SABON GARI MEDIA FORUM

SABON GARI MEDIA FORUM Domin samun Ingantattun labarai da Rahotanni na Ƙaramar Hukumar Sabon Garin Zariya.

MATASA SUN GINE ƊAKIN WATA DATTIJUWA  A SABON GARIN ZARIA—Daga: Aliyu Muhammad Sulaiman A jiya Litinin, 15 — 09 — 2025, ...
16/09/2025

MATASA SUN GINE ƊAKIN WATA DATTIJUWA A SABON GARIN ZARIA

—Daga: Aliyu Muhammad Sulaiman

A jiya Litinin, 15 — 09 — 2025, Dandalin Matasan Harƙar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na Amirul Muminin Zone a garin Zaria sun gudanar da aikin taimakon al’umma a Sabon Gari, hayin Ojo, wajen gina gidan wata tsohuwa.

Matasan sun gyara gidan wata mata mai suna Hajara Gurwa, inda s**a samar da bulo da siminti, s**a gina katangar gidan da ya rushe tun tsawon shekara guda.

Al’ummar unguwar sun yaba da wannan aiki tare da yin addu’a ga jagora Sayyid Zakzaky (H). Haka kuma, matar da aka taimaka wa ta nuna farin ciki da godiya bisa wannan gagarumin taimako.

— Youth Forum Media Team,
Amirul Muminin Zone, Zaria
1 6 — 0 9 — 2 0 2 5
SABON GARI MEDIA FORUM

CIKIN HOTUNA| Yadda aka rufe taron Makon Hadin Kan Musulmi na bana karo na 6, wanda yan uwa Almajiran Shaikh Zakzaky na ...
15/09/2025

CIKIN HOTUNA| Yadda aka rufe taron Makon Hadin Kan Musulmi na bana karo na 6, wanda yan uwa Almajiran Shaikh Zakzaky na Da'irar Zariya s**a shirya a Muhallin Makarantar Fudiyyah da ke cikin birnin Zariya. A yau Litinin 15 Ga Watan Satumba, 2025.

Taron ya haɗa al'ummar musulmi masu mabanbanta fahimta daga ciki da wajen Musulunci. Ya kuma sami halartar manya malaman Ɗarikar Tijjaniyya irin su, Shaikh Abidurrahman Muhammad da kuma Shaikh Baka Mahmud da s**a gabatar da jawabi a muhallin taron na "Hadin Kan Musulmi" wanda ya gudanar a filin makarantar Fudiyyah da ke Zariya.

Ana gabatar da taron ne domin samun hadin kan al'umma Musulmi domin ganin an zama tsintsiya madaurinki ɗaya.

Haka kuma, Mawakan Harkar Musulunci a Najeriya tare da haɗin gwiwar yan uwa na Ɗarikar Tijjaniyya sun gabatar da wajen haɗin kai tare da yabon Manzon Allah (S), inda daga bisani kuma ƴan tamsiliyya s**a gabatar da tamsiliyya wacce s**a bawa suna mabudin kunnuwa.

Wakilin yan uwa Musulmi na Da'irar Zariya da kewaye, Shaikh Abdulhamid Bello ya yi ta'alikin a wajen taron.

© Zaria Media Forum
15th September, 2025
SABON GARI MEDIA FORUM

"Ina mamakin yadda mutane suke sakin jiki suna shantakewa da zaman duniyar nan. Ya ce masu jin daɗin duniya kamar misali...
15/09/2025

"Ina mamakin yadda mutane suke sakin jiki suna shantakewa da zaman duniyar nan. Ya ce masu jin daɗin duniya kamar misalin a ce ana bikin aure yau amma an sani gobe amarya za ta mutu.! Ya kuke gani za a saki jiki ai ta raye-raye kuwa.? To haka duniyar nan take".

"Kai ka san dole za ka mutu. Duk lokacin da aka saka to ya ka ƙare, kuma duk abunda ya yi farko dole da ƙarshen shi. Amma mutane da gafala Malam da dogon buri, ga neman mulki ido rufe".__-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h) a Sharhin Nahjul Balagha babin Mutuwa.

SABON GARI MEDIA FORUM

15/09/2025

A yau Litinin za a rufe taron MAKON HAƊIN KAN MUSULMI Karo Na 6, wanda Almajiran Shaikh Zakzaky na Da'irar Zariya ke gabatarwa.

“Inda za a zo Nageriya a tambayi mutane 10 (Goma) ace: Mene ne Shi'a? To lallai zaka sami amsa Goman ne domin kowa da ya...
15/09/2025

“Inda za a zo Nageriya a tambayi mutane 10 (Goma) ace: Mene ne Shi'a? To lallai zaka sami amsa Goman ne domin kowa da yadda zaka ji ya bada tashi Amsa ne alhali sam ba yadda suke faɗin bane.”__-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

SABON GARI MEDIA FORUM

'MASU CEWA MANZON ALLAH (S) YA JE MADINA NE A MATSAYIN 'DAN GUDUN HIJIRA. BA A 'DAN GUDUN HIJIRA BANE..'_Shaikh Ibraheem...
14/09/2025

'MASU CEWA MANZON ALLAH (S) YA JE MADINA NE A MATSAYIN 'DAN GUDUN HIJIRA. BA A 'DAN GUDUN HIJIRA BANE..'

_Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) Yace;

“Aiko Annabi (S) ya zama wani muhimmin abu, amma babba a cikin muhimman abubuwan shine Hijirarsa zuwa Madina, dalili shine saboda yanzu addinin nasa ke iko a Madina, yanzu addini ya kafu ne. Manzon Allah (s) ba ya je Madina ne a matsayin dan gudun Hijira ba.”

“Ba an ba Annabi mafakar siyasa a Madina bane, an bashi Madina ne, da sunanta Yasrib, sai aka canza mata suna zuwa Madinatun Nabiy (S), yanzu sunanta Birnin Annabi (S). Yanzu Annabi (S) shine shugaban al’umma… Tunda yanzu addininsa ne ya kafu daram, wannan sakon da Allah ya aiko da shi ne ya kafu, sai ya zama Hijira shine ya fi zama muhimmi a wajenmu. Shi yasa ma aka fara kidaya da shi, saboda daga lokacin addini ya kafu.

-Cikin Jawabin Shaikh Zakzaky (H) A shekarun baya.

Ja'afar Muhammad Jr.
SABON GARI MEDIA FORUM

“Inma mutum bai san Allah ba, bai san lahira ba, Bazai yiwu yace wani mutum nada magoya baya, ya kashe shi ya zauna lafi...
13/09/2025

“Inma mutum bai san Allah ba, bai san lahira ba, Bazai yiwu yace wani mutum nada magoya baya, ya kashe shi ya zauna lafiya ba.”__-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

Aliiy Usman Nayara
SABON GARI MEDIA FORUM

A yau Asabat ga Kaɗan daga cikin hotonan Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (h) lokacin da suke fareti a wajen TAKUTAHA a...
13/09/2025

A yau Asabat ga Kaɗan daga cikin hotonan Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (h) lokacin da suke fareti a wajen TAKUTAHA a karamar Hukuma Sabon Gari Zariya.

SABON GARI MEDIA FORUM

“Mai ilimi mai ilimi ne ko a ina yake, mutunin kirki mutumin kirki ne ko a ina yake. Kuma komai yanada lokaci da iyaka.”...
12/09/2025

“Mai ilimi mai ilimi ne ko a ina yake, mutunin kirki mutumin kirki ne ko a ina yake. Kuma komai yanada lokaci da iyaka.”__-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

Aliiy Usman Nayara
SABON GARI MEDIA FORUM

“Ba mu da alami, wanda zai hada mu gabadayanmu ba tare da rarraba ba kamar shi Manzon nan (S) da ya zo da addini. Shi ne...
12/09/2025

“Ba mu da alami, wanda zai hada mu gabadayanmu ba tare da rarraba ba kamar shi Manzon nan (S) da ya zo da addini. Shi ne Qudwa, shi ne abin koyi, shi ya zo da addini, shi ya aikata addini, ya dora mutane akan addinin, to wannan koyarwar na shi kan kansa, shi ne alami. Domin shi ne wanda za a gani a kwafa. Allah Ta'ala yana cewa: “لَّقَدْ كَانَ لَكُمْ فِي رَسُولِ اللَّهِ أُسْوَةٌ حَسَنَةٌ” Muna da kyakkyawan misali ga Manzon Allah (S), abin koyi ne shi wanda za a gani a kwafa.”__-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

SABON GARI MEDIA FORUM

Shaikh Zakzaky ya bayyana yadda sama da shekaru 50, tun suna karatun 'Advance level' har zuwansu Jami'a, duk daga Jami'a...
12/09/2025

Shaikh Zakzaky ya bayyana yadda sama da shekaru 50, tun suna karatun 'Advance level' har zuwansu Jami'a, duk daga Jami'ar London da ke Ingila ake shiryo musu jarabawar karatun 'Islamic Studies', kuma duk kusan tambayoyin da ake shiryawa na baƙanta Shi'a ne a lokacin. Ya ce: “Tsarin karatun Islamic Studies na jami'o'i, asalinsa daga Ingila ne, wasu Malaman ma Yahudawa ne, domin mu a lokacinmu Malamanmu na jami'a 'product' ne na Ingila. Gwagwarmayar Imam Khomeini (QS) ce ta fito da asalin yadda Shi'a suke, a yayin da Shi'a sun boye kansu ne kafin 'revolution' din Imam (QS).”

Don haka, Jagora (H) ya bayyana mamakinsa akan wanda yake jin cewa yanzu zai koma yin Shi'a ba gwagwarmaya. “Kai a matsayinka na wanda ya fahimci Shi'a ta hanyar gwagwarmaya, ta yaya za ka karbi wannan ra'ayi, alhali ta hanyar aikin wasu na gwagwarmaya ne ka fahimci Shi'ancin kansa?" __-Sheikh Ibraheem Zakzaky (h)

SABON GARI MEDIA FORUM

12/09/2025

Yau 12 September shekaru 29 dai-dai da Gen. Sani Abacha yasa sojoji s**a afkawa Almajiran Sheikh Zakzaky (h) da kisa a Nageriya.

Address

Sabon Gari

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SABON GARI MEDIA FORUM posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share