Ina Muka Dosa

Ina Muka Dosa Kafar Watsa Labarai Dake Kawo Maku Labaran Cikin Gida Nigeria Harma Da Ketare. Muna Tallata Hajojinku Cikin Sauki Da Rahusa. Neman Karin Bayani 09036485281

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bichi kuma Shugaban kwamitin kasafi a Majalisar Tarayya, Hon. Abubakar Kabir Abubakar...
13/08/2025

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Bichi kuma Shugaban kwamitin kasafi a Majalisar Tarayya, Hon. Abubakar Kabir Abubakar a wajen taron bayar da tuta ga ɗan takarar majalisar jihar Kano mai wakiltar mazaɓar Bagwai/Shanono a zaɓen cike giɓi da za a yi ranar Asabar mai zuwa.

Shugaba Tinubu Ya Nada Ummusalama Isyaka Rabiu A Matsayin Kwamishina a Hukumar FCCPCShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya n...
13/08/2025

Shugaba Tinubu Ya Nada Ummusalama Isyaka Rabiu A Matsayin Kwamishina a Hukumar FCCPC

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Ummusalama Isiyaka Rabiu daga Jihar Kano a matsayin Kwamishina Mai Kula da Harkokin Gudanarwa (Executive Commissioner, Corporate Services) a Hukumar Kare Hakkin Masu Saye da abokan kasuwanci ta Tarayyar Najeriya (FCCPC).

A bisa tanadin Dokar FCCPC ta 2018, za ta bayyana a gaban Majalisar Dattawa dan tantancewa da amincewa.

Ummusalama, mai shekaru 35, ta kafa Gidauniyar Usir Foundation, da ke taimaka wa marasa galihu da al’umma ta hanyar ilimi, horas dasu don samun ƙwarewa, da ayyukan jin ƙai.

Ta samu digiri a fannin Gudanar da Kasuwanci (Business Administration), sannan ta shahara a matsayin ƴar siyasa mai kusanci da al’umma, wacce ke fafutukar ganin gwamnati ta haɗa da kowa da kowa, tare da ƙarfafawa matasa da mata wajen shiga harkokin siyasa.

Yadda Jam'iyyar APC a jahar Kano  ta  gudanar da gangamin yakin neman zaben dan takarar Majalisar Jiha a karamar hukumar...
13/08/2025

Yadda Jam'iyyar APC a jahar Kano ta gudanar da gangamin yakin neman zaben dan takarar Majalisar Jiha a karamar hukumar Bagwai da Shanono.

A ranar Asabar mai zuwa ne za'a sake gudanar da zaben a yankin sak**akon soke zaben da akayi a kwanakin baya.

Shugaba Tinubu Ya Sake Nada Abubakar Sadiq Yelwa a Matsayin Shugaban N-HYPPADEC Karo Na BiyuShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tin...
13/08/2025

Shugaba Tinubu Ya Sake Nada Abubakar Sadiq Yelwa a Matsayin Shugaban N-HYPPADEC Karo Na Biyu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya amince da sabunta nadin Alhaji Abubakar Sadiq Yelwa a matsayin Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Hukumar Cigaban Yankunan da Ke Samar da Wutar Lantarki ta Ruwa (N-HYPPADEC) domin yin wa’adi na biyu kuma na ƙarshe na tsawon shekaru huɗu.

Sanarwar da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya ta fitar ta bayyana cewa wannan nadin ya yi daidai da tanadin Sashe na 93 na Dokar Wutar Lantarki ta 2023. Shugaba Tinubu ya bukaci Yelwa da ya ci gaba da tabbatar da nasarorin da hukumar ta samu a baya tare da kawo ƙarin kirkire-kirkire da jajircewa wajen aiwatar da aikin sa.

Shugaban Ƙasa ya kuma jaddada muhimmancin inganta ayyukan hukumar don tabbatar da cewa yankunan da ake kula da su sun amfana sosai daga albarkatun da suke samarwa ƙasar.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta ce ta k**a mutane daban-daban bisa laifuka da s**a haɗa da sata, lalata kayayyakin g...
13/08/2025

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta ce ta k**a mutane daban-daban bisa laifuka da s**a haɗa da sata, lalata kayayyakin gwamnati da kuma zargin fyade, tare da kwato bututun ƙarfe, wayoyin wutar lantarki da katakon ƙarfe na layin dogo.

Wannan na cikin Wata sanarwar da kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar a madadin Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Bello Yahaya.

Sanarwar ta ce an k**a mutane bakwai da ake zargi da satar kayayyakin layin dogo, wani matashi ɗan shekara 18 da ake nema bisa laifin fashi, da kuma wani mutum ɗan shekara 55 bisa zargin fyade.

Rundunar ta ce za a mika duk wadanda ake zargi kotu da zarar an kammala bincike.

Shugaban Tinubu ya tattauna ta wayar tarho da firaministan ƙasar Netherlands, H.E Dick Schoof inda ya tabbatar masa da c...
13/08/2025

Shugaban Tinubu ya tattauna ta wayar tarho da firaministan ƙasar Netherlands, H.E Dick Schoof inda ya tabbatar masa da cewa yana nan a raye.

Cikin Hotuna: Yadda Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya jagoranci taron yaƙin neman zaɓen ADC a zaɓen cike gu...
13/08/2025

Cikin Hotuna: Yadda Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya jagoranci taron yaƙin neman zaɓen ADC a zaɓen cike gurbin Majalisar Tarayya ta Chikun Da Kajuru a garin Chikun.

- Kamal Fari Abdullahi

Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano ta yi Allah-wadai da mummunar dabiʼar da wasu ɗalibai mata...
13/08/2025

Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano ta yi Allah-wadai da mummunar dabiʼar da wasu ɗalibai mata s**a yi da sunan ʼRanar Cikin Karyaʼ wato “Fake Pregnancy Day” ba tare da izini ba.

Arewa Updates ta rawaito wannan na cikin sanarwar da shugaban sashen kula da harkokin dalibai na jami’ar, Farfesa Abdulkadir Muhammad Dambazau, ya fitar a ranar Laraba 13 ga Agusta 2025.

Sanarwar ta ce wannan abin ya saba ka’idojin ɗabi’ar dalibai kuma ya sabawa ƙa’idojin jami’ar, tare da jawo wa makarantar mummunar illa da ɓata suna da martabarta.

Ta kuma ce jami’ar za ta gano duk wanda ya shirya ko ya taka rawa a wannan abin, tare da ɗaukar matakin ladabtarwa.

Jami’ar ta kuma yi kira ga dukkan dalibai da su kasance jakadu nagari na jami’ar, tare da neman izini kafin gudanar da kowanne irin aiki a nan gaba.

Me za ku ce?

Allahu Akbar 😭 Yau Wata Daya Da Rasuwar Tshon Shugaban kasa Baba Muhammadu Buhari Mai Gaskiya 😭😭Muna rokon Allah ya jika...
13/08/2025

Allahu Akbar 😭 Yau Wata Daya Da Rasuwar Tshon Shugaban kasa Baba Muhammadu Buhari Mai Gaskiya 😭😭

Muna rokon Allah ya jikansa Da rahama Amin

Daga Ashir Mai jama'a sokoto

Gwamnatin tarayya ta haramta gina sabbin jami'o'i da kwalejin ilimiGwamnatin Tarayya ta sanya takunkumin shekaru bakwai ...
13/08/2025

Gwamnatin tarayya ta haramta gina sabbin jami'o'i da kwalejin ilimi

Gwamnatin Tarayya ta sanya takunkumin shekaru bakwai na dakatar da kafa sabbin jami’o’i, kwalejojin fasaha da kwalejojin ilimi na tarayya, saboda yawaitar makarantu da ake da su amma ba a cikakken amfani da su ba, ƙarancin kuɗaɗen gudanarwa, da kuma raguwar ingancin ilimi.

Wannan matakin ya samu amincewar majalisar zartarwa ta tarayya a zaman da ta yi ranar Laraba a fadar shugaban kasa da ke Abuja, ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, bayan gabatarwar da Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa ya yi.

Tinubu Zai Ci Gaba da Ƙarfafawa NDLEA Wajen Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi – RibaduMai Ba wa Shugaban Ƙasa Shaw...
13/08/2025

Tinubu Zai Ci Gaba da Ƙarfafawa NDLEA Wajen Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi – Ribadu

Mai Ba wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai ci gaba da ƙarfafawa Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) saboda muhimmancin ta wajen nasarar tsare-tsaren tsaron ƙasa. Ya bayyana haka ne a lokacin ƙaddamar da sabbin motocin aiki 48 ga manyan ofisoshin sassa na NDLEA a fadin ƙasar, a Abuja ranar Laraba. Ribadu ya yaba wa shugaban hukumar, Manjo Janar Buba Marwa (Rtd), bisa jajircewa da tsayuwa tsayin daka wajen yaƙar matsalar miyagun ƙwayoyi da ke barazana ga tsaro, zaman lafiya da lafiyar jama’a.

Ribadu ya ce ƙaruwar kayan aiki da tallafin da Shugaba Tinubu ke bayarwa ya taimaka wajen inganta ayyukan hukumar, ya kuma bayyana cewa fataucin miyagun ƙwayoyi na da alaƙa kai tsaye da matsalar tsaro a ƙasar nan, inda ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga ke samun kuɗaɗen gudanar da ayyukansu daga haramtattun ƙwayoyi. Ya ƙara da cewa motocin za su taimaka wa NDLEA wajen ƙarfafa sa ido, da tabbatar da cewa ba wanda ya tsere cikin masu aikata laifi daga hukunci.

A nasa jawabin, Marwa ya bayyana cewa wannan lamari alama ce ta ci gaba wajen maida NDLEA hukuma ta zamani mai inganci da ƙima a idon duniya. Ya gode wa Shugaba Tinubu bisa goyon bayan da yake bai wa hukumar, yana mai cewa ƙaruwar motocin aikin na nuna jajircewar gwamnati wajen magance tushen matsalar rashin tsaro da tabarbarewar zamantakewa. Ya ƙara da cewa a ƙarƙashin shirin Renewed Hope, Shugaba Tinubu ya sanya tsaron ƙasa, gyaran hukumomi da kare rayukan ‘yan ƙasa a matsayin ginshiƙai na gwamnatinsa.

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin jihar Gombe za ta kirkiri sabbin kananan hukumomi guda (13). Ga jerin sabbin kananan hukumomin d...
13/08/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin jihar Gombe za ta kirkiri sabbin kananan hukumomi guda (13).

Ga jerin sabbin kananan hukumomin da za a kafa tare da hedikwatocinsu;

Ga jerin su k**ar haka;

1. Akko Arewa (Hedikwata: Amada)

2. Akko Yamma (Hedikwata: Pindiga)

3. Balanga Kudu (Hedikwata: Bambam)

4. Billiri Yamma (Hedikwata: Tal)

5. Dukku Arewa (Hedikwata: Malala)

6. Funakaye Kudu (Hedikwata: Tongo)

7. Gombe Kudu (Hedikwata: Bolari)

8. Kaltungo Gabas (Hedikwata: Wange)

9. Kwami Yamma (Hedikwata: Bojude)

10. Nafada Yamma (Hedikwata: Birin Fulani)

11. Pero-Chonge (Hedikwata: Filiya)

12. Yamaltu Gabas (Hedikwata: Hinna)

13. Yamaltu Yamma (Hedikwata: Zambuk).

Adresse

Ogunia

Notifications

Soyez le premier à savoir et laissez-nous vous envoyer un courriel lorsque Ina Muka Dosa publie des nouvelles et des promotions. Votre adresse e-mail ne sera pas utilisée à d'autres fins, et vous pouvez vous désabonner à tout moment.

Contacter L'entreprise

Envoyer un message à Ina Muka Dosa:

Partager