Waseela

Waseela Domin samun Ingantattun labarai da Rahotanni a harshen Hausa

An gudanar Da ‎Mauludin Manzon Allah (s.a.w.w) Majalisin Tsugugi Da Ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari Zariya...Daga: Aliiy U...
08/11/2025

An gudanar Da ‎Mauludin Manzon Allah (s.a.w.w) Majalisin Tsugugi Da Ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari Zariya...

Daga: Aliiy Usman Nayara

‎A daren jiya Juma'a 7 ga watan Nuwambar 2025 ne, ƴan uwa Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na majalisin Tsugugi dake ƙaramar Hukumar Sabon Gari Zariya, s**a gudanar da Mauludin Manzon Allah , Annabi Muhammad Rasulullah (s.a.w.w) a kofar gidan Malam Jibril Anakallah, wakilin majalisin ƴan uwa Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na Tsugugi

‎Tunda farko an fara ne da buɗe taro da addu'a, sai aka yi karatun Alqur'ani mai girma, daga bisani aka karanta ziyarar Nabiyul-kareem, sannan aka yi Display, daga bisani kuma Malam Shehu Tsugugi ya gabatar da babban bako mai jawabi wato Sheikh Saluhu Garba.


Yayin jawabin nasa Sheikh Salihu ya yi dogon tsokaci ne akan rayuwa da kyawawan ɗabi'u na fiyayyan halitta (s.a.w.w) a matsayin abin koyi ga dukkan halitta, har wala yau shehin malamin yayi kira ga wajicin haɗin-kai Al'umma Musulmi domin tunkarar kafirci da kafirai duniya.

Bayan kammala jawabinsa ne, Iliyasu Kalifa Shehi Tajul'izzi kano ya gabatar da majalisi , daga bisani kuma Ittihadu-shu'ara s**a gudanar da nasu majalisi ɗin, wanda Malam Ahmad Algwadawy ya jagoranta

‎Bayan kammala Jawabai da majalisi ne aka yi addu'a aka sallami kowa Alhamdulillah. Anyi an fara taron lafiya an tashi lafiya . Daga kasa wasu daga cikin hotunan yanda taron ya gudana ne.

©‎Zaria Media Forum
08112025

"Bamu ce maka ba'a ilimi a samu wani abu ba, amma ba ana yi ne domin a samu duniya ba. Abin duniya yana bin ka ne. Kai d...
07/11/2025

"Bamu ce maka ba'a ilimi a samu wani abu ba, amma ba ana yi ne domin a samu duniya ba. Abin duniya yana bin ka ne. Kai dai kayi ilimin kawai, kayi shi kawai... 'To in na gama ina zan samu aiki, me zan ci?' Manta da wannan!"

"Arrizƙu rizƙani; rizƙun taɗlubuhu, wa rizƙun yaɗlubuk [Arziki kala biyu ne; Arziki wanda kake bin shi da arziki wanda yake bin ka]. In kayi ilimi fi sabilillah rizƙ din zai biyo ka ne. Biyo ka zai yi"
.."Akwai masu ilimi domin neman duniya; ko su sami duniyar ko kar su samu, ladan su kenan. Ba su da wani lada wurin Allah"

"Masu yi kuma domin Allah su suke da ladan su. Kuma duniyar ba zata tsere musu ba, za ma ta bisu ne. Duniyar zata bisu ne! Mutum ya gwada ya gani"

-Sayyid Ibrahim Zakzaky (H)

*'KOFAR GIDAN SAYYIDA ZAHRA (SA) S**A CINNAMA WUTA, TA KONE S**A AUKA CIKI..'*_Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)"S**a hadu su ...
06/11/2025

*'KOFAR GIDAN SAYYIDA ZAHRA (SA) S**A CINNAMA WUTA, TA KONE S**A AUKA CIKI..'*

_Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

"S**a hadu su jimla su dari takwas. S**a kewaye gidan. Jagoransu ya ce; ko ku fito ko kuma in kona gidan da duk wanda ke ciki!

"Aka ce masa; akwai fa 'yar Manzon Allah (S) a cikin gidan. Sai yace," ko da ita fa!" Ya ce; a kawomin kirare. Aka kawo kirare yasa a kofar gidan. (Ba zai boyenma mutane cewa gida ne ba. Ma'ana akwai kofar shiga gidan. Sannan in ka shiga gidan akwai sarari wanda kake duban sama hororo. Sannan kuma akwai dakuna. Wato akwai tsakar gida, anan ke da rijiya da wurin nika da ire-iren wadannan na wancan lokaci da kuma dakin kwana. Akwai dakuna. Saboda haka su sauran Ansar da s**a goya baya har da Zubair bn Awwam, wanda yake dan gwaggon Annabi ne shi. Shima ya mara wa Ali baya a wannan lokacin, shima yana cikin wanda s**a ankara kan kuskuren da akayi. S**a je s**a zauna a gidan).

"Saboda haka, sauran jama'a suna tsakar gidan ne. Ita kuma Sayyida Fatimatuz Zahra da Mai gidanta da 'ya'yanta suna cikin daki. Saboda haka kofar shiga gidan, shi ne aka cinnama wuta. Akasa kirare aka banka wuta, kofa ta kone, s**a auka ciki.

— Cikin jawabin Shaikh Ibraheem Zakzaky a lokacin zaman juyayin Shahadar Sayyida Zahra (SA) a shekarar 1435H a Husainiyyah Baqiyatullah.

Ja'afar Muhammad Jr.
05/11/2025.

06/11/2025

Sabon Gari Media sun canza sunan shafinsu na Fesbuk zuwa Waseela, sun Sallamawa sabon tsarin Media Forum na ayi aiki da Murya 1.

06/11/2025

A Safiyar yau Maƙabartun Sabon Gari Zariya ta Hayin ojo data Tsugugu da Unguwa gwado duk an kai mamata.

“Tutar mai kalmar nan ta Allah, La'ila Ha'illallah Muhammad Rasulullah (saww), mu ita muke so ta filfila ta zama ita tak...
05/11/2025

“Tutar mai kalmar nan ta Allah, La'ila Ha'illallah Muhammad Rasulullah (saww), mu ita muke so ta filfila ta zama ita take iko damu a ƙasar nan bata jahiliya ba.”__-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

Kar ku yarda a  hada Ku rigima da juna koda da wani Irin abu za'a kira rigimar,Ko da Sunan Addini Ko da Sunan Qabila ku ...
05/11/2025

Kar ku yarda a hada Ku rigima da juna koda da wani Irin abu za'a kira rigimar,

Ko da Sunan Addini Ko da Sunan Qabila ku haɗe Kai ku zauna Lafiya.

Kiristoci ba Sunan Su Arna ba, Sunan da Allah ya ambace su a Qur'ani Ma'abotan littafi."-Jagora (H) yayin da yake masu bayanin muhimmancin zaman lafiya.

Sannan dağa karshe sun karrama sheikh zakzaky (H) a mazaunin mutum mai son hadin kai da kuma zaman lafiyan al’ummah.

Yanzu muke samun labarin Allah ya kubutar da dan uwa Ali na Allama daga hannun masu garkuwa da mutane, bayan ya shafe ts...
04/11/2025

Yanzu muke samun labarin Allah ya kubutar da dan uwa Ali na Allama daga hannun masu garkuwa da mutane, bayan ya shafe tsawon kwanaki a hannusu, Allah ya kara mishi lafiya ya kiyaye na gaba.

04/11/2025

أعظم الله أجورنا وأجوركم بمصابنا بشهادة سيدة نساء العالمين سلام الله عليها

04/11/2025

“ Gara ka ziyarci Yahudawa daka ziyarci Sheikh Zakzaky a wajen wasu masu kiran kansu musulmai.”_-Prof Ibraheem Maƙari

“‎Daidai gwargwado Ni Allah ya sanar dani wallahi faɗa tsakanin musulmi da musulmi bazai kaimu ko ina ba.”__-Inji Sheikh...
03/11/2025

“‎Daidai gwargwado Ni Allah ya sanar dani wallahi faɗa tsakanin musulmi da musulmi bazai kaimu ko ina ba.”__-Inji Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

Aliiy Usman Nayara

A jiya lahadi Ƴan uwa musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (h) s**a gudanar da karatun Ta'alim a Fudiyya Orag Marke...
03/11/2025

A jiya lahadi Ƴan uwa musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (h) s**a gudanar da karatun Ta'alim a Fudiyya Orag Market Mararaba Nyanya Abuja.

Aliiy Usman Nayara

Address

Sabon Gari

Telephone

+2348068113532

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Waseela posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share