Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia Ayzan Multimedia – Bringing news, Islamic education, and history. Under Ayzan Group, connected with مجالس النوابغ لتكوين العلماء & Tamkeen Qur'anic Channel.

Tsohon gwamnan na Kano Malam Ibrahim Shekarau ya ce idan har Gwamnan Kano yana da dalilinyunkurin komawarsa jam’iyyar AP...
06/01/2026

Tsohon gwamnan na Kano Malam Ibrahim Shekarau ya ce idan har Gwamnan Kano yana da dalilin
yunkurin komawarsa jam’iyyar APC, shi bai ga laifinsa ba, shi ma Kwankwaso ya sauya sheka ba sau daya ba.

18/12/2025
Allah Ga Katagum 🤲🤲🤲Duk me son samun flyer irin wannan yayi Dm wa.me/2348069727995
12/12/2025

Allah Ga Katagum 🤲🤲🤲
Duk me son samun flyer irin wannan yayi Dm wa.me/2348069727995

12/12/2025
Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Rivers, Martin Amaewhule, ya sauya sheƙa tare da wasu ƙarin mambobi 15 na majalisar zuwa...
05/12/2025

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Rivers, Martin Amaewhule, ya sauya sheƙa tare da wasu ƙarin mambobi 15 na majalisar zuwa jam’iyyar APC a ranar Juma’a. Wannan mataki ya sake tayar da kura cikin siyasar jihar, wadda ke fama da rikice-rikicen cikin gida tsawon watanni.

Rahotanni sun nuna cewa wannan sauya sheƙar na da alaƙa kai tsaye da rikicin siyasa da ya dabaibaye jihar tun baya-bayan nan.

Da wannan ci gaban, adadin mambobin majalisar da s**a koma jam’iyyar APC ya kai 16 gaba ɗaya.

Sauya sheƙar dai ya gudana ne a wani zama na musamman da majalisar ta gudanar, inda mambobin s**a bayyana cewa sun yi nazari tare da yanke shawarar komawa jam’iyyar APC.

HOTUNA: Yadda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu Ya Rantsar da Janar Christopher Musa (mai ritaya) a Matsayin Sabon Minista...
04/12/2025

HOTUNA: Yadda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu Ya Rantsar da Janar Christopher Musa (mai ritaya) a Matsayin Sabon Ministan Tsaron Najeriya a Fadar Shugaban Ƙasa

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Janar Christopher Gwabin Musa (mai ritaya) a matsayin sabon Ministan Tsaro na Najeriya, a wani gagarumin biki da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Taron rantsuwar ya samu halartar manyan jami’an tsaro, ministoci da sauran manyan baki daga sassa daban-daban na ƙasar. Sabon ministan tsaron, wanda ya jagoranci rundunar sojin ƙasar a baya a matsayin CDS, ya sha alwashin yin aiki tukuru wajen inganta tsaro, da karfafa haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro domin shawo kan matsalolin da ƙasar ke fuskanta.

Bayan rantsuwar, shugaban ƙasa ya jaddada muhimmancin sake fasalin tsarin tsaro da ƙarfafa rundunonin soji, yana mai cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da bai wa tsaro muhimmanci a dukkan matakai.

Hotunan daga wajen taron sun nuna sabon ministan tsaro tare da shugaban ƙasa, yayin da yake karɓar takardar nade shi, da kuma lokacin da yake ɗaukar rantsuwar k**a aiki.

DA DUMI-DUMI: Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Sanata Shehu Buba a matsayin Shugaban kwamitin Dabbobi da Kiwo (Liv...
02/12/2025

DA DUMI-DUMI: Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Sanata Shehu Buba a matsayin Shugaban kwamitin Dabbobi da Kiwo (Livestock and Animal Husbandry).

Wannan na zuwa ne makonni bayan sauke shi daga mukaminsa na baya, Shugaban Kwamitin Tsaro da Leken Asiri (National Security and Intelligence).

Sabon nadin yana cikin tsarin sauye-sauyen kwamitoci da shugabancin Majalisar Dattawa ta gudanar domin inganta aiki da inganta kulawa da muhimman bangarori na gwamnati.

Sanata Shehu Buba zai jagoranci kwamitin da ke da alhakin duba harkokin kiwo, ci gaban noma, da batutuwan da s**a shafi wadatuwan abinci a Najeriya.

Yan bindiga sun kai hari a wani coci da ke Ejiba, Yagba West, jihar Kogi, inda s**a sace fasto, matarsa da wasu masu bau...
01/12/2025

Yan bindiga sun kai hari a wani coci da ke Ejiba, Yagba West, jihar Kogi, inda s**a sace fasto, matarsa da wasu masu bauta a safiyar Lahadi.

Rahotanni sun ce maharan sun fara harbe-harbe, lamarin da ya sa jama’ar cocin tserewa domin kare rayukansu. Hukumomi dai har yanzu na tantance adadin mutanen da aka sace.

Mai magana da yawun gwamnatin jihar, Kingsley Fanwo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa suna aiki tare da jami’an tsaro da kungiyoyin sa-kai domin ceto wadanda aka sace.

Fanwo ya ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin an kubutar da mutanen, musamman ganin yadda matsalar hare-hare da sace-sace ta yi k**ari a yankunan Arewa da Tsakiyar Najeriya.

Lamarin ya biyo bayan wasu hare-hare da s**a hada da sace dalibai sama da 300 a Neja, da kuma wasu ‘yan mata a Kebbi, tare da sace masu bauta a wasu wuraren ibada a Kwara.

29/11/2025
29/11/2025
Fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasuSheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasu k**ar yadda daya...
27/11/2025

Fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasu

Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya rasu k**ar yadda daya daga cikin 'ya'yansa ya tabbatar wa da DCL Hausa. Ya shaida mana cewa jagoran na Darikar Tijjjaniya ya rasu ne a safiyar Alhamis din nan a garin Bauchi

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ayzan Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share