28/08/2026
Gwamnatin Tarayya ta goyi bayan tsarin cigaban Taraba, ta yi alƙawarin ƙarfafa haɗin gwiwa
Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyar ta ta yin aiki tare da Gwamnatin Jihar Taraba wajen amfani da damar da jihar take da ita a fannonin noma, mak**ashi, yawon buɗe ido, ababen more rayuwa da albarkatun ma’adinai.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Jalingo, a wurin bikin cika shekara 35 da kafa Jihar Taraba da kuma ƙaddamar da Babban Tsarin Cigaban Yankin Taraba.
Idris, wanda ya isar da gaisuwar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Majalisar Zartarwa ta Tarayya ga gwamnati da al’ummar Taraba, ya bayyana Babban Tsarin a matsayin muhimmin tsari na cigaban jihar mai ɗorewa.
Ya yaba wa Gwamna Agbu Kefas kan ɗaukar tsarin cigaba na dogon lokaci, yana mai cewa nasarar tsarin za ta dogara ne da ci gaba da aiwatar da shi da kuma irin tasirin da zai yi ga rayuwar jama’a.
Ya ce: “Ba za a auna nasarar wannan Babban Tsari da bikin ƙaddamar da shi ba, sai dai da hanyoyin da aka gina, sana’o’in da aka samar, ayyukan yi da aka samar, al’ummomin da aka haɗa da juna da kuma rayukan jama’a da aka inganta.”
Idris ya bayyana Taraba a matsayin ɗaya daga cikin jihohin Nijeriya da ke da babbar damar bunƙasa tattalin arziki, yana mai nuni da damar da jihar ke da ita a noma da sarrafa amfanin gona, kiwo, samar da wutar lantarki daga ruwa, yawon buɗe ido, masana’antu da albarkatun ma’adinai.
Ya yi nuni da yarjejeniyoyin samar da kuɗaɗen ayyuka da s**a kai kusan dala miliyan 268 da Jihar Taraba ta ƙulla da Bankin Zuba Jari da Bunƙasa Tattalin Arzikin ECOWAS domin gina wani katafaren yankin masana’antu, noman shinkafa ta hanyar ban-ruwa da sarrafa ta a fili mai girman hekta 10,000, da kuma gina tashar samar da wutar lantarki ta hasken rana mai ƙarfin megawat 50 a Jalingo.
Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya tana tallafa wa ƙoƙarin jihar na samun cigaba ta hanyar manyan ayyukan ababen more rayuwa da take gudanarwa, ciki har da hanyar Gembu–Mbamnga–Yang (Lip), hanyar Bali–Serti–Gashaka–Gembu, ayyuka a kan hanyar Jalingo–Mutum Biyu–Tella–Wukari, da kuma aikin hanyoyin Mayo Selbe–Gembu, Mutum Biyu–Garba Chede da Jalingo–Numan.
“Waɗannan ba hanyoyi kawai ba ne. Zuba jari ne a haɗa al’ummomi, kasuwanci, yawon buɗe ido, noma, tsaro da zirga-zirgar mutane da kayayyaki,” inji shi.
Dangane da tsaro, Idris ya ce Gwamnatin Tarayya tana ci gaba da sauye-sauye domin kafa rundunar ’yan sandan jihohi, da nufin kusantar da aikin ’yan sanda ga al’umma, tare da tabbatar da ƙwarewa, ɗaukar alhaki da kuma kare jama’a daga cin zarafi.
Ya kuma ambaci kafa Rundunar Sojojin Nijeriya ta 10 da ke da hedikwata a Jalingo kuma yake da alhakin gudanar da ayyukan tsaro a Taraba da Adamawa, a matsayin wata shaida ta ƙudirin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa tsaro a yankin.
“Dole ne tsaro da cigaba su tafi tare. Mutane ba za su zuba jari ba, manoma ba za su kai amfanin gonakin su kasuwa ba, masu yawon buɗe ido ba za su zo ba, sannan kasuwanci ba zai bunƙasa ba idan al’umma ba ta da tsaro,” inji Idris.
Ministan ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa tushen kuɗaɗen gwamnati, yana mai cewa cire tallafin man fetur ya samar wa Tarayya ƙarin kuɗi har naira tiriliyan 15.8 tsakanin Yuni 2023 da Disamba 2025.
A cewar sa, kusan ₦5.4 tiriliyan ne Gwamnatin Tarayya ta samu, yayin da kusan ₦10.4 tiriliyan s**a tafi jihohi da ƙananan hukumomi, lamarin da ya samar da ƙarin kuɗaɗen gudanar da ayyukan ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, tsaro da bunƙasa ƙwarewar jama’a.
Idris ya yi alƙawarin ƙara haɗin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Sake Wayar da Kai ta Jihar Taraba, domin tabbatar da cewa jama’a sun fahimci manufofin Babban Tsarin kuma sun rungume su.
“Dole ne hangen nesan da ke cikin wannan Babban Tsari ya wuce ofisoshin gwamnati. Dole ne ya isa ga manomi, ɗan kasuwa, ɗalibi, mai saye da sayarwa da al’ummomi a faɗin Taraba, domin tsarin cigaban Taraba dole ne ya zama tsari ne na dukkan mutanen Taraba,” inji shi.
Gwamna Kefas, a nasa jawabin, ya yi kira da a tabbatar da ci gaba da tafiyar da gwamnati ba tare da katsewa ba, yana mai cewa gwamnatin sa za ta gina kan nasarorin da aka samu a baya, ta gyara abubuwan da ke buƙatar gyara, ta kammala ayyukan da s**a dace kuma ta buɗe sababbin hanyoyin cigaba ga al’ummomin da za su zo nan gaba.
“Gwamnati tafiya ce da ba ta yankewa. Cigaba kuma yana ginuwa ne a kan abin da aka riga aka samu. Taraba ta fi kowace gwamnati, kowace hukuma, kowace jam’iyyar siyasa, kowace ƙabila ko mutum ɗaya girma,” inji shi.
Kefas ya yi kira ga tsofaffin shugabannin jihar da su ci gaba da bayar da gudunmawar su ta hanyar amfani da ƙwarewar su da ilimin da s**a samu a harkokin gwamnati wajen samar da zaman lafiya, haɗin kai da cigaban jihar.
Taron ya samu halartar tsohon Gwamnan Taraba, Rev. Jolly Nyame; Sakataren Gwamnatin Jihar, Cif G.T. Kataps; Darakta-Janar na Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA), Salihu Abdulhamid Dembos; Darakta-Janar na Hukumar Rediyon Tarayya ta Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; Manajan Darakta na Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), Dakta Abubakar Dantsoho; da sauran manyan baƙi.