Arewa News Hausa

Arewa News Hausa Don samun labarai daga arewacin Najeriya , dama duniya baki daya.

YANZU-YANZU: An Cimma Yarjejeniyar Sulhu Tsakanin Al’umma Da Ƴan Bindiga A Faskari, Jihar KatsinaRahotanni daga ƙaramar ...
14/09/2025

YANZU-YANZU: An Cimma Yarjejeniyar Sulhu Tsakanin Al’umma Da Ƴan Bindiga A Faskari, Jihar Katsina

Rahotanni daga ƙaramar hukumar Faskari da ke Jihar Katsina sun tabbatar da cewa an kulla zaman sasanci tsakanin al’ummar yankin da wasu daga cikin ƴan bindiga da ke addabar yankin tsawon lokaci.

Wannan yarjejeniya ta samu ne a yayin wani zama na musamman da aka gudanar, inda aka cimma matsaya cewa ƴan bindigar za su daina kai hare-hare ko cutar da al’umma, amma za su rika shigowa gari don gudanar da rayuwar yau da kullum cikin lumana.

Wannan mataki ya zo ne bayan dogon lokaci na tashin hankali da kashe-kashe da garkuwa da mutane da aka sha fama da su a yankin, wanda hakan ya tilasta wasu al’umma barin muhallansu.

Yayin da wasu ke kallon wannan mataki a matsayin nasara da ci gaba wajen dawo da zaman lafiya, wasu na nuna damuwa kan amincewa da ’yan bindiga su shiga gari ba tare da an hukunta su ba.

Ana sa ran hukumomi za su ci gaba da sa ido kan yarjejeniyar tare da daukar matakin da ya dace don tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.

Me zaku ce kan wannan sulhu?

Kana son samun sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa yanzu daka ka bari a wuce ka.

Irene Papas Jarumar da tafito a matsayin Hindu matar Abu Sufyan wacce ta sa aka kashe Sayyidina Hamza (AS), a film din (...
10/09/2025

Irene Papas Jarumar da tafito a matsayin Hindu matar Abu Sufyan wacce ta sa aka kashe Sayyidina Hamza (AS), a film din (The Message) na tarihin Annabi muhammad (SAW). A hoton na sama lokacin da aka dauki film din ne a shekarar 1976, hoto na kasa hotonta ne a shekarar 2022.

Irene Papas ko Irene Pappas yar kasar Girka ce (Greece) an haife ta a ranar 3 ga watan Satumba 1929 ta mutu a ranar 14 ga watan Satumba 2022 ), yar wasan kwaikwayo ce kuma mawaƙiya ta Girka wacce ta zama tauraruwa a cikin fina-finai sama da 70 a cikin sana'ar da ta shafe sama da shekaru 50 tanayi.

Ta sami karbuwa a duniya ta hanyar shahararrun fina-finan da s**a sami lambar yabo k**ar The Guns of Navarone (1961), Zorba the Greek (1964) and Z (1969). Ta kasance jaruma mai ƙarfi a cikin fina-finai da s**a haɗa da Trojan Women (1971) da Iphigenia (1977). Ta taka rawa a film din Antigone (1961) da Electra (1962). Ta fito a cikin film din tarihin Annabi muhammad (SAW) maisuna the (message) 1976 ta taka rawa a matsayin Hindu.

-Muhammad Cisse

Wasu cibiyoyin bincike na Pew Research da CIA World Factbook sun tabbatar da cewa Najeriya ce ƙasa ta biyar mafi yawan M...
10/09/2025

Wasu cibiyoyin bincike na Pew Research da CIA World Factbook sun tabbatar da cewa Najeriya ce ƙasa ta biyar mafi yawan Musulmai a duniya, inda ƙasar ke da Musulmai kimanin mutane miliyan 124.

Ƙididdigar ta waɗannan cibiyoyi ta nuna Musulunci na ci gaba da zama addini na biyu mafi girma a duniya, wanda yawan mabiyansa s**a kai kusan mutane biliyan 2.45 a shekarar 2023.

Ƙasar Indonesia ce ke kan gaba da Musulmai miliyan 242, sai kuma Pakistan mai miliyan 235. Sai kuma ƙasar India da miliyan 213 sa'annan kuma Bangladesh da miliyan 150. Daga nan kuma sai Najeriya wacce ta biyo su da mutane miliyan 124.

Tarihi ya nuna cewa Musulunci ya fara shigowa Najeriya tun daga ƙarni na 11 ta hanyoyin kasuwanci na ‘trans-Sahara’ daga Arewaci da kuma Yammacin Afirka. Sai kuma a ƙarni na 19, an kafa Daular Musulunci ta Sakkwato wacce ta ƙara jaddada addinin Musulunci musamman a yankin Arewacin ƙasar.

Me zaku ce Akan wannan maganar?
10/09/2025

Me zaku ce Akan wannan maganar?

Mataimakin gwamnan jahar Sokoto ya Sa an k**a wannan mutun akan wannan rubutun da ya Yi.Me zaku ce Akan wannan maganar?K...
09/09/2025

Mataimakin gwamnan jahar Sokoto ya Sa an k**a wannan mutun akan wannan rubutun da ya Yi.

Me zaku ce Akan wannan maganar?

Kuna son samun sahihan labarai kuyi Following dinArewa News Hausa yanzu kada ka Bari a wuce ku.

JARRABAWA DAGA ALLAHAnnoba 'yan ta'addan B0k0 Har@m sun kaddamar da harin ta'addanci a garin Darajamal dake karamar huku...
07/09/2025

JARRABAWA DAGA ALLAH

Annoba 'yan ta'addan B0k0 Har@m sun kaddamar da harin ta'addanci a garin Darajamal dake karamar hukumar Bama Jihar Borno

Sun ka$he mutane 63 fararen hula da Sojoji, wato sun kashe fararen hula 58 da Sojoji 5 a lokacin harin

Maigirma Gwamnan jihar Borno ya ziyarci garin da harin ya faru, ya yaba wa jaruntar da Sojoji s**a nuna

Mutanen garin Darajamal basu jima da komawa garinsu ba bayan shafe tsawon shekaru 10 suna gudun hijira, sun koma kenan sai wannan harin ya faru, Gwamna Zulum ya jajanta musu

Akwai wata rundina ta tsaro wanda Shugaban Kasa Tinubu ya kafa domin suyi aikin bada tsaro wa dazuka (Forest Guards), Gwamna Zulum yace da zaran sun kammala karban horo za'a kawosu garin domin su tallafawa Sojoji wajen tabbatar da tsaron garin Darajamal

Muna rokon Allah Ya karbi shahadarsu, Ya kawo mana karshen wannan masifa.

Kuna so samun sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa Yanzu kada ku Bari a wuce ku.

Gwamnatin Jihar Neja ta sanar da cewa ba za a sake yin wa’azi a fadin jihar ba sai da samun lasisi daga hukumar kula da ...
06/09/2025

Gwamnatin Jihar Neja ta sanar da cewa ba za a sake yin wa’azi a fadin jihar ba sai da samun lasisi daga hukumar kula da harkokin addini ta jihar.

Daraktan hukumar, Umar Farooq ne ya bayyana cewa masu wa’azi na da wa’adin watanni biyu kacal domin su je su cike fom, sannan su fuskanci kwamitin tantancewa kafin a basu damar yin wa’azi a hukumance.

Sai dai matakin ya jawo cece-kuce daga bangarori daban-daban, inda babban Limamin Jami’ar Fasaha ta Tarayya, Minna, Malam Bashir Yankuzo, ya ce wa’azi umarni ne daga Allah, ba abin da gwamnati za ta iya takaitawa ba. Ya ce sai dai idan wa’azin ya kunshi batanci ko kuma ya zama barazana ga tsaro, gwamnati ta iya shiga tsakani.

Shi ma sakataren kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Niger, Raphael Opawoye, ya ce basu samu sanarwa kan wannan hukunci ba tukunna.

Wani malamin addinin Musulunci, Ustaz Hassan, ya bayyana cewa dokar ya k**ata ta bi matakan majalisar dokokin jihar kafin a aiwatar da ita.

A nasa bangaren, wani marubuci kuma malamin addini daga Minna, Uthman Siraja, ya yi Allah-wadai da matakin, yana mai cewa hakan take hakkin dan kasa ne na yin ibada da addini. Ya bukaci gwamnati ta takaita hukunci ne kawai ga masu wa’azin da ke tada fitina a cikin al’umma..

Me zaku ce kan wannan maganar?

Kana son samun sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa yanzu kada ka Bari a wuce ka

Bayanan Da Ke Shigomu A Karamar Hukumar Mulkin Tambuwal  An K**a Barayi Masu Satar Mutane Wadannan Sune Barayinda Anka K...
06/09/2025

Bayanan Da Ke Shigomu A Karamar Hukumar Mulkin Tambuwal An K**a Barayi Masu Satar Mutane

Wadannan Sune Barayinda Anka K**a Mata Da Maza A Cikin Wani Kangon Gida Anan Cikin Garin Tambuwal, Yanzu Haka Dai Jami'an Tsaro Suna Kara Samun Nasarar K**a Miyagun Mutane Wadanda Ke Addabar Wannan Gari Tambuwal

Kawo Yanzu Dai Ana Cigaba Da Tattara Bayanai Tareda Gamsassun Hujjoji Akan Wadannan Barayin

Allah Yakara Yimana Kariya Akowane Mataki Kuma Ya Kara Bamu Lafiya Da Zaman Lafiya

~ Alhj Zaidu Tambuwal ~

MASHA ALLAHWannan tsoho dan shekara 85 sunansa Lazarus, dazu ya karbi addinin Musulunci, kuma ya zabi sunan AdamuDayan j...
05/09/2025

MASHA ALLAH

Wannan tsoho dan shekara 85 sunansa Lazarus, dazu ya karbi addinin Musulunci, kuma ya zabi sunan Adamu

Dayan jikansa ne wanda muke tare dashi anan Facebook, yanzun nan ya sanar dani Kakansa ya Musulunta, kuma yace mu roka masa Allah domin ya tabbata cikin Musulunci

Muna fatan Allah Ya tabbatar dashi a cikin Musulunci har zuwa karshen rayuwarsa da namu.

Kuna son samun sahihan labarai kuyi Following Arewa News Hausa yanzu kada ku Bari a wuce ku.

Fitaccen Mawakin Yabon Manzon Allah (S) Sulaiman Da'ira Ya Kara Da Cewa Shiyasa lokacin Da Marigayin Ya Rasu Ya Bayyana ...
04/09/2025

Fitaccen Mawakin Yabon Manzon Allah (S) Sulaiman Da'ira Ya Kara Da Cewa Shiyasa lokacin Da Marigayin Ya Rasu Ya Bayyana Farin Cikinsa A Zahiri A Shafukansa Na Yanar Gizo.

Ya Kara Da Cewa Saboda Duk Wanda Baya Farin Ciki Da Maulidin Manzon Allah (S) To Ba Musilmi Bane.

‎A Cikin Wani Sako Da Ya Wallafa Mawakin Yayi Ikirarin Cewa Har Yanzu Idan Ya Tina, Malamin Baya Duniya Yana Jin Dadi A Ransa.

Kana son samun sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa yanzu kada ka Bari a wuce ka.

Me Zaki ce kan wannan maganar?

Uwargidan shugaban Najeriya, Remi Tinubu ta ce maimakon a yi mata duk wata kyauta ko wani abun saboda a burge ta - albar...
04/09/2025

Uwargidan shugaban Najeriya, Remi Tinubu ta ce maimakon a yi mata duk wata kyauta ko wani abun saboda a burge ta - albarkacin zagayowar ranar haihuwarta, ta ba da asusun banki na musamman domin a zuba kudaden da za ta yi amfani da su wajen gina wani katafaren dakin karatu na kasa. A cewarta hakan zai taimaka wa cikar burinta na taimaka wa ilimi.

Shin nawa zaka iya saka mata?

Duk Nigeria babu mai degree ɗin da bashi da N5 million. ✅-Bincike.Cewar matashin kuma malamin crypto Adam Muhammad Mukht...
04/09/2025

Duk Nigeria babu mai degree ɗin da bashi da N5 million. ✅
-Bincike.

Cewar matashin kuma malamin crypto Adam Muhammad Mukhtar

Me zaku ce kan wannan maganar tashi?,

Kana son Samu sahihan labarai kuyi Following din Arewa News Hausa yanzu kada ka Bari a wuce ka

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share