08/09/2025
Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayayyakin kiwon lafiya na mata masu juna biyu da jarirai kyauta har na Naira Biliyan 2.9
Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayayyakin kiwon lafiya na mata masu juna biyu da jarirai kyauta da darajarsu ta kai naira biliyan 2.9 a fadin Najeriya.
An kaddamar da shirin ne a birnin tarayya Abuja a ranar Litinin, inda babban daraktan hukumar kula da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (NPHCDA), Dakta Muyi Aina, ya ce wannan mataki wani bangare ne na kudirin gwamnati na samar da ingantaccen kiwon lafiya ga mata da kananan yara, a kokarin rage mace-macen mata masu juna biyu a kasar.
Ya ce za a fara rabon ne a jihohi goma da suka fi fama da mace-mace a lokacin haihuwa, tare da kai kayan zuwa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko.
“Shirin ya yi daidai da ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Tinubu, wacce ta mayar da hankali wajen kare rayukan mata da yara,” in ji shi.
A cewarsa, an ware kashi 60 cikin 100 na kayan zuwa yankin Arewa maso Yamma, kashi 34 zuwa Arewa maso Gabas, yayin da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Gabas suka raba sauran kaso.
Ya kara da cewa, shirin bai tsaya a kan raba kayayyaki kawai ba, domin za a inganta cibiyoyin kiwon lafiya, da horar da ma’aikata da kuma kara kayan aiki.
Haka zalika, wakiliyar kungiyar lafiya ta duniya (WHO), Dakta Mary Brantwo, ta tabbatar da goyon bayansu ga Najeriya, tare da cewa daga yanzu za a rika bin diddigin alkaluman mace-macen mata a kowace shekara domin a ga yadda ake samun cigaba.
Kungiyar UNICEF, UNFPA da kuma gidauniyar Gates su ma sun yaba da matakin gwamnatin, tare da shan alwashin ci gaba da bada goyon baya.
Kayayyakin da aka fara raba wa sun hada da kayan da ake bukata yayin haihuwa “delivery packs”, magungunan jinya ga mata masu juna biyu, abubuwan karin gina jiki, sanke mai maganin sauro da kuma muhimman magunguna ga mata da jarirai.