01/12/2025
Yan bindiga sun kai hari a wani coci da ke Ejiba, Yagba West, jihar Kogi, inda s**a sace fasto, matarsa da wasu masu bauta a safiyar Lahadi.
Rahotanni sun ce maharan sun fara harbe-harbe, lamarin da ya sa jama’ar cocin tserewa domin kare rayukansu. Hukumomi dai har yanzu na tantance adadin mutanen da aka sace.
Mai magana da yawun gwamnatin jihar, Kingsley Fanwo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa suna aiki tare da jami’an tsaro da kungiyoyin sa-kai domin ceto wadanda aka sace.
Fanwo ya ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin an kubutar da mutanen, musamman ganin yadda matsalar hare-hare da sace-sace ta yi k**ari a yankunan Arewa da Tsakiyar Najeriya.
Lamarin ya biyo bayan wasu hare-hare da s**a hada da sace dalibai sama da 300 a Neja, da kuma wasu ‘yan mata a Kebbi, tare da sace masu bauta a wasu wuraren ibada a Kwara.