Arewa News Hausa

Arewa News Hausa Don samun labarai daga arewacin Najeriya , dama duniya baki daya.

LABARI DA DUMI-DIMIN SA!!!Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci kan tsaro a Najeriya, inda ya bawa shugabannin rundunonin tsaron ...
04/11/2025

LABARI DA DUMI-DIMIN SA!!!

Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci kan tsaro a Najeriya, inda ya bawa shugabannin rundunonin tsaron ƙasar da gwamnonin jihohi 36 waɗanda sune Chief Security a jihohi, wa'adin kwana 30 su kawo masa rahoton yin nasarar kawar da dukkannin ƴan ta'adda a faɗin ƙasar.

Me za ku kan wannan maganar?
Arewa News Hausa

AlhamdulilLah Musulunci Ya Sami QaruwaDA ƊUMI-ƊUMI: Mawakin Duniya Dan Kudanciɲ Najeriya, Burna Boý Ya Kàrbì MusuĺùɲcìSh...
04/11/2025

AlhamdulilLah Musulunci Ya Sami Qaruwa
DA ƊUMI-ƊUMI: Mawakin Duniya Dan Kudanciɲ Najeriya, Burna Boý Ya Kàrbì Musuĺùɲcì

Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da 'Burna Boy', ya bayyana cewa ya karɓi Musuluɲci bayan dogon lokaci yana nazari da neman gaskiya game da addini da manufar rayuwa.

A cewar Burna Boy, babu wanda ya tilasta masa sauya addini, sai dai ya samu nutsuwa da fahimtar gaskiya bayan zurfin tunani.

“Na binciki addinai da yawa, ina tambayar kaina menene gaskiya game da rayuwa. A ƙarshe zuciyata ta samu natsuwa da Musulunci, don haka na karɓe shi,” in ji shi.

Mawakin ya ƙara da cewa yana mutunta dukkan addinai, kuma yana kira ga jama’a su zauna lafiya da juna, su guji rarrabuwa saboda addini ko ƙabila.
Boy, wanda ya yi fice da wakoki kamar “Last Last” da “City Boys”, ya ce burinsa shi ne ya rayu cikin gaskiya da mutunci, ba wai don sunan addini kawai ba.

Arewa News Hausa

LABARI MAI DAƊI: Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da Burna Boy, ya bayyana cewa Allah ya Gan...
03/11/2025

LABARI MAI DAƊI: Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da Burna Boy, ya bayyana cewa Allah ya Ganar dashi Gaskiya ya bar addinin Kiristanci ya karɓi Musulunci ne bayan dogon tunani da bincike kan neman gaskiya.

A cewar Burna Boy, matakin da ya ɗauka ba wai saboda matsin lamba ba ne, sai don ƙwarewar da ya samu ta tunani da nazari game da manufar rayuwa da ma’anar addini.

“Na dade ina bincike da tambayar kaina meye gaskiya game da rayuwa da addini. Daga ƙarshe, na ji zuciyata ta natsu da Musulunci. Wannan shi ne dalilin da ya sa na rungumi wannan hanya,” in ji shi.

Mawakin ya bayyana cewa, duk da wannan sauyi, yana girmama sauran addinai, tare da kira ga mutane su zauna lafiya da juna ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba.

Burna Boy, wanda ya shahara da wakokinsa na duniya kamar “Last Last” da “City Boys”, ya ce burinsa shi ne ya zama mutum mai gaskiya da mutunci, komai bambancin fahimta.

Shigo Shafin Jaridar 👉 Arewa News Hausa👈 Ta Nan, Ku Yi Following Yanzu Karku Bari Komai Ya Wuceku...

YANZU-YANZU: Jaridar Premium Times ta rawaito cewa rundunar sojin Najeriya ta bayyana sunayen sojoji 16 da Hukumar Leƙen...
01/11/2025

YANZU-YANZU: Jaridar Premium Times ta rawaito cewa rundunar sojin Najeriya ta bayyana sunayen sojoji 16 da Hukumar Leƙen Asirin Tsaron Najeriya ke tsare da su bisa zargin yunƙurin shirya juyin mulki a ƙasar.

‎1. Brigadier Janar Musa Abubakar Sadiq

‎An haife shi a ranar 3 ga Janairu, 1974. Yana da lambar aiki N/10321. Ya fara karatun soja a NDA daga 14 ga Agusta 1992 zuwa 20 ga Satumba 1997. Ana zargin shi ne jagoran shirin juyin mulkin.

‎Dan asalin jihar Nasarawa ne, kuma mamba ne na Regular Course 44. Ya zama kolonel a 2015 sannan brigadier janar a 2019. Yana daga Infantry Corps.

‎A watan Oktoba 2024, an taba tsare shi bisa zargin karkatar da kayan tallafin palliative na shinkafa da kuma sayar da kayan aikin soja, ciki har da injinan janareta da motocin aiki. Ya taɓa zama kwamandan 3rd Brigade, Kano da kuma Garrison Commander, 81 Division, Lagos.

‎2. Kolonel M.A. Ma’aji

‎Dan asalin jihar Neja (Nupe). An haife shi a 1 ga watan Maris, 1976, yana da lambar aiki N/10668. Ya fara koyon soja a 18 ga Agusta 1995 ya kammala a 16 ga Satumba 2000.

‎Ana zargin shi da kasancewa ɗaya daga cikin masu tsara shirin juyin mulkin. Yana daga Infantry Corps, kuma ya zama kolonel a 2017.

‎Ya kasance kwamandan 19 Battalion a Okitipupa, jihar Ondo, kuma ya shiga cikin aikin soja na Operation Crocodile Smile II a 2017.


‎-3. Laftanar Kolonel S. Bappah

‎Dan asalin jihar Bauchi, mai lambar aiki N/13036. An haife shi a 21 ga Yuni, 1984.
‎Memba ne na Signals Corps, kuma ya shiga NDA daga 27 ga Satumba 2004 zuwa 4 ga Oktoba 2008.
‎Yana cikin 56 Regular Course.

‎4. Laftanar Kolonel A.A. Hayatu

‎Dan asalin jihar Kaduna, mai lambar aiki N/13038. An haife shi a 13 ga Agusta, 1983.
‎Yana daga Infantry Corps kuma mamba ne na 56 Regular Course.


‎5. Laftanar Kolonel P. Dangnap

‎Dan asalin jihar Filato, mai lambar aiki N/13025. An haife shi a 1 ga Afrilu, 1986.
‎An taba gurfanar da shi a kotun soja tare da wasu jami’ai 29 a 2015 saboda laifuka da s**a shafi yakin Boko Hara

Kowane Dan Adam Allah ya bashi wata baiwa wadda bai ba wani ita ba, Dame ka fi Dangote?
30/10/2025

Kowane Dan Adam Allah ya bashi wata baiwa wadda bai ba wani ita ba, Dame ka fi Dangote?

ALLAH YA KARA NAUYIN KASA!!!Wannan Sunan Shi Jankare Yana da sansani a cikin karamar hukumar Dutsinma ta jahar Katsina.B...
30/10/2025

ALLAH YA KARA NAUYIN KASA!!!

Wannan Sunan Shi Jankare Yana da sansani a cikin karamar hukumar Dutsinma ta jahar Katsina.

Bayanai sun nuna wasu Yan ta'adda daga wata daba sun kashe shi yau.

Jankare baida imani ko kadan, ya kashe mutane da dama, da yiwa mata fyade.

An ce saboda rashin imani Yana baiwa karnenshi Naman mutane suna ci.

Shima idan yayi shaye-shaye Yana sa yaranshi su soya mishi Naman mutane Yana ci.

Me zaku ce game lamarin Jankare?

Kuna son samun sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa yanzu kada ku bari a wuce ku.

DAUKAR NAUYIN JUYIN MULKI A NAJERIYA.Tsohon gwamnan jahar Bayelsa Timi Silver ya tsere ya bar Najeriya inda ya tsallaka ...
28/10/2025

DAUKAR NAUYIN JUYIN MULKI A NAJERIYA.

Tsohon gwamnan jahar Bayelsa Timi Silver ya tsere ya bar Najeriya inda ya tsallaka ta yankin Niger Delta ya fada Kasar Senegal.

Ana zargin shi da daukar nauyin yunkurin yiwa Shugaba Tinubu juyin mulki Wanda ba a Samu Nasara ba.

Yanzu haka dai jami'an tsaro sun rufe gidanshi.

Kuna son samun sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa yanzu kada ku bari a wuce ka.

27/10/2025

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya ya sake lashe zabe..
Wace fata za ku yi mishi?

WAI ME YASA SHUGANNIN AFRICA SU KE SON MULKI  IDO RUFE FIYE DA RAYUWAR MUTANE?Wannan shi ne Isah Chiroma shi ne Dan taka...
24/10/2025

WAI ME YASA SHUGANNIN AFRICA SU KE SON MULKI IDO RUFE FIYE DA RAYUWAR MUTANE?

Wannan shi ne Isah Chiroma shi ne Dan takarar shugaban kasar kamaru Wanda ya fafata zabe da shugaba Mai ci Paul Bia, a zaben da aka gudanar Yan kwanakin nan da su ka gabata Wanda har yanzu ba a Fadi sakamakon zaben ba a hukumance saboda zaben ya zo da tangarda ana zargin an tafka magudi.

Isa Chiroma ya hakikance shi ya ci Zabe, shima Shugaba Paul Bia Yace shi yaci zabe.

Yanzu Isah Chiroma ya yi Kira ga Yan kasa akan su fito suyi zanga-zanga su nunawa duniya Shi yaci Zabe Amman an Hana shi.

Abin tambaya anan tsawon wane lokaci talakawan kamaru ke cikin matsin rayuwa Bai ce a fito a yi zanga-zanga ba sai yanzu?

Abin tambaya anan shin idan mutane su ka fito zanga-zanga tare da yayanshi za a yi?

Shin wannan zanga-zanga da yake son a yi Don cigaban kasa da al'umma ya ke son ayi ta ko don biyan bukatar kan shi?.

Shin idan aka yi zanga-zanga aka kashe mutane wa yayi asara?

Talakawa yakamata mu fahimta mafi yawan shugabannin Africa suna son mulki ido rufe Koda kowa mutane zasu rasa rayukan su.

Kada mu kuskura wani Dan siyasa ya tunzuramu muje yin zanga-zanga a kashe mu a banza don biyan bukatar shi.

Shawara kyauta.
🏃🏃🏃

Inji Abdulaziz Bello

Ana zargin Abokan sa da kashe shi ta hanyar sanya masa guba (Poison) a lemo yasha a garin Abuja……Wannan ango sunansa Abd...
23/10/2025

Ana zargin Abokan sa da kashe shi ta hanyar sanya masa guba (Poison) a lemo yasha a garin Abuja……

Wannan ango sunansa Abdurrahman Sabo sale maina wanda akafi sani da DUDU BOY.

Dealern motoci ne a garin Abuja, amma haifaffen Garin Gombe.

Yana da matarsa daya kafin daga bisani ya hadu da wacce kuke gani acikin hoto ta Zama ta biyu acikin matansa wanda har zuwa lokacin da aka kasheshi ya ajjeta a gidansa dake Gombe.

Tsahon lokaci maina, na rayuwarsa cikin farinciki da annushuwa kafin aka sanya masa guba a lemon kwalba, wanda itace tayi sanadin mutuwarsa a jiya lahadi.

Ana zargin wasu daga abokan kasuwancinsa ne s**a sanya masa guba a lemon saboda maganar kudi daya shiga tsakaninsu.

Allah kajikan Abdurrahman da rahama, kasa ya huta

22/10/2025

Wasu da ake zargin masu kwacen waya ne sun hallaka wata ma’aikaciyar jinya a Asibitin Gambo Sawaba da ke Zariya, Jihar Kaduna, mai suna Hadiza Musa, wadda ta kasance mataimakiyar shugabar sashen karbar haihuwa a asibitin.

Bayanan da aka samu sun nuna cewa, lamarin ya faru ne da yammacin Asabar, lokacin da marigayiyar ke dawowa daga aiki. Mijinta, Hamza Ibrahim Idris, wanda ke aiki a Abuja, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce matarsa ta hau babur din haya misalin karfe 6:30 na yamma, amma daga baya wasu s**a kai mata hari domin kwace wayarta.

A cewarsa, bayan barayin sun sace wayarta, sai s**a jefar da ita a gefen t**i kusa da filin Idi na Mallawa, Tudun Wada Zariya. Wani mutum mai taimako ne ya kai ta asibiti, daga bisani aka tura ta zuwa Asibitin Koyarwa na ABU, Shika, inda likitoci s**a tabbatar da rasuwarta.

Sakataren Asibitin Gambo Sawaba, Abdulkadir Balele Wali, ya bayyana marigayiyar a matsayin kwararriya mai jajircewa da sadaukarwa wajen ceton rayukan jama’a, yana mai cewa rasuwarta babban rashi ne ga asibitin gaba ɗaya.

Majiyarmu tayi kokarin Jin ta bakin Kakakin rundunar ’yan sanda na Jihar Kaduna, Mansur Hassan, sai hakan yaci tura.

ALLAH YA JIKAN MAZAN YAKIB0k0 Har@m sun yiwa mayakan Sojoji a yankin Bama jihar Borno harin kwanton bauna inda aka samu ...
21/10/2025

ALLAH YA JIKAN MAZAN YAKI

B0k0 Har@m sun yiwa mayakan Sojoji a yankin Bama jihar Borno harin kwanton bauna inda aka samu asaran rayuka na sojoji da Civilian JTF

Laftanar Kanar Aliyu Sa'idu Paiko shine Commanding Officer 202 Tank Battalion wanda suke fafata yaki B0k0 Har@m a Borno, yana daga cikin wadanda s**a mutu a harin

Kuskure aka samu, lokacin da Sojoji s**a farmaki 'yan B0k0 Haram, da s**a tashi dawowa madadin su canza hanya sai s**a dawo ta hanyar da s**a bi s**a kai hari, shine 'yan ta'addan s**a shirya wa Sojojin mummunan harin kwanton bauna

Yana daga cikin dabarun yaki da aka koya daga Manzon Allah (SAW) shine canza hanya, Sunnah ne a dinga canza hanya saboda kaucewa shirin abokan gaba

Muna rokon Allah Ya karbi shahadar Laftanar Kanar Aliyu Paiko da sauran wadanda aka kashe a harin

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share