Ina Muka Dosa

Ina Muka Dosa Kafar Watsa Labarai Dake Kawo Maku Labaran Cikin Gida Nigeria Harma Da Ketare. Muna Tallata Hajojinku Cikin Sauki Da Rahusa. Neman Karin Bayani 09036485281

Wallahi tunda aka fara wannan daminar hankalina bai taba tashi ba alokacinda ruwan sama suke sauka🌧️ kamar yau dinnan na...
08/09/2025

Wallahi tunda aka fara wannan daminar hankalina bai taba tashi ba alokacinda ruwan sama suke sauka🌧️ kamar yau dinnan na tsorata matuka hankalina ya tashi. Alaji ruwan sama ni'ima ne fa amma wallahi na tsorata dajin yanda ruwa da iska ga walkiya da stawa suke sauka wallahi bansan lokacinda nayi jifa da waya na dauko charbi📿 na kama Istigfari ba.

Wallahi ko kankanuwar azabar uban giji bazamu iya dauka ba, Allah yasa mucika da Imani.👏

Matsayinmu na Gwamnati tsakaninmu da jami'an tsaro, daga lokacinda muka samu wani Îñf0rmér daga ranar ya Kare"~Inji Gwam...
08/09/2025

Matsayinmu na Gwamnati tsakaninmu da jami'an tsaro, daga lokacinda muka samu wani Îñf0rmér daga ranar ya Kare"

~Inji Gwamna Amadu

MATSALAR TSARO A JAHAR SOKOTO : ME YA RAGE KUMA ?1- Jami'an tsaro sunce kayan aiki :Gwamna Amadu ya bada motochi hilux f...
08/09/2025

MATSALAR TSARO A JAHAR SOKOTO : ME YA RAGE KUMA ?

1- Jami'an tsaro sunce kayan aiki :

Gwamna Amadu ya bada motochi hilux fiye da 350, ya bada motochi Bufallo na yàkí guda 80, ya bada Mashuna fiye da dubu 12, ya bada riguna na kariyar búllét fiyeda dubu 11.

2- Jami'an tsaro sunce kuddinsu na Monthly Operational Allowances :

Gwamna Amadu yasa a biyasu dukkan watannin da tsohuwar gwamnatin Tambuwal ta rike masu allowances na yaki da yan ta'adda, sannan ya linka kuddi zuwa sau ukku garesu domin ya karama jami'an tsaro kwarin guiwa. Yanzu duk Najeriya Jahar Sokoto ce kadai ke biyan Jami'an tsaro allowances linki ukku.

3- Jami'an tsaro sukace sunason Gwamna ya basu kwana daya cikin kowane wata :

Gwamna Amadu yace wata daya kam yayi nisa da yawa, shi kowane sati sai ya hadu dasu jami'an tsaro domin suyimasa bayanin inda ake da inda aka kwana ga yaki da yan ta'adda saboda shi ba Gwamna ba ne me yawon neman takarar Shugaba kasa ba, kullum yana cikin al'ummarsa.

4- Jami'an tsaro na sojojin sama suka ce suna bukatar karin jiragen yàkí :

Gwamna Amadu yaje ya zauna da Karamin Ministan tsaro Bello Matawalle ya gayyatoshi har Jahar Sokoto ya karbomasu kari na jiragen yãkí daga gwamnatin tarayya.

5- Jami'an tsaro sukace a karomasu 'yan banga don aiki da 'yan cikin gida :

Gwamna Amadu bai tsaya ba sai da ya kirkiro da dubban jami'an tsaro na Community Guard a Jahar Sokoto kuma ya basu kayan aiki na Motochin Hilux 20 da Mashuna guda 710 domin su kamama jami'an tsaro.

6- Jami'an Tsaro sukace sansanin zama suke so :

Gwamna Amadu ya samar da sansanin zama garesu a dukkanin inda akeda matsalar tsaro, kuma ya fara ginawa jami'an Community Guard ofisoshi a Kananan hukumomi.

7- Jami'an tsaro sukace wajen aje 'yan gudun hijira kamin su koma garuruwansu :

Gwamna Amadu ya sake sayen wasu katafarun gidaje ga 'yan gudun hijira domin zaman 'yan gudun hijira inda gwamnati ke kulawa da cinsu da shan su da kuma suturar su.

8- Kananan hukumomi sukace suna bukatar Karin tallafi ga kuddin tsaro :

Gwamna Amadu ya ware kowane wata ana baiwa kowace Karamar hukuma me matsalar tsaro kudaden tsaro domin daukar matakan tsaro a mataki na Karamar hukuma.

9- Jami'an tsaro suka bukaci hanyoyin tituna don cimma 'yan ta'adda har mabuyarsu :

Gwamna Amadu yasa aka aiwatar da tituna a garuruwa daban daban inda yan ta'adda ke boyo domin jami'an tsaro sukai har chan cikin mabuyarsu su fatattakesu.

10- Akayi Maganar tallafi ga wadanda 'yáñ tà'àddà suka yiwa ta'ãddáncí :

Gwamna Amadu ya shirya da kansa tare da tawagarsa yana zuwa gari gari inda 'yân tâ'ãddâ suka kai fãrmâkí yana yimasu jaje kuma ya basu kuddi da kayan abinci, wadanda suka samu raunuka kuma gwamnati ta dauki nauyin jinyarsu.

11- Shuwagabanni sun bada shawara kan daukar Matasa aiki don rage Matsalar tsaro :

Gwamna Amadu bai bata lokaci ba, ayau ya nada kwamiti da gaggawa yace aje a dauki Matasa aiki daga Kananan hukumomi 23 na jahar Sokoto don rage rashin aikinyi da shigar matasa harkar iñf0rmâñts wadda ke kara kawo matsalar tsaro.

Jama'a me ya rage kuma Gwamna Amadu yayi yanzu akan matsalar tsaro ? Tambayar Hon. Naseer Bazza

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayayyakin kiwon lafiya na mata masu juna biyu da jarirai kyauta har na Naira Biliyan 2....
08/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayayyakin kiwon lafiya na mata masu juna biyu da jarirai kyauta har na Naira Biliyan 2.9

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayayyakin kiwon lafiya na mata masu juna biyu da jarirai kyauta da darajarsu ta kai naira biliyan 2.9 a fadin Najeriya.

An kaddamar da shirin ne a birnin tarayya Abuja a ranar Litinin, inda babban daraktan hukumar kula da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (NPHCDA), Dakta Muyi Aina, ya ce wannan mataki wani bangare ne na kudirin gwamnati na samar da ingantaccen kiwon lafiya ga mata da kananan yara, a kokarin rage mace-macen mata masu juna biyu a kasar.

Ya ce za a fara rabon ne a jihohi goma da suka fi fama da mace-mace a lokacin haihuwa, tare da kai kayan zuwa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko.

“Shirin ya yi daidai da ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Tinubu, wacce ta mayar da hankali wajen kare rayukan mata da yara,” in ji shi.

A cewarsa, an ware kashi 60 cikin 100 na kayan zuwa yankin Arewa maso Yamma, kashi 34 zuwa Arewa maso Gabas, yayin da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Gabas suka raba sauran kaso.

Ya kara da cewa, shirin bai tsaya a kan raba kayayyaki kawai ba, domin za a inganta cibiyoyin kiwon lafiya, da horar da ma’aikata da kuma kara kayan aiki.

Haka zalika, wakiliyar kungiyar lafiya ta duniya (WHO), Dakta Mary Brantwo, ta tabbatar da goyon bayansu ga Najeriya, tare da cewa daga yanzu za a rika bin diddigin alkaluman mace-macen mata a kowace shekara domin a ga yadda ake samun cigaba.

Kungiyar UNICEF, UNFPA da kuma gidauniyar Gates su ma sun yaba da matakin gwamnatin, tare da shan alwashin ci gaba da bada goyon baya.

Kayayyakin da aka fara raba wa sun hada da kayan da ake bukata yayin haihuwa “delivery packs”, magungunan jinya ga mata masu juna biyu, abubuwan karin gina jiki, sanke mai maganin sauro da kuma muhimman magunguna ga mata da jarirai.

Har Gobe A Gidanmu Nake Kwana Idan Na Dawo Daga Daukar Fim, Ba Na Kwana A Ko'ina, Daga Wurin Daukar Shiri Sai Gida, Domi...
08/09/2025

Har Gobe A Gidanmu Nake Kwana Idan Na Dawo Daga Daukar Fim, Ba Na Kwana A Ko'ina, Daga Wurin Daukar Shiri Sai Gida, Domin Haka Iyayena Suka Sabar Min Tun Daga Lokacin Da Na Fara Fim Har Zuwa Yanzu, Cewar Jaruma Amal Umar

MADUGUN ADAWA YA ZIYARCE SANATA TAMBUWALTsohon Mataimakin Shugaban Kasa Kuma madugun Adawa Atiku Abubakar Yakaiwa Tsohon...
08/09/2025

MADUGUN ADAWA YA ZIYARCE SANATA TAMBUWAL

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Kuma madugun Adawa Atiku Abubakar Yakaiwa Tsohon Gwannan Jihar Sokoto sen Aminu Waziri Tambuwal ziyara a Gidansa Dake Abuja.

Atiku Abubakar ya Wallafa a shafinsa Na Facebook Cewa, ya ziyarci Sanata Aminu Waziri Tambuwal a gidansa da ke Abuja a yau da safiyar nan, Inda yace yayi farin ciki ganin shi cikin ƙoshin lafiya, da ƙarfin gwiwa ba tare da gajiya ba.

~ Ina Muka Dosa

Tunda Allah Ya Sa Mun Fafata Da Ƴan Bìñdìģà Kuma Sun Ji Wuta, Har Suna Neman Sulhu, To A Shirye Muke Mu Yi Sulhu Da Su, ...
08/09/2025

Tunda Allah Ya Sa Mun Fafata Da Ƴan Bìñdìģà Kuma Sun Ji Wuta, Har Suna Neman Sulhu, To A Shirye Muke Mu Yi Sulhu Da Su, Kuma Sulhu Na Ainahin Gaskiya Da Gaskiya Ba Na Ƙarya Ba, Inda Za Mu Tallafawa Waɗanda Suka Cutar, Shima Wanda Ya Karɓi Sulhun Gwamnati Ta Tallafa Masa, Cewar Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Raɗɗa

Daga Jamilu Dabawa, Katsina

Karin Harajin mai na 5% ba sabon haraji ba ne, kuma ba za a aiwatar da shi yanzu baKwamitin Shugaban Kasa kan Tsarin Har...
08/09/2025

Karin Harajin mai na 5% ba sabon haraji ba ne, kuma ba za a aiwatar da shi yanzu ba

Kwamitin Shugaban Kasa kan Tsarin Haraji da Sauye-sauyen Haraji ya ce karin kashi 5% a kan farashin mai ba sabon haraji ba ne da gwamnatin Tinubu ta kawo.

A cewar kwamitin, wannan kudiri daman akwai shi a cikin dokar Federal Roads Maintenance Agency (FERMA) ta 2007, sai dai an sake saka shi a sabuwar dokar haraji ne domin samar da daidaito da kuma gaskiya.

Kwamitin ya ce karin ba zai fara aiki nan take ba har sai Ministan Kuɗi ya fitar da oda ta musamman a cikin sanarwar gwamnati.

Haka kuma, an bayyana cewa karin ba zai shafi dukkan kayan da ake saku daga man fetur ba, musamman wanda ake amfani da su a gidaje kamar gas ɗin girki (LPG), Kalanzir, da CNG, domin tallafawa burin Najeriya na wanzar da makamashi mai tsafta.

Kwamitin ya ce an samar da karin kuɗin ne domin samar da kuɗaɗen ginawa da gyaran manyan hanyoyi. Ya ce idan an aiwatar da shi yadda ya kamata, zai rage yawaitar aukuwar haɗari a hanya, zai sauƙaƙawa matafiya, da kuma rage kuɗin sufuri.

Shugaban Tinubu ya bayar da umarnin tura ƙarin sojoji da jirage marasa matuka, domin murkushe 'yán ta'âddâ.Mataimakin Sh...
08/09/2025

Shugaban Tinubu ya bayar da umarnin tura ƙarin sojoji da jirage marasa matuka, domin murkushe 'yán ta'âddâ.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya sanar da hakan a wani sakon jajanta wa gwamnati da al'ummar Jihar Borno kan harin da 'yân ta'âddâ suka kai wa yankin Darajamal da ke Karamar Hukumar Bâma, harin, wanda aka kai a daren Juma'a, ya yi sanadiyyar mutuwar fararen hula da sojojin Najeriya.

Shettima Ya kuma bayyana cewa gwamnatin tarayya na duba yiwuwar kafa 'yan sandan jihohi domin tunkarar kalubalen tsaro a matakin farko.

Tuni gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ziyarci yankin da abin ya shafa a ranar Asabar domin jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

Mataimakin Shugaban Kasar ya tabbatar wa da al'ummar jihar cewa za su ci gaba da samun goyon bayan gwamnatin tarayya a yakin da jahar ke yi da rashin tsaro.

yadda Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Radda ya ziyarci kabarin Tsohon shugaban kasa Buhari a garin Daura na jihar Katsi...
07/09/2025

yadda Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Radda ya ziyarci kabarin Tsohon shugaban kasa Buhari a garin Daura na jihar Katsina

Gwamna Radda Yayi addu'ar Allah ya jiƙanshi da rahama ya kai haske ƙabarinsa.

📸 -Gwamnatin jihar Katsina.

MATAKIN FARKO NA LALATA ZUMUNCI1- Bai Kirani ba, bazan kira shi ba.2- Bai neme ni ba, saboda me zan nemeshi.3- Bai yi ma...
07/09/2025

MATAKIN FARKO NA LALATA ZUMUNCI

1- Bai Kirani ba, bazan kira shi ba.
2- Bai neme ni ba, saboda me zan nemeshi.
3- Bai yi mani magana ba, don me zanyi masa magana.
4- Bai zuwa wurina, saboda me zanje wurinsa.
5- Idan Naje Zasuce kwaɗayi ne Yakaini
6- Zaice saboda ganin Yasami abin Duniya ne .

Jama'a rayuwa bata da tabbas, sai da uzuri da kaunar juna na Zahiri / Ɓoye.

7. Ya riƙe samun shi, Ni kuma inriƙe talaucina.
8. Ayar Shaiɗan wache ya dasa a zukatan Ƴan Boko :
*Don't associate your self with failures*

MU RIKE ZUMUNCI MUCI RIBAR RAYUWAR DUNIYA DA LAHIRA.

ALLAH Yasa Mudace

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ina Muka Dosa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ina Muka Dosa:

Share