03/05/2026
Pantami ya yi watsi da sasancin da aka yi aka fitar da Jamilu Gwamna takarar Gwamnan jihar Gombe a APC
Wata sanarwa daga bangaren masu goyon bayan Isa Ali Ibrahim Pantami ta bayyana rashin amincewa da abin da s**a kira “nadi” a matsayin consensus domin tsayar da dan takarar Gwamna a jihar Gombe, tana mai cewa hakan ya saba da tanadin dokar zabe ta Nijeriya.
Sanarwar da aka wallafa a shafin Pantamin na Facebook, ta jaddada cewa babu sahihin sasancin consensus sai idan dukkan masu neman takara sun amince a rubuce su janye, idan ba haka ba dole ne jam’iyya ta koma zaben fidda gwani kai tsaye.