Tauraruwa-H

Tauraruwa-H Tauraruwa Shafin Jarida ne dake kokarin kawo maku sabbin rahotanni na labaran duniya a cikin harshen Hausa kyauta

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EUƘungiyar Nigeria Unite ta aika wa ...
14/11/2025

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EU

Ƙungiyar Nigeria Unite ta aika wa ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) da wasika mai zafi, tana zargin Ministan Abuja, Nyesom Wike, da haifar da barazana ga dimokiraɗiyar Najeriya ta hanyar murkushe ‘yan adawa da goyon bayan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin tabbatar da wa’adi na biyu ba tare da hamayya ba.

Ƙungiyar ta ce bayan rugujewar dimokiraɗiya a Mali, Burkina Faso da Nijar, yanzu haka Najeriya ma na kan layin tangal-tangal, saboda irin matakan zaluntar ‘yan adawa da kuma amfani da cin hanci wajen tilasta sauya sheƙa.

Ta gargadi cewar idan ba a dauki mataki ba, lamarin zai iya jefa Najeriya cikin rikici, ya kawo bacewar tsaro a yankin Sahel, tare da tura miliyoyin ‘yan Najeriya zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘yan gudun hijira.

Nigeria Unite ta kuma bukaci EU, AU, Amurka da Birtaniya su sanya takunkumi kan Wike da dakatar da shi daga tafiye-tafiye, tare da daukar mataki kan wasu manyan alkalan ƙasar, kwamishinan ‘yan sanda Abuja da hukumar INEC, domin cewar suna sabawa dokokin siyasa da na aikinsu.

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi KanuKungiyar Gamayyar Kungi...
19/10/2025

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi Kanu

Kungiyar Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) ta bayyana adawa da s**a mai tsanani kan shirin gudanar da zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu.

CNG ta ce wannan yunkuri da wasu shugabannin siyasa da na al’ada na kabilar Igbo, da masu kiran kansu ‘yan gwagwarmaya k**ar Omoyele Sowore, ke jagoranta tare da wasu ‘yan Arewa marasa kishin ƙasa wani makirci ne na yi wa ƙasa karan tsaye da barazana ga zaman lafiya da doka.

Kungiyar ta bayyana cewa Nnamdi Kanu da IPOB sun haifar da mutuwar fiye da mutane 1,200 ciki har da jami’an tsaro sama da 400, sun ƙone ofisoshin ‘yan sanda fiye da 100, kuma sun jawo asarar dukiya da ta haura ₦450 biliyan a Kudu maso Gabas.

CNG ta tunatar da cewa tun daga 2016 Kanu ya kasance mai yada ƙiyayya, tashin hankali da rarrabuwar kai ta hanyar IPOB da rundunarsa ta ESN, inda aka kashe ‘yan Arewa da dama, aka lalata kasuwanci, tare da hana zaman lafiya.

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da shari’ar Kanu ta tafi yadda doka ta tanada ba tare da matsin lamba na siyasa ba, tare da bukatar jami’an tsaro su hana duk wata zanga-zangar da zata kawo tashin hankali.

CNG ta gargadi ‘yan siyasa da masu daukar nauyin zanga-zangar da cewa za a bincike su, tare da kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya bari a yi masa barazana wajen yin doka bisa ra’ayi ko jin kai.

A ƙarshe, CNG ta jaddada cewa sakin Nnamdi Kanu ba zai kawo zaman lafiya ba, sai dai ya kara dagula ƙasa da karya tsarin shari’a. Ƙasar da ba ta mutunta doka ba, ba za ta samu zaman lafiya ba.

Sa hannu:
Comrade Jamilu Aliyu Charanchi
Koodineta Na Ƙasa, CNG
Abuja, Najeriya

Sanata Shehu Buba Ya Gaza Wajen Kare Martabar Arewa a Bangaren Tsaro – Cewar Comr. Haidar H. HasheemBa mutanen Bauchi ka...
08/10/2025

Sanata Shehu Buba Ya Gaza Wajen Kare Martabar Arewa a Bangaren Tsaro – Cewar Comr. Haidar H. Hasheem

Ba mutanen Bauchi kaɗai ba ne ke kuka da Sanata Shehu Buba saboda gazawarsa, mu ma a matsayinmu na al’ummar Arewacin Najeriya muna nuna takaicinmu da damuwarmu kan yadda ya kasa cika alkawarin da ke kansa a matsayin shugaban kwamitin tsaro da tattara bayanan sirrin tsaro a majalisar dattawan Najeriya.

A matsayinsa na wanda yake rike da wannan muhimmin matsayi, al’ummar Arewa sun yi tsammanin ganin sabon salo na yaki da rashin tsaro, da tsari mai inganci na kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Amma abin takaici, ko satin daya wuce an sace wasu kansiloli da wasu mutane a jihar Zamfara, amma bamu taɓa jin Shehu Buba yace komai ba akan matsalar tsaron Arewacin Najeriya.

Sanata Shehu Buba ya zama tamkar wanda ya kame baki, ya kasa amfani da matsayinsa wajen tsawatarwa da neman ingantacciyar dabarar kawo karshen kashe-kashe da satar mutane da ya addabi Arewa.

A yanzu lokaci ne da ‘yan Arewa za su tashi tsaye su tambayi irin gudunmawar da yake bayarwa, ko dai yana kare al’umma ne ko kuwa yana kare siyasa kawai. Domin idan gaskiya ne yana son Arewa ta samu tsaro, da tuni ya zamo murya mai ƙarfi wajen kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro su tashi tsaye wajen kawo karshen wannan bala’i.

Arewa ta gaji da jin alkawura marasa tasiri, muna bukatar aiki, ba magana ba.

~ Comr. Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writers

Gwamnatin Filato ta k**a ƴar fafutuka saboda fallasa gazawar gwamnati – ‘Yan Najeriya na s**ar matakinJos, Filato — Raho...
07/10/2025

Gwamnatin Filato ta k**a ƴar fafutuka saboda fallasa gazawar gwamnati – ‘Yan Najeriya na s**ar matakin

Jos, Filato — Rahotanni daga Jos sun tabbatar da cewa jami’an tsaro a jiya sun k**a Ummulkhair Abdulmumin Iliyasu, wata matashiya ‘yar fafutuka kuma mai amfani da kafafen sada zumunta wajen bayyana matsalolin da al’umma ke fuskanta a jihar Filato, musamman a cikin karamar hukumar Jos ta Arewa.

Lauyan ta da ya tabbatar wa da Zinariya faruwar lamarin ya bayyana cewa k**a Ummulkhair ya biyo bayan wallafe-wallafen da take yi a dandalin Facebook inda take bayyana gazawar gwamnati wajen samar da ingantattun ayyuka, tsaro da kula da matasa a yankin.

Majiyoyi sun ce jami’an tsaron ƴan sandan jahar Filato a sashin binciken manyan lefuka sun kai farmaki gidanta ne inda basu sameta ta ba sai s**a gayyace ta, inda nan take ta amsa gayyatar tare da ayarin lauyoyin ta.

A ofishin nasu, sun nemi ta goge dukkan bidiyon da ta yi tana s**ar gwamnatin Filato da shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa tare da basu haƙuri. Lamarin da ya sa lauyoyin ta s**a turɓune s**a ce, hakan ba mai faruwa bane domin kuwa gaskiya ta faɗa bata yi ƙage ga kowa ba.
An hangi shugaban ƙaramar hukumar Jos ta Arewa Barr. JK Chris yana ta zarya a ofishin shugaban ƴan sandan jahar Filato inda ya buƙaci sai an kulle Ummulkhair.


Bayan tsare ta na dogon lokaci, lauyan ta ya nemi belin ta inda aka ba shi kuma aka ce su koma yau Talata domin ci gaba da tuhumar da ake mata.

Ƴan Najeriya da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun yi martani

Masu kare hakkin bil'adama a kafafen sada zumunta irin su Abba Hikima, Ɗan Bello, Human Rights Watch Nigeria, Amnesty International Nigeria, da wasu ‘yan fafutuka a Jos da lungu da saƙon Najeriya sun bayyana cewa k**a Ummulkhair cin zarafi ne ga ‘yancin faɗar albarkacin baki k**ar yadda Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya tanada a sashe na 39.

Wata sanarwa da ƙungiyar Centre for Civic Freedom (CCF) ta fitar ta ce:

“K**a Ummulkhair saboda ta bayyana ra’ayinta kan yadda gwamnati ke gudanar da mulki, babban abin damuwa ne. Wannan lamari na iya zama barazana ga sauran matasa masu rajin gaskiya a jihar Filato.”

Gwamnatin Filato Da Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa Basu Ce Komai Ba Game Da Lamarin

Kawo yanzu, gwamnatin Filato da shugaban ƙaramar hukumar Jos basu ce komai game da lamarin ba inda matasa suke zargin da hannunta wajen wasu maƙarraban gwamnati wajen k**a ƴar fafutukar.

Kiran Neman Adalci

A halin yanzu, ana kiran gwamnatin Filato ƙarƙashin Caleb Mutfwang da Shugaban Karamar hukumar Jos ta Arewa Barr JK Chris su saki Ummulkhair nan da nan tare da binciken adalci kan yadda aka yi gumurzu wajen k**a ta.

Kammalawa

K**a Ummulkhair Iliyasu Abdulmumin ya sake tayar da muhawara kan irin matsin lamba da masu fafutuka da ‘yan jarida ke fuskanta a Najeriya, musamman idan s**a fallasa gazawar gwamnati ko shugabanni.
Masana na ganin cewa irin waɗannan abubuwa na iya ta’azzara rashin yarda tsakanin gwamnati da jama’a, idan ba a bi hanyoyin dimokuraɗiyya wajen magance su ba.

Auwal Saleh
Jos, Filato.
7 ga Oktoba, 2025.

Kun Gaza Samar Da Tsaro a Najeriya Amma Kuna Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro Na UN – Comr Haidar H Hasheem........
29/09/2025

Kun Gaza Samar Da Tsaro a Najeriya Amma Kuna Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro Na UN – Comr Haidar H Hasheem
......Permanent peace a gida kafin Permanent seat a UN!

Na tabbata al’ummar Najeriya musamman mu a Arewacin ƙasar nan mun gaji da ji da gani: tsaro ya gagara, rayuka da dukiyoyin al’umma suna salwanta kullum, amma gwamnati ta kasa kawo mafita ta dindindin.

Abin takaici shi ne, duk da wannan gazawa, har yanzu ana neman kujera ta dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (UN Security Council). Tambayata ita ce: ta yaya za a nemi kujerar dindindin a wajen duniya alhali kuwa an kasa samar da tsaro na dindindin a gida?

Idan har gwamnati na son ta gina karɓuwa a kasashen duniya, to wajibi ne ta fara tabbatar da zaman lafiya da tsaro a cikin ƙasar nan. Ba za mu ci gaba da zama cikin halin kashe-kashe, garkuwa da mutane, da hare-haren ta’addanci ba, a lokacin da shugabanni ke neman kujerar yabo a waje.

Daga farko ya k**ata a samar da tsaro na hakika ga ‘yan ƙasa kafin a nemi tsayuwa kan babban kujerar duniya.

✍️ Comr Haidar H Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writers

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar  Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad ...
28/09/2025

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad Abubakar Isah Ana Zarginsu da Karɓar Naira Miliyan 23 a Badakalar Kwangila Da Aka Danganta Da Hon. Adamu Aliyu

Daga Tukur I. Tukur

Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, tare da Sa’ad Abubakar Isah, ana zargin sun karɓi Naira miliyan 23 daga hannun Mohammad Jidda, wanda ya shigar da ƙara kan batun badakalar kwangila a Jami’ar Jos ƙarar tana hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka (ICPC).

Wannan batu ya fito fili ne a wata hira da mai aikin, Mr. Lawal Abubakar, wanda yake cikin rashin lafiya a gidansa da ke Dutsin-Ma, Jihar Katsina. Ya ce Hon. Idrisa Jidda ɗan’uwan mai ƙarar ne, Mohammad Jidda.

Mr. Lawal Abubakar ya bayyana cewa Hon. Idrisa Jidda, wanda a halin yanzu yake matsayin Mashawarcin Gwamna kan Harkokin Gidaje ga Gwamna Babagana Umara Zulum na Jihar Borno, ya karɓi Naira miliyan 20 daga asusun Zenith Bank na kamfanin Imanal Concept Ltd, mallakar Sa’ad Abubakar Isah wannan kuɗi na daga cikin abin da ake tuhuma da shi da aka danganta da sunan Hon. Adamu Aliyu.

Mr. Abubakar ya ce shi dai kawai ya gabatar da Hon. Adamu Aliyu ga mai kasuwancin Mohammad Jidda, ya kuma umarce shi ya sanya kuɗi a asusunsa. Bayan kwangilar ta karye, “na faɗa wa Adamu ya mayar da duk abin da aka biya shi, kuma an shaida min cewa ya mayar.”

A cewar Mr. Lawal Abubakar, Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah sun tunkari Mohammad Jidda s**a karɓi kuɗaɗe daga kamfaninsa, Mohibba Investment Limited, s**a raba su tsakaninsu.

“Sun yaudari Mohammad Jidda suna cewa an biya Hon. Adamu Aliyu. Amma a ranar 29 ga Disamba, 2023, Alhaji Idrisa Jidda ya karɓi Naira miliyan 20 da aka shigar masa a asusun Zenith Bank daga Imanal Concept Ltd. Ina da rasit ɗin banki da zai tabbatar da hakan. Dukkanin asusun da aka yi ma’amala da su suna a Zenith Bank,” in ji Mr. Lawal Abubakar.

Ya ƙara cewa akwai ƙarin takardu da hujjoji da ke nuna wasu ma’amaloli da s**a shafi Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah.

“Sa’ad Abubakar Isah tare da Hon. Idrisa Jidda sun taɓa haɗuwa da mai ƙarar s**a ce suna wakiltar Mr. Lawal Abubakar. S**a karɓi Naira miliyan 23 s**a raba tsakanin su. Saboda haka ya k**ata mai ƙarar ya mayar da ƙarar ne a kan Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah (mai kamfanin Imanal Concept Ltd), ba kan Hon. Adamu Aliyu ba,” ya yi nuni.

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar KebbiKungiyar Democ...
19/09/2025

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.

A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.

Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.

DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.

Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Has...
18/09/2025

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Hasheem

Shugaban ƙungiyar Arewa Media Writer’s, na ƙasa ya bayyana matuƙar takaici da bacin rai kan kisan gilla da ‘yan bindiga s**a yi wa Hakimin Dogon Daji a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda s**a yi masa yankan rago har lahira. Wannan lamari abin kunya ne ga ƙasa baki ɗaya kuma babban ƙalubale ne ga gwamnati da hukumomin tsaro k**ar yadda rahotan BBC Hausa da Leadership s**a kawo rahotan.

Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa lamarin tsaro a Arewacin Najeriya na ta ƙara tabarbarewa, inda ake ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, sace jama’a, kona gidaje da gonaki, tare da hallaka shugabannin al’umma ba tare da tsoro ba. Wannan yanayi ya jefa dubban mutane cikin fargaba, gudun hijira, da rasa amincewa ga gwamnati.

Ya k**ata gwamnati ta gane cewa tsaro ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshiƙin kowace al’umma, kuma kariya ga rayuka da dukiyoyi wajibi ne na gwamnati. Rashin ɗaukar mataki mai tsauri na iya ƙara dagula rayuwar jama’a da kuma barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya.

A wannan yanayi, muna kira da:

1. Gwamnati ta tashi tsaye da gaggawa wajen murkushe ‘yan bindiga da duk wata ƙungiya ta ta’addanci a Arewa.

2. A samar da kayan aiki na zamani ga jami’an tsaro, tare da horo da ƙarfafawa domin su iya gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata.

3. A shimfiɗa tsare-tsare na dindindin don tabbatar da tsaro a ƙauyuka da birane.

A madadin al’ummar Arewa da ƙungiyar Arewa Media Writer’s, ina kira da a ɗauki wannan kisan da aka yi wa hakimin Dogon Daji a matsayin kira na musamman ga shugabanni a dukkan matakai, domin lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan masifar tsaro da ta addabi yankinmu.

A ƙarshe, ina addu’a ga Allah Madaukakin Sarki Ya jikan hakimin da aka kashe, Ya ba iyalansa da al’ummarsa juriya, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai ɗorewa ga Najeriya baki ɗaya.

✍️ Rubutawa:
Comr. Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer’s

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin SiyasarsaDaga Abdul-...
09/09/2025

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin Siyasarsa

Daga Abdul-Azeez Suleiman

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna, ya gamu da zanga-zangar ƙin karɓarsa a Owerri, Jihar Imo, lokacin da ya halarci Taron Odenigbo 2025 a Assumpta Cathedral. Jama’a sun fito da kwalaye da ƙorafe-ƙorafe, suna zarginsa da kalaman wariya kan kabilar Igbo a baya.

Wannan martani bai tsaya kan shi kaɗai ba, ya kuma fito da tsohuwar matsalar rashin haɗin kai, raunin Yaƙin Basasa, da kuma gajiyar jama’a ga shugabannin da ake ganin sun rabu da halin rayuwar talakawa.

Masu zanga-zangar har sun yi kira ga a tsawatar wa Peter Obi saboda kusancinsa da shi, abin da ya nuna cewa kowane ɗan siyasa na iya fuskantar tambaya muddin yana da alaƙa da mutanen da ake kallon masu raba kan ƙasa.

Zanga-zangar ta zama alamar cewa jama’a na da ƙarfi wajen kalubalantar manyan ‘yan siyasa, musamman a wannan zamani na kafafen sada zumunta. Darasin da ke ciki shi ne shugabanni su daina rarrabuwar kawuna, su rungumi tattaunawa, su girmama tarihi, domin kawai haka za a samu haɗin kan ƙasa mai bambance-bambance.

Jama’a Sun Yi Masa Watsi, Sun Nuna Ƙiyayya da Siyasar Rarrabuwar irin ta El'rufai, sun kuma shawarci Peter Obi da ya gaggauta nesanta kansa da El'rufai don tsira da mutuncinsa.

Rashin Tsaro: Lokaci Yayi Da Gwamnati Za Ta Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Arewa ~ Cewar Shugaban Kungiyar M...
30/08/2025

Rashin Tsaro: Lokaci Yayi Da Gwamnati Za Ta Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Arewa ~ Cewar Shugaban Kungiyar Marubutan Arewa

Shugaban ƙungiyar marubutan Arewa a kafafen sadarwar zamani Arewa Media Writer, Comr Haidar H. Hasheem, yayi kira da kakkausar murya ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da gwamnatin jahohi da su dauki matakan gaggawa da na dindindin wajen kawo karshen matsalar tsaron da ta addabi al’ummar Arewa musamman a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da sauran sassa na Arewacin Najeriya.

Shugaban ya nuna matuƙar damuwa kan yadda yan ta’adda ke ci gaba da kai hare-hare cikin ƙauyuka, suna kashe mutane a masallatai, suna sace jama’a tare da ƙona gidaje da dukiyoyi. Wannan lamari ya jefa dubban mutane cikin tsananin fargaba, barin garuruwansu da kuma rasa amincewa ga gwamnati da hukumomin tsaro.

Ya k**ata gwamnati ta fahimci cewa tsaron ƙasa ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshikin ci gaban kowane al’umma, don haka wajibi ne a ɗauki matakin gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Rashin yin haka na iya sa al’umma su rasa kwarin gwiwar dogaro ga gwamnati.

Kare rayukan al'umma wajibi ne ga gwamnatin kasa, haka kuma ya k**ata ita gwamnati ta samarwa da jami'an tsaro kayan aiki na zamani tare da basu ƙarfin gwiwa wajen daƙile matsalolin tsaron da ake fama da su.

A madadin al’ummar Arewa baki ɗaya, da marubutan Arewa muna kira ga shugabanni a kowane mataki da su yi tsayuwar daka wajen ganin cewa an kawo karshen wannan matsalar tsaron da ta yi katutu a Arewa.

A ƙarshe, ina roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya kawo ƙarshen wannan fitina, Ya ba Najeriya da Arewa zaman lafiya da tsaro nagari.

Rubutawa ✍️
Comr Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer's

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gy...
02/08/2025

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gyara Jam’iyya Cikin Gaskiya

Ofishinmu na Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) yana bayyana damuwarsa matuka kan yadda wasu sarakunan gargajiya ke kiran waya da nufin matsin lamba ga Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Alhaji Nafiu Bala Gombe, domin ya sauya matsayinsa na kare tsarin dimokuradiyya da doka na jam’iyyar.

Wannan barazana da kuma kiran da ake yi ga wasu mambobin Kwamitin Zartaswa na Kasa (NWC) domin su ja da baya daga goyon bayan shugabansu, abin takaici ne kwarai, musamman ganin cewa sarakuna sun bar turbarsu ta raya al’adu da zaman lafiya, sun rungumi muradin wasu 'yan siyasa masu son karbe jam’iyya ta kowane hali.

MAKIRCI NA BAYA-BAYAN NAN

Bayanan sirri daga majiya mai karfi na nuni da cewa wasu manyan ’yan siyasa da s**a hada da Janar David Mark da Mallam Nasir El-Rufai da wasu gungun mutane sun hada wata kungiya da ke shirin tura dattawa su je Gombe domin matsawa mahaifiyar Shugaban rikon kwarya da nufin tilasta masa mika jam’iyyar da nufin cinma burinsu na siyasa a shekarar 2027.

Wannan yunkuri na ziyarar mahaifiyar Shugaban jam’iyyar abu ne da ba za mu lamunta da shi ba. Hakan na nuna cewa wasu sun sadaukar da dimokuradiyya ga son zuciya da yin coge don biyan muradinsu na 2027.

1. Muna da tabbaci daga bayanen sirri masu inganci cewa wadannan sarakuna na kokarin tilasta Alhaji Nafiu Bala Gombe ya mika jam’iyya ga 'yan siyasa masu matasanancin kwadayin mulki ta hanyar matsa masa da kiraye-kiraye a wayarsa tare da shisshigi a boye. Wadannan sarakuna ba su kyauta ba, saboda suna neman rage kima da martabar al'adunmu masu nagarta ta hanyar neman zama 'yan koren masu mayatar son mulkin siyasa a shekarar 2027. Wannan abin jimami ne ga dukkan mai kishin martabar masarautinmu.

2. Wannan kuskure ne mai muni daga bangaren sarakuna, wadanda ya k**ata su tsaya a gefe su kasance iyayen kasa masu kima.

3. Mu na kara fayyacewa: Sarakuna ba su da hurumin shiga harkokin jam’iyyar ADC ko zama 'yan gada-gadar 'yan siyasa. Wannan ba shekarar 1983 ba ce; yanzu idon kowa a bude yake. ADC ba ta sayarwa ba ce!

4. Alhaji Nafiu Bala Gombe ba zai ja da baya ba, yana da cikakken goyon bayan dokokin jam’iyya da mambobinta masu kishin kasa.

5. Wadanda suke fakewa da cewa suna hidimar “sasantawa”, yaudarar jama'a suke, da nufin biyan muradin 'yan cogen Hadaka ta Zaben 2027. Su sani cewa za mu bayyana sunayensu da cikakken bayani game da boyayyiyar manufarsu, in bukatar yin hakan ta taso.

6. Ga wadanda suke matsayin sarakuna amma s**a tsunduma siyasa da goyon bayan hargitsi, muna ba ku shawara: ku koma ku kula da masarautunku. Kada ku sayar da martabarku da al'adunmu masu nagarta don biyan bukatun 'yan siyasan da s**a shahara wajen yaudarar al'umma shekara da shekaru.

MATSAYARMU A KAN WANNAN KATSALANDAN:

Jam’iyyar ADC ba ta sayarwa ba ce. Ba za mu bar makircin wasu mayaudaran 'yan siyasa ya kassara mulkin dimokuradiyyan kasar nan ba, ko ya lalata alkiblar jam’iyyar ADC ba. Kuma za mu fallasa kowane mai hannu a ciki — ko saraki ne shi ko dan bangar siyasa.

In kunne ya ji, jiki ya tsira.

Sanya hannu:
Dr. Aminu Sani Alhassan
Mai Baiwa Shugaban Rikon Kwarya Shawara kan Harkokin Jama’a
Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC)
Abuja

Rikicin ADC Ya Kara Ta'azzara: Bala Gombe Ya Ayyana Kansa a  Matsayin Shugaban Jam'iyya, Ya fatattaki su El-Rufa’i Rikic...
31/07/2025

Rikicin ADC Ya Kara Ta'azzara: Bala Gombe Ya Ayyana Kansa a Matsayin Shugaban Jam'iyya, Ya fatattaki su El-Rufa’i

Rikicin cikin gida a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ya ƙara ɗaukar sabon salo, bayan Nafiu Bala Gombe, Mataimakin Shugaban ƙasa na jam’iyyar, ya ayyana kansa a matsayin Shugaban rikon kwarya.

A cewarsa, hakan ya zama dole sak**akon abin da ya kira ƙoƙarin wasu manyan 'yan siyasa – ciki har da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i – na mallake jam’iyyar tare da cusa son zuciya a harkokin tafiyar da ita.

Bala ya zargi tsoffin shugabannin jam’iyyar da mika madafun iko ga wasu 'yan bangar siyasa a cikin ADC, inda ya bayyana su a matsayin ‘sojojin gona’ masu burin hallaka tsarin dimokuradiyya da jam’iyyar ta gina tsawon shekaru.

Ya ce wadannan sojojin haya, wadanda ba su wata alaka da ADC, suna shirin mayar da ita jam’iyyar aljihun mutane irin su Elrufai, domin cimma muradun kansu na siyasa.

A cewarsa, El-Rufa’i da magoya bayansa suna kokarin amfani da ADC a matsayin wani tsani na wucin-gadi domin cimma wata manufa ta siyasa da ke nuni da shirinsu na fuskantar zaben 2027.

Ya bayyana yunkurin Elrufai da 'yan korensa a matsayin babbar barazana ga tsarin shugabanci na jam’iyyar da dimokuradiyya gaba ɗaya.

Bala ya kuma bukaci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da ta girmama kundin tsarin mulkin jam’iyyar ADC, tare da kin amincewa da duk wani yunƙurin da ya saba da tsarin. Ya ce matakin da ya ɗauka na zama Shugaban rikon kwarya yana da cikakken tushe a kundin tsarin mulkin jam’iyyar, kuma ya ti hakan ne don kare mutuncin ADC daga mamayar da ke neman hana ta numfashi.

Ya jaddada cewa ba za su yi shiru ba yayin da wasu ke yunƙurin lalata abin da s**a gina na tsawon shekaru, kuma duk wani yunkuri da El-Rufa’i da abokan tafiyarsa ke yi ba zai kai ga nasara ba.

A karshe ya bukaci Hukumar Zabe ta Kasa ta jaddada kasancewarsa shugaba a hukumance.

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tauraruwa-H posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tauraruwa-H:

Share

Category