Ina Muka Dosa

Ina Muka Dosa Kafar Watsa Labarai Dake Kawo Maku Labaran Cikin Gida Nigeria Harma Da Ketare. Muna Tallata Hajojinku Cikin Sauki Da Rahusa. Neman Karin Bayani 09036485281

HOTUNA: Kalli yadda aka yi wa ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa ado da tufafin mahauta a bikin al’adu na Kudanc...
30/05/2026

HOTUNA: Kalli yadda aka yi wa ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa ado da tufafin mahauta a bikin al’adu na Kudancin Kaduna da aka gudanar a Kafancan.

📸: Ahmed Ali, Kafancan

DAN TAKARAR GWAMNAN JIHAR SOKOTO NA ADC YAYI GANAWA DA MANYAN JAGORORIN SOKOTO TA GABAS A ZIYARAR BARKA DA SALLAHA wani ...
30/05/2026

DAN TAKARAR GWAMNAN JIHAR SOKOTO NA ADC YAYI GANAWA DA MANYAN JAGORORIN SOKOTO TA GABAS A ZIYARAR BARKA DA SALLAH

A wani mataki da ke ci gaba da jan hankalin masu bibiyar harkokin siyasa a Jihar Sokoto da ma Najeriya baki ɗaya, ɗan takarar gwamnan Jihar Sokoto a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, Hon. Manir Muhammad Dan Iya (Walin Sokoto), ya karɓi baƙuncin manyan shugabanni da jagororin jam’iyyar ADC daga shiyyar Sokoto ta Gabas a gidansa da ke birnin Sokoto.

Ziyarar wadda aka gudanar a cikin yanayi na mutunta juna da zumunci na barka da Sallah, ta haɗa manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar waɗanda s**a bayyana jin daɗinsu kan irin karɓar da s**a samu daga Walin Sokoto.

A yayin ganawar, an tattauna batutuwa masu muhimmanci da s**a shafi ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar, bunƙasa ayyukan siyasa a matakin ƙasa da jiha, tare da duba hanyoyin da za su taimaka wajen kawo ci gaba da inganta rayuwar al’ummar Sokoto.

Masu ziyartar sun bayyana cewa jam’iyyar ADC na ci gaba da samun karɓuwa daga al’umma, tare da jaddada muhimmancin haɗin kai da aiki tare domin cimma manufofin da za su anfani jama’a.

Hon. Manir Muhammad Dan Iya ya nuna matuƙar farin cikinsa da wannan ziyara, inda ya gode wa shugabannin da jagororin ADC na Sokoto ta Gabas bisa girmamawar da s**a nuna masa. Ya kuma yi addu’ar Allah Ya maimaita bukukuwan Sallah cikin koshin lafiya, zaman lafiya da ci gaba ga jihar Sokoto da Najeriya baki ɗaya.

Ganawar ta ƙara nuna irin kusanci da fahimtar juna da ke tsakanin Walin Sokoto da jagororin ADC, lamarin da masu sharhi ke ganin na iya ƙara wa jam’iyyar ƙarfi yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa a nan gaba.

Ina Muka Dosa
30/05/2026

DA DUMI-DUMI ll Ƴan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojan Kasan Najeriya, Mejo Janar Rabe Abubakar (Mai Ritaya) Da Matar...
30/05/2026

DA DUMI-DUMI ll Ƴan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojan Kasan Najeriya, Mejo Janar Rabe Abubakar (Mai Ritaya) Da Matarsa A Daidai Garin Matazu Akan Hanyarsa Ta Zuwa Katsina, Yau Asabar .

Majiya: Sahara Reporters

HUKUMAR HISBAH TA FARA ZAGAYE A CIBIYOYIN BUKUKUWAN SALLAH A SOKOTOA jiya Juma'a, 29 ga Mayu, 2026, Hukumar Hisbah ta Ji...
30/05/2026

HUKUMAR HISBAH TA FARA ZAGAYE A CIBIYOYIN BUKUKUWAN SALLAH A SOKOTO

A jiya Juma'a, 29 ga Mayu, 2026, Hukumar Hisbah ta Jihar Sokoto ta fara gudanar da zagaye a cibiyoyin da ake shirya bukukuwan Sallah domin tabbatar da bin ka'idojin tarbiyya da kuma kauce wa cakuduwar maza da mata yayin gudanar da bukukuwan.

Cibiyoyin da tawagar ta ziyarta sun haɗa da Mascow, Albishir, Marakish, Plus Center, K7 Mall, Sky Land da Six20 DS.

Zagayen ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin Mukaddashin Kwamandan Hisbah na Jihar Sokoto, Imam Sirajo Abubakar, tare da Board Member Sheikh Abdurrahman Sani Mai Tawul da AC Intelligence Malam Hassan Mu'azu.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani bayani da ya nuna cewa hukumar ta k**a wani mutum ko ta ɗauki wani mataki kan karya dokokin da ta sanya ido a kai.

Wannan na haifar da tambaya a tsakanin al'umma: Shin jama'a sun karɓi kiraye-kirayen Hisbah wajen gudanar da bukukuwan Sallah cikin tsari da tarbiyya? Ko kuwa masu gudanar da cibiyoyin taruka ne s**a ɗauki matakan da s**a taimaka wajen kauce wa cudanyar maza da mata?

✍️ Ashir Mai Jama'a Bado
--->Daga Sokoto
--->30 May 2026

30/05/2026

Jam’iyyar PDP ta tsayar da Goodluck Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa domin babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027.

GWAMNONIN NIJERIYA NA DUBA YIWUWAR ƘARA MAFI ƘARANCIN ALBASHI ZUWA N100,000Rahotanni na nuna cewa gwamnonin jihohin Nije...
30/05/2026

GWAMNONIN NIJERIYA NA DUBA YIWUWAR ƘARA MAFI ƘARANCIN ALBASHI ZUWA N100,000

Rahotanni na nuna cewa gwamnonin jihohin Nijeriya na nazarin yiwuwar ƙara mafi ƙarancin albashin ma'aikata zuwa Naira 100,000 domin daidaita rayuwar ma'aikata a daidai lokacin da ake fama da hauhawar farashin kayayyaki da tsadar rayuwa.

Idan wannan mataki ya tabbata, ana sa ran zai taimaka wajen ƙara ƙarfin sayen kayan masarufi ga ma'aikata tare da rage wasu daga cikin matsalolin tattalin arzikin da suke fuskanta.

Sai dai wasu masana na ganin cewa akwai buƙatar a tabbatar jihohi da ƙananan hukumomi na da ƙarfin biyan sabon albashin ba tare da jinkiri ba.

A halin yanzu, ana Hasashen ana ci gaba da tattaunawa da nazari kan batun, yayin da Ake Hasashen ma'aikata da kungiyoyinsu zasu sa ido kan yadda lamarin zai kaya.

Tambaya ga al'umma: Shin kuna ganin mafi ƙarancin albashi na N100,000 zai taimaka wajen rage raɗaɗin tsadar rayuwa a Nijeriya, ko kuwa akwai buƙatar a ɗauki wasu ƙarin matakai?

✍️ Ashir Mai Jama'a Bado
--->Daga Sokoto
--->30 May 2026

HÂTSÃRÎN MOTA YA JIKKATA MUTANE DA DAMA A BAUCHIWasu mazauna yankin Darazo da ke Jihar Bauchi da s**a nufi Kasuwar Soro ...
30/05/2026

HÂTSÃRÎN MOTA YA JIKKATA MUTANE DA DAMA A BAUCHI

Wasu mazauna yankin Darazo da ke Jihar Bauchi da s**a nufi Kasuwar Soro sun yi Hâtsãrîn mota a safiyar yau, a gaban Nahuta da ke mashigar Yalwan Darazo.

Rahotanni sun nuna cewa mutane da dama sun samu raunuka daban-daban sak**akon Hâtsãrîn, yayin da aka garzaya da waɗanda s**a jikkata domin samun kulawar likitoci.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a tabbatar da adadin waɗanda s**a jikkata ko Rasa Rai ba da musabbabin hatsarin ba.

Muna addu’ar Allah Ya ba waɗanda s**a ji rauni lafiya. 🤲

Ina Muka Dosa
30/05/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN😭😭Allah Ya yiwa wata mata rasuwa a cikin mota daga Sokoto zuwa Kware, kuma har yanzu b...
29/05/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN😭😭

Allah Ya yiwa wata mata rasuwa a cikin mota daga Sokoto zuwa Kware, kuma har yanzu ba a tantance ko wacece ba b***e a gano danginta.

Ana roƙon duk wanda ya santa ko ya san wani daga cikin ‘yan uwanta da ya taimaka wajen sanar da su cikin gaggawa.

📞 Domin ƙarin bayani: a Kira 081*076*832*14
Ko a tuntubi Ofishin ‘Yan Sanda na Garin Kware.

Allah Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya haɗa ta da Aljannatul Firdausi. Amin.

🙏 Don Allah a taimaka da sharing domin saƙon ya isa ga iyalanta.

✍️ Ashir Mai Jama'a Bado
--->Daga Sokoto
--->29 may 2026

Yadda Bello El-Rufa’i Ya Ziyarci Atiku AbubakarƊan gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Bello El-Rufa’i, ya kai ziyarar ba...
29/05/2026

Yadda Bello El-Rufa’i Ya Ziyarci Atiku Abubakar

Ɗan gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Bello El-Rufa’i, ya kai ziyarar ban girma ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC, Alhaji Atiku Abubakar.

Ziyarar ta jawo cece-kuce da martani daga jama’a musamman a dandalin siyasa, inda mutane da dama ke kallon hakan a matsayin wani sabon yanayi na siyasar Najeriya gabanin zaɓe mai zuwa.

Har yanzu ba a bayyana cikakken dalilin ganawar tasu ba, sai dai ana hasashen ta mayar da hankali ne kan batutuwan siyasa da makomar ƙasar nan.

Ina Muka Dosa
29/05/2026

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,663 kuɗin makaranta a Jami’ar Northwest da ke KanoAsusun bayar da lamuni ga ɗaliban jami'o'...
29/05/2026

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,663 kuɗin makaranta a Jami’ar Northwest da ke Kano

Asusun bayar da lamuni ga ɗaliban jami'o'i ta ƙasa (NELFUND) ta raba zunzurutun kuɗi har Naira miliyan 394 da dubu 861 (₦394,861,000) ga Jami’ar Yusuf Maitama Sule (wadda aka fi sani da Northwest University) da ke Jihar Kano, domin biya wa ɗalibai dubu shida da ɗari shida da sittin da uku (6,663) kuɗin rajista.

Wannan tallafi ya shafi kuɗaɗen rajistar ɗaliban ne na karatun zangon karatu na shekarar 2025/2026, domin tabbatar da cewa sun ci gaba da karatunsu ba tare da wata fargaba ko tsaiko na kuɗi ba.

A cikin wata wasiƙar godiya da amincewa da karɓar kuɗaɗen mai ɗauke da kwanan wata 17 ga watan Afrilun 2026, wadda Shugabar Jami’ar, Farfesa Amina Salihi Bayero ta sanya wa hannu, jami’ar ta tabbatar da cewa kuɗaɗen sun shigo asusunsu.

"Ina mai tabbatar muku da karɓar kuɗi har Naira 394,861,000.00. Wannan adadi zai shafi kuɗin rajista na ɗalibai 6,663 na Jami’ar Northwest a ƙarƙashin tsarin ba da rance na NELFUND. Muna mika godiyarmu ta musamman kan wannan tallafi da ya zo a kan gaba, wanda zai rage wa ɗalibanmu raɗaɗin matsin tattalin arziki," in ji Farfesa Amina.

Wannan mataki ya zo ne a daidai lokacin da iyalai da dama ke fuskantar ƙalubalen tattalin arziki, inda ake sa ran tallafin zai kawo babban sauƙi ga iyaye da kuma ɗaliban jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya.

Hukumar NELFUND ta bayyana cewa wannan shiri yana ɗaya daga cikin manyan manufofin gwamnatin tarayya na dawo da karsashi da "Sabunta Fata" (Renewed Hope) a ɓangaren ilimi, domin ganin cewa ’ya’yan talakawa ba su fita daga makaranta ba saboda rashin kuɗin karatu.

Yadda Ɗan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar PDP Prof. Isa Ali Pantami tare Senator Ibrahim Hassan Dankwambo, s**a ...
29/05/2026

Yadda Ɗan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar PDP Prof. Isa Ali Pantami tare Senator Ibrahim Hassan Dankwambo, s**a gabatar da Sallar Jumma'a, a Masallacin ADP dake GRA Gombe.

📸 -Professor Isa Ali Pantami.

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ina Muka Dosa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ina Muka Dosa:

Share