19/12/2025
Wani jami’in ɗan sanda mai muƙamin DSP, Isah Abdullahi, ya kashe kansa bayan an zarge shi da hannu wajen kai mak**ai ga ’yan ta’adda a jihar Neja.
Marigayin dai na aiki ne a sashen rundunar rundunar ’yan sandan ko-ta-kwana ta 12 da ke Minna, babban birnin jihar.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sanda a jihar, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an k**a ɗan sandan ne tun a ranar 15 ga watan Disamba na shekarar 2025 bisa zargin safarar mak**ai ba bisa ka’ida ba.
A cewarsa, yayin bincike da kuma kirga mak**ai da aka gudanar ranar 16 ga watan Disamba na shekarar 2025 domin gano bindigogi da harsasai da s**a bace, Isah ya harbi kansa a ka da bindigar pistol da ya dauka daga ofis, inda ya mutu nan take.
Abiodun ya kara da cewa an k**a jami’an da aka tura domin gudanar da bincike da kirga mak**an saboda sakaci, saboda sun bari wanda ake zargi ya mutu ba tare da an kammala bincike ba.
Ya ce, “Ranar 16 ga Disamba, 2025 da misalin karfe 2:30 na rana, DSP Abdullahi Isah wanda aka k**a tun ranar 15 ga watan Disamba bisa zargin safarar mak**ai ba bisa ka’ida ba, an kai shi ofis dinsa domin kirga mak**ai na yau da kullum.
“Abin takaici, yayin da ake cikin aikin kirga mak**ai, sai jami’in ya dauki pistol daga ofis ya harbi kansa a kai, inda ya mutu nan take.
“A halin yanzu, an k**a ‘yan sanda da aka tura tare da shi domin aikin kirgawa da bincike saboda sakaci a bakin aiki, saboda sun bari lamarin ya faru. Bincike na ci gaba,” in ji Abiodun.
Ana zargin cewa Isah, wanda shi ne ke kula da sashen mak**ai, ya rika kai mak**an da harsasai ga ’yan ta’adda ta hannun wani abokin aikinsa a jihar.
Me zaku ce akan wannan al'amarin?