
16/09/2025
MATASA SUN GINE ƊAKIN WATA DATTIJUWA A SABON GARIN ZARIA
—Daga: Aliyu Muhammad Sulaiman
A jiya Litinin, 15 — 09 — 2025, Dandalin Matasan Harƙar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na Amirul Muminin Zone a garin Zaria sun gudanar da aikin taimakon al’umma a Sabon Gari, hayin Ojo, wajen gina gidan wata tsohuwa.
Matasan sun gyara gidan wata mata mai suna Hajara Gurwa, inda s**a samar da bulo da siminti, s**a gina katangar gidan da ya rushe tun tsawon shekara guda.
Al’ummar unguwar sun yaba da wannan aiki tare da yin addu’a ga jagora Sayyid Zakzaky (H). Haka kuma, matar da aka taimaka wa ta nuna farin ciki da godiya bisa wannan gagarumin taimako.
— Youth Forum Media Team,
Amirul Muminin Zone, Zaria
1 6 — 0 9 — 2 0 2 5
SABON GARI MEDIA FORUM