Ni'ima online tv

Ni'ima online tv Tashar dake shirye shirye da harshen Hausa tana zaune a Nigeria

Yanzu yanzu a jamhoriyar Niger ankama wani mutum mai shigar aljannu kuma yana buga jabun kuddi
11/07/2025

Yanzu yanzu a jamhoriyar Niger ankama wani mutum mai shigar aljannu kuma yana buga jabun kuddi

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir Lawal, ya bayyana a hukumance cewa ya fice daga jam’iyyar APC.Lawal, ...
08/07/2025

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir Lawal, ya bayyana a hukumance cewa ya fice daga jam’iyyar APC.

Lawal, wanda ya yi aiki a matsayin SGF a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a zangon mulkinsa na farko, ya sanar da wannan mataki ne cikin wata wasika mai kwanan wata 29 ga Yuni, 2025, wacce ya aike wa shugaban jam’iyyar APC na mazabarsa ta Bangshika, a ƙaramar hukumar Hong, Jihar Adamawa.

Gwamnatin Tinubu zatayi taro da masu ruwa da tsaki akan rage farashin litar man feturHaka bai faru ba sai da s**a ga an ...
04/07/2025

Gwamnatin Tinubu zatayi taro da masu ruwa da tsaki akan rage farashin litar man fetur

Haka bai faru ba sai da s**a ga an fara hadakar siyasa da zata kawo karshen mulkinsu a 2027, kuma talakawa sun karbi tafiyar na hadakar siyasa

Dama suna sane, sun san cewa cire tallafin mai da s**ayi shine abinda ya jefa mu cikin bala'i na tsadar rayuwa, to yanzu sun fara shirin sassauta mana

Jama'a kuna ganin mutanen nan abin yarda ne ba yaudaran mu zasuyi da rage farashin man fetur ba domin su zarce?

Harin yau da Iran takaiwa Kasar Israel ya haifar da
19/06/2025

Harin yau da Iran takaiwa Kasar Israel ya haifar da

07/06/2025

Yanda yan mata keyin kwalliya da ado a ranar jajibirin sallah

17/05/2025

YANZU YANZU: Yan Bindiga Sun kusa k@she Ni a jihar Kaduna Allah ya tseratar dani, inji Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma wanda ya kafa Jami’ar American University of Nigeria (AUN), Atiku Abubakar, ya bayyana yadda ya tsira daga yunkurin kashe shi a Jihar Kaduna.

Atiku ya ce ya ɓoye matarsa da ’ya’yansa a cikin kabad (wardrobe), inda ya fuskanci waɗanda s**a zo su kashe shi. Ya bayyana cewa sun harbe shi amma harsashensu bai same shi ba.

Ya bayyana haka ne a yayin da yake jawabi ga daliban da ke kammala karatu a AUN a ajin 2025.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP ya kuma tuna yadda gwamnatin soja a wani lokaci ta ba shi kujerar gwamna ba tare da an yi zaɓe ba.

Ya ce ya ƙi karɓar tayin, amma daga baya ya samu kujerar mataimakin shugaban ƙasa a shekarar 1999 ta hanyar da ta dace.

A cewarsa:

> “Na ɓoye matata da ’ya’yana a cikin kabad, sai na fito na fuskanci waɗanda s**a shigo. Sun harbe ni amma s**a ci kuskure. Na tashi na ce, ‘Me ya sa kuka harba?’ Wannan shi ne jarumta.

> “Na fuskanci ƙalubale da dama. An far wa rayuwata, amma ban taɓa ja da baya ba.

> “Haƙuri ba rauni ba ne. Makamin masu hikima ne. A lokacin da muke adawa da mulkin soja, sun ba ni kujerar gwamna ba tare da zaɓe ba, na ƙi karɓa. Amma a 1999, na samu ta halastacciyar hanya kuma na zama Mataimakin Shugaban Ƙasa.”

Ya kuma tuna yadda ya koyi jarumta daga ubangidansa, marigayi Janar Shehu Musa Yar’Adua, wanda ya fuskanci hukuncin kisa ba tare da tsoro ba.

> “Ranar da aka shirya kashe shi, jinin sa yana daidai. Wannan soja ne. Wannan shi ne jarumta,” in ji Atiku.

DA DUMI DUMI: Bola Tinubu ya roƙe Ni kan cewa na koma jam'iyyar Apc Amma na faɗa Masa cewa dana koma APC gara Na Haƙura ...
16/05/2025

DA DUMI DUMI: Bola Tinubu ya roƙe Ni kan cewa na koma jam'iyyar Apc Amma na faɗa Masa cewa dana koma APC gara Na Haƙura da Siyasa gaba ɗaya—Kwankwaso

A safiyar yau tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya fito ƙarara ya yi watsi da labaran komawarsa APC da ake ta yaɗawa inda yace,

"Babu shakka Tinubu ya roƙe ni da in dawo kuma duk condition ɗin da nake so za a bi don in dawo APC amma naƙi amsa tayin sa kuma ba zan koma ba saboda gara in bar siyasa da in sake komawa APC, batun zaɓen 2027 kuma zamu ƙirƙiro tafiya mai ƙarfin gaske da zata kawar da mulkin APC" in ji shi

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Wakiliya 👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

15/05/2025

Commissioner jin dadi da walwala ulumar jihar sokoto ta tace sunyi kyakkyawan Shiri Don inganta rayuwar masu lalura ta musamman

14/05/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Dan Arewa Ontop, Balarabe Umar Shagari

12/05/2025

Tattaunawa da commissioner na lafiya jihar sokoto akan cigaban da gwamnati ta samar a bangaren su

Kwamishina ya mayar da Naira miliyan 301 ragowar kuɗin ciyarwar azumi a Jigawa Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar J...
07/05/2025

Kwamishina ya mayar da Naira miliyan 301 ragowar kuɗin ciyarwar azumi a Jigawa

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Auwalu Danladi Sankara, ya mayarwa baitul malin jihar Naira miliyan 301 da su ka yi ragowa bayan kammala shirin ciyarwa na watan Ramadan bana.

Sankara ya sanar da mayar da kudaden ne a yayin taron majalisar zartarwa na jiha wanda gwamna Malam Umar Namadi ya jagoranta.

Kudin sun yi ragowa ne biyo bayan ware naira biliyan 4.8 da gwamnatin jihar Jigawa ta baiwa ma’aikatar don shirin ciyar da abinci, wanda ya kunshi dukkanin kananan hukumomi 27 da kuma cibiyoyi kusan 700 na ciyarwa.

An ba da rahoton cewa, shirin wanda wani kwamiti ya jagoranta, ya ciyar da mutane sama da 5,550 a kullum a tsawon kwanaki 29 na azumi.

Majalisar zartaswar jihar ta yaba wa matakin da kwamishinan Sankara ya dauka na dawo da ragowar kuɗin, inda ta bayyana hakan a matsayin wani abin yabawa da nuna gaskiya da rikon amana da kuma tattalin dukiyar al'umma.

25/09/2023

Shugaban kungiyar makarantu masu zaman kansu yayi kira ga iyayen yara dasu gaggauta maida yaransu makaranta cikin lokaci don daukar darasi

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ni'ima online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ni'ima online tv:

Share