Ina Muka Dosa

Ina Muka Dosa Kafar Watsa Labarai Dake Kawo Maku Labaran Cikin Gida Nigeria Harma Da Ketare. Muna Tallata Hajojinku Cikin Sauki Da Rahusa. Neman Karin Bayani 09036485281

DA DUMI DUMI: Iyalan Marigayi Janar Buhari Za Su Rika Karban Albashi 300,000 Duk Wata.A yunkurin gwamnatin tarayya na ky...
17/07/2025

DA DUMI DUMI: Iyalan Marigayi Janar Buhari Za Su Rika Karban Albashi 300,000 Duk Wata.

A yunkurin gwamnatin tarayya na kyautata goben iyalan Marigayin tsohon Shugaban Ƙasa Janar Buhari, gwamnatin tarayya zata rika bawa iyalan nasa naira dubu dari uku duk wata tare da basu alawi-alawi naira dubu dari biyu da hamsin duk karshen shekara, za a gina masu gida daya a duk In da su ke so a fadin Najeriya gwamnati zakuma ta basu motoci uku.

Bugu da kari gwamnatin tarayya zata bawa Iyalan tsohon Shugaban Ƙasar jami'an tsaro guda hudu, biyu 'yan sanda biyu na farar kaya, sannan za a rika fita dasu yawon bude ido duk shekara, bihasali tare da duba lafiyar su kyauta tun daga gida Najeriya har wajen kasar.

Shin ko menene ra'ayoyin ku game da matakan da gwamnatin tarayya ta dauka kan iyalan Marigayin?

KAJI RABO: Yahaya Bello ya kara Aure, mata ta hudu cif.Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya auri mata ta huɗu, ma...
17/07/2025

KAJI RABO: Yahaya Bello ya kara Aure, mata ta hudu cif.

Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya auri mata ta huɗu, mai suna Hiqma Yahaya Bello a wani biki na sirri da aka yi a Abuja.

A Yau ta ruwaito Matar sa ta uku, Hafiza Bello, ce ta bayyana auren bayan ta bayyana farin cikinta a shafinta na Instagram inda ta marabci sabuwar amaryar cikin addu’o’i da fatan alheri.

Yanzu Yahaya Bello na da mata huɗu: Oyiza, Rashida, Hafiza, da sabuwar amarya Hiqma.

MADALLAH TAKARBE ADDININ MUSULUNCIWannan Da Kuke Gani Takarbe Addinin Musulunci Inda Ada Ake Kiranta Da Suna Happy John ...
17/07/2025

MADALLAH TAKARBE ADDININ MUSULUNCI

Wannan Da Kuke Gani Takarbe Addinin Musulunci Inda Ada Ake Kiranta Da Suna Happy John Daga Bisani Bayan Ta Musulunta Ta Zabe Asauya mata Suna Zuwa Khadija.

Maganar Gaskiya Akwai Bukatar Musaka Wannan Yarinyar Cikin Addu'a Akan Allah Yatabbatarda Ita Cikin Addinin Musulunci, Saboda Akwai Wani Qalubale Da Take Fuskanta Wanda Yana iya Zama Sanadiyar Komawarta Addinin K!ristanc!.

Yanzu Haka Dukkanin Family Nata Ba Musulmai bane Kuma S**an Kore Mutun Daga Cikin Gidansu Idan Ya Musulunta Kamar Yadda Dan Uwa Adam Ashaka Ya Bayyana, Inda Yace Ko yanzu Sunada Kusan Mace Ukku Da S**a Musulunta Kuma Duk An koresu Daga Gidajensu, Dayar Saida Aka Karyata Lokacin Da Zasu Koreta Inda Yanzu Haka Take Jinya.

A Irin Wannan Yanayi Da Suke Tsintar Kansu Ke Sa Idan Babu Wani Musulmi Da Zai Rikesu Ya Kuladasu Yadda Yakamata anaji Ana Gani Zasu Bar Musulunci Su koma Gidansu Na jiya Dan Gudun Raguwar su ta tozarta Musamman a matsayinsu Na Mata Wa 'Yanda Ake Daukar TaQalihunsu.

Musulmai Munyi Sakaci Bamuda Wata Hukuma Wacce Ke Kula Da Irin Wannan Abubuwan, Amman Kuduba Kugani Duk Musulmin Da Qaddara Ta Gitta Akansa Yabar Musulunci Ya koma K!ristanc!, Zaka ga Yadda K!rist0c!n Zasu Bashi Mafaka Tareda Daukar Duk Wani Nauyinsu.

Ina Rokon Allah Ya Tabbatar Da Wannan Matar a Cikin Addinin Musulunci Amin.

Rubutawa✍️✍️
Ashir Mai jama'a sokoto
Alhmis 17_07_2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaba Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Jami’ar Muhammadu BuhariShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinu...
17/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaba Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari (Muhammadu Buhari University) domin girmama tsohon Shugaban Ƙasa, marigayi Janar Muhammadu Buhari (rtd), GCFR.

Shugaban Ƙasa ya bayyana wannan mataki ne a yau, yayin wani zaman musamman na Majalisar Zartarwa ta Tarayya, wanda aka shirya domin marigayin, wanda ya rasu a birnin London, Birtaniya.

Shugaba Tinubu ya ce wannan girmamawa ce ta musamman domin tunawa da gudummawar da marigayin ya bayar wajen ci gaban ilimi, tsaro da zaman lafiya a Najeriya, musamman a Arewa maso Gabas inda matsalar tsaro ta daɗe tana addabar al’umma.

Ya ce Jami’ar Maiduguri ta taka rawar gani wajen ilimantar da dubban ɗalibai daga sassa daban-daban na ƙasa, kuma sauya sunan ta zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari zai kasance tarihi da tunatarwa ga sabbin ƙarni na dalibai da malamai game da sadaukarwa da kishin ƙasa da marigayin ya nuna.

Zaman majalisar ya gudana cikin yanayi na tausayi da alhini, inda mambobin majalisar s**a bayyana irin kyawawan halayensa da saukin kai, da kuma jajircewar sa wajen hidimar ƙasa.

A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya roƙi Allah da ya ji ƙan marigayin Muhammadu Buhari, ya kuma karɓe shi cikin rahamarSa, yana mai bayyana cewa Najeriya ba za ta taɓa mantawa da irin tasirin da ya bari ba.

DA DUMI-DUMI: Domin girmama marigayi Buhari, Tinubu ya canjawa University Of Maiduguri (UNIMAID) suna zuwa Muhammadu Buh...
17/07/2025

DA DUMI-DUMI: Domin girmama marigayi Buhari, Tinubu ya canjawa University Of Maiduguri (UNIMAID) suna zuwa Muhammadu Buhari University Maiduguri.

Daga Abba Sani Pantami

Cikin hotuna :Yadda Babbar diyar shugaban kasa Haj. Iyaloja  Bola Ahmad Tinubu ta sauka jihar Katsina domin gaisuwa ta'a...
17/07/2025

Cikin hotuna :Yadda Babbar diyar shugaban kasa Haj. Iyaloja Bola Ahmad Tinubu ta sauka jihar Katsina domin gaisuwa ta'aziyyar marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Tinubu: Buhari Ya Rayu da Gaskiya, Ya Mutu Cikin Girma, Najeriya Za Ta Ci Gajiyar AlƙairansaShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tin...
17/07/2025

Tinubu: Buhari Ya Rayu da Gaskiya, Ya Mutu Cikin Girma, Najeriya Za Ta Ci Gajiyar Alƙairansa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya jagoranci wani zama na musamman na Majalisar Zartarwa ta Ƙasa domin girmama tsohon Shugaban Ƙasa, Marigayi Muhammadu Buhari, GCFR, wanda ya rasu a kwanan nan, yana mai bayyana shi a matsayin mutum mai gaskiya, dattijo na kwarai, kuma gwarzon da Najeriya ba za ta manta da shi ba.

A cikin jawabin sa, Shugaba Tinubu ya bayyana Buhari a matsayin jagora da ya kasance misali na kwarai a rayuwar siyasa da shugabanci, wanda bai yarda da almubazzaranci ko yabon kai ba, kuma bai taɓa rungumar mulki domin jin daɗin kansa ba.

“Shi ne na farko a cikin mayaƙa lokacin yaƙi, na farko a cikin ‘yan ƙasa a lokacin zaman lafiya, kuma na farko a cikin zukatan al’umma ba tare da son zuciya ba. Rayuwarsa ta kasance wa’azi ga masu ɗabi’a marasa kyau, kuma mafaka ga masu ɗabi’a ta gari,” in ji Tinubu.

Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa ko a lokacin mulkinsa da bayan kammala wa’adinsa, Buhari bai taɓa nuna son mulki ko shisshigi ba, inda ya jaddada cewa marigayin ya koma Daura cikin nutsuwa, ba don akwai wani rinjaye akan sa daga gwamnati ba.

Ya kara da cewa: “Rayuwarsa ta fi nuna kishin ƙasa a aikace fiye da surutai. A fagen mulki, ya kasance mai biyayya ga ƙasa. Bayan mulkinsa, ya koma rayuwar gida cikin sauƙi, ya bar ci gaba da mulki ga waɗanda s**a gada.”

“Rayuwar Buhari ta shafe fiye da shekaru 50 a hidimar ƙasa, daga kasancewar sa gwamna, zuwa shugaban mulki na soja, zuwa shugaban ƙasa na mulkin dimokuraɗiyya, zuwa jagoran amana a hukumar PTF.” Inji Tinubu.

A karshen jawabin nasa, Shugaba Tinubu ya miƙa ta’aziyya ga Hajiya Aisha Buhari da iyalansa gaba ɗaya, tare da gwamnatin Jihar Katsina da al’ummar Najeriya, yana addu’ar Allah ya gafarta masa kurakuransa, ya ba shi Aljannatu Firdaus.

Shugaban Ƙasa ya kuma yaba da yadda Kwamitin Jana’iza, ƙarƙashin jagorancin George Akume da Gwamna Dikko Radda, s**a shirya jana’izar Shugaba Buhari.

NELFUND Za Ta Kaddamar da Manhajar Neman Aikin Yi Don Tallafawa DalibaiHukumar Bashi ta Daliban Najeriya (NELFUND) ta ba...
17/07/2025

NELFUND Za Ta Kaddamar da Manhajar Neman Aikin Yi Don Tallafawa Dalibai

Hukumar Bashi ta Daliban Najeriya (NELFUND) ta bayyana cewa tana kammala shirye-shiryen bude wata manhajar neman aiki domin ba wa masu cin gajiyar bashin damar samun aikin yi cikin sauki, a gida da kasashen waje.

Manajan Darakta na NELFUND, Akintunde Sawyerr ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a Abuja don bikin cika shekara daya da fara aikin hukumar. Ya ce shirin zai fara aiki a shekarar 2026, kuma zai hada da jerin guraben aiki daga bangarorin gwamnati da masu zaman kansu da kuma kamfanonin kasa da kasa da ke da niyyar daukar ma’aikata daga Najeriya.

Sawyer ya bayyana cewa dalibai ba za su fara biyan bashin da s**a karba ba har sai sun samu aiki, kuma biyan zai fara ne bayan kammala hidimar kasa (NYSC). Ya ce, “idan ba ka da aiki, ba za ka biya komai ba. Idan kuma ka samu aiki, za a cire kashi 10 cikin dari na albashinka kai tsaye a kowane wata.”

Idan aka sallami ma’aikaci ko ya ajiye aikinsa, cire kudin zai tsaya. Idan kuma wanda ke bin bashi ya rasu, za a goge bashin gaba daya ba tare da matsa wa iyalansa ba.

Kazalika, ya bukaci makarantu da su mayar da kudaden da dalibai s**a biya da kansu kafin NELFUND ta aika kudin su. Ya ce makarantu na jan ƙafa wajen maidowa dalibai wadannan kudade. Hukumar ta ce ta samu koke-koke da dama daga dalibai, kuma hukumomin bincike kamar ICPC da EFCC sun shiga tsakani don tilasta wa wasu makarantu da s**a ki maidowa dalibai hakkokinsu. A cewar Daraktan Ayyuka na NELFUND, Mustapha Iyal, hukumar na da bayanan dalibai fiye da miliyan 3.2 a tsarin ta, kuma tana sa ran sabbin aikace-aikace miliyan daya kafin karshen shekarar 2025 domin rage yawan ficewar dalibai daga makarantu saboda karancin kudi.

DA DUMI-DUMI: An fara taron majalisar zartarwa na musamman domin girmama margayi Buhari inda aka gayyace iyalan margayin...
17/07/2025

DA DUMI-DUMI: An fara taron majalisar zartarwa na musamman domin girmama margayi Buhari inda aka gayyace iyalan margayin a fadar Shugaban kasa ta A*o Villa.

Mataimakin shugaban kasa da Mai girma Gwamnan Jihar Katsina Sun tashi daga filin sabka da tashin jiragen sama na Malam U...
17/07/2025

Mataimakin shugaban kasa da Mai girma Gwamnan Jihar Katsina Sun tashi daga filin sabka da tashin jiragen sama na Malam Umaru Musa Yaradua zuwa babban birnin tarayya Abuja

Sun tashi domin halartar addu'a ta musamman ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, da shugaban kasa Tinubu ya shirya masa ƙara nema ma tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari rahama a waje Allah.

Cikin Hotuna:Yadda Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar da sabon shugaban ma’aikatan fadar Gwamnatin ...
17/07/2025

Cikin Hotuna:Yadda Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar da sabon shugaban ma’aikatan fadar Gwamnatin jihar Kano, Dr Sulaiman Wali Sani mni, da sababbin masu bashi shawara na musamman da sauran wasu mukamai da ya nada a baya bayan nan.

📸 Kano Online News

Bayan kammala addu'ar kwana uku ta rasuwar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Sh...
17/07/2025

Bayan kammala addu'ar kwana uku ta rasuwar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima, ya tashi daga filin jirgin jihar Katsina zuwa Abuja a yau Alhamis.

📸 DCL Hausa

Adresse

Ogunia

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Ina Muka Dosa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Ina Muka Dosa:

Partager