Ni'ima online tv

Ni'ima online tv Tashar dake shirye shirye da harshen Hausa tana zaune a Nigeria

16/10/2025
Shugaban gidan talabijin na hausa7 tv ya nada sirajo garba amatsayin director general a jamhuriyar niger
15/10/2025

Shugaban gidan talabijin na hausa7 tv ya nada sirajo garba amatsayin director general a jamhuriyar niger

DA DUMI-DUMI: Wata ‘yar Amurka ta rasu a Najeriya yayin da ta kawo wa saurayinta ziyaraDaga NI'IMA tv Wata mata ‘yar ƙas...
30/09/2025

DA DUMI-DUMI: Wata ‘yar Amurka ta rasu a Najeriya yayin da ta kawo wa saurayinta ziyara

Daga NI'IMA tv

Wata mata ‘yar ƙasar Amurka mai suna Jacqueline Bolling Elton, mai shekara 60, ta rasu a garin Warri dake Jihar Delta, yayin da take ziyara wurin abokinta ko saurayin ta, Alawode Olaide, mai shekara 39.

Rahotanni sun bayyana cewa Elton ta isa Warri ne a ranar 15 ga Satumba, amma a ranar 29 ga watan, da misalin ƙarfe 3:00 na rana, kwatsam ta fara rashin lafiya. NI'IMA tv ta ruwaito an garzaya da ita zuwa wani asibiti dake Otokutu, daga bisani aka tura ta zuwa Asibitin Gwamnati na Warri, inda likitoci s**a tabbatar da ta mutu tun kafin a kai ta asibitin.

Hukumomi sun shiga lamarin tare da k**a Olaide domin bincike.

FOLLOW NI'IMA TV page for more hausa stories

Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Nasarawa, kuma tsohon Ministan Birnin Tarayya (FCT), Sanata Solomon Ewuga ya riga gidan ...
24/09/2025

Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Nasarawa, kuma tsohon Ministan Birnin Tarayya (FCT), Sanata Solomon Ewuga ya riga gidan gaskiya.

Ya rasu ne a ranar Talata bayan fama da rashin lafiya.

Da dumi'dumi: Hukumar DSS ta Gayyaci Malami SAN domin Amsa Tambayoyi.Tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a ...
22/09/2025

Da dumi'dumi: Hukumar DSS ta Gayyaci Malami SAN domin Amsa Tambayoyi.

Tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a na Najeriya, Abubakar Malami (SAN), ya tabbatar da cewa Hukumar Tsaro ta DSS ta gayyace shi domin yi masa tambayoyi kan binciken harin da aka kai masa da tawagarsa a Jihar Kebbi ranar 1 ga Satumba, 2025.

Malami ya bayyana cewa binciken na DSS yana da nasaba da wata korafi da wasu fitattun ‘yan siyasa na jihar s**a shigar.

Ya kuma yaba wa DSS bisa yadda take gudanar da binciken cikin kwarewa da gaskiya, tare da bayyana aniyarsa ta ci gaba da ba da hadin kai domin a kammala binciken cikin nasara.

following
'IMA tv domin samun labarai ciki da wajen gida

DA DUMI-DUMI: FAAC ta raba mafi girman kudin shiga a tarihin Najeriya: Naira Tiriliyan 2.225 a watan AgustaDaga Ayau New...
18/09/2025

DA DUMI-DUMI: FAAC ta raba mafi girman kudin shiga a tarihin Najeriya: Naira Tiriliyan 2.225 a watan Agusta

Daga Ayau News

Kwamitin Raba Kudaden Shigar Tarayya (FAAC) ya raba Naira tiriliyan 2.225 ga gwamnatin tarayya, jihohi da kananan hukumomi a watan Agusta 2025 wanda shine mafi girma a tarihin kasar

Ayau News ta ruwaito bayanai sun nuna wannan shi ne karo na biyu a jere da aka wuce Naira tiriliyan 2 a rabon kudaden FAAC, a zamanin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Kudin sun karu ne sak**akon harajin mai da gas, VAT da kuma kudaden CET.

Daga cikin rabon:

Gwamnatin Tarayya ta samu N684.4bn daga kudaden haraji, jihohi sun sami N347.1bn, Kananan hukumomi kuma sun samu N267.6bn, yayin da jihohin da ke samar da mai s**a karɓi N179.3bn a matsayin kason 13%.

Daga VAT N672.9bn, Tarayya ta samu N100.9bn, jihohi N336.4bn, Kananan hukumomi N235.5bn.

Haka kuma, an raba kudaden EMTL da bambancin musayar kudin kasashen waje.

FAAC ta ce jimillar kudaden shiga na watan ya kai N3.635trn, inda aka cire wasu kuɗaɗe na ayyuka, ajiya da tallafi kafin rabawa.

Shin kuna gani a kasa kuwa?

Follow us => # 'IMA TV

12/09/2025

Shirin muleka mugano tareda chairman na kasuwar sidi

DA DUMI-DUMI: Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris Kauran Gwandu ya dakatar da Kwamishinan Kiwon Lafiya, Comrade Yunusa Isma...
11/09/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris Kauran Gwandu ya dakatar da Kwamishinan Kiwon Lafiya, Comrade Yunusa Isma’il bayan bullar bidiyon Asibitin Jihar Kebbi dake fama da ambaliya.

Me zaku ce?

Ƙungiyar Matasan Arewa ta nemi a ɗauki mataki akan Sanata Shehu Buba kan zargin sa da hannu a ta'addanciƘungiyar Ci-gaba...
06/09/2025

Ƙungiyar Matasan Arewa ta nemi a ɗauki mataki akan Sanata Shehu Buba kan zargin sa da hannu a ta'addanci

Ƙungiyar Ci-gaban Matasan Arewa AYM, ta kirayi Sufeto-Janar na ƴan sanda (IGP) da ya gaggauta ɗaukar matakin doka akan Sanatan Bauchi ta Kudu, Shehu Umar Buba, bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta'addanci a garuruwan Arewacin Nijeriya.

A wata takarda da ke ɗauke da sanya hannun Kakakinta, Kwamared Yahaya Muhammed Garba, AYM ta bayyana kaɗuwarta game da ƙamarin ayyukan ta'addanci da ke ƙoƙarin mamaye shiyyar ganin yadda ake rasa rayukan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba a kullum.

Ta ce, ƙalubalen da al'umma ke fuskanta a sanadiyyar ayyukan ƴan bindiga da ɓarayin daji na garkuwa da ta'addanci akan dukiyoyinsu ya zama ruwan dare a sassan jihohin ƙasar, lamarin da ya ɗaiɗaita mutane da dama daga muhallansu da jefa su cikin tsoro.

A cewarta, hakan ya yi mummunan tasiri ga haɗin kan al'umma da tattalin arziƙi, wanda ya jefa iyalai da dama cikin matsi akan matsin da suke fuskanta sak**akon taɓarɓarewar harkokin tattali a ƙasar.

Ta ƙara da cewa, ayyukan garkuwa da mutane da neman a biya kuɗaɗen fansa ya zama babban kasuwanci ga masu aikata manyan laifuka, saboda amfani da hakan wajen harin mutane da ɓangarorin daban-daban wanda ya zama sababin ɗaiɗaita dubunnan mutane da iyalansu.

Har'ilayau AYM ta yi tsokaci da jinjina akan matakan da Gwamnatin Tarayya ke ɗauka wajen ganin tsaro mai ɗorewa ya samu a shiyyar da s**a haɗa da ƙara jami'an sojoji da ƴan sanda da sauransu a wuraren da ke fama da rashin tsaro.

Saidai, AYM ta bayyana ayyukan ire-iren Sanata Shehu Buba a matsayin abinda ka iya daƙile ƙoƙarin gwamnati na kawo ƙarshen matsalar.

A kwanan nan aka ga wani faifan bidiyo yana nuna kuɗaɗe da babura da aka tura daga gidan Sanatan zuwa wajen ƴan bindiga a Zamfara, lamarin da ke ƙoƙarin tabbatar da zargi akansa da hannu a ayyukan ta'addanci a shiyyar, k**ar yadda sanarwar ta bayyana.

DA DUMI-DUMI: Gwmanan jihar Niger, Mohammed Umaru Bago ya sauke duka kwamishinoninsa da masu bashi shawaraMe kuke fata?
01/09/2025

DA DUMI-DUMI: Gwmanan jihar Niger, Mohammed Umaru Bago ya sauke duka kwamishinoninsa da masu bashi shawara

Me kuke fata?

19/08/2025

A jihar kebbi gidan talabijin na NI'IMA TV sun karrama hon shehu Muhammad wamban Koko da lambar yabo mai daraja

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ni'ima online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ni'ima online tv:

Share