Arewa News Hausa

Arewa News Hausa Don samun labarai daga arewacin Najeriya , dama duniya baki daya.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJU'UN😭😭😭Yanzu cikin Daren Nan, an jefo wani abin fashewa ko mizayil, ko Bam ko Nakiya a gar...
25/12/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJU'UN
😭😭😭

Yanzu cikin Daren Nan, an jefo wani abin fashewa ko mizayil, ko Bam ko Nakiya a garin jabo cikin karamar hukumar mulkin Tambuwal ta Jahar Sokoto.

Ba a San daga ina abin fashewar ya fito ba, sai dai ya an Samu sa'a Bai fado inda mutane su ke ba.

Idan ba a manta ba, shekaru masu yawa da s**a gabata an taba jefo wani daga wani wuri inda ya fado wani kauye a cikin jahar Sokoto,.

A halin yanzu dai za a fara bincike don sanin ko minene da gano inda aka jefo shi.

Idan ba a manta ba, America ta ce zata kawo hari a Najeriya shin ko harin ne ta fara kawo wa?

Miye hasashen Ku a wannan lamarin?

Yau Shekaru 16 da k**a dan Najeriya Umar Farouk Abdulmutallab da yunkurin tada bam a wani jirgin saman Amurka a shekarar...
25/12/2025

Yau Shekaru 16 da k**a dan Najeriya Umar Farouk Abdulmutallab da yunkurin tada bam a wani jirgin saman Amurka a shekarar 2009

A ranar Kirsimetin shekara ta 2009 ne aka k**a Abdulmutallab a kan hanyarsa ta zuwa birnin Detroit na kasar Amurka, inda kuma aka zarge shi da yunkurin tayar da bam a jirgin. Jami'an tsaron Amurka dai sun ce ya yi kokarin tayar da bom din ne wanda ya boye a wandonsa.

Hankulan jama'a dai sun karkata sosai ne a kan lamarin bayan kwanaki uku bayan kisan Anwar Al-Awlaqi na kungiyar Al-ka'ida da wani jirgin saman Amurka yayi a kasar Yemen. Jami'an hukumar leken asirin Amurkan dai sun sha nanata cewa Anwar Al-Awlaqi na da hannu a yunkurin tada bam din a jirgin saman Amurka a shekarar 2009.

Sun zargi Al-Awlaqi da tunzura Abdulmutallab bayan da s**a hadu a kasar Yemen. Umar Farouk Abdulmutallab ya amsa laifukan da aka tuhume shi da aikatawa guda takwas a watan Octoban shekarar 2011. Daga Bisani Wata kotu a Amurka ta yankewa Umar faruk Abdulmutallab hukuncin daurin rai-da-rai.

Umar Farouk Abdulmutallab, dan shekaru 25 a lokacin, ya amsa laifin yunkurin tarwatsa wani jirgin saman kasuwanci na Amurka, a wani lamari da ake ganin yunkurin kunar bakin wake ne.

Abdulmutallab ya kone sosai lokacin da bam din da ya boye a kamfansa ya kasa tashi gaba daya, k**ar yadda masu gabatar da kara s**a ce.

Akalla mutane 300 ne a cikin jirgin wanda ya taso daga Amsterdam na kasar Holland zuwa birnin Detroit na Amurka. Umar Faruk Mutallab wanda mahaifinsa Abdulmutallab, shahararren dan kasuwa ne kuma ma'aikacin banki, ya fuskanci tuhuma kan laifuka takwas da s**a hada da ta'addanci da kuma kisan gilla. Kungiyar Al-Qa*eda a yankin Larabawa da ke da hedkwata a kasar Yemen, ta ce ita ce ta dauki shirya harin.

Danginsa sun koka

Sai dai danginsa sun koka kan yadda mahukunta a Amurka s**a yi watsi da hujjojin da lauyoyin Abdulmutallab s**a gabatar.

"Muna kira ga sashen shari'a na Amurka da su sake yin nazari akan hukuncin daurin rai-da-ran da aka yankewa Umar Faruk M

25/12/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJU'UN
😭😭😭

Dubi yadda masallaci da mutane ke ci da wuta a harin Bam na masallaci Unguwar Gamboru cikin Birnin Maiduguri jiya ana tsaka da gabatarda sallar magariba.

Allah ya kawo muna karshen wannan bala'in
🙏🙏🙏

A ranar 25 ga watan Disamba a shekara ta 336 Miladiyya, cocin kirista a Roma ta fara yin bikin Kirsimeti.A lokacin Sarki...
25/12/2025

A ranar 25 ga watan Disamba a shekara ta 336 Miladiyya, cocin kirista a Roma ta fara yin bikin Kirsimeti.

A lokacin Sarkin Roma Constantine a ka fara yin bikin. Duk da a zahiri Romawa ne s**a ƙirƙiri bikin, amma har yanzu ba a sami sunan tak**aiman mutumin da aka tabbatar da shi ne ya fara yin bikin ba.

Asalin Kirsimeti

Kirsimeti ya samo asali ne daga al'adun Ar*na da na Romawa. Romawa, su na yin bukukuwa biyu a watan Disamba. Na farko shi ne bikin Saturnalia, wanda shi ne bikin makonni biyu na girmama Ubangijin aikin gona na Saturn. A ranar 25 ga Disamba, su na yi bikin haifuwar Mithra, ubangijin rana. Bukunkunan biyun sun kasance Masu ban sha'awa, da shaye-shaye.

Haka kuma a cikin watan Disamba, in da rana ba ta yin haske sosai saboda sanyi, a al'adun maguzawa (Pagan) suna kunna wuta da kyandir don kawar sa duhu. Romawa sun shigar da wannan al'ada cikin bukukuwan nasu.

Yayin da addinin Kiristanci ya yaɗu a turai, limaman Kirista ba za su iya hana al’adu da bukukuwan ar*na na al'ada ba, tun da ba wanda ya san ranar haihuwar Yesu, kuma ba rubuta ranar da aka haifeshi a cikin Bible ba, sai su ka mai da al’adar ar*na (Maguzawa) ta zama bikin ranar haihuwarsa.

Bikin ya bazu daga Roma zuwa wasu majami'u na Kirista, kuma yawancin Kiristoci su na fara bikin haihuwar Kristi a ranar 25 ga Disamba.

Allah ya tsayarda mu akan Gaskiya
🙏🙏🙏

Wani jami’in ɗan sanda mai muƙamin DSP, Isah Abdullahi, ya kashe kansa bayan an zarge shi da hannu wajen kai mak**ai ga ...
19/12/2025

Wani jami’in ɗan sanda mai muƙamin DSP, Isah Abdullahi, ya kashe kansa bayan an zarge shi da hannu wajen kai mak**ai ga ’yan ta’adda a jihar Neja.

Marigayin dai na aiki ne a sashen rundunar rundunar ’yan sandan ko-ta-kwana ta 12 da ke Minna, babban birnin jihar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda a jihar, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an k**a ɗan sandan ne tun a ranar 15 ga watan Disamba na shekarar 2025 bisa zargin safarar mak**ai ba bisa ka’ida ba.

A cewarsa, yayin bincike da kuma kirga mak**ai da aka gudanar ranar 16 ga watan Disamba na shekarar 2025 domin gano bindigogi da harsasai da s**a bace, Isah ya harbi kansa a ka da bindigar pistol da ya dauka daga ofis, inda ya mutu nan take.

Abiodun ya kara da cewa an k**a jami’an da aka tura domin gudanar da bincike da kirga mak**an saboda sakaci, saboda sun bari wanda ake zargi ya mutu ba tare da an kammala bincike ba.

Ya ce, “Ranar 16 ga Disamba, 2025 da misalin karfe 2:30 na rana, DSP Abdullahi Isah wanda aka k**a tun ranar 15 ga watan Disamba bisa zargin safarar mak**ai ba bisa ka’ida ba, an kai shi ofis dinsa domin kirga mak**ai na yau da kullum.

“Abin takaici, yayin da ake cikin aikin kirga mak**ai, sai jami’in ya dauki pistol daga ofis ya harbi kansa a kai, inda ya mutu nan take.

“A halin yanzu, an k**a ‘yan sanda da aka tura tare da shi domin aikin kirgawa da bincike saboda sakaci a bakin aiki, saboda sun bari lamarin ya faru. Bincike na ci gaba,” in ji Abiodun.

Ana zargin cewa Isah, wanda shi ne ke kula da sashen mak**ai, ya rika kai mak**an da harsasai ga ’yan ta’adda ta hannun wani abokin aikinsa a jihar.

Me zaku ce akan wannan al'amarin?

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Koli ta soke afuwar da Gwamnatin Tarayya ta yi wa Maryam Sanda, ta sake tabbatar mata da hukuncin ki...
12/12/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Koli ta soke afuwar da Gwamnatin Tarayya ta yi wa Maryam Sanda, ta sake tabbatar mata da hukuncin kisa.

Kotun ta yanke wannan hukunci ne yau, inda ta ce afuwar ba ta da tasiri kan hukuncin da wata kotu ta gaba ta yanke tun da farko.

Maryam Sanda dai an same ta da laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, a shekarar 2017.

INA MASOYANA ADUK INDA SU KE, MUSAMMAN NA WANNAN KAFAR TA FACEBOOK, YAU INA NEMAN ALFARMAR KU.🙏🙏🙏NA FITO CIKIN YAN TAKAR...
11/12/2025

INA MASOYANA ADUK INDA SU KE, MUSAMMAN NA WANNAN KAFAR TA FACEBOOK, YAU INA NEMAN ALFARMAR KU.
🙏🙏🙏

NA FITO CIKIN YAN TAKARAR MR.&MISS NORTHERN NIGERIA, A MATSAYIN MR. FULANI.

YADDA ZA KA ZABENI!!!
Zaka tura kudi naira N100 zuwa ga wannan account number din, sannan kayi screenshot din receipt ka tura zuwa ga lambar da ke jikin hoton ta wats app.

Sai ka rubuta sunana k**ar haka
ABDUL-AZIZ BELLO ACHIDA
Mr. Hausa Fulani.
Vote Contestant Number 21

Kuma kana iya zabena ko sau nawa kake bukata Amman kowane zabe zaka tura N100.

Idan Kuma baka iya turawa kana iya turomin da kudin sai in zaba da kaina.

Sai Kun zabeni zan Samu wannan nasarar.

Ina son ku nuna min kauna, don Allah

Idan Kuma baka fahimceni ba, kana iya tambaya ta DM ko Kuma ta wannan lambar tawa ta wats app.
08031577538

Nagode
🙏🙏🙏

Ya rasu a hannun 'yan bindiga bayan sun karbi miliyan 15 kudin fansaBayan 'yan bindiga sunyi garkuwa dashi kimanin wata ...
11/12/2025

Ya rasu a hannun 'yan bindiga bayan sun karbi miliyan 15 kudin fansa

Bayan 'yan bindiga sunyi garkuwa dashi kimanin wata 5 sun ce sai an basu 30 miliyan su sako shi, daga baya aka nemi ragi s**a yarda akawo miliyan 15, bayan an kai miliyan 15 su ka kuma zo dashi a mashin yana kallo s**a karbi 15 miliyan, bayan sun karbi 15 miliyan din, su ka ce baza su sake shi ba har sai an ciko miliyan 15 sun zama miliyan 30 sannan su sake shi.

Daga karshe yau mun samu labarin Allah ya yi masa cikawa 😭 .

Hon Mu'azu Gwashi Allah ya kai rahama a kabarin ka

Kuna son samun sahihan labarai kuyi Following dinArewa News Hausa yanzu kada ku Bari a wuce ku

Bello Turji yayi Barazanar Kashe Kallamu Buzu! (Yaron Turji mai wakiltar Gabascin Isa da Sabon Birni). Wanda shine ya Ja...
09/12/2025

Bello Turji yayi Barazanar Kashe Kallamu Buzu! (Yaron Turji mai wakiltar Gabascin Isa da Sabon Birni). Wanda shine ya Jagoranci Harin Ta'addancin da s**a kai Fadamar Kurawa da Tarah yau 8-12-2025 misalin 6am. ba suyi nasara ba.

Ga dukkan Alamu Jami'an Tsaro sun kashe yaran da Turji keji dasu a Farmakin Fadamar Kurawa da Tarah. Ko kuma Kallamu ya Jagoranci wannan Ta'addanci ne bada izinin mai gidan shi Turji ba.

Bayan Ya sha dakyar Daga hannun Jami'an Tsaro!
Mutanen yankin da yake iko sunga Kallamu Buzu Yana waya da Bello Turji, bayan kammala wayar ne akaji yana sambatu yana cewa Turji ya wulakanta shi har yace sai ya kashe shi.

Muna Rokon Allah ya hada su fada da junan su, su kashe junan SU!.

Cikin awa biyu bayan umarnin da Tinubu ya bayar sojojin saman Nigeria dana kasa sun shiga kasar Benin sun ragargaji sojo...
08/12/2025

Cikin awa biyu bayan umarnin da Tinubu ya bayar sojojin saman Nigeria dana kasa sun shiga kasar Benin sun ragargaji sojoji masu yin juyin mulki.

Inda cikin kwarewa da saiti ba kuskure jirgin yakin Nigeria ya dinga
zuba boma-bomai kan ayarin motocin da suke dauke da sojoji masu juyin mulki inda sojojin kasan mu kuma su kayi musu luguden wuta.

Tuni aka kori sojoji masu yin juyin mulki.

Muna rokon wannan nuna kwarewar da karfin a yishi akan ƴan ta'addan jeji da suke kashe talakawa a yankin Arewa maso yamma.

Allah yasa mudace.

Arewa News Hausa

TAMBAYA?Misali shin idan Ahmad Aliyu ya gama wa'adin shekarunsa na Zama gwamna, Yana son wucewa Sanata shin Yaya zai yi ...
06/12/2025

TAMBAYA?

Misali shin idan Ahmad Aliyu ya gama wa'adin shekarunsa na Zama gwamna, Yana son wucewa Sanata shin Yaya zai yi da uban gidanshi Alu Wamakko?

Shin Alu zai hankura ya zauna Gida Ahmad ya tafi Sanata, ko Kuma Amadu zai yi hankuri Alu yaci gaba da mulki, ko Kuma baranbaran za a yi?

Inji Abdulaziz Bello

LABARI DA DUMIN SA!!!Badaru Abubakar ya sauka daga mukaminsa na Ministan tsaro....
01/12/2025

LABARI DA DUMIN SA!!!

Badaru Abubakar ya sauka daga mukaminsa na Ministan tsaro....

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share