GDK Hausa

GDK Hausa Labaran Hausa

23/05/2025

Ku shaƙata da wannan 😂// Shugaban Masu son banza na Nigeria 😂

Sojojin Najeriya sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a BornoSojojin rundunar Operation Hadin Kai na Najeriya sun fatattaki wani h...
23/05/2025

Sojojin Najeriya sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno

Sojojin rundunar Operation Hadin Kai na Najeriya sun fatattaki wani hari da 'yan ta'adda na kungiyar ISWAP s**a kai a garin Damboa da ke jihar Borno.

TheCable ta rawaito cewa, an ce sojojin, tare da haɗin gwiwar sojojin sama, sun fara da ƴan ta'addan na tsawon sa'o'i biyu.

A cewar wata sanarwa daga rundunar sojin kasa a ranar Juma’a, da misalin karfe 1 na dare ranar 23 ga Mayu, sojojin sun hango 'yan ta’addan a Damboa kuma s**a shiga musayar wuta da su nan take.

Sanarwar ta ce wannan farmaki ya yi sanadiyyar hallaka aƙalla 'yan ta’adda 16.

“Sojoji sun kashe ƴan ta’adda 16 a wannan arangama, kuma a halin yanzu suna ci gaba da bin sawun wadanda s**a tsere"

Duk da cewa dakarun sun sami nasarar kwace iko da al'amura, wani abin fashewa da 'yan ta'addan s**a harba ya haddasa gobara a wurin ajiye mak**ai.

© Daily Nigerian Hausa

21/05/2025

DA ƊUMIƊUMI: Ƙarye ne ba'a k**a Matar Ɗan bindiga Ado Alieru ba, ba'a k**a Mahaifiyarsa a Saudiyya ba- Inji Sheikh Yusuf Musa Asadus Sunnah 👇👇👇👇👇👇

21/05/2025

Gwamnatin jihar Zamfara ta musanta labarin da ake yaɗawa na wata Zainab da aka ce ta canza addini

Buɗaɗɗiyar wasiƙa da tinatarwa ga Gwamnan jihar Kano akan Sheikh Abduljabbar Kabara!Daga Khalifa Habeebu Rasulullah وَإِ...
21/05/2025

Buɗaɗɗiyar wasiƙa da tinatarwa ga Gwamnan jihar Kano akan Sheikh Abduljabbar Kabara!
Daga Khalifa Habeebu Rasulullah
وَإِذَا حَكَمْتُم بَيْنَ النَّاسِ أَن تَحْكُمُوا بِالْعَدْلِ

Wannan wasiƙa da zan rubutawa mai girma Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf akan sha'anin Sheikh Abduljabbar Kabara nayi tane da zuciya mai kyau da kuma yaƙinin cewa wannan saƙo zai isa zuwa gare shi da kuma kyautata zaton samun mafita a lamarin.

Bani kađai ba duk wani mazaunin jihar Kano yasan irin yanda mai girma gwamna yake ƙoƙari wajen aiki wa al'ummar sa da kuma ƙoƙarin faranta musu da gina musu rayuwa, wajen bunƙasa ilimi, lafiya da sauran ababen more rayuwa, kuma a zahiri mutum ne mai tausayi da nuna jinƙai ga talakawan sa, sannan muna ganin yanda yake ƙoƙarin kyautatawa har maƙiyan sa wanda duniya ma ta sani, mutumin da ya kyautatawa maƙiyi bana jin zai kasa farantawa masoyin sa.

Tabbas lamarin Mal. Abduljabbar abu ne mai matuƙar nauyi da kuma hađari a wajen mutumin da yake son ya shiga wannan case đin duba da irin bita da ƙulli da aka bi akan abin wajen siyasantar da lamarin Annabi Muhammadu ﷺ da juya abubuwa tare da hađa baki da wanda ake da saɓanin fahimta dasu har aka cimma abinda ake so a cimma akan sa.

Bawai buƙatar mu Gwamna ya saki Mal. Abduljabbar ba kai tsaye ba, mun san wannan abu ne mai wahala matuƙa, duba da yanayin komai anayin sa ne ƙarƙashin doka da oda bawai kara zube ba, abinda muke buƙata a wajen mai girma gwamna abu biyu ne ;

1. Sabunta Shari'a
2 Hukunci na Adalci

Babu wanda besan akwai san rai da wata manufa akan sha'anin Mal. Sarki da Gwamnatin da ta shuđe ba, wannan shine abinda ya haifar da wannan yanayi da aka jefa wannan bawan Allahn a ciki, maganar kuma da ake akan hadithn da yake magana akan su ita gaskiya tafin hannu baya rufe ta, tun da ran Mal. Abduljabbar abubuwan da yake yaƙa har yakai shi ga wannan halin da yake ciki gasu dai sai ƙara bayyana suke, kuma gaskiyar sa tana fitowa.

A duk lokacin da zanyi irin wannan maganar ina fađa bana kan cewa duk abinda Mal. Abduljabbar yake a da'awar sa daidai ne akwai kuskure, amma kuskuren sa bai kai ai masa zaluncin da akai masa na raɓa masa zagi a janabin Shugaba ﷺ ba, kuskure ne irin wanda duk wani mai karantarwa zai iya yin sa ko waye.

Mai girma Gwamna ka sani Mal. Abduljabbar yana da haƙƙi akan ka, na ka neman masa adalci a matsayin ka na shugaban sa kuma wanda kasan an zalunce shi, nasan abinda kake tsoro shine mutane su zage ka akan ka goyi bayan sa kuma ga irin laifin sa, kada ka kalli abinda mutane zasu ce ka tina abinda Allah ya fađa ;

يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا كُونُوا قَوَّامِينَ بِالْقِسْطِ شُهَدَاءَ لِلَّهِ وَلَوْ عَلَىٰ أَنفُسِكُمْ أَوِ الْوَالِدَيْنِ وَالْأَقْرَبِينَ إِن يَكُنْ غَنِيًّا أَوْ فَقِيرًا فَاللَّهُ أَوْلَىٰ بِهِمَا

Yaku wanda kukai imani ku kasance masu tsayawa akan adalci tsakanin ku da Allah, koda akan kune, ko iyayen ku da makusantan ku, (idan wanda zakuyiwa hukunci ya kasance) mai kuđi ne ko mulki, ko kuma ya kasance talaka ne (to kuyi masa hukunci na adalci, kada ku duba mai kuɗi ne ku ƙyale shi, ko ku duba shi takala ne bashi da wanda zai tsaya masa ku zalunce shi), kuyi adalci da mai kuɗin da talakan duk Allah ya fiye muku su...

Suratu Nisa'e 4/135...

Allah Subhanahu Wa ta'allah yace ;

اعْدِلُوا هُوَ أَقْرَبُ لِلتَّقْوَىٰ

Kuyi adalci domin cewa adalci shine mafi kusa da tsoron Allah (Ma'ana yin adalci shine yake nuna mutum mai tsoron Allah ne)...

Suratu Ma'eda 5/8...

Saboda haka mai girma gwamna sabunta wannan shari'a shine abinda zai kuɓutar dakai daga haƙƙin wannan bawan Allah, ka samar da alƙalai amintattu wanda zasuyi adalci akan kowa, komai a buđe duniya tana gani kuma kana bibiya da kanka, ka tsaya tsayin daka wajen anyi adalci kuma babu nuna ɓangaren ci ko goyon baya ga kowane ɓangare kowa gaskiyar sa ta kwace shi.

Tabbas idan kayi haka babu wanda zai zarge ka da ka goyi bayan Mal. Sarki ko ka goyi bayan wanda s**a zalunce shi akan wannan mummunan ƙazafin da s**ai masa, amma yin shirun ka akan abinda kana da haƙƙi kayi magana akan sa tamkar yarda ne, b***e wanda ya nuna maka soyayya ka zama abinda ka zama yau tare da ƙuri'un sa dana mabiyan sa tabbas duk abinda kai masa ba alfarma bace, b***e ba cewa mukai ka futo dashi kai tsaye ba, abinda muke cewa a sabunta Shari'a ai masa adalci.

Amma barin Mal. Abduljabbar a halin da yake ciki an zalunce shi, an raba shi da iyalin sa da Ƴan uwan sa da đaliban sa da harkokin sa na nema da karantarwa akan abinda an san sarai san rai ne a ciki da biyan buƙatar wasu gurɓattun mutane.

ga Ƴan As'habul Kahfi kuyi haƙuri da abinda zan fađa da yawan ku kuna zaton da zarar Abba ya hau kan kujerar sa abinda zai muku shine ya fito da sadauki, wannan abinda kuka sakawa ranku shine rashin samun sa abin ya dame ku kuma tabbas har yau kuna kallon Abba da wannan baƙin fenti na abinda yai muku, amma kuyi masa uzuri akan haka k**ar yadda kuka kyautata masa zato na mutumin kirki ne to kada rashin samun abinda kuke so ya mayar dashi mutumin banza a idon ku.

Kun san irin ƙalubalen da ya fuskanta akan mulkin sa wanda kuma har yau yana kai, magauta na wahalar dashi, har yaushe kujerar tasa ma ta tabbata? Kuyi masa uzuri yana kan zafin kan ƙalubalen makiya ba lallai ya waiwayi wannan abin yanzu ba, amma ina tabbatar muku duk daran dađewa Mal. Sarki zai futo In Sha Allah.

Yana da kyau ku yiwa tafiyar ku committee na musamman mai zaman kansa akan wannan sha'anin nakai ƙorafin ku ga gwamnati tare da bibiyar abin akai akai, gwamnati abune mai fađi da kuma yawa bata taɓa kammala abubuwan dake gaban ta b***e ta samu lokacin da babu busy akan ta, amma idan kuna bibiya a ƙungiyance ina tabbatar muku za'a samu cigaba a cikin lamarin sosai.

Ina fatan wannan saƙon zai isa har kunnen mai girma Gwamna, tare da duba abinda yake cikin saƙon da kuma samun mafita ta alkhairi.

Ina addu'ar Allah ya ƙarawa jiha ta zaman lafiya da yalwar arziƙi, ya taimaki jagororin mu wajen yi mana adalci da ciyar damu gaba ta kowane fanni.

Ni ba đan Ashabil Kahfi ba ne, mabiyin gaskiya ne!

- Khalifa Habeebu Rasulullah .

Kuyi following 👉 GDK Hausa
Kuyi Likes
Kuyi Share
Mun gode

Sabon Shekau ya fito tare da barazana ga CDS, sojoji da malaman addini Wani kwamandan Boko Haram da ya kira kansa da cew...
20/05/2025

Sabon Shekau ya fito tare da barazana ga CDS, sojoji da malaman addini

Wani kwamandan Boko Haram da ya kira kansa da cewa shi ne sabon “Shekau,” ya yi barazana ga babban hafsan hafsoshin Najeriya, CDS, Christopher Musa, da malaman addinin Musulunci, da jami’an tsaro, da kuma al’ummomin da ke goyon bayan ayyukan gwamnati na yaki da ta’addanci.

Barazanar ɗan ta’addan ba ta rasa nasaba ga gargadin da Musa ya yi tun farko a cikin harshen Hausa, inda ya yi kira ga yan ta’addan da su mika wuya ko kuma su fuskanci fushin sojojin Najeriya.

A wani sabon faifan bidiyo da kafar yada labarai ta PRNigeria ta samu kuma ta fassara daga Hausa zuwa turanci, maharin ya mika sakon ban tsoro ga Janar Musa, inda ya bukaci shi da rundunar sojojin Najeriya da su yi watsi da yakin da suke yi da kungiyar.

Ya yi ikirarin cewa, k**ar magabatan sa, Musa ba zai yi nasarar murkushe Boko Haram ba.

"Wannan sakon na babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ne, muna kira gare ka da ka tuba ka daina ayyukan da kake yi, domin ba za ka yi nasara a kan wadanda mu ke yaki da gwamnatinka ba," in ji ɗan tawayen.
Kamar yadda jaridar Daily Nigeria Hausa ta wallafa.

follow up GDK Hausa

YAUSHE WAKEN SUYA YAZO ƘASAR HAUSA ?Waken suya (Soybean – _Glycine max_ ) an kawo shi zuwa Arewacin Najeriya tun farkon ...
20/05/2025

YAUSHE WAKEN SUYA YAZO ƘASAR HAUSA ?
Waken suya (Soybean – _Glycine max_ ) an kawo shi zuwa Arewacin Najeriya tun farkon shekarun 1900, amma bai shahara sosai ba har sai a shekarun 1970 zuwa 1980, lokacin da Cibiyar Bincike kan Noma ta Ƙasashe Masu Zafi (IITA) da ke Ibadan, tare da Cibiyar Bincike kan Harkokin Noma (IAR) Samaru, s**a fara ingantaccen, bincike, da rarraba nau'ikan waken suya da s**a dace da yanayin arewacin Najeriya.

Dalilan da yasa waken suya bai shahara ba kafin wancan lokacin:

1.*Bashi ne na asalin yankin nan ba* : Waken suya asalin sa daga Ƙasar China da Gabashin Asiya ne. Ba ya cikin amfanin gona na gargajiya a Afirka, don haka manoman Najeriya ba su da tarihi ko al’adar shuka shi.

2.*Matsalolin da s**a shafi dacewar yanayi* : Nau’o’in farko da aka kawo daga Asiya ko Amurka ba su dace da yanayin Najeriya ba – musamman dangane da tsawon rana da kuma juriyar cututtuka da kwari na gida.

*3.Rashin sanin amfaninsa* : Kafin shekarun 1970, manoma da jama'ar Najeriya ba su da isasshen ilimi akan amfanin sinadaran gina jiki da na tattalin arziki da wake mai mai ke da shi. Haka kuma, ba a cika amfani da shi a cikin abincin gargajiya ba.

4 *.Rashin bukata a kasuwa* : Tun da ba ya cikin abinci na gargajiya, babu bukata sosai a kasuwanni. Wannan ya canza ne lokacin da mutane s**a fahimci yawan furotin da yake dauke da shi da kuma amfani da shi wajen abincin jarirai, dabbobi, da kayan sarrafaffen abinci.

5 *.Raguwar bincike da wayar da kai* : Sai bayan da cibiyoyi k**ar IAR Samaru s**a ƙirƙiri nau’o’i da suke girma cikin kankanin lokaci kuma sun dace da ƙasa da yanayin arewa ne, sai shuka waken suya ya fara yaduwa sosai.

A takaice

An kawo waken suya zuwa arewacin Najeriya tun farkon karni na 20, amma sai bayan shekarun 1970 ya zama muhimmi saboda nau'o'in da aka inganta, wayar da kai, da kuma goyon bayan cibiyoyin bincike na noma.
Agriculture Hausa

GDK Hausa

SANARWA GA ƘAFAFEN YAƊA LABARAI:SAKAMAKON TARON MAJALISAR ZARTASWA TA JIHAR KANO KARO NA 28, WANDA AKA GUDANAR A RANAR L...
20/05/2025

SANARWA GA ƘAFAFEN YAƊA LABARAI:

SAKAMAKON TARON MAJALISAR ZARTASWA TA JIHAR KANO KARO NA 28, WANDA AKA GUDANAR A RANAR LITININ, 19 GA MAYU, 2025 / 21 GA DHUL-QIDAH, 1446AH

Majalisar Zartaswa ta Jihar Kano ta gudanar da taronta na 28 a ranar Litinin, 19 ga Mayu, 2025 (wanda ya yi daidai da 21 ga Dhul-Qidah, 1446AH), inda aka tattauna muhimman al’amura da s**a shafi shugabanci da ci gaban jihar cikin zurfi.

Bayan doguwar tattaunawa, Majalisar ta amince da kashe jimillar kuɗi har naira biliyan talatin da shida da miliyan dari bakwai da biyar, dubu dari uku da ashirin da huɗu, da dari biyu da arba'in da biyu, da kobo talatin da huɗu (₦36,705,324,242.34) domin aiwatar da muhimman ayyuka a fadin jihar.

Muhimman Abubuwan Da Aka Amince Da Su Sun Haɗa Da:

Kuɗi ₦450,000,000.00 domin tallafa wa ayyukan aikin Hajjin 2025 a Saudiyya.

Gyaran dandalin yaye ɗalibai na Jami’ar Aliko Dangote (Fage na ɗaya): ₦126,199,628.54.

Ginin masallaci a fadar Gwamnati, Kano: ₦269,447,115.39.

Gyaran Ofishin Hukumar Kungiyoyi Masu Zaman Kansu a kan titin Wudil: ₦129,517,058.39.

Fannin Ilimi:

₦3,178,225,400.00 don ɗaukar nauyin jarabawar NECO, NABTEB da AIED/NBIAS ga 'yan asalin Kano.

₦1,678,521,098.88 matsayin kuɗin haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya (FGN-UBE Matching Grant) na zangon farko, 2025.

Sauran Ayyuka:

Diyya ga gidaje da filaye da za su shafa a tashar lantarki ta 330kV TCN, Rimin Zakara: ₦317,598,771.46.

Sayen buhunan taki guda 199,000 domin aikin noma na damina 2025: ₦4,000,545,000.00.

Aikin hana ambaliya a Rijiyar Zaki, titin Gwarzo: ₦427,730,335.74.

Sayen motar Toyota Hilux da Hiace ga Hukumar Ci Gaban Arewa maso Yamma: ₦160,000,000.00.

Ginin sabbin hanyoyi a karamar hukumar Gwale: ₦1,705,807,390.06.

Gyaran gadar ruwan da aka lalata a Dankunkuru, Nassarawa: ₦123,636,804.05.

Ginin gada biyu a hanyar Soro Daya–'Yan Awaki–Asayaya, Tsanyawa: ₦164,661,031.73.

Biya na dizil ga masu kaya na watan Afrilu 2025: ₦723,400,000.00.

Tsabtace magudanan ruwa da ƙaddamar da kamfen ɗin “Desilt Kano”: ₦260,000,000.00.

Gyaran katangar ɗakin kwanan mata da gina sabuwa a Kwalejin Audu Bako, Dambatta: ₦204,248,399.84.

Biya na kuɗin makaranta da aka bari tun shekarar 2013/2014 na shirin haɓaka malamai: ₦182,980,000.00.

Manyan Ayyukan Gina Hanya:

Sabunta kwangilar ginin titin 5km mai layi biyu a Ajingi: ₦4,347,710,789.29.

Ginin madatsar ruwa da aikin ban ruwa a Dansoshiya, Kiru: ₦6,868,951,609.84.

Layin biyu na titin Audu Sambo daga AA Rano zuwa Gandun Albasa: ₦1,803,378,236.48.

Sabunta kwangilar titin 5km a Bunkure: ₦2,927,737,275.65.

Sabunta titin 5km a Kura: ₦3,207,480,443.31.

Faɗaɗa ayyukan kamfanonin da ke yin alamar hanya da gyaranta: ₦1,472,532,983.71.

Ayyukan tallafin musamman na 2025 a kananan hukumomi: ₦1,999,984,946.53.

Kammala cibiyar mata ta zamani da aka bari a K/Na’isa: ₦354,252,878.29.

Ɗaukaka cibiyar mata ta Gyadi-Gyadi: ₦196,976,673.70.

Ƙirƙirar Kwamitin Musamman Don Rage Cunkoson Gidajen Yari:

Kwamitin zai kula da:

Gudanar da bincike kan gidajen yari da wuraren tsarewa,

Shirya ayyukan tattalin arziki ga fursunoni,

Kamfen wayar da kai kan illar laifuka.

Mambobin kwamitin sun haɗa da:

Kwamishinan Shari’a (Shugaba),

Kwamishinan Tsaro da Ayyuka na Musamman,

Kwamishinan Harkokin Mata,

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha,

Kwamishinan Harkokin Addini,

Shugaban Hukumar Kula da Gidajen Yari, Kano,

Shugabar Kwamitin Yafe Wa Fursunoni,

Wakilin Alkalai,

Wakilin ‘Yan Sanda,

Wakilin Ma’aikatar Kananan Hukumomi,

Shehu Abdullahi (Hukumar Kare Hakkin Dan Adam).

Sauran Abubuwan da Aka Gudanar:

Soke kwangilar hanyoyi 5km a Garun Mallam, Madobi, T/Wada, Tsanyawa, Kura, Bebeji, Bunkure da Ajingi saboda rashin aiwatarwa.

Rantsar da AVM Ibrahim Umaru (Rtd.) a matsayin sabon Kwamishinan Tsaro da Ayyuka na Musamman.

Bayar da lambar yabo guda uku ga Gwamna Abba Kabir Yusuf daga Kungiyar Likitoci ta Najeriya (NMA) da Daily News Agency a matsayin Gwamnan Shekara da Mai Gidauniyar Jin Kai na Gaskiya 2024.

Sa hannu a cikin dokar “Water Users Associations Law 2025”.

Amincewa da mika wasu ƙudirin dokoki zuwa Majalisar Dokoki ta Jihar Kano:

Sauya dokar Hukumar Kula da yawon buɗe ido (Tourism Board) ta Kano 2025.

Sauya dokar Hukumar Zoological da Kula da Dabbobi ta Kano 2025.

Sauya dokar Hukumar Tarihi da Al’adu ta Kano 2025.

Sa hannu: Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida
20/5/2025

Shin haɗewar Atiku Abubakar da Peter Obi zata yi tasiri wajen kawar da Gwamnatin APC a 2027 ??
20/05/2025

Shin haɗewar Atiku Abubakar da Peter Obi zata yi tasiri wajen kawar da Gwamnatin APC a 2027 ??

Menene ra'ayin ku akan k**a waɗanda ake zargin Mata da Mahaifiyar riƙaƙƙen Ɗan bindiga Ado Alieru ne ? Da hukumomin Saud...
20/05/2025

Menene ra'ayin ku akan k**a waɗanda ake zargin Mata da Mahaifiyar riƙaƙƙen Ɗan bindiga Ado Alieru ne ? Da hukumomin Saudiyya s**a k**a

Photos: Muhammad T. Shehu

Lokutan sallah a jihar Kano da kewaye na yau Asabar 3 Jumada sani, 1445 AH/ 16 December, 2023.
16/12/2023

Lokutan sallah a jihar Kano da kewaye na yau Asabar 3 Jumada sani, 1445 AH/ 16 December, 2023.

Allah Ya Karbi rayuwar Mahaifiyar Sheikh Abdur-Razaq Yahya HaipanCikin daren yau, Muna rokon Allah Yajikanta da rahama  ...
16/12/2023

Allah Ya Karbi rayuwar Mahaifiyar Sheikh Abdur-Razaq Yahya Haipan

Cikin daren yau, Muna rokon Allah Yajikanta da rahama da Iyayen Mu baki ɗaya

Allah Ya gafarta Mata. Ya Kai Haske Kabarinta
Junaidu Ibrahim Adam As-salafy

Address

Sokoto

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GDK Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share