Ina Muka Dosa

Ina Muka Dosa Kafar Watsa Labarai Dake Kawo Maku Labaran Cikin Gida Nigeria Harma Da Ketare. Muna Tallata Hajojinku Cikin Sauki Da Rahusa. Neman Karin Bayani 09036485281

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Malam Nata'ala Na Shirin Dadinkowa Ya RasuRahotanni sun nuna cewa ya rasu ne a asib...
02/11/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Malam Nata'ala Na Shirin Dadinkowa Ya Rasu

Rahotanni sun nuna cewa ya rasu ne a asibitin koyarwa na garin Maiduguri dake jihar Borno.

Majiya Rariya

DA DUMI DUMI: Jim kaɗan bayan Ƙasar Amûrkã tace Zata kawowa Nigeria Hârí Yanzu haka Gwamnatin Tarayya Zata rabawa Sojoji...
02/11/2025

DA DUMI DUMI: Jim kaɗan bayan Ƙasar Amûrkã tace Zata kawowa Nigeria Hârí Yanzu haka Gwamnatin Tarayya Zata rabawa Sojojin Najeriya sabbin motocin yâƙî, Za'a tura da wasu hanyar Kaduna zuwa Abuja, da jihar Borno da Katsina da Zamfara da Sauran jihohin Nigeria.

Daga Jaridar Wakiliya

Yadda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II da mai dakinsa, Hajiya Sadiya Ado Bayero (Giwa Sarkin Kano) s**a gudanar da...
02/11/2025

Yadda Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II da mai dakinsa, Hajiya Sadiya Ado Bayero (Giwa Sarkin Kano) s**a gudanar da bikin cika shekaru 40 da aure.

📸: Jameela Faruk Jamo

Yadda Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Kudancin jihar Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya tallafa wa mat...
02/11/2025

Yadda Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Kudancin jihar Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya tallafa wa mata 203 masu ƙananan sana'o'i da ₦100,000 a taron bajekolin da su ka gudanar a jiya Asabar a garin Sokoto.

ABIN DA DONALD TRUMP YA YI:1. Abin da shugaban America Donald Trump ya yi na karɓar sharri, da ƙage, da ƙaryar da shugab...
02/11/2025

ABIN DA DONALD TRUMP YA YI:

1. Abin da shugaban America Donald Trump ya yi na karɓar sharri, da ƙage, da ƙaryar da shugabannin ƙungiyar CAN s**a sharara wa Duniya na cewa wai musulmin Nigeria suna yi wa kiristocin Nigeria kisan ƙare dangi shi ne asalin aƙidar kirista a duk inda yake a Duniyan nan sai ƴan kaɗan da Allah Ya kuɓutar daga cikinsu!!

2. Mu da ma can Ubangijinmu Ya gaya wa Annabinmu da ma kowa daga cikinmu a cikin Alƙur’aninSa mai girma, a Suratul Baƙarah Ayah ta 120 cewa: ((Har abada Yahudawa da Kiristoci ba za su yarda da kai ba har sai ka bi addininsu tukun, to ka ce: Lalle shiriyar Allah ita ce Shiriya)). ((ولن ترضى عنك اليهود ولا النصارى حتى تتبع ملتهم قل إن هدى الله هو الهدى)).

3. Yanzu dai ni a ganina sai dukkanmu ƴan Nigeria musulminmu da kiristocinmu mu shirya wa fiskantar musibar rayuwa da za ta same mu saboda zaluncin Donald Trump da zai tinƙare mu, zaluncin da shi Trump ɗin zai gina shi a kan ƙarairayin da ƙungiyar CAN ta Nigeria ta sharara wa Duniya.

4. Allah muke roƙon Ya taimaki ƴan Nigeria Ya kuɓutar da su daga sharrin dukkan wani mai sharri a Duniyan nan. Ameen.

~Ibrahim Jalo Jalingo

Yadda Gwamna Radda ya jaraba hawan Keke a lokacin kaddamar da rabon kayan tallafi ga jama'a a garin Kusada na jihar Kats...
01/11/2025

Yadda Gwamna Radda ya jaraba hawan Keke a lokacin kaddamar da rabon kayan tallafi ga jama'a a garin Kusada na jihar Katsina.

Me za kuce?

Wai Me Ya Samari Fararen Hula Ba Sa Shigowa Bariki Domin Yin Soyayya Da 'Yan Matan Sojoji?
01/11/2025

Wai Me Ya Samari Fararen Hula Ba Sa Shigowa Bariki Domin Yin Soyayya Da 'Yan Matan Sojoji?

Wani Dan Nijeriya Mazaunin Kasar Amurka Ya Shiga Hannun Hukuma Bayan Ya Yi Shigar Mata Ya Shiga Bandakin Mata, A Wani Gi...
01/11/2025

Wani Dan Nijeriya Mazaunin Kasar Amurka Ya Shiga Hannun Hukuma Bayan Ya Yi Shigar Mata Ya Shiga Bandakin Mata, A Wani Gidan Motsa Jiki (gym), Inda Ya Rika Daukar Bìdìyon Mata A Àsirce

Daga Zainabu Abu

Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan kalaman Donald Trump na ikirarin kãshé-kãshén KîrîstôcîGwamnatin Tarayyar Naj...
01/11/2025

Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan kalaman Donald Trump na ikirarin kãshé-kãshén Kîrîstôcî

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta karyata kalaman Shugaban Amurka, Donald J. Trump, da ya yi ikirarin cewa ana kãshê Kîrîstôcî da yawa a Najeriya, tare da kira da a sanya kasar cikin jerin kasashen da ke take hakkin Addínì.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar ranar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025, mai dauke da sa hannun Kimiebi Imomotimi Ebienfa, mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, gwamnatin ta ce kalaman Trump ba sa nuni ga ainihin halin da ake ciki a kasar ba.

Sanarwar ta ce: “Najeriya tana godiya da damuwar kasashen duniya game da kare hakkin bil’adama da ‘yancin Addínì, amma wannan ikirari ba shi da tushe. ‘Yan Najeriya mabiya dukkan Addínìi suna rayuwa, aiki da kuma ibada tare cikin lumana.”

Ma’aikatar ta kara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ci gaba da jajircewa wajen yâƙî da taáddânci, karfafa zumuncin Addínìi, da kare rayuka da hakkokin dukkan ‘yan kasa.

Najeriya ta kuma bayyana cewa za ta ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Amurka domin inganta fahimtar juna kan harkokin yankin da kuma kokarin da ake yi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar.

Yadda Shugaban ƙaramar Hukumar Roni yayi Empowerment ga matasa, yaraba Masu Baro Maicin jarka 10.🤔
31/10/2025

Yadda Shugaban ƙaramar Hukumar Roni yayi Empowerment ga matasa, yaraba Masu Baro Maicin jarka 10.🤔

Sama Da Shekaru 35 Babu Wanda Ya San 'Yan Uwan Wannan Dattijo Ko Kuma Garin Da Ya FitoWannan bawan Allah sama da shekaru...
31/10/2025

Sama Da Shekaru 35 Babu Wanda Ya San 'Yan Uwan Wannan Dattijo Ko Kuma Garin Da Ya Fito

Wannan bawan Allah sama da shekaru 35 yana rayuwa a wata unguwa, har yanzu babu wanda ya san sunansa, kuma babu wanda ya san 'yan uwansa ko sunan garinsu.

Daga karatun alƙur'ani, sallah, sai sana'arsa.

Baya alaƙa da kowa ko mu'amala da mutanen wannan unguwar tsawon shekaru (35)

Yanzu haka yana rayuwa a cikin garin "Ore Babu" a ƙaramar hukumar mulkin Odigbo dake jihar Ondo.

Saboda haka idan 'yan uwansa s**a yi ido biyu da wannan bawan Allah, su zo su sulhunta tsakaninsu.

Daga Alhassan Mailafia

An Gudanar da Jana’izar Kwamandan Yãƙî da Ƙwacen Waya na KanoAn gudanar da jana’izar marigayi Inuwa Salisu, kwamandan kw...
30/10/2025

An Gudanar da Jana’izar Kwamandan Yãƙî da Ƙwacen Waya na Kano

An gudanar da jana’izar marigayi Inuwa Salisu, kwamandan kwamitin yãƙi da masu ƙwacen waya na jihar Kano, a unguwar Sharada.

Taron jana’izar ya samu halartar gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da wasu jami’an gwamnati, ƴan uwa da abokan marigayin, wadanda s**a bayyana jimaminsu kan rasuwar tasa.

Rahotanni sun ce wasu ɓatagari ne s**a kai masa hârí a gidansa da ke Sharada a daren ranar Talata, inda s**a kãshê shi.

Hukumomi sun ce ana ci gaba da bincike domin gano wadanda s**a aikata wannan aika-aika.

~dailynews

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ina Muka Dosa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ina Muka Dosa:

Share