Arewa News Hausa

Arewa News Hausa Don samun labarai daga arewacin Najeriya , dama duniya baki daya.

Wata Budurwa ɗalibar makarantar sakandire ta karɓi addinin Musulunci kuma ta canza suna daga Elizabeth zuwa Fatima, sai ...
22/07/2025

Wata Budurwa ɗalibar makarantar sakandire ta karɓi addinin Musulunci kuma ta canza suna daga Elizabeth zuwa Fatima, sai dai tace ba zata koma gidansu ba saboda iyayenta zasu iya yanka ta, don haka a halin yanzu ana ƙoƙarin ganin an samu wanda zai iya riƙe ta ya koya mata addinin Musulunci.

Ana roƙon ƴan'uwa musulmi don Allah duk wanda yaga wannan labarin ya taimaka wajen tura shi zuwa sauran groups ko Allah zai sa ya kai inda ya dace a taimaka mata

Ƙarin bayani Arewa News Hausa

Gwamnan jahar Katsina Dikko Umar Radda ya Yi hadarin mota kan hanyarshi ta zuwa Daura.Ya Yi taho mu gama da wata motar s...
21/07/2025

Gwamnan jahar Katsina Dikko Umar Radda ya Yi hadarin mota kan hanyarshi ta zuwa Daura.

Ya Yi taho mu gama da wata motar safa kirar Golf jiya, injin din motar Golf sai da ya fita.

Tare da Shi akwai shugaban ma'aikata da wani Dan majalisar tarayya.

An garzaya dasu asibitin Daura, in da aka basu kulawar gaggawa kafin daga baya aka dauke su zuwa wata asibiti ta daban.

To sai dai wadanda ke cikin Golf din ba a bayyana halinda su ke ciki ba.

Allah ya kiyaye gaba ya Basu lafiya.

TIRKASHI: ’Yan sanda sun tabbatar da mutuwar malamin Jami'ar Prince Abubakar Audu da ke jihar Kogi, yana lalata da wata ...
19/07/2025

TIRKASHI: ’Yan sanda sun tabbatar da mutuwar malamin Jami'ar Prince Abubakar Audu da ke jihar Kogi, yana lalata da wata dalibarsa a dakin Hotel bayan da yasha maganin karfin Maza yana zagaye na biyu. Allah ya kyauta.

Kullum anata kara daukan darasi ga masu shan maganin karfin Maza.

Me zaku ce akan wannan batun?

DA DUMI-DUMI: Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kirkiro sabbin jihohi 12! A wani gagarumin yunkuri na zurfafa tsa...
18/07/2025

DA DUMI-DUMI: Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kirkiro sabbin jihohi 12!

A wani gagarumin yunkuri na zurfafa tsarin tarayya da kuma kusantar da mulki ga jama'a, majalisar dattawan Najeriya ta yi karatu na karshe na samar da sabbin jihohi goma sha biyu a shiyyoyi shida na siyasar kasar.

Wannan ci gaba mai cike da tarihi ya biyo bayan shawarwarin da kwamitin majalisar dattijai kan samar da Jihohi ya yi a fadin kasar, wanda ke nuna wani gagarumin mataki na samun daidaito, hadewa, da daidaiton ci gaba.

1. Kudu maso Yamma
Jihar Ijebu – Daga Jihar Ogun
Jihar Ibadan – Daga Jihar Oyo

2. Kudu maso Gabas
Jihar Anim – Daga jihohin Anambra da Imo
Jihar Adada – Daga Jihar Enugu

3. KUDU KUDU
Jihar Toru-Ibe - Daga sassan Ondo, Edo da Delta
Jihar Obolo – Daga Jihar Akwa Ibom

4. AREWA GABAS.
Jihar Savanna – Daga Jihar Borno
Jihar Amana – Daga Jihar Adamawa

5. AREWA MASO YAMMA
Jihar Tiga – Daga Jihar Kano
Gurara State – Daga Kudancin Kaduna

6. AREWA TA TSAKIYA
Jihar Okura – Daga Jihar Kogi
Jihar Apa – Daga Jihar Benue

Wannan shawarar ta nuna kudurin Majalisar Dattawa na tabbatar da gaskiya, hadin kai, da ci gaban kasa.
Amsa ce da aka dade ana jira don tada zaune tsaye, don samar da ingantacciyar wakilci, ingantaccen shugabanci, da hanzarta ci gaba a matakin farko.

'YAR JAHAR SOKOTO DA ZATA WAKILCI YANKIN AREWA A GASAR SARAUNIYAR KYAU TA NAJERIYA :Matashiya Saudat Aliyu Kware daga ka...
17/07/2025

'YAR JAHAR SOKOTO DA ZATA WAKILCI YANKIN AREWA A GASAR SARAUNIYAR KYAU TA NAJERIYA :

Matashiya Saudat Aliyu Kware daga karamar hukumar Kware dake jahar Sokoto, Ita ce aka zaba da zata wakilci yankin Jihohin Arewa Domin shiga gasar Sarauniyar kyau ta Najeriya wato (Miss One Nigeria 2025)

Wace fata kuke Gareta?

INA JIN HAUSHIN MASU DORA HOTON YUSUF BUHARI SUNA TAUSAYA MISHI.Ina Jin haushin mutane wadanda ke dora hoton wannan yaro...
17/07/2025

INA JIN HAUSHIN MASU DORA HOTON YUSUF BUHARI SUNA TAUSAYA MISHI.

Ina Jin haushin mutane wadanda ke dora hoton wannan yaron Yusuf Buhari suna tausaya mishi wai Don mahaifinshi ya mutu.

1 Da farko kafin mutuwar mahaifinshi, ya kammala karatunshi na Degree a Kasar Turai Yana aiki, ko yanzu albashin sa ya Isa ya dauki nauyin kanshi har ta taimakawa wasu, kunga kenan ya wuce maraya.

2 Mahaifinshi ya mutu ya bar musu dukiya Mai tarin yawa wadda Basu Isa su cinyeta ba har karshen rayuwarsu, kwata-kwata Yusuf bai San talauci ba.

3 Kafin mutuwar mahaifinshi a lokacin mulkinsu an kiyasta Yusuf ya fi duk wani matashi kudi a Najeriya.

4 Cin su, da Shan su, da karatunsu da kulawa dasu, duk Yana hannun gwamnati.

5 Yana da alfarma a Kasar Nan, Babu inda zai je ya nemi alfarma ba a yi mishi ba, saboda manyan Kasar Nan suna tare da Shi.

KU LURA DA WANNAN!!!
Allah kadai yasan iyakar marayu kananan yara, wadanda iyayensu su ka mutu, Basu da Mai kula da su, su wuni da yunwa su kwana da ita, Babu inda zasu Samu abinci, shin wa ya taba daukar hotonsu ya Dora a social media Yana tausaya musu?

Akwai dimbin marayu, wadanda yan ta'adda su ka kashe iyayensu, suna zaune sansanin yan gudun hijra Babu Mai kula da su.

Matasa nawa su ka kammala karatu Babu aikin yi, Babu jarin kasuwanci, Babu alfarma, Kuma Babu Wanda ya San su?, Kuma Babu Wanda ya tausaya musu.

Shin Kai Mai daukar hoton Yusuf Buhari ka Dora kana tausaya mishi, da Kai da Shi wa yafi gata a Kasar Nan?

Shin mu da iyayenmu su ka mutu, su ka barmu, Babu kudi, Babu gata, Babu alfarma me yasa ba a daukar hotonmu a Dora Ana tausaya muna, ko namu maraicin ba maraici ba ne, maraicin Yusuf Shi ne maraici?

KARSHE!!!
Idan aka kwatanta maraicin Yusuf Buhari da namu maraicin, da yanayin maraicin Yusuf da namu shin a cikinmu waye maraya Kuma wa yakamata a tausayawa.?

Mai karatu kayi alkalanci, sannan kayi tsokaci a comment section.

Inji Abdul-Azeez Bello Achida

Jaridar Arewa News Hausa muna Taya daya daga cikin ma'aikatanmu wato Abdul-Azeez Bello Achida murnar zagayowar ranar hai...
16/07/2025

Jaridar Arewa News Hausa muna Taya daya daga cikin ma'aikatanmu wato
Abdul-Azeez Bello Achida murnar zagayowar ranar haihuwarshi.

Allah ya karo lafiya da nisan kwana masu albarka.

A ganinku shekarunsa nawa?

Happy birthday to you Sir
❤️💖💕

Yadda Jadawalin Shirye-Shiryen Jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari Zai Kasance1-An ayyana ranar Talata a mat...
15/07/2025

Yadda Jadawalin Shirye-Shiryen Jana'izar Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari Zai Kasance

1-An ayyana ranar Talata a matsayin ranar hutu a Najeriya don makokin Marigayin

2-An kafa Kwamitin Manyan Jami'an gwamnati don tsara jana'izar girmamawa ga tsohon shugaba Buhari wanda sakataren gwamnatin tarayya Sen. George Akume ya jagoranta.

3-An dage taron Majalisar Zartarwa ta Kasa daga gobe zuwa juma'a don zaman makoki

4 An umarci mambobi 25 na Majalisar Zartarwar da su wuce Daura don halartar jana'izar zaman makoki na kwanaki uku

4-An ayyana kwanaki 7 na zaman makoki a ilahirin Najeriya tare da yin ƙasa-ƙasa da tutar kasar

5- Babbar tawaga karkashin jagorancin mataimakin shugaban kasa na can na kammala shirye-shiryen kawo gawar da iyalan mamacin gida

6- Za a yi takaitaccen faretin Sojoji a filin jirgin sama na jahar Katsina don tarbar gawar.

7- Za a yi Sallar Jana'iza da rufe gawar a Daura.

8 An bude shafin karbar ta'aziyya a dukkan ma'aikatun gwamnatin tarayya, da na hukumomi, da ilahirin ofisoshin jakadanci na Najeriya da ke kasashen waje.

9- Ana sa ran isowar gawar Katsina da karfe 12 na rana ranar Talata.

10- Za a yi Jana’iza a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025.

11- Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai karbi gawar tsohon shugaban kasa a Katsina tare da manyan baƙi

12- An aiyana gidan tsohon shugaban kasar na Daura amatsayin inda za'a binne gawarsa

Muna addu'a Allah ya jikansa da rahama 🤲

DAGA KARAMAR HUKUMAR MULKIN ILLELA. Inda aka gabatarda janazar  mutane Uku da Bandits s**a yiwa kisan gilla  har lahira ...
14/07/2025

DAGA KARAMAR HUKUMAR MULKIN ILLELA.

Inda aka gabatarda janazar mutane Uku da Bandits s**a yiwa kisan gilla har lahira a kauyen Tarke dake Mazabar Damba a karamar hukumar Illela ta jahar Sokoto a safiyar yau Litinin.😭

Rayuwa kenan, dame za ka tunawa da Margayi Muhammadu Buhari?
13/07/2025

Rayuwa kenan, dame za ka tunawa da Margayi Muhammadu Buhari?

DA DUMI DUMI: Ranar Zaɓe idan Kunje Bakin Akwatin zaɓe kada ku tsaya Tunani ko kuma Shakku kawai ku zaɓi jam'iyyar Apc N...
12/07/2025

DA DUMI DUMI: Ranar Zaɓe idan Kunje Bakin Akwatin zaɓe kada ku tsaya Tunani ko kuma Shakku kawai ku zaɓi jam'iyyar Apc Na tabbata Ba Zakuyi Nadama Ba, Bola Tinubu ga Nigeriya

Me Zaku ce?

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Arewa News Hausa 👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

12/07/2025

Tudun Wada Achida
Tudun Wada Sokoto
Tudun Wada Gombe.
Shin akwai wasu garuruwa masu unguwannin Tudun Wada?

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share