyya ta bada belin mutumin da ya wallafa hotunan barkwanci ta hanyar batanci ga Annabi Muhammad (SAW) a jaridar LeMan, sai dai kotun ta bada umarnin a ci gaba da tsare shi a gidan yari sakamakon zagin Shugaba Recep Tayyip Erdogan.

12/11/2025

مجالس النوابغ لتكوين العلماء

Barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin Kano, ya yi awon gaba da daya daga cikin ayarin motocin mataimakin gwamnaWan...
12/11/2025

Barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin Kano, ya yi awon gaba da daya daga cikin ayarin motocin mataimakin gwamna

Wani barawon mota ya shiga cikin Gidan Gwamnatin Kano da safiyar Litinin, ya yi awon gaba da wata motar Toyota kirar Hilux wacce ta ke daya daga cikin ayarin motocin mataimakin gwamnan jihar.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito barawon ya arce da motar ne da misalin ƙarfe 5 na asuba. Bidiyoyin CCTV da aka duba sun tabbatar da lamarin.

Har ya zuwa yanzundai jami’an tsaro na bincike kan lamarin domin kamo mai laifin.

10/11/2025

"Tare da Dr. Nura Abdullahi — Maganganu masu ma’ana waɗanda ke tunasar da mu cewa ilimi ba wai karatu ba ne kawai, aiki da shi shine ainihin fahimta.”

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya dawo Abuja bayan jagorantar tawagar Najeriya zuwa taron sauyin yana...
09/11/2025

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya dawo Abuja bayan jagorantar tawagar Najeriya zuwa taron sauyin yanayi na duniya, COP30, da aka gudanar a ƙasar Brazil.

Faransa ta umarci dukkan ‘yan ƙasarta da ke zaune a ƙasar Mali da su bar ƙasar cikin gaggawa sakamakon tsanantar hare-ha...
08/11/2025

Faransa ta umarci dukkan ‘yan ƙasarta da ke zaune a ƙasar Mali da su bar ƙasar cikin gaggawa sakamakon tsanantar hare-haren 'yan ta'adda

Barazanar Trump ga Nijeriya: Ya kamata Amurka ta san cewa akwai doka a duniya - Russia Gwamnatin Russia ta yi kira ga sh...
08/11/2025

Barazanar Trump ga Nijeriya: Ya kamata Amurka ta san cewa akwai doka a duniya - Russia

Gwamnatin Russia ta yi kira ga shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump da ya san da cewa akwai dokoki a duniya kuma ko wacce ƙasa tana da ikon cin gashin kan ta.

Ta kuma bayyana cewa ta na lura da irin rahotannin da ke cewa Amurka na iya ɗaukar matakin soja a Najeriya, bayan kalaman tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump, da ya ce zai iya tura dakarun Amurka domin “kare Kiristoci” a kasar.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha, Maria Zakharova, ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a Moscow ranar Juma’a, inda ta jaddada cewa Rasha na kira ga Amurka da sauran ɓangarorin da abin ya shafa su bi ƙa’idojin dokokin ƙasa da ƙasa.

Zakharova ta ce, “Muna bibiyar wannan batu sosai, kuma muna kira da a yi taka-tsantsan tare da mutunta ikon mallakar ƙasa.”

Kalaman nata sun biyo bayan jawabin Trump a ranar 1 ga Nuwamba, inda ya ce ya umarci Ma’aikatar Tsaron Amurka (Pentagon) da ta tsara shirin yiwuwar kai farmaki a Najeriya.

Duk da cewa babu wata sanarwa ta hukuma daga Washington kan lamarin, furucin Trump ya haifar da martani daga ƙasashen waje, ciki har da Moscow, wadda ta yi gargadin cewa duk wani mataki ya zama bisa tsarin doka da girmama ‘yancin kowace ƙasa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ayzan Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share