Mu'asasatu Aliyul Akbar.

Mu'asasatu Aliyul Akbar. Shafin Mu'assasatu Sayyid Aliyul Akbar (As)

10/02/2025

Muna neman shawarar ku akan wannan Shafin, kuna ganin mugoge shi ko mu canja mai suna mu cigaba da anfani dashi?

SANARWA GA DUKKAN MAMBOBI!Muna mai sanar da dukkan mambobi cewa: an yanke shawarar dakatar da dukkan ayyukan forum na Mu...
10/02/2025

SANARWA GA DUKKAN MAMBOBI!

Muna mai sanar da dukkan mambobi cewa: an yanke shawarar dakatar da dukkan ayyukan forum na Mu’Assasatu Aliyul Akbar daga yau [10/2/2025]. Wannan mataki an ɗauke shi ne bisa Jawabin da Sayyid Zakzaky (H) ya yi, a yayin ganawar su da Harisawa a gidanshi dake Abuja.

Sannan Muna sake sanar da yan'uwa cewa: an soke Mauludin da a shirya za,ayi yau na tunawa da ranar Haihuwar Sayyid Aliyul Akbar.

Muna gode wa dukkan mambobin da s**a taka rawar gani a cikin forum ɗin nan, tare da fatan alheri ga kowa. Idan akwai wata tambaya ko karin bayani, ana iya tuntuɓar masu ruwa da tsaki ta hanyar [0903 798 4822, 07042479039].

Allah ya sa mu dace, ya kuma sada mu da alheri.

Wassalamu Alaikum Warahmatullah.

Sanarwa daga Ahmad Assaminaky a madadin masu gudanarwa.

SAKON SAYYID ZAKZAKY (H) GA WANDA ZA SU YI AURE.KARANTA KA JI DAN UWA.Allamah Sayyid Zakzaky (H) ya ce; "To sai kuma (na...
09/02/2025

SAKON SAYYID ZAKZAKY (H) GA WANDA ZA SU YI AURE.

KARANTA KA JI DAN UWA.

Allamah Sayyid Zakzaky (H) ya ce; "To sai kuma (nasihata ga) wanda ba su yi aure ba, ya k**a mu yi iya kokarin mu muga cewa in za mu yi aure, to tun daga neman, ya zama mun daddage, mun ga cewa lallai an bi shari'a.

"Wasu (wai) akan dan sassauta musu, na san akwai malaman Kaduna, masu dan yin sassauci haka, in shari'a ta cika tsauri, in ka samu malami, ba ruwan sanyi (kawai zai zubawa shari'ar) ba, qanqanra ma yana iya zuba mata, duk abin ma ya baje gaba daya duk a huta! (Wato in shari'a) ta cika zafi, sai a dan sassautata.

"To, bai k**ata (idan gidan Amarya sun jero al'adu a lokacin aure), sai a ce ka ga sun zubo mana al'ada, amma ya aka iya? Tunda ba da ikon ka ba ne, ka dan yi al'adar kawai, tunda Allah ya san nufinka, idan aka yi auren sai a canza!

"A'a! A'a!! Ya k**ata ne a dage a ce ba za a yi al'adar ba! Shari'a za a yi!! Idan da muna yin wannan dagewar, da tuntuni mun kori al'ada (a aurarrakin mu), mu ne muke wa al'adar sassauci, shi ya sa har muke jin tsoronta, har kuma ta fi karfinmu!!

"Kowa sai ya ce wai al'adar haka nan aka ce (a yi ta), don haka in ba mu yi ba za a fasa auren! Alhali da za mu dake! Mu ce shari'a kawai za a bi! To da yanzu ba wanda ma zai yi tunanin ya kawo maka al'ada (a cikin hidimar aurenka)!

"Saboda haka kar kullum mu rinka tunanin wai wasu ne za su dage ba mu ba, mu din ne za mu dage!! In duk gaba dayanmu muka dage, to insha Allah an dinga yin aurarraki ta hanyar shari'a kenan, kuma ita shari'ar ita za ta gudanar da aurarrakin namu baki daya.

"To amma kuma in har a wajan neman aure ka yi masa "Assalamu Alaikum" da Al'ada, to zai fa ci gaba a al'adance ne, in ka yarda tun a wajan neman auren aka yi Al'ada, to kana cikin zaman auren za a kawo maka Al'ada, ba ka kuma isa ka ce a'a ba!

"Amma in tun farko ka dake! To su ma (dakarun al'adar) za su ji a jikinsu (dole su hakura su sallama maka)..... Wato in tun farko s**a ga an ginu akan shari'a, to ba za su iya cewa a yi Al'ada ba.

"Wannan ya k**ata ya zamo mun yi shi a aikace ne!".

Daga jawabin Allamah Sayyid Zakzaky (H) a ranar walimar bikin auren Alhaji Aminu Yabo (karin aurensa), shekarun baya a birnin Kaduna.

TAMBAYA?

Watakil wani ya yi tambaya cewa menene al'adu a cikin hidimar aure?

To Sayyid Zakzaky (H) duk ya bada amsa a cikin wannan jawabi mai albarka, ga abin da ya ce a tsakiyar jawabin nasa.

"Dan karamin misalina anan shi ne, har yanzu ana wasa da Sadaki, sai a yi wasu abubuwa bisa kimar yadda Al'ada ta tanada, daga ciki akwai wani abu;-

"Wai ko kayan na gani ina so!? A kai (gidan su Amarya).

"Da wani ko Rigar Uba ne? Shi ma a kai.

"Da wani wai ko menene na uwa? Shi ma a kai.

"A je a leka (yawon gaida dangin Amarya), shi ma a yi.

"Dangin Uba ma da akwai abin miqawa (kudin daukar Amarya).

"Da wani abu wai sunansa wai Baiwa.

"A zo a yi wani abu wai sunansa wai SA RANA!

"A zo kuma a yi wani abu wai sunansa wai KAYAN ASIN DA ASIN.

"A zo kuma a yi wani abu wai KAYAN AURE (KO LEFE!)

"Zuwa can a zo a ce wai a yi TUWON JIBI!!

"Zuwa can a zo a ce wai a yi TUWON BIKO!!

"Al'aduka iri-iri dai, duk a gama wadannan, amma wai in aka zo daurin aure, sai ka ji an ce SADAKI NAIRA GOMA!!!!!!!!

"Abin da addini ya yi tanadi, sai aka maishe shi wargi da wasa! Su kuma wadancan al'adu duk an sa ka'idojinsu, kuma (an ba su karfi tamkar addini ne su, ta yadda) in ba ka yi su ba har ma sai a ce an fasa auren!!

"A ce (ya za a yi mutum) ya kawo Sadaki, amma bai kawo kayan aure (Lefe) ba!! Ko kuma in ya kawo din a ce a kidaya a ga Turmin (zani) nawa ya kawo? Nawa ya dinka? Super Shadda nawa ya sa a ciki?

"Sai a ce ai a zamanin nan yayin kaza ake yi, sai ya sa kaza (da kaza a cikin kayan lefen)!!

"To (abin da ya k**ata mu sani shi ne), idan Al'ada ta dauki matsayin shari'a, to kar kuma mu tsammaci samun lada (cikin hidimar)!

"To kuma auren mu zai zama bai da bambancin da na Katafawa kenan, tunda su ma sunayin aure na Al'ada!!".

(Mai karatu, Jagora (H) ya zuba bayani kan aure a wannan jawabi na auren Alhaji Aminu Yabo).

Nakaltowa; Ahmad Assaminaky

DARASIN DA NA DAUKA GAME DA ZAMAN DA JAGORA (H) YAYI DA HARISAWA. Rubutun nan zai zamo tamkar shawara kuma darasi garemu...
09/02/2025

DARASIN DA NA DAUKA GAME DA ZAMAN DA JAGORA (H) YAYI DA HARISAWA.

Rubutun nan zai zamo tamkar shawara kuma darasi garemu baki daya.
Amma kafin nan bari mu dan kawo wani sharhi.

A shekarun baya na kasance mai bibiyar programs din Farfesa Ali Mazure, dan kasar Tanzaniya a kan tarihi, addini da al'adun mutane da kasashe daban daban musamman na Afirka.
Farfesan ya taba yin wani sharhi wanda har yanzu ina yawan tuna sharhin nasa a ko yaushe idan irin lamarin ya faru sai kawai na tuna sharhin nasa wanda na kalla shekaru kusan 25 a baya.

Farfesan Mazure, a cikin sharhin nasa ya bayyana cewar wasu mutane ko al'umma s**an iya tsintar kansu a wata al'ada ko fahimta ko addini wanda zasu doru a kai suna gudanar da rayuwarsu ko al'amuransu a kan wannan fahimtar ko tunanin, kuma su rika yinsa bilhakki alhali hakan kuskure ne babba tun daga asalinsa, wanda kuma kodai basu samu hakikanin gaskiyar ba ko kuma gaskiyar bata je musu ba. Sai yace da zarar gaskiyar lamarin ta bayyana garesu, sak**akon dadewar da s**a yi suna rayuwa a kan wancan tunanin sai kuma a fara samun mushkila wajen karbar gaskiya din.

Ya bada tarihin yadda wasu annabawa s**a sha wahala sossai a hannun sarakunan zamaninsu, laifin annabawan shi ne sun zo da gaskiya kuma gaskiyar taci karo da abinda s**a dora talakawansu a kai, don haka sai su fito da dukkanin karfinsu domin yakar annabwan da s**a zo musu da sakon gaskiya din.
Farfesa ya bayyana yadda wasu sarakuna a nan Africa s**a rika fafatawa da wasu maluman addini da yan kawo sauyi wajen kin karbar gaskiyar da s**a zo musu dashi..
Inda ya bata misali da shehu Usman Dan Fodiyo da sarakunan kasar hausa.

Farfesa Ali Mazure ya bayyana cewar jarumai a cikin sarakuna da talakawansu sune wadanda lokacin da gaskiya ta bayyana garesu sai s**a karbeta nan take to wadannan sune jarumai na hakika, wadanda ya dace a jinjina musu kuma sune wayayyun a cikin sarakuna ko mabiya, domin karbar gaskiya ba nakasu bane jarumtaka ne wanda kuma ya dace a jinjina wa wanda yayi hakan.

Ya bayyana wasu dalilan dake hana mutane karbar gaskiya idan ta zo musu k**ar haka:
Na farko suna tsoron kar su rasa muk**ansu da s**a dade a kansa. Wasu kuma suna tsoron kar mulkinsu ya subuce daga hannunsu.
Sannnan wasu suna tsoron kar jama'ar dake tare dasu su waste su koma wani wajen.

Wasu kuma suna jin kunyar kar wasu su yi musu dariya. Wasu kuma na tsoron kar su rasa dukiyar da suke samu daga mabiyansu da sauran wasu dalilan masu yawa. Amma da dama suna iya fahimtar gaskiya idan tazo musu, domin ita gaskiya a ko da yaushe tana bayyana kanta ta yadda kowa zai iyanganeta kuma bata bukatar ado.

Wadannan bayanan na Farfesa Ali Mazure sun sa na tuna da Kadiyar Shaikh Saleh Lazare, da aka ce a baya yana jagorantar dubban mutane a matsayinsa na mukaddamin tijjaniya, wanda yake da girman shuhura da zawiya babba a kasar Nijar, amma da gaskiya ta bayyana masa (ilimin gidan annabta) sai ya tara mabiyansa yayi musu bayanin hakikanin sabuwar fahimtar tasa. An bayyana cewar da dama cikin almajiran nasa sun tsere sun barshi, amma da ya dake ya tsaya kyam sai Allah ya dawo masa da almajiran nasa har da karin wasu masu yawa, wadanda s**a linka na baya yawa da kuma sadukarwa.

A karshe, na taba jin shaikh Turi (qss) yace.
'In da za'a fada masa cewar jagora yace daga yau aikinsa a harka shine tsince ledar fiyo wata (Pure water) idan an sha an jefar da ledar a wajen programs, ya ce "wallahi daga rannan zan koma yin tsintar ledar fiyo wata domin yin biyayya ga su sayyid (H) kuma ya kara da cewar, zai yi ne iya yinsa.

Allah ya sa mu zama abin alfahrin su jagora, Allah ya hada kanmu baki daya.

Nasir Isa Ali

Katin Gayyata! Sati me zuwa muna da Bukukuwa wasu daga Matasan Yankin Da'irar Saminaka. Idan Allah ya kaimu Juma’a da As...
09/02/2025

Katin Gayyata!

Sati me zuwa muna da Bukukuwa wasu daga Matasan Yankin Da'irar Saminaka. Idan Allah ya kaimu Juma’a da Asabat 14-15 ga February 2025, muna da Ɗaurin Auren wasu daga cikin ƴan uwa da abokan arziƙi.

Ahmad Abdul-rahman Ibrahim da Amaryarsa Fatima Ahmad da Musa Jafar da Amaryarsa Hussaina Babangida, Yakubu Ali Kafinta da Amaryarsa Hassana Babangida, duk ranar Juma’a 14 ga Feb.

Hayatuddeen Sani da Amaryarsa Fateema Khamees, Mahadi Ibraheem da Amaryarsa Zainabal Khubra Adam Abdallar ranar Asabat.

Muna gayyatarku. Allah Ta’ala ya nuna mana lokacin. Ya bamu ikon halarta.

— Jawad Sabi'u

Rana ita yau 15 ga Sha'aban, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) zai cika shekaru 74 da haihuwa. A yayin da aka shafe kus...
07/02/2025

Rana ita yau 15 ga Sha'aban, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) zai cika shekaru 74 da haihuwa. A yayin da aka shafe kusan shekaru 48 yanzu haka yana wannan Da'awar ta kira zuwa ga komawa tafarkin Allah Ta'ala da bin tsarinSa. Wanda yake nufin tun yana matashi dan shekaru 26 yake wannan Da'awar.

Dattijon nan bai huta ba, mutum ba zai san haƙiƙanin Mazlumiyar Jagora (H) ba, har sai ya ji sashinsu daga gare shi. A takaice, ko a jawabin da ya yi na karshen nan ga Harisawa, ya yi bitan wasu daga waki'o'i da kame-kamen da azzaluman mahukuntan kasar nan s**a masa, wanda samun cikakken bayanai akansu zai zo a littafan da ya rubuta da kansa don ba da tarihin rayuwa da gwagwarmayarsa.

Idan mutum yana iƙirarin shi almajirin wannan Dattijon Bawan Allah din ne, to duk almajiri zai so tausayawa Malaminsa wajen ganin ya rayu cikin natsuwar zuciya, da lafiyar jiki, da yalwataccen dama na fuskantar matsalolin da ke fuskantarsa.

Kamar zai zama akwai rashin kunya na ƙarshe, mutum ko da ya kai sa'an Jagora (H) a shekaru, ko ya girme shi, in dai yana raya cewa shi mabiyansa ne, Jagoran ya yi wata matsaya, shi ya tsaya yana guna-guni da ƙoƙarin nuna in kaza ne, to ai kaza, ko tuhumar me zai sa kaza, mu ai kaza. Ballantana wannan ɗin ya zama yaro ne da bai kai ko shekaru 40 ko ma 30 ba. Ina ma mutum rantsuwa da Allah, ko a zuciyarsa ya ji wani ɗar, ko zafi, ko kokonto, to ya samu matsala, ya dage da Istigfari da addu'ar tabbatan Imani a zuciyar.

Sauƙaƙaƙƙen bayani Jagora (H) ya yi a cikin abin da bai wuce awa 1 ba, ya fitar da komai dalla-dalla, har ma da dalilai. Kuma ya ba da uzuri, akan cewa sun yi hakan ne da nufin gyara, ba su yi don su batawa kowa rai ba. Wannan fa k**ar rarrashi Jagora yake yi, wanda a wajenmu, abin jin nauyi ne ma hakan. Kuma Jagoran nan, wadanda s**a je gabansa sun ga dukkan karamci da mutuntawa da ya musu, an yi nishadi da farin ciki, an gaisa cikin sakin fuska, an sha shayi, an ci abinci, har ma sai da ya bi kowa a duk mutanen da s**a je da Hadiyya ta musamman.

Ba za mu taimaki kanmu ba mu kasance cikin amincin Allah Ta'ala da karban matsayar wanda muke cewa shi ne silan shiriyarmu a duniya da dacewarmu a lahira? Wai me ma aka yi ne na ɓaci? Bisa sa'ayin wasu 'yan uwa, a bayan Waki'a, Jagora na tsare, sun rika ƙirƙiran rundunoni daban-daban, wasu da Iklasi s**a ƙirƙira, Allah Ya sani, wasu kuma da manufa. Kuma har bayan fitowar Jagora ba an daina ƙirƙiran ba ne, duka kuma da sunan Harka Islamiyya ƙarƙashin Jagorancinsa (H), mene ne aibu idan yace duka a dakatar da su, babu bukatarsu, in da bukatar nan gaba zai samar da kansa ko bisa Irshadinsa?

Wasu suna guna-guni akan Jaishi Shaheed Ahmad (JASAZ) wadda take ƙarƙashin Mu'assasatu Abul Fadl Abbas, cewa ita ma bayan Waki'a aka samar da ita. Eh haka ne, bayan Waki'a ne, amma tun samarwar, har ta kafu, har zuwa cigabanta duk da masaniya da irshadin su Jagora (H) ake yinta. Ba wasu ne kawai s**a ƙirƙira don kansu suke gudanarwa don kansu ba ba tare da kai bayanansu inda ya dace ba. Saboda haka, in an samar da wata runduna, komai kyawun sunan da aka saka mata, in ya zama bata da tushe ko sila da Jagora, me zai sa ka yi tsammanin dole ya amshe ta?

Harka na da tsari da nizami, a hankalce in kowa zai zama yana da damar ya ƙirƙiri runduna ko tawaga an san shi ko ba a san shi ba, su rika saka kaya suna Display ko Fareti, ko su zo wajen taron Harka suna raba Duty, za a wayi gari Maƙiya ko Jahiliyya za ta samar da nata, sai a fara ɓarna da rigima, irin wanda ba tun yanzu ba ya fara aukuwa. Ƙarshe su je suna wani abin mare kyau wanda Harkar za a kalla da shi. Saboda haka, in har mutum na da tunani, ko da yana wata Jaishu ko Runduna, ko Mu'assasa ire-iren wadannan da basu da 'stamp' din Jagora (H), sai Jagora ya ankarar da shi hatsarin hakan, zai yi godiya ga Allah ne, ya yi fatan Allah Ya karbi sa'ayinsa da ya gabata a wannan rundunar, Ya yafe masa gazawarsa, sai ya watsar da ita.

Akan haka nake jinjina ga masu gudanar da JAISHU ƘAASIM SULAIMAN, bisa bayyana matsayarsu na rushe rundunar, da fatan Allah Ya karbi kokarinsu. Haka ma na ga JAISHU ALIYUL AKBAR su ma sun yi takarda da ke nuna sun dakatar da duk wani activities da suke karkashin wannan sunan. Dazu ma na ga Sanarwar ANSARU ZAKZAKY (H) sun dakatar da ayyukansu a ƙasa bakidaya. Allah Ya girmama lada gabadaya. Ya karbi sa'ayi.

Akwai Jaishohi da Rundunoni, da Ƙungiyoyi sun fi 20 da aka samar, wanda dukkansu akwai bukatar su karbi Irshadin su Jagora (H), ko sun bayyana a Public ko basu bayyana ba, su dakatar da duk abubuwan da suke yi. Mambobinsu su koma su shiga wasu Lajanoni da ake da su a cikin Harka Islamiyya, k**ar Dandalin Matasa in dai mutum bai kai shekaru 40 ba, ko Academic Forum in shi ɗalibi ne ko Malami, ko Sisters Forum in mace ce matashiya ko tsohuwa, ko Resource Forum in ma'aikaci ne, ko Huffaz Forum in mahaddaci ne ko mai niyyar haddan, ko Ittihadu in mawaki ne, ko Ahluddusur, in kai dan kasuwa ne ko manomi ko mai kudi, ko ISMA in mai karanta bangaren kiwon lafiya ne, ko ma in duk ba zai yi su ba ya zama cikin Brothers Forum ya yi ta ba da gudummawa a Da'irarsu.

Jagora (H) ya taba bamu misali da shirya taro, inda yace tana iya yiwuwa mai dafa shayi ko abincin da za a ci a wajen taro, ya fi Malamin da ya yi jawabi a wajen taron lada a wajen Allah Ta'ala, in ya fi shi yi da Iklasi. Haka ma mai shirya takalma ko ababen hawa, ko mai gyara shimfida. Aiki a Harka akwai bigiren yinsa da dama fa. Ga Fudiyya nan tana bukatar masu ba da gudummawar koyarwa.

Idan kuma mutum ma yana sha'awar kasancewa a wani waje ne da ake Fareti ko Display, zai iya kwankwasa JASAZ, idan sun tashi diban ma'aikata, in ya cika sharuddansu sai su dauke shi. Ko kuma ya jira Harisanci ta bude ƙofar diban sababbin Harisawa, sai ya shiga shima in zai iya cike sharudda.

Babu bukatar hargowa da hayaniya sam. Ko da muke ganin muna garuruwanmu ne, amma in muka zo muna hayaniya a Social Media akan wani abu da mun tabbatar matsayar Jagora ne, kuma mun tabbatar Jagora din nan yana tare da ku har a Media din, to k**ar muna gabansa ne muna masa hayaniya da hargowa irin yadda wasu s**a ma Annabi (S) a yayin jinyarsa na ajali. Sai mu kasance cikin tsinuwar Allah Ta'ala. Allah Ya tsare mu.

Mu yi haƙuri, mu yi sa'ayi, mu dinke kanmu, mu daina ganin akwai bangare biyu a Harka, kuma muna ɓangare kaza ne, kowa ya ji Harka abu guda ce, kuma Jagoranta shi ne Sayyid Zakzaky (H), mu so shi, mu ƙaunace shi, mu taimake shi akan Da'awar da yake yi, har mu riski ajali ta hanyar karbabbiyar Shahada insha Allah, ko ta hanyar cikawa da imani.

Wadanda aka ba Mas'uliyyar, duk girmanta da bayyanarta, fata shi ne a yi aiki saboda Allah, k**ar yadda na kawo a sama, mai dafa shayi a Markaz ya ba mutane su sha, ko mai jera takalman masu zuwa Ta'alimi, ko mai hada na'ura, duk suna iya fin Kwamandan Harisawa, ko su fi Amir matsayi da daraja da fifikon lada a wajen Allah Ta'ala. Saboda haka Mas'uliyyar Harka Islamiyya amana ce kawai, Nauyi ne, ba matsayi ba ne. Zai zama matsayi ne ga mutum kawai a Lahira in ya kyautata yinsa. Allah Ya dafa mana.

— Saifullahi M. Kabir
8 Sha'aban 1446
7 February 2025

PRESS RELEASES THURSDAY, FEBRUARY 6,2025Jaish Aliyul Akbar na sanar da dakatar da dukkan ayyukansa a dukkan jihohin da y...
07/02/2025

PRESS RELEASES
THURSDAY, FEBRUARY 6,2025

Jaish Aliyul Akbar na sanar da dakatar da dukkan ayyukansa a dukkan jihohin da yake da su, k**ar su Kaduna, Zariya, Kano, Potiskum, Lafia, Bauchi, da sauran wurare. Wannan mataki ya biyo bayan umarni da nasihohin da Maigirma Sayyid Zakzaky (H) ya bayar yayin ganawarsa da Hurras.

Sak**akon haka, an soke bikin haihuwar Sayyid Aliyul Akbar da aka shirya gudanarwa a ranar 10 ga Fabrairu, 2025, a dukkan sassan ƙasar nan.

Muna nan daram a kan biyayya da jajircewa ga Maigirma Sayyid Zakzaky (H) kuma za mu ci gaba da bin koyarwarsa da umarninsa ba tare da kaucewa ba.

Bugu da ƙari, muna son bayyana cewa duk wani abu da aka gani ko aka ji daga yanzu ba daga Jaish Aliyul Akbar ba ne. AN DAKATAR DA DUK KAN WANI NAU’IN AYYUKANSU.

SIGNED
KWAMITIN GUDANARWA.

Ko da Jagora (H) ya yi magana a kan ƙirƙiro da wasu Jaishoshi da wasu s**a a yi Harka... To hakan ba yana nuni da mu zo ...
06/02/2025

Ko da Jagora (H) ya yi magana a kan ƙirƙiro da wasu Jaishoshi da wasu s**a a yi Harka... To hakan ba yana nuni da mu zo Social Media mu yi ta yaɓa musu maganganu ba ne har mu yi ta furta abun da idan ya gani ba zai ji daɗi ba, su Sayyid suna nufin gyara a inda aka yi kuskure ne, kuma ina da tabbacin waɗanda abun ya shafa sun ji kuma za su gyara. Ba mu ne Jagoransu ba da za mu zo nan mu yi ta maganganu har mu fita daga inda aka yi magana akai ɗin. Yana daga cikin yin ladabi ga Jagora (H) rashin faɗin abubuwan da shi bai faɗa ba.

Allah Ta'ala ya tausaya mana ya kare mana ya kare Jagoranmu ya cika masa burinsa ya sa mu zamo masu yi masa ɗa'a ya barmu tare da shi duniya da lahira.

Sidi Murtadha Kaduna.

Nine Muhammad Qaseem! Sunana Muhammad Qaseem, yaya ga Ahmad, Hameed da karamar kanuwarmu, Fatima. Musibar da ta samemu b...
06/02/2025

Nine Muhammad Qaseem!

Sunana Muhammad Qaseem, yaya ga Ahmad, Hameed da karamar kanuwarmu, Fatima. Musibar da ta samemu bata buyar wa da yawan mutane ba, amma a hakikanin gaskiya, girman musibar ya zarce abubuwan da kuka taba ji da wanda ma baku ji ba.

Kalma guda da za ta fassara rayuwar mu itace 'Bakin ciki'. Mu yaya ne ga wani jajirtaccen bawan Allah mai hangen nesa, sannan dan gwagwarmaya. Shine ya saita muna rayuwa zuwa hanya sahihiya sannan ya doramu akan tafarki ingantacce.

An haifeni ni ne a shekarar 1996, sauran kannena yara ne yan kasa ga shekara ashirin in bayan dayansu. Kaf din rayuwar mahaifinmu ya yita ne akan fada da zalunci, tare da fafatukar neman adalci ga raunana. Wannan hanya ce mai wahala a dabi'a, domin ta kan zo da wahalhalu da kuma musibu, duk da haka mahaifinmu bai karaya ba, ala basiratan ya gwammace haka.

Wannan shine hakikanin rayuwarmu. Mahaifinmu ya rasa kusan komai a wannan fafatukar, a wannan hanyar ya jure wahalhalu iri-iri, k**a daga dauri, azabtarwa da kuma kuncin rayuwa. Ku duba, Mahaifinmu na daure a kurkun Abacha aka haifeni, haka ya jure tsawon lokaci ba tare da yasa dan karamin jinjirin sa a ido ba.

A haka rayuwarmu ta faro, kuma a haka ta cigaba da gudana. A shekarun da muka yi na rayuwa, ban shekara goma tare da mahaifinmu ba. Muna ji muna gani, azzalumai sun yanke tsakaninmu ta karfi da yaji.

Ba zan iya misalta yanda wannan ya cutar da ni ba. Hakan yana man kunci, amma duk da haka idan na tuna yan kananun kannena, sai in rasa ma me zance. Ga Ahmad nan; kanina, wanda ya dauko siffa da kuma basira k**ar mahaifinmu.

Idan ni na jure, Hameed fa, ka tuna da tsananin shakuwa da kulawa da take tsakanin mahaifi da karamin yaron sa wanda bai wuce shekara sha hudu ba. Har yau ina tuna bankwanan mahaifinmu da shi da kanina Hameed, a gabana Baba yake yin ban kwana da karamin yaron sa, wannan yanayi ya tabani ya sosa man rayuwa, na ji k**ar zan yi wafati, na kasa jurewa.

Karamar kanwata fa, Fadima, wadda ta kasance sanyin idon mahaifinmu, wadda tun bayan rasuwar mahafyarmu, ita muke kallo mu tuna mahaifiyar mu, da wata shakuwa ta musamman da ta shiga tsakaninta da Baba, ashe azzalumai gab suke da su raba su.

Azzalumai sun saka mahaifinmu a cikin rayuwa mai tsanani da kunci. Kacokaf din rayuwar, an yi ta ne, kodai ana gidan yari a daure, ko kuma ana kulle a wurin yan sanda. Sun yi masa mummunar illa; kunci na zuciya da raunuka na sanadiyar duka da azabtarwa, ko dayan idonsa su s**a jaza masa samuwar matsala.

A haka mahaifinmu ya shafe shekaru bakwai a gidan yari. Kai kace iya azabar kenan, shekaru hudun bayan haka s**a kara halbeshi, wannan karon a Abuja, a muzaharar neman yancin jagora (H), ana tafiya cikin lumana, s**a saitashi, s**a harbe shi a cinya da harsashi mai guba.

Duk a cikin wahalhalun da mahaifinmu ya sha, wannan ta zama ta daban. Satuttukan da muka yi yana jinya sun kasance kwanaki mafi kunci, sannan sun bar miki a rayuwar mu na har abada.

Yau mahaifinmu ne a kwance, yana jinyar harsashi mai guba da tsananin radadi; gubar ta cigaba da azabtar da shi, kullu-yaumin k**ar ba zai kai safe ba. Wasu lokutan in azabar radadin ciwon ta yi yawa har sai ya suma, yana dadewa bai farfado ba. A irin wannan yanayin ya rayu na sati uku, muna zaune yana shan azabar dafi, amman ba taimakon da za mu iya yi masa. A rayuwata ban taba sani ko kaddara ya ake ji in an shayar da mutum guba mai tsananin dafi ba, sai wadannan kwanakin da na kasance tare da mahaifinmu guba tana galabaitar da shi!

A haka na kasance da shi, cikin tsananin dafin guba; ina kallo ya fara shirin komawa ga Allah, a gabana ya yi numfasawa ta karshe, ina rike da shi a hannuna yake nunmfasawa shedarsa na daukewa, ina tsaye a wurin. Ina kallo. Ina rike da shi sadda yanayin sa ya canza, shedarsa ta canza, ina kallon lokacin da yake shedar fitar rai, na ga sadda ya ja numfashi na karshe.

Daga karshe dai ga ni ga gawar mahaifinmu. Gangar jikinsa a tare da ni amma babu ran, an zare. Wannan ba zai taba goguwa ba daga zukatan mu, tsawon shekaru, watanni musamman wannan sati ukun karshen rayuwar mahaifin namu, wanda na sheda a idanuna, da sadda yake bankwana da kannena su uku, Ahmad, Hameed da kuma karamar kanuwarmu, Fadima, har abada ba zai taba goguwa ba daga zukatan mu.

A bisa haka, godia ga Allah madaukakin sarki wanda ya azurtamu da daya daga cikin nagartattun bayinsa a matsayin uba mahaifi. Mahaifinmu baiyi tafiyar kaico ba, kuma hanyar da ya doramu za mu cigaba da bi har zuwa karshen rayuwa. Biyayya da da'ar mu ta har abada za ta dawwama a gurin shugaba kuma Jagoran gaskiya, Sayyid Zakzaky (H)

Muhammad Qaseem

Al'amarin Hurras: Daga Na Ga Ake Gane Zurfin RuwaBayan duk abubuwan da s**a dinga faruwa tsawon lokaci, kan al'amarin ai...
06/02/2025

Al'amarin Hurras: Daga Na Ga Ake Gane Zurfin Ruwa

Bayan duk abubuwan da s**a dinga faruwa tsawon lokaci, kan al'amarin aikin harisanci, matsalolin harisawa a cikinsu, alaƙar harisawa da sauran ƴan uwa, da kuma uwa-uba alaƙar harisawa da Jagora (H), a jiya Allah ya yi lokaci an yi wa tufkar hanci. An rushe, an sauke, an yi sabbin zubi, an gyara, an ɓata wa wasu shirinsu da sauransu. Misali ni yanzu ba a rusa min komi ba, don dama ni ba memban Hurras bane, ni ba ɗan Jaishun da aka rushe bane, alaƙar ita ce su ƴan uwana ne a addini. A ka yi musu gyara, aka saita su, aka ceto wasu daga cikinsu.

Yanzu tunda ni ba Hurras bane, ba ɗan jaishun bane, shikenan abinda aka yi na rushewa da gyarawa da saitawa bai shafe ni ba kenan? In muka koma baya, zan yi mana tuni, yadda Hurras suke a Harkar nan, yadda aka kallonsu, irin gudunmawar da suke bayarwa, kai, sai da su ka zama babu wata fuskar Harkar nan a wajen wanda ba ɗanta ba k**ar Hurras, kowa ma an dauka Haris ne, an dauka duk Harkar ma harisanci ce. Saboda irin tasirinsu, da abubuwan da suke gudanarwa a lokutan baya.

Yanzu akwai fora (dandamaloli) akwai jaishu masu licence, akwai sauran gasu nan dai. Dama shi al'amari irin wannan ba yadda aka fara bane, ko yadda ake ciki a yanzu bane mafi muhimmanci, yadda za a kare ne mafi muhimmanci. Wannan abinda ya faru da Hurras a yanzu, in ka waiwaya baya ka kalli irin gudunmawar da s**a bayar ya isa ya sa ka dawo cikin hayyacinka, ka dauka gyaran, kai ma har da kai, duk da kai ba Haris bane, dama daga na gaba ake gane zurfin ruwa. Inda su ka samu matsala ka gyara, ko kai ba ɗan wani dandamali bane, inda s**a dace ka dauka, don kuwa basu kaɗai ne za su shiga jarabawa ba, kowa ma a cikinta yake.

Musamman ma dai in kana Harkar uban gida, wato ka dauka akwai wani mutum da in baka rike shi ba a Harkar nan toh k**ar ba ka Harkar ne ma gaba ɗaya, in dai wannan mutumin ba Jagora (H) bane. Wannan ya na daga cikin matsalolin da Hurras s**a faɗa, shi mutumin nan ko wakilin ƴan uwa ne da aka tura shi wani gari, ko kuma wanda ƴan uwan garin s**a wakilta ne da kansu, ko wanda yanayin gudanar da al'amura ne ya samar da shi, duk ɗaya suke, duk wakilai ne na ƴan uwa, duk almajirai ne na Jagora, k**ar yadda ni da kai muke almajiran Jagora. Kiyaye jingina da wani, zai kawar da hatsarin afkawa rudani a lokacin da aka fada cikin yanayin shakku da firgici, irin na waƙi'ar da ta gabata.

Sannan akwai gaɓoɓin da a cikin jawabin Jagora ya nuna mana Harkar nan ba mukami bace, ba wane babban mutum mai matsayi kaza bace, ga fuskancin yi don Allah kuma, ai ba wanda zai ce da Hurras kawai ake yi a nan ko? Ga sauran nasihohi nan dai da duk sun shafe mu. Akwai abin murna a gyara aikin Harisanci, akwai abu mai sosa zuciya, wanda yanzu ya wuce, sai dai mu dau darasi daga gare shi. Kullum yadda nake ƙara fahimtar alkiblar Jagora kenan, akwai wani jawabi da aka taba yi, Jagora ya ce mai fahimta 100 percent namu ne muna tare da shi, har sai da Jagora ya sauko kan 1 percent ya ce shi ma namu ne. Wato dukkan ƴan uwa na Jagora ne, baka da hurumin korar wani daga haular Jagora. Allah ya sa mu dace.

– Baqeer Mohammed Awwal

Address

Saminaka

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mu'asasatu Aliyul Akbar. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mu'asasatu Aliyul Akbar.:

Share