Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ayzan Multimedia, Broadcasting & media production company, Kano.

AYZAN MULTIMEDIA
Gidan jarida ne na zamani da ke kawo Labaran Duniya, Iliman-Tarwa, Ni Shadan-Tarwa, da Tarihi domin faɗakar da zukata, gyara halaye, da gina al’umma bisa gaskiya da ilimi.

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin jihar Katsina ta sayo sabbin motocin yaƙi guda 8 masu sulke, domin fatattakar ‘yan bindiga a faɗ...
24/08/2025

Da Dumi-Dumi: Gwamnatin jihar Katsina ta sayo sabbin motocin yaƙi guda 8 masu sulke, domin fatattakar ‘yan bindiga a faɗin jihar.

Wannan matakin ya biyo bayan harin da ‘yan bindiga s**a kai ana tsaka da Sallar Asuba a garin Mantau da ke ƙaramar hukumar Malumfashi a jihar ta Katsina.

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ta yi gargaɗi ga Ministan Abuja, Nyesom Wike, da wasu mambobin jam’iyyar kan yunkurin d...
23/08/2025

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ta yi gargaɗi ga Ministan Abuja, Nyesom Wike, da wasu mambobin jam’iyyar kan yunkurin da zai iya lalata babban taron jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 ga Nuwamba, 2025.

Hakan na cikin sanarwar bayan taron gwamnonin karo na bakwai da aka gudanar a Gusau, Jihar Zamfara, ranar Asabar, 23 ga Agusta, 2025.

Hotuna: Yadda Gwamnonin PDP ke gudanar da wani muhimmin taron Jam'iyyar a yau Asabar 23 ga Augustan 2025, a garin Gusau,...
23/08/2025

Hotuna: Yadda Gwamnonin PDP ke gudanar da wani muhimmin taron Jam'iyyar a yau Asabar 23 ga Augustan 2025, a garin Gusau, babban birnin jihar Zamfara, don tattauna halin da ƙasar nan ke ciki da kuma shirye-shiryen babban taron PDP mai zuwa.

Hotunan taron gwamnonin jam’iyyar PDP da ake gudanarwa a jihar Zamfara, gabanin babban taron NEC na 102 da za a gudanar ...
23/08/2025

Hotunan taron gwamnonin jam’iyyar PDP da ake gudanarwa a jihar Zamfara, gabanin babban taron NEC na 102 da za a gudanar ranar Litinin, 25 ga Agusta, 2025.

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin KajiWani matashi dan shekara 43 da ...
23/08/2025

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Wani matashi dan shekara 43 da ake zargin dan Kasar Indiya ne mai suna Sumit Sood, wanda aka k**a bisa zargin satar wasu dalibai uku na makarantar Bishop Cotton School da ke gundumar Shimla, da farko ya yi kokarin dora laifin a kan wasu ‘yan kungiyar asiri na Nijeriya, k**ar yadda jaridar PUNCH Metro ta ruwaito.

A cewar jaridar The Indian Edpress, ‘yansanda sun ce bayan sace daliban, Sood ya yi kira ta hanyar lambar waya ga iyayensu, yana mai nuna cewa “gungun ‘yan Nijeriya ne” s**a tilasta shi ya nemi kudin fansa.

An yi zargin cewa ya ba da umarnin a biya kudin fansa a cikin Bitcoin kuma ya gargadi iyayen “ka da su sanar da kowa, musamman jami’an makarantar, idan ba haka ba ‘yan kungiyar za su cutar da yaran da shi.”

Shimla Sufeto na ‘yansanda, Sanjeeb Gandhi, ya shaida wa jaridar The Indian Edpress cewa, “An yi wannan kiran ne ta manhajar TedtMe. Wanda ake zargin ya so a biya kudin fansa a Bitcoin.

“Binciken wayar salular Sood ya nuna cewa ya bincika kuma ya bincuke shafukan intanet sama da dozin uku, tashoshi na labarai na gida, da intanet BCS don duba ko labarin sacewar ya yadu.”

Gandhi ya kara da cewa lokacin da Sood ya samu labarin da misalin karfe 8 na daren ranar Asabar cewa rahotannin daliban da s**a bata sun bayyana, “ya yi shirin dauke su daga kauyensa Kokunala zuwa Chandigarh.

“Sood ya ajiye daliban a gidansa mai hawa uku da ke Kokunala saboda wurin da yake da nisa.” “Babu kowa a gidan lokacin da ya kawo su. Kafin ya aikata laifin, Sood ya sace bindigar mahaifinsa mai lasisi.”

Da yake karin haske game da motsin wanda ake zargin kafin yin garkuwa da shi, SP ya ce, “A daren da ya gabata, ya zauna a gidan kakaninsa da ke Ram Bazar na Shimla.

“Ya kauce wa CCTB ta hanyar daukar hanyar Bemloi-New Shimla kuma ya jira fiye da sa’o’i hudu a cikin motarsa, dauke da farantin karya, wanda ya ajiye kimanin mita 100 daga kofar makarantar. Har ma ya yi fitsari a cikin kwalbar a cikin motar.”

A yayin sake gina wurin da ake aikata laifukan, ‘yansanda sun ce Sood ya gano wurin da ke kusa da Dhalli inda ya rufe idanuwan dalibai uku, inda ya canza lambar motarsa, da kuma hanyoyin da ya bi ya isa gidansa na Kokunala da ke kusa da Kotkhai a ranar 9 ga watan Agusta. An shirya Sood zai gurfana a gaban kotu.

Gwamnonin na arewacin Najeriya na wannan taro a birnin Gusau na jihar Zamfara da nufin fidda matsaya kan sabon rikicin d...
23/08/2025

Gwamnonin na arewacin Najeriya na wannan taro a birnin Gusau na jihar Zamfara da nufin fidda matsaya kan sabon rikicin da ke barazana ga babban taron kwamitin zartawa na jam'iyyar adawar wanda za a gudanar a ranar Litinin mai zuwa.

Taron na kuma zuwa ne kwana guda bayan da jiga-jigan jam'iyyar na kudu s**a gana a birnin Lagos.

Gwamnatin Nijeriya na shirin ciyo bashin dala miliyan 238 daga Japan don inganta rumbun ajiyar lantarki na ƙasar
23/08/2025

Gwamnatin Nijeriya na shirin ciyo bashin dala miliyan 238 daga Japan don inganta rumbun ajiyar lantarki na ƙasar

Takardun kotu sun nuna tuhume-tuhumen da ake wa hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Rogo bisa zargin karkatar da Naira biliy...
23/08/2025

Takardun kotu sun nuna tuhume-tuhumen da ake wa hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Rogo bisa zargin karkatar da Naira biliyan 6.5

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka Masu Alaka (ICPC) tare da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Satar Dukiyar Jama’a (EFCC) sun gano Naira biliyan 6.5 da ake zargin suna da alaka da Abdullahi Ibrahim Rogo, Darakta Janar na harkokin tafiye-tafiyen gwamnan jihar Kano.

A cewar wasu takardu da jaridar DAILY NIGERIAN ta samu, hukumomin yaki da cin hanci da rashawar sun zargi hadimin na Gwamna Abba Kabir Yusuf da karkatar da kudaden jihar ta hannun wakilai.

An ruwaito cewa wannan gagarumar satar ta dukiyar al'umma ta faru tsakanin shekarar 2024 zuwa Fabrairu 2025.

Takardun sun bayyana cewa Rogo ya yi amfani da kamfanonin H&M Nigeria Limited, A.Y. Maikifi Petroleum, da Ammas Oil and Gas Limited wajen karkatar da kudi daga ofishin sa zuwa ga abokan harkallar sa.

Binciken hukumomin ya nuna cewa kudaden an biya su ne a matsayin kwangiloli na bogi da ba a taba bayarwa ko aiwatarwa ba.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta gano cewa A.Y. Maikifi Petroleum Limited da Ammas Oil and Gas Limited sun karɓi naira biliyan 1.17 daga Asusun Kason Kudaden Gwamnatin Tarayya na Jihar Kano.

“A wasu lokuta daban-daban, an sa wadannan kamfanoni biyu su sanya hannu a kan takardun izini daga tsohon Akanta Janar na Jihar Kano, Abdulsalam Abdulkadir, inda ya baiwa ma’aikatar albarkatun ruwa ta jihar izini da ta tura N539,230,000.00 da N570,000,024.50 bi da bi, zuwa asusun kamfanonin canjin kudi guda biyu, Kazo Nazo Global Resources da Namu Naku Ne, a matsayin biyan kuɗin kwangilolin bogi.

“Daga nan sai aka canja kudaden zuwa dalar Amurka sannan aka mika su a tsabar kudi ga Abdullahi Ibrahim Rogo, ta hannun Nasiru Girma [Manajan Daraktan Kazo Nazo] da wani Ghali Muhammad [abokin kasuwancin Nasiru Girma], wanda ya hada Rogo da su.”

Takardun kotu da wannan jarida ta samu sun nuna cewa Rogo da wasu da aka ambata sun amsa laifinsu ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa.

Sai dai daga baya ya canja baki, har ya shigar da kara a babbar kotun jihar Kano, reshen Bichi, domin hana a k**a shi ko a gurfanar da shi.

A cikin bayanan ƙarar da s**a shigar, duka ICPC da EFCC sun bayyana cewa akwai shaidu karara da ke nuna cewa wadanda ake zargi sun aikata satar kudade.

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin K**a Dukkan Masu Hannu a Kisan Masu Ibada a MalumfashiGwamnatin Tarayya ta bayyana cew...
22/08/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin K**a Dukkan Masu Hannu a Kisan Masu Ibada a Malumfashi

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta bi diddigin masu hannu a mummunan kisan da aka yi wa masu ibada a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina, tare da tabbatar da cewa an gurfanar da su a gaban shari’a.

A cikin wata sanarwa, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya ce wannan ta’addancin da aka aikata kan mutanen da s**a taru domin bauta wa Allah ba zai taɓa wucewa babu hukunci ba.

Ya bayyana cewa jami’an tsaro sun soma ƙoƙarin farauto waɗanda s**a aikata wannan mummunan aiki, tare da tabbatar da cewa an kamo su da hukunta su.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan waɗanda s**a rasu, al’ummar Malumfashi da gwamnatin Katsina, yana addu’ar Allah ya jikansu ya kuma ba iyalan juriyar wannan rashi.

Sanarwar ta kuma bayyana nasarorin da aka samu a yaƙin da ake yi da ta’addanci, inda kwanan nan cibiyar yaki da ta’addanci NCTC ta k**a manyan shugabannin ’yan ta’adda ciki har da Mahmud al-Nigeri, da kuma Mahmud Muhammad Usman (Abu Baraa) na ƙungiyar Ansaru.

Gwamnati ta jaddada cewa duk mai zubar da jinin al’ummabba zai sami mafaka a Najeriya ba, tare da tabbatar da cewa ƙarshen ayyukan ta’addanci a ƙasar ya kusa.

NNPC ya ce ribar sa ta ragu da kashi 79% a watan YuliKamfanin Mai na Ƙasa (NNPC) ya bayyana cewa ya samu ribar bayan har...
22/08/2025

NNPC ya ce ribar sa ta ragu da kashi 79% a watan Yuli

Kamfanin Mai na Ƙasa (NNPC) ya bayyana cewa ya samu ribar bayan haraji (PAT) na Naira biliyan 185 a watan Yuli.

A cikin sabon “Rahoton Watan Yuli 2025”, kamfanin ya ce wannan adadi ya ragu da kashi 79.56% idan aka kwatanta da Naira biliyan 905 da aka samu a watan Yuni.

NNPC ya ce raguwar ribar ta samo asali ne daga farashin kayan sayarwa da kuma gyaran harajin kuɗin shiga.

Rahoton ya ce adadin ya ƙunshi jimillar kuɗaɗen shiga na rukunin kamfanin gaba ɗaya, ciki har da ma’amalolin cikin gida.

A cewar NNPC, fitar da danyen mai da ya kai matsakaicin ganga miliyan 1.7 a kullum a watan Yuli, yayin da samar da iskar gas ya kai miliyan 7.72 a kullum.

Za a shafe kwanaki 3 ana mamakon ruwan-sama a Najeriya - NiMet Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar da y...
22/08/2025

Za a shafe kwanaki 3 ana mamakon ruwan-sama a Najeriya - NiMet

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar da yiwuwar samun ruwan sama da iska daga ranar Juma’a zuwa Lahadi a sassa daban-daban na ƙasar.

A cewar rahoton da ta fitar, jihohin Arewacin ƙasa k**ar Kano, Katsina, Sokoto, Kebbi, Zamfara, Kaduna, Jigawa, Borno, Yobe da Taraba za su fuskanci guguwar iska da ruwan sama matsakaici.

A tsakiyar ƙasa kuma, akwai yiwuwar samun ruwan sama kaɗan a Babban Birnin Tarayya, Nasarawa, Benue, Kogi, Kwara, Neja da Filato.

Haka zalika, a yankin Kudu anyi hasashen yanayi mai zafi da ruwan sama kaɗan a jihohi irin su Oyo, Osun, Ekiti, Ondo, Edo, Enugu, Imo, Abia, Anambra, Delta, Rivers, Bayelsa, Cross River da Akwa Ibom.

NiMet ta gargadi jama’a da su guji tuƙi a lokacin ruwan sama mai yawa, a cire na’urorin lantarki daga soket, a guji zama ƙarƙashin manyan itatuwa, sannan a ɗaure kayayyakin da ba su da ƙarfi.

Haka kuma ta shawarci manoma da su guji amfani da taki da maganin kwari kafin ruwan sama, yayin da ta bukaci kamfanonin jiragen sama da su riƙa samun rahoton yanayi na musamman domin tsara tashi yadda ya k**ata.

Rahotanni sun nuna cewa Ibrahim Bakura, wanda ake kira Abu Umaima, ya jagoranci wani ɓangare na Boko Haram bayan mutuwar...
22/08/2025

Rahotanni sun nuna cewa Ibrahim Bakura, wanda ake kira Abu Umaima, ya jagoranci wani ɓangare na Boko Haram bayan mutuwar Abubakar Shekau, kuma ya tafi yankin Diffa a Jamhuriyar Nijar da mayaƙansa.

Address

Kano

Telephone

+2349042713230

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ayzan Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share