Ina Muka Dosa

Ina Muka Dosa Kafar Watsa Labarai Dake Kawo Maku Labaran Cikin Gida Nigeria Harma Da Ketare. Muna Tallata Hajojinku Cikin Sauki Da Rahusa. Neman Karin Bayani 09036485281

ANGO YA FASA AURE SABODA AN YIWA AMARYA LALLE A BAYANTAWani ango ya janye daga yin aure bayan ya gano cewa an yi wa amar...
01/09/2026

ANGO YA FASA AURE SABODA AN YIWA AMARYA LALLE A BAYANTA

Wani ango ya janye daga yin aure bayan ya gano cewa an yi wa amaryarsa lalle a bayanta kafin ranar aurensu.

Rahotanni sun ce matar da ta yi mata lallen ce ta dauki bidiyon yadda aka yi lallen, sannan ta wallafa bidiyon a shafukan sada zumunta, lamarin da ya sa bidiyon ya bazu sosai.

Bayan ango ya ga bidiyon, rahotanni sun ce hakan ya jawo ce-ce-ku-ce tare da kai ga matakin da ya yanke shawarar fasa auren.

Lamarin ya jawo martani daban-daban daga jama'a a kafafen sada zumunta, inda wasu ke ganin bai k**ata a yada irin wannan bidiyo ba ba tare da la'akari da abin da zai iya haifarwa ba.

A ra'ayinku, shin ango ya yi daidai da ya fasa auren saboda wannan dalili?

01/09/2026

Ga yadda aikin hanyar Abuja–Kaduna da ake yi da kankare ke ci gaba da gudana. 🚧🛣️ Ana sa ran aikin zai inganta zirga-zirga tare da samar da hanya mai ɗorewa ga masu amfani da ita.

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin sama wa ƙwararrun ’yan Nijeriya aiki a ƙasashen wajeGwamnatin Tarayya ta ƙaddama...
01/09/2026

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin sama wa ƙwararrun ’yan Nijeriya aiki a ƙasashen waje
Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da wani shiri mai suna “Hire from Nigeria” (wato 'A ɗauki ma'aikata daga Nijeriya') domin bai wa ’yan ƙasar nan damar yi wa kamfanoni da masu ɗaukar ma’aikata na ƙasashen waje aiki.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wani taron manema labarai da aka yi a ofishin sa a Abuja.

Ya ce: “Ƙaddamar da wannan shiri wani muhimmin mataki ne a ƙoƙarin da Nijeriya take yi na sanya ɗaya daga cikin manyan kadarorin ƙasar mu, wato mutanen mu, a sahun gaba wajen hulɗar tattalin arzikin mu da duniya.”

Ya ce yawan matasan Nijeriya, da ɗimbin ƙwararrun ma’aikatan ta da kuma bunƙasar fasahar zamani sun ba ƙasar damar yin gogayya da sauran ƙasashe a fagen tattalin arzikin duniya.

Idris ya ce: “Makomar tattalin arzikin Nijeriya za ta ƙara dogara ne kan ƙwarewa, ƙirƙire-ƙirƙire, fasaha da kuma ƙwazon jama’ar mu. A shirye Nijeriya take ta yi gogayya a fagen duniya. A shirye ƙwararrun ’yan Nijeriya suke su yi aiki, kuma ya k**ata duniya ta mayar da hankali kan Nijeriya."

Ya ƙara da cewa gangamin ya haɗa ma’aikatun tarayya na Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari da na Ilimi, NATEP, iDICE da kamfanoni masu zaman kan su domin haɗa ƙwararrun ’yan Nijeriya da masu neman ƙwararrun ma’aikata a duniya.

Ya ce shirin ya yi daidai da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma burin Gwamnatin Tarayya na samar da guraben aiki miliyan ɗaya ta hanyar fitar da ayyuka zuwa ƙasashen waje.

“Ba sai matashi ɗan Nijeriya ya bar ƙasar ba kafin ya samu damar shiga harkokin tattalin arzikin duniya. Idan aka ba shi ƙwarewar da ta dace, ababen more rayuwa, ƙa’idojin sana’a da damar shiga kasuwanni, ’yan Nijeriya za su iya rayuwa, su yi aiki kuma su samu kuɗi a nan gida, yayin da suke samar da ayyuka ga abokan ciniki da masu ɗaukar ma’aikata a faɗin duniya,” inji shi.

Shi kuma Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa, ya ce ma’aikatar sa tana inganta ƙwarewar ’yan Nijeriya ta hanyar inganta tsarin koyarwa, koyar da sana’o’i da dabarun fasahar zamani, da kuma horar da su bisa buƙatun masana’antu.

“Manufar Ma’aikatar Ilimi ita ce, a duk inda ake neman ma’aikata a duniya, muna son ’yan Nijeriya su samu horo, su samu takardar shaidar ƙwarewa kuma su kasance a shirye don a ɗauke su aiki,” inji shi.

A nata ɓangaren, Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Jumoke Oduwole, ta ce gangamin zai taimaka wajen samar da ayyukan yi ga matasan Nijeriya, da ƙara fitar da ayyuka zuwa ƙasashen waje da jawo zuba jari.

“Shirin ‘Hire from Nigeria’ ya wuce kamfen na wayar da kai kawai; shiri ne na ƙasa da aka tsara domin bunƙasa tattalin arziki,” inji Oduwole.

Ta ce za a gabatar da kamfen ɗin a taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 81, inda Nijeriya za ta bayyana fa’idar ɗaukar ’yan Nijeriya aiki ga masu ɗaukar ma’aikata na duniya.

Tun da farko, Babbar Mataimakiya ta Musamman kan Sadarwa ta Dabaru da NATEP, Misis Olajumoke Dan-Okayi, ta ce shirin zai magance matsalolin da ke hana ƙwararrun ’yan Nijeriya samun damar aiki a duniya.

Ta ce: “Ba ƙwarewa ce matsalar ba, kuma ba buri ba ne. Matsalar ita ce yadda za a gano ƙwararrun ’yan Nijeriya, amincewa da su da kuma samun damar shiga kasuwannin duniya. Don haka, shirin ‘Hire from Nigeria’ yana da ayyuka uku masu sauƙi: ya sauƙaƙa wa duniya gano Nijeriya, ya sauƙaƙa amincewa da ƙwararrun ’yan Nijeriya, sannan ya sauƙaƙa ɗaukar ’yan Nijeriya aiki.”

Ana sa ran kamfen ɗin zai haɗa ƙwararrun ’yan Nijeriya da masu ɗaukar ma’aikata, kamfanoni masu neman ma’aikata, masu zuba jari da kasuwannin ƙasashen waje.

TSOHUWA TA TAYA JIKARTA MURNAR KAMMALA KARATU A UNIJOSWata tsohuwa ta bayyana matukar farin cikinta yayin da ta tsaya a ...
31/08/2026

TSOHUWA TA TAYA JIKARTA MURNAR KAMMALA KARATU A UNIJOS

Wata tsohuwa ta bayyana matukar farin cikinta yayin da ta tsaya a gefen jikarta, Jessica Akutse Moses, domin taya ta murnar kammala karatun digirin farko a fannin Zoology a Jami’ar Jos, wato UNIJOS.

Lamarin ya kasance mai cike da farin ciki da tarihi, yayin da kakar ta nuna irin kauna da alfaharin da take ji game da wannan gagarumar nasarar da jikarta ta samu a fagen ilimi.

Wannan ba wai nasarar Jessica kadai ba ce, nasara ce ga iyali baki daya, Bayan shekaru na karatu, jajircewa da sadaukarwa, ta kai ga wannan matsayi, in jita.

Labarin da Ake yadawa akan Dakatar Da Ayukkan Opay Labarin kanzon kurege ne Bai da asali Bala'i tushe.
31/08/2026

Labarin da Ake yadawa akan Dakatar Da Ayukkan Opay Labarin kanzon kurege ne Bai da asali Bala'i tushe.

Shettima ya dawo gida bayan wakiltar shugaba Tinibu a Taron (AU)Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shetti...
31/08/2026

Shettima ya dawo gida bayan wakiltar shugaba Tinibu a Taron (AU)

Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya isa Abuja bayan ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron Zama na 21 na Musamman na Majalisar Shugabannin Kasashe da Gwamnatocin Tarayyar Afirka (AU) da aka gudanar a Angola.

Shettima ya bayyana cewa Najeriya na ci gaba da jajircewa wajen warware duk wata matsala da ke tsakaninta da Afirka ta Kudu ta hanyar tattaunawa da zaman lafiya, amma kasar ba za ta yi shiru ba idan aka barazana ga mutunci da tsaron 'yan Najeriya.

Ya kuma yi kakkausar magana kan yadda ake mu'amala da wasu 'yan Najeriya a Afirka ta Kudu, inda ya tunatar da cewa Najeriya ta taka muhimmiyar rawa wajen yakar wariyar launin fata da kuma gwagwarmayar 'yantar da 'yan uwansu a Kudancin Afirka.

“Wadanda aka fasa musu dabino da taimakon ruhohi masu alheri ya k**ata su koyi tawali’u.”

Shettima ya ce abin yana masa matukar ciwo ganin yadda ake k**a wasu 'yan Najeriya tare da wulakanta su, yana mai jaddada cewa Najeriya za ta ci gaba da kare mutunci da hakkokin 'yan kasarta a duk inda suke.

Daga Ashir Mai Jama'a Sokoto

Wasu Daga Cikin Dabbobin Da S**a Dawo Gida Bayan Fafatawa Da ‘Yan Bîndîgå a tureta.Wasu daga cikin dabbobin da ‘yan bîñd...
31/08/2026

Wasu Daga Cikin Dabbobin Da S**a Dawo Gida Bayan Fafatawa Da ‘Yan Bîndîgå a tureta.

Wasu daga cikin dabbobin da ‘yan bîñdîgâ s**a yi awon gaba da su sun dawo gida, bayan jami’an tsaronmu sun fatattaki ‘yan biñdigar tare da yin bata-kashi da su a jiya, a yankin da ke tsakanin Lambar Tureta da Tureta gari.

Rahotanni sun nuna cewa yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da gudanar da ayyukansu na kare al’umma da dukiyoyinsu, wasu daga cikin dabbobin sun samu damar komawa wajen masu su, Kamar yadda Wani Dan asalin Yankin Kabeer Tureta ya Tabbatar.

Muna rokon Allah Ya ƙara bai wa jami’an tsaronmu nasara, Ya ƙarfafa musu guiwa, Ya kare su daga dukkan sharri, tare da kawo ƙarshen ayyukan 'yan ta'âddã.

Rubutawa ✍️✍️
Ashir Mai Jama'a Sokoto
Litinin 31, August, 2026

ABIN TAKAICI: Wata Budurwa Ta Haifi Jariri Ita Kaɗai A Gefen Hanya A BiuWata budurwa ta haifi ɗa namiji ita kaɗai a kan ...
30/08/2026

ABIN TAKAICI: Wata Budurwa Ta Haifi Jariri Ita Kaɗai A Gefen Hanya A Biu

Wata budurwa ta haifi ɗa namiji ita kaɗai a kan titin Dibiro Hotel da ke garin Biu, Jihar Borno, a safiyar yau, Lahadi, 30 ga Agusta 2026.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne dab da lokacin Sallar Asuba, yayin da budurwar ke fama da nakuda ita kaɗai a gefen hanya.
Wasu bayin Allah da s**a fito domin zuwa Sallar Asuba ne s**a gan ta cikin wannan hali, inda s**a garzaya domin taimaka mata.

Sai dai daga bisani ta samu nasarar haihuwa, inda ta haifi santalelen ɗa namiji. Daga nan ne aka taimaka aka kai ta wurin ’yan sanda, inda ake ci gaba da bincike domin gano cikakken bayani game da abin da ya faru.

An kuma bayyana cewa budurwar ’yar garin Damchoba ce, sai dai har yanzu ba a bayyana cikakken dalilin da ya sa ta tsinci kanta a wannan hali ba.

Ina Muka Dosa

Minista Idris ya yi jimamin rasuwar Shugaban Hukumar Ƙidaya, Aminu WushishiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji...
28/08/2026

Minista Idris ya yi jimamin rasuwar Shugaban Hukumar Ƙidaya, Aminu Wushishi

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana matuƙar kaduwa da alhini kan rasuwar Shugaban Hukumar Ƙidaya ta Kasa (NPC), Dakta Aminu Yusuf Wushishi, Talban Wushishi.

A cikin wata sanarwa da Mataimakin sa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabi'u Ibrahim, ya fitar, Ministan ya ce: “Na samu labarin rasuwar Dakta Aminu Yusuf Wushishi cikin tsananin baƙin ciki. Rasuwar sa babban rashi ne ga Hukumar Kidaya ta Kasa, ma’aikatan gwamnati da ƙasa baki ɗaya.”

Marigayi Shugaban Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC), Dakta Aminu Wushishi

Idris ya bayyana marigayin a matsayin abokin sa na ƙut-da-ƙut kuma ma’aikacin gwamnati mai kishin ƙasa, wanda jajircewar sa wajen cigaban ƙasa ta bayyana a cikin ɗan gajeren lokacin da ya yi a hukumar.

Ya ce Dakta Wushishi ya fara aikin sa da kyakkyawar manufa ta gudanar da sahihiyar ƙidayar jama’a da gidaje wadda za a yi amfani da fasahar zamani wajen gudanar da ita, domin samar da ingantattun bayanai da za su taimaka wajen tsara manufofin ƙasa.

Ya ce wannan batu na daga cikin muhimman abubuwan da ya sanya a gaba tun bayan k**a aikin sa.

“Shirin sa da jajircewar sa na gudanar da sahihiyar ƙidayar jama’a da za a yi amfani da fasahar zamani wajen gudanar da ita, sun nuna irin nauyin da yake ji na alhakin ƙasa da kuma ƙudirin da yake da shi na barin gagarumar gudunmawa mai ɗorewa ga ci gaban Najeriya,” inji shi.

Idris ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Jihar Neja, da kuma ɗaukacin al’ummar Wushishi, inda marigayin ya riƙe babbar sarautar gargajiya ta Talban Wushishi.

Ministan ya miƙa ta’aziyyar sa ga iyalan marigayin, abokan aikin sa, abokan sa da ma’aikatan Hukumar Ƙidaya ta Kasa, yana addu’ar Allah ya ba su ƙarfin jure wannan babban rashi.

Ya roƙi Allah ya gafarta wa marigayin kurakuran sa, ya sanya shi cikin Aljannatul Firdausi, sannan ya ba duk waɗanda ke alhinin rasuwar sa haƙurin jure wannan babban rashi.

Gwamnatin Tarayya ta goyi bayan tsarin cigaban Taraba, ta yi alƙawarin ƙarfafa haɗin gwiwaGwamnatin Tarayya ta sake jadd...
28/08/2026

Gwamnatin Tarayya ta goyi bayan tsarin cigaban Taraba, ta yi alƙawarin ƙarfafa haɗin gwiwa

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyar ta ta yin aiki tare da Gwamnatin Jihar Taraba wajen amfani da damar da jihar take da ita a fannonin noma, mak**ashi, yawon buɗe ido, ababen more rayuwa da albarkatun ma’adinai.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Jalingo, a wurin bikin cika shekara 35 da kafa Jihar Taraba da kuma ƙaddamar da Babban Tsarin Cigaban Yankin Taraba.

Idris, wanda ya isar da gaisuwar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Majalisar Zartarwa ta Tarayya ga gwamnati da al’ummar Taraba, ya bayyana Babban Tsarin a matsayin muhimmin tsari na cigaban jihar mai ɗorewa.

Ya yaba wa Gwamna Agbu Kefas kan ɗaukar tsarin cigaba na dogon lokaci, yana mai cewa nasarar tsarin za ta dogara ne da ci gaba da aiwatar da shi da kuma irin tasirin da zai yi ga rayuwar jama’a.

Ya ce: “Ba za a auna nasarar wannan Babban Tsari da bikin ƙaddamar da shi ba, sai dai da hanyoyin da aka gina, sana’o’in da aka samar, ayyukan yi da aka samar, al’ummomin da aka haɗa da juna da kuma rayukan jama’a da aka inganta.”

Idris ya bayyana Taraba a matsayin ɗaya daga cikin jihohin Nijeriya da ke da babbar damar bunƙasa tattalin arziki, yana mai nuni da damar da jihar ke da ita a noma da sarrafa amfanin gona, kiwo, samar da wutar lantarki daga ruwa, yawon buɗe ido, masana’antu da albarkatun ma’adinai.

Ya yi nuni da yarjejeniyoyin samar da kuɗaɗen ayyuka da s**a kai kusan dala miliyan 268 da Jihar Taraba ta ƙulla da Bankin Zuba Jari da Bunƙasa Tattalin Arzikin ECOWAS domin gina wani katafaren yankin masana’antu, noman shinkafa ta hanyar ban-ruwa da sarrafa ta a fili mai girman hekta 10,000, da kuma gina tashar samar da wutar lantarki ta hasken rana mai ƙarfin megawat 50 a Jalingo.

Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya tana tallafa wa ƙoƙarin jihar na samun cigaba ta hanyar manyan ayyukan ababen more rayuwa da take gudanarwa, ciki har da hanyar Gembu–Mbamnga–Yang (Lip), hanyar Bali–Serti–Gashaka–Gembu, ayyuka a kan hanyar Jalingo–Mutum Biyu–Tella–Wukari, da kuma aikin hanyoyin Mayo Selbe–Gembu, Mutum Biyu–Garba Chede da Jalingo–Numan.

“Waɗannan ba hanyoyi kawai ba ne. Zuba jari ne a haɗa al’ummomi, kasuwanci, yawon buɗe ido, noma, tsaro da zirga-zirgar mutane da kayayyaki,” inji shi.

Dangane da tsaro, Idris ya ce Gwamnatin Tarayya tana ci gaba da sauye-sauye domin kafa rundunar ’yan sandan jihohi, da nufin kusantar da aikin ’yan sanda ga al’umma, tare da tabbatar da ƙwarewa, ɗaukar alhaki da kuma kare jama’a daga cin zarafi.

Ya kuma ambaci kafa Rundunar Sojojin Nijeriya ta 10 da ke da hedikwata a Jalingo kuma yake da alhakin gudanar da ayyukan tsaro a Taraba da Adamawa, a matsayin wata shaida ta ƙudirin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa tsaro a yankin.

“Dole ne tsaro da cigaba su tafi tare. Mutane ba za su zuba jari ba, manoma ba za su kai amfanin gonakin su kasuwa ba, masu yawon buɗe ido ba za su zo ba, sannan kasuwanci ba zai bunƙasa ba idan al’umma ba ta da tsaro,” inji Idris.

Ministan ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa tushen kuɗaɗen gwamnati, yana mai cewa cire tallafin man fetur ya samar wa Tarayya ƙarin kuɗi har naira tiriliyan 15.8 tsakanin Yuni 2023 da Disamba 2025.

A cewar sa, kusan ₦5.4 tiriliyan ne Gwamnatin Tarayya ta samu, yayin da kusan ₦10.4 tiriliyan s**a tafi jihohi da ƙananan hukumomi, lamarin da ya samar da ƙarin kuɗaɗen gudanar da ayyukan ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, tsaro da bunƙasa ƙwarewar jama’a.

Idris ya yi alƙawarin ƙara haɗin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Sake Wayar da Kai ta Jihar Taraba, domin tabbatar da cewa jama’a sun fahimci manufofin Babban Tsarin kuma sun rungume su.

“Dole ne hangen nesan da ke cikin wannan Babban Tsari ya wuce ofisoshin gwamnati. Dole ne ya isa ga manomi, ɗan kasuwa, ɗalibi, mai saye da sayarwa da al’ummomi a faɗin Taraba, domin tsarin cigaban Taraba dole ne ya zama tsari ne na dukkan mutanen Taraba,” inji shi.

Gwamna Kefas, a nasa jawabin, ya yi kira da a tabbatar da ci gaba da tafiyar da gwamnati ba tare da katsewa ba, yana mai cewa gwamnatin sa za ta gina kan nasarorin da aka samu a baya, ta gyara abubuwan da ke buƙatar gyara, ta kammala ayyukan da s**a dace kuma ta buɗe sababbin hanyoyin cigaba ga al’ummomin da za su zo nan gaba.

“Gwamnati tafiya ce da ba ta yankewa. Cigaba kuma yana ginuwa ne a kan abin da aka riga aka samu. Taraba ta fi kowace gwamnati, kowace hukuma, kowace jam’iyyar siyasa, kowace ƙabila ko mutum ɗaya girma,” inji shi.

Kefas ya yi kira ga tsofaffin shugabannin jihar da su ci gaba da bayar da gudunmawar su ta hanyar amfani da ƙwarewar su da ilimin da s**a samu a harkokin gwamnati wajen samar da zaman lafiya, haɗin kai da cigaban jihar.

Taron ya samu halartar tsohon Gwamnan Taraba, Rev. Jolly Nyame; Sakataren Gwamnatin Jihar, Cif G.T. Kataps; Darakta-Janar na Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA), Salihu Abdulhamid Dembos; Darakta-Janar na Hukumar Rediyon Tarayya ta Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; Manajan Darakta na Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), Dakta Abubakar Dantsoho; da sauran manyan baƙi.

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ina Muka Dosa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ina Muka Dosa:

Shortcuts

Share